Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da cewa da gaske ne ta suma ba
Na juya ina kallonsa a lokacin da ya kama hanyar fita kenan abujan ya nufa saboda an ce masa yarinya ta suma. Aikuwa dai ga dukkanin alamu mutumin nan so yake yi ya yi mutuwar tsaye.
Kwana uku da tafiyarsa bai kira ni a waya ba ni ma ban kira shi ba ana hudun ne ya zo tare da yarinyar da akwatin kayanta. Ta ma'kalkale ni tana dariya da shafa fuskata duk garin jikin nan nata sai da ya rairaye ta yi d'an wuya. Ko da na gaishe shi sama-sama ya amsa ya bar wajen. Na ri'ke hannunta muka haura saman a tare yana wanka da ya fito ya gan ni a zaune ya sake d'aure fuska ya d'auki basiline ya zauna can nesa da ni yana shafawa a jikinsa. Yarinyar ta fara zagaye d'akin tana neman abin wasa.
Ni abinda yake yi ma dariya yake ba ni abinda ba zai iya ba. Duk tsananin gabar sa ban san me ya sanya yanzu ta daina tasiri a kan kansa ba domin daga ya fara ma yake bari kwana daya biyu zuwa uku ya fara neman hanyar da za a shirya.
Na ce." Ina 'yan biyu na ga Minal ita kadai ai ba haka muka yi da kai ba."
Ya ce." Tunda kin haife ni Amina ai ya zame mini dole na bi umarininki kada na lalace ko?"
Na danne dariyar da nake ji tana yun'kuro mini na ce." Ban haife ka ba amma abinda yake a hakkina nake tambayarka ni 'yan biyu na ce ka kawo mini."
Ya furta." Wannan din da na kawo miki sai ki yi cilli da ita tunda ai ba gidan ubanta ba ne."
Na ce." Mu yi magana wadda take daidai kuma ta fahimta mu kuma cire son zuciya. Ban ce ba zan ri'ke yarinyar nan ba tunda har ka kawo mini ita amma ba ni son tashin hankali daga kowane 'bangare. Idan har da sanin uwarta ka daukota ta amince da hakan babu damuwa a wajena. Amma ya zama dole a kawo mini yarana."
Ya ce." Wannan ne kuma ba ki isa ba. Ba za ki dinga gindaya mini sharadai ba. Hauwa ta da ba ta yanzu ba ce domin duk yadda ki ke tunanin tana 'kin ki na tabbatar da cewa ba zata zalinci yara ba, kuma sanin da ki ka yi mata ta canza sosai ta kuma kar'bi dukkanin kuskuranta."
Na ce." Babu ruwana wannan matsalarka ce kai da ita. Ni dai Hauwa ko za ta had'iyi al'kur'ani don tsoron Allah da gaskiya ba zan yarda da ita ba domin ita din mutuniyar banza ce mara tsoron Allah."
Ya ce." Cin fuska ne ki dinga kiranta da irin wannan kalaman Amina kwanakin baya kin mare ta a fuska duka ta yi hakuri saboda tana jin maganata."
Na ce." Me yasa baka rama mata ba a lokacin ba, ai da ka sani kawai ka d'aukar mata fansa kuma yanzu ma ai bata 'baci ba ga ni zaune kusa dakai ka rama mata kawai......
'
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700.....0542382124. BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*148*
Share ni ya yi ya tafi ya je ya d'auko rigarsa jallabiya mai yankakken hannu ya sanya a jikinsa ya fesa turare sosai sannan ya sauka kasa ya bar ni da yarinyar a d'akin. Na tashi tare da kama hannunta muka sauka baya falon k'asa da alama fita ya yi.
Kai tsaye kicin na nufa na d'ora sanwar dare gefe guda kuma kasan marata na d'an yi mini ciwo kadan da cijewar kafa gobe alhamis asibiti zan yi sammakon zuwa domin duba lafiyata da abinda yake cikina a auna abinda yake cikin domin tabbatar da lafiya yake kwance.
Duk inda na ajiye kafata nan yarinyar take ajiye tata tana yi mini hirar 'yan uwan nata biyu can kasan zuciyata kewarsu ta ishe ni haka kawai yanzu nake tsananin jininsu a cikin raina ba kuma na tsammanin zan iya bar wa Hauwa su wallahi sai dai duk rigimar da za mu yi muyi ta a shirye nake gabad'aya na gama dawowa daga rakiyar Hauwa.
Bayan sallah Isha'i ya shigo muna d'aki ni da Minal na bata wayata tana game ya buk'aci abinci ya kama hanya ya fita da jin haushi domin ya'ki sakin fuskarsa tun da ya dawo.
Na shirya masa abinda na dafa na hau saman da tire din a hannuna cikin jan kafa daya ta ri'ke mini cikin ya yi mini nauyi ainun.
Na same shi yana waya na ajiye tiran kusa da shi na juya zan fita ya dakatar da ni.
Na juyo ina kallonsa fuskata a had'e sai kuma ya ce" Je ki kawai."
Na kada kaina ba tare da nace komai ba na sauka yarinyar tana ta game cikin nishadi cikin zuciyata na ce ikon Allah kenan ban haifi yarinyar nan ba Allah Ya jarabbeta da kaunata haka zalika ni ma ina sonta sosai domin ba ta d'auko kamanin uwarta ba fuskar ta ubanta ce garin jikin ni kuma na washeta tunda uwar da uban duka sirira ne.
Ya kwana can shi kadai na kwana da Minal da safe na yi mata wanka na shirya ni ma na kintsa. Ruwan shayi kawai na iya dafawa na soya 'kawai zalla na had'a mata tea din ta karya.
Ina yin nawa karin kummalon ne ya shigo ya shirya shi ma da alama fita zai yi da wuri a haka har yanzu babu nutsuwa da cikakkiyar walwala a tare dashi tana ganinsa ta fara fad'in." Baba ka ga." Tana nuna masa wayata dake ajiye game din dana kamo mata tana yi ban kashe ba. Tana ta maimaita maganar "Baba ka gani."
Ya karaso ciki sosai ya kar'bi wayar yana dubawa ya d'an saki fuska yana cewa." Na gani Minal mu gaisa ko?''
Ta daga kanta sai ya mika hannu ya kamo nata yana fad'in." Haka ake cewa ina kwana."
Ta sake daga kanta tana fad'in." Baba ina kwana."
Ya amsa yana dariya wadda ban ga ya yi ta ba tunda ya shigo jiya.
Ya d'an tsira mini ido na wani lokaci kafin ya ce." Ba za ki gaishe ni ba?"
Na ajiye kofin shayin da yake hannuna na ce." Ina kwana?"
Ya amsa a tak'aice tare da tankwashe kafa a gabana. Sai na yi kasa da kaina ban sake ce masa komai.
Ya furta." Had'a mini tea din ma nasha.
Ya janyo flat din dake gabana da soyayyan kwai fefe uku manya na d'auki kofi na tsiyaya masa ruwan shayin nasa madara kad'an da milo domin wasu lukutan ma ya fi shan tsura shima amma dai shi yana shan madarar amma kadan ba kamar Baban Saude da gabad'aya madarar ce ma ba ya sha.
Yana kurbar ruwan shayin yana kallona kamar wadda ya samu tibi can na ji yana fad'in." Naga duk kin tasa kin kara girma ina fatan lafiya." Ya fad'a yana duba yatsun hannuna da suma suka d'an yi kumburi duk irin na masu ciki.
Na ce." Lafiya lau in sha Allahu amma dai yanzu shirin da na yi asibiti zan je ina so su yi mini awo sannan kafata na ciwo amma dai hakan ba matsala ba ne in sha Allahu idan ciki ya yi nauyi ya shiga watanni shida zuwa bakwai akan ci karo da irin wad'annan matsaltsalun."
Ya gyad'a kansa yana cigaba da yi mini kallon kurulla kafin ya ajiye kofin hannunsa ya furta." Za mu je na kai ki asibitin da kaina idan ya so zan yi magana da magaji direban Hajja idan kin kammala sai ya zo ya d'auke ki ku je da Minal ku gaisa." A tak'aice na ce to shikkenan.
A mota yake gaya mini daga asibitin bunkure zai nufa domin dai gobe ne za a daura aure bayan an yi sallar Juma'a akwai zai d'auko yarinyar still su dawo asibitin a tare domin akwai likitan da ya yi magana da shi a sirrin ce zai yi mata (genotype) tunda shi dama tuntuni ya san matsayin jininsa.
Na ce." Wane irin a sirrin ce sai kace munafurci me yasa baka so a san za ka yi aure ka bugo kati kana d'ora shi a status dinka menene abin boyewa.
Ya furta." Ni yarinyar ce ba ni so a gani."
Na ce." Kasan abin kunya ne kenan ko?"
Ya yi shiru bai ce komai ba can kuma ya furta." Babu wata kunya fa akan yin koyi da annabin rahama ni dai a yadda nake garau Amina ba na shakkar zamantakewata da mu'amula ta aure da yarinya irin Hajara saboda nasan kaina zan kuma yi mata iyakacin bakin kokarina. Kawai dai har yanzu abin ne bai kwanta mini a rai ba. Maganar buga kati ai ba wani abu ba ne na bugawa bazawara ma balle budurwa."
Na yi shiru ina auna maganarsa. Ni dai lokacin daurin aure na babu wani kati da ya buga tunda abin duka ya zo mana a bazata sai da aka d'aura tukkuna gidajen jaridu suka sani. Yana nufin Hajiya Maryam ne.
Sai na share ban tanka masa ba duk 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~ kuwa da cewa na ji zafin maganar da yake akan yarinya ya nuna budurwa ta fi bazawara kenan ita ya kamata ace an bugawa kati.
Duk tsayin rayuwar da muke yi ban ta'ba ganinsa yana tu'ka mota ba sai yau duk da yake ya ce tafiyar sirri ce har da sanya takunkumi da rufe hancinsa da bakinsa da (fecemark)
Haka muka isa asibitin Malam Aminu Kano yana ta yi mini zantukan marasa dadin saurare tunda duka akan auran da zai daura gobe ne ni Ina nake da wata shawara da zan bashi a ce sai da asiki ya zo gaban goshi tukkuna zai yi gwajin jinin ya so wata matsala ta faru idan ba su samu haduwar jini ba fadi yake yi akwai matsala domin dai shi ba zai iya gayawa malam 'Daha ya fasa ba saboda wannan dalili zai bari a d'aura auran amma fa zai bar yarinyar a gidansu kafin ya yankewa kansa hukunci.
Jin haka ya sanya jikina yin sanyi tabbas wannan son rai ne tsagowaronsa babu yadda za a yi na yarda ya lalatawa yarinya kuruciya wane irin wulakanci ne wannan gwara duk yadda za a yi a yau din idan results bai daidaita ba a zauna zama na mussaman da muhukunta domin su fayyacewa Malam D'aha illar hakan.
Yana had'a ni da likitan da zai duba ni ya yi mini sallama a ka yi sa'a cikin asibitin in banda likitan babu wanda ya fahimci shine tunda motar da muke ciki babu tambarinsa kamar sauran motocinsa na zurga-zurga wanda suke tabbatar da zuwansa waje idan an gan su a ajiye.
Scanning ya ba ni naje na yi da result ya fito ya gama dubawa ya dinga washe baki yana fad'in." Hajiya wannan albishirin ni ya kamata na yi wa Yallabai please a yi mini wannan." Na yi murmushi ina fad'in." To shikkenan duk da bai gaya
mini abinda sakamako ya nuna ba a jikina na ji cewa tagwaye zan sake haifa domin yanayin wannan cikin yanayin cikinsu Hassana sai dai wannan din da d'an bambanci kad'an.
Na ji yana fad'in." Yara maza ne biyu yadda sakamako ya nuna dukkaninsu cikin koshin lafiya sun kuma juya yadda ake so nan da sati hud'u sai ki sake zuwa a yi miki awo domin mu sake tabbatar da yanayin kwanciyarsu.
Cikin zuciyata na kira sunan Allah tare da yin godiya a gare shi.
Na ce." In sha Allahu Dr na gade sosai.
Muka fito dare da Minal da takardar result din a hannuna sai sannan na sanyata a jakata can na hangi Magaji zaune a gindin wata bishiya ya taso da sauri ya karaso tare da risinawa yana gaishe ni na amsa da kulawa ya kama hannun Minal muka nufi inda ya ajiye motar a tare.
Hajja ta ji dadin ganinmu su biyu kacal a falo ita da Kamalu suna hira yana 'bare ta mata lemo zaki.
Ta dinga washe bakinta ganina da Minal tana cewa." Ke yaushe aka kawo ki ne k'awata."
Minal ta no'ke kafad'arta ta'ki zuwa wajanta ta tsaya kusa da ni tare da dafa cinyata.
Na gyara zamana a hankali cikin kulawa na gaisheta ta amsa tana ta yi mini maraba.
Na dubi Kamalu lokacin da yake gaishe ni girma ya yi mini a ido kwarai ya sake yin fad'i da 'barage mazantaka dai ta bayyana tunda dama tuntuni muryarsa ta fashe an balaga ga wani gemu zororo a ha'barsa. Cikin zuciyata na ce yaron nan dai ya rantse sai ya zama d'an izala
Gashi makarantar da ya yi ta almajiranci ba ni tsammanin ta 'yan alhalissuna ce. Kawai dai abinda ransa ya fi ra'ayi kenan yaro ya nutsu sosai cike da wata iriyar kammala ta mussaman zahirin kammaninsa da mahaifinsa ta fito 'baro-'baro bambamcinsu kawai shi Yaya Aminu ba shi da gemu kuma bashi da kuzarin yaron amma duk wanda ya ga Kamalu a yanzu zai tabbatar da cewa hoton ubansa ne
Hajja ta fad'i take daga Ina kuke cikin wannan rana ta k'arfe d'aya Amina."
Na ce." Wallahi Hajja daga asibiti nake shine na ce bari na biyo mu gaisa kawarki mata ta gaishe ki."
Ta sanya dariya tana jan hannun yarinyar tana sake no'kewa a jikina. Ta ce." Ina fatan dai lafiya ko Amina sannunki da ibada Ubangiji Allah Ya raba ku lafiya."
Na ce." Amin ya rabbi Hajja lafiya lau wallahi abinda sakamako ya nuna kenan.
Ta dinga fad'in." Alhamdulillahi cike da godiyar da Allah da jin dadi kafin ta shiga kwalawa iyami kira mai aikinta wai ta kawo mana ruwa."
Kamalu ya ce." Hajja ni me nake yi bari na kawo mata da kaina.
Ya ajiye lemon zaki da yake hannunsa ya nufi kicin da sauri lokacin Hajja ta d'auki lemon da ya gama 'barewa tana mikawa yarinyar da fad'in." Zo ki kar'ba to tunda kin 'ki zuwa mu gaisa."

kada ki karanta mini littafi ba tare da kin biya ni hakkina ba.

Ta kuwa tafi za ta kar'bo lemon saboda rashin kunya gabad'aya muka fashe da dariya.
Ta ce." Yusi ai yau tun safe ya fita kasuwa da yake ya ce bashi da karatu yau shine ya yi sammakon fita amma nan da biyar da rabi za ki gan shi ya dawo."
Na ce." Ya zama sarkin kasuwa ai."
Tana dariya ta ce." Haka ake son namiji ya kasance ai."
Kamalu ya ajiye mini ruwa da lemo masu sanyi a gabana. Na dube shi ina fad'in." Baka da hankali wanene zai sha wannan ruwan da wannan sanyin."
Yana murmushi ya ce." Mama ai na ga ana rana ne sosai ruwan sanyi zai fi kashe miki ishi."
Na ce"D'auke ka kawo mini mara sanyi."
Da sauri ya yi yadda na ce din ya kawo mini ya bude ya tsiyaya mini a Kofi.
Na d'auka na sha na bawa Minal Tasha na ajiye kofin saman plate din da ya kawo ruwan..
Hajja ta ce me za a sanya Iyami ta dafa muku Amina ni dai ce mata na yi ta saka mini danwake."
Na ce." Aikuwa a yi dani Hajja har na yi sha'awarsa. Tana dariya ta shiga k'walawa iyami kira ta fito ganina ya sanya ta risinawa tana gaishe ni na amsa mata da kulawa Hajja ta ce da ita ta kara garin danwaken ta saka shi da d'an dama. Ta amsa cike da bin umarni ta koma bakin aikinta.
Kamalu ya shiga dakinsu tsayin minti goma ya fito da wasu littafai a hannunsa gabad'aya muka bi shi da ido Hajja ta ce." Makarantar za ka tafi da wuri haka?"
Ya ce." E, Hajja amma kafin nan zan biya gidan Gwaggo."
Ta ce." Yawwa gwara da ka tuna mini shiga kicin ka ce da iyami ta baka garin danwaken nan leda biyar sai ka tafi mata da shi."
Ya ce." To shikkenan. Ta dube ni tana cewa." Abu ne na marmari duk ranar da ta yi sha'awa sai ta tsumbula.
Na yi shiru ina murmushi gefe guda kuma ina kara kambaba mutunci da halin dattako irin nata ga kyauta ga kirki Hajja mutuniyar kirki ce sosai Gwaggo ta zama 'kawarta kuma aminiyarta. Na tsinkayi maganarta tana fad'in." Ai ya sanar da ku d'aurin auransa gobe ne a Bunkure ko."
Na ce." Eh ya gaya mana Hajja Allah Ya sanya alheri."
Ta amsa da Amin. Kamalu ya fito da ledar garin danwaken a hannunsa yana yi mana sallama tare da ce mini zai zo cikin satin nan in sha Allah.
Ta dube ni cikin nutsuwa kafin ta furta." Amina Malam D'aha mutumin kirki ne kwarai da aniya kuma mutumin maigidana ne tare na san su abokai ne kuma masu rufawa juna asiri ta kowace siga. Lokacin da Tajo yake gaya mini kyautar auren 'diya da Malam 'Daha ya ba shi na yi farinciki domin sanin da na yi cewa gidan karamci ne da ilimi da addini gidan yi wa al'kur'ani hidima tabbas had'a iri da jinin Malam D'aha abin alfahari ne tare da fatan samun zuri'a nagartattu. Sai dai kuma jikina ya yi sanyi sosai lokacin da ya nuna mini hoton yarinyar na ganta 'yar karama nama sheda fuskarta tunda itace ta dinga dawainiyar kawo mana abinci a lokacin da Tajo ya kwanta ciwo a gidan. A mizani na tunanina yarinyar ba tsarar auransa ba ce domin ya yi mata nisa sosai babu hadi gabad'aya babu dacewa.
Amma a mizani na shari'a hakan ba haramun ba ne domin manzon Allah s.a.w shi ma ya yi irin wannan aure ya raini Nana Aisha har ta kai munzali kafin ya fara rayuwar aure da ita.
Malam D'aha Tajo ya yi niyyar bawa d'iyarsa kuma na tabbatar da cewa da zuciya daya ya kulla wannan al'amarin ba don samun abin duniya ba na sanshi sosai a can baya abin duniya bai dame shi ba mutum ne mai dattako da sanin ya kamata."
Ta yi shiru tana sauke ajiyar zucciya. Ni kuwa cikin raina ina fad'in anan dai bai san ya kamata ba Hajja tunda har ya iya bawa dattijo yarinya karama irin wannan ai zamanin annabawa daban da wanda muke ciki yanzu.
Ta cigaba da cewa." Na bashi goyon baya akan ya kar'bi kyautar da aka yi masa da kyakykyawar zuciya ku yi hakuri, ku kara akan wanda kuke yi in sha Allahu rabbi ba za ku samu matsala da yarinyar ba. Itama Hauwa zan kira ta a waya domin na kara tausar zuciyata dama itace fitinanniya ku yi hakuri ku kawar da kan ku na dan wani lokaci komai zai wuce."
Na ce." Wallahi babu komai Hajja ai yarinyar bata da matsala zamu zauna lafiya da juna kuma na yi miki alkawari ba za a samu matsala ta wajena ba."
Godiya da sanya albarka har sai da na ji nauyi da kunya na ce ta daina gode mini domin ban yi abinda ya kai ta yi mini irin wannan godiyar ba a ganina ni ce zan yi mata godiya bisa ayyukan alheran da take yi wa a alhalina.
Biyar daidai na fito da niyyar tafiya har lokacin Yusi bai dawo ba fadi take yi zai ji takaici kuwa idan ya dawo ya ji labarin kin zo.
Na ce." Kawai sai ya zo gida ya same ni Hajja ba zan zauna jiran dawowarsa ba zan yi abinci idan na koma."
Muka yi sallama cikin girmama juna da mutuntawa Magaji direbanta ya d'auke ni a mota har gidana.
Sai da na yi magriba tukkuna na shiga kicin jallop nake sha'awa ta taliya da kifi ita na yi na zuba mana ni da Minal muka ci a kwano d'aya na ajiye wa maigidan 'yar kad'an dalili nasan ko zai ci ba dayawa ba tunda ba cimarsa ba ce taliya da makaroni. Abinda ya fi so dangin towo kowane iri sakawara funkaso ko wainar masa ta bauchi Yana son faten doya ma abinci da miya bai dame shi sosai ba sai ya ce asa masa miya kad'an saman shinkafa. Yana kuma son gurasa da miya sosai.
Wajan goma saura ya shigo tare da Sukairaju ashe tare suka zo garin. Ya d'an tsaya daga bakin kofa ya kar'bi wayoyinsa daga hannuna ya gaishe ni na amsa babu yabo babu fallasa ya juya da sauri ya fita shi kuma ya karaso wajan da nake zaune hannunsa ri'ke dana Minal
A d'an hargitse yake gaskiya tsabar ma baya hayyacinsa gilashinsa a hannu yake abinda bai ta'ba faruwa ba duk rintsi da wahala baya cire gilashin nan na idonsa, sai sau daya lokacin da ya fad'i a garin bunkure yana dawowa hayyacinsa kuwa ya mayar da abinsa kamar wanda aka haifa tare da shi na ta'ba tambayarsa ko yana da matsalar Ido ya ce mini a a yana sanya shine domin kara karfin gani kuma dai ya zame masa jiki idan ma Babu shi a idonsa baya jin dad'i......
'
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA,#700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*149*
Na zura masa ido jikina a sanyaye ga dukkanin alamu akwai matsala. Da kyar na bud'e bakina da ya yi mini nauyi na ce masa barka da zuwa. Ya amsa yana ri'ke hannun Minal da take ta jan babbar rigar jikinsa. Da ya amsa mini bai sake cewa komai ba ya wuce. Na bi shi da kallo cikin lissafi a zuciyata shin menene ya gigita shi hakane? ko dai akwai matsala ta fannin daidaituwar jini shi da yarinyar tunda ya gaya mini zai ce ya d'aukota a yi mata genotype din tunda shi ya sanya nasa As ne kamar yadda nake As. Idan hakan shi ya hadda masa wannan gigicewar lallai ya fito da abinda yake cikin ransa wanda yake ta nuku-nuku da shi yana kuma so ya yaudare mu kan cewa baya son auranta. Alamu sun nuna lallai zuciyarsa ba ta so faruwar hakan ba.
Na tashi na bi shi saman na same shi zaune gefan gado Minal na ta wasa da agogon hannunsa da ya cire ya ajiye shi kuma yana zaune ya dai cire babbar rigar ya ajiye amma har yanzu yana cikin rashin hayyaci.
Motsin shigowata ya sanya shi dubana. Bai janye idonsa ba har na isa kusa da shi na zauna still idona a kansa a takaice na ce." Me yake faruwa ne?"
Ya yi jim kafin dube ni da wani yanayi ya furta "Yarinyar As ce Amina. Akwai matsala tunda ni ma As ne duka d'anjuma ne da d'anjummai, gidan Malam D'aha cike yake da ba'ki na nesa dana kusa sun d'ora manya tukuwane domin abincin jama'ar d'aurin aure dalili shi mutum ne na mutane k'warai da gaske da yawa jamaarsa ta mahaifina ne cikinsu wad'anda suka rage da iyalinsu babu wanda bai san da maganar wannan auran ba. Babban abinda ya fi d'aga mini hankali anan shine yadda zan gaya masa cewa a janye d'aurin auran nan saboda wannan matsalar da bai zama lallai ya yarda da ita ba tunda ke kan ki kin sani abu ne mai wahala ya amince da koyarwar yahuduwa a matsayinsa na malamin addini kuma mutumin karkara."
Na yi shiru ina kallonsa zuciya na gaya mini ba wannan dalilin kad'ai ya sanya shi gigicewa ba akwai wani dalilin dai da yake boyewa.
Na ce." Yanzu wace shawara ka yanke?"
Ya yi shiru kawai yana kallona sai da na sake maimaita maganata tukkuna ya furta." Ban yanke ba har yanzu Amina bana jin zan iya dakatar da Malam 'Daha dangane da abinda ya niyyata ya kuma yi gangami a kansa."
Na furta." Za ka bari a d'aura auran kenan ?"
Ya gyad'a kansa yana kallona."
Sai na ce." To idan hakane menene abin damuwa tunda ka ji ka gani me yasa za ka daga hankalinka. Ka bar wa Allah wata'kila sai ka ga kun samar da yara masu lafiya ba irin wanda ake tsammani ba."
Ya ce." Ai ba wani sonta nake ba Amina. Maccan da nake tsoron rabuwa da ita itace nake jin zan yi hakuri na zauna zaman aure da ita idan aka ci karo da wannan matsalar ga misali nan a kanki. Amma ina ji ina gani ba zan yi gangancin ba gaskiya magana kenan."
Murmushin takaici na yi kafin na ce." Akwai zalinci tsantsa idan har abinda ka fada da gaske ne a cikin zuciyarka to bari na gaya maka daka kai har malamin kun zalinci yarinyar nan. Ya kamata duk wani b'oye -boye da kake yi ka fito fili ka yi wa mahukutanku bayani nufi na walliyanku wai shin kai karamin yaro ne? A tunanina saurayi dan shekara a shirin da biyar ba zai yarda a yi masa irin

Please Login or Register in order to submit comment