Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

haka na ce miki wai ke wace irin yarinya ce ne, idan har ba ki nemi fitina ba ba kya jin dadi a rayuwarki ke ba za ki ta'ba ba ni nutsuwa da kwanciyar hankali ba."

Cikin dauriya na ce." Babban abinda ya daga mini hankali yadda har ka iya rufe Idonka ka gaya mata cewa Kamalu ya ta'ba yin fitina irin ta 'kuruciya a baya, sannan ka fitar da rikicin da ya faru a gidan nan har jama'a suna yamadidi da mu cewa mun had'e mata kai ni da Hauwa ba ma yin mu'amula da ita."

Ido ya tsira mini a rikice ya ce." Yanzu wanene ya kawo maganar Kamalu anan?"
Na ce." Ni ce na kawota domin na yi iyakacin bakin kokarina akan na ga na danne maganar a zuciyata na kasa abinda ya sanya ni sake gazgata cewa kai ka gaya mata a ina mutane za su samu labarin zaman da muke yi har su zage mu akan mun ware matarka tuntuni ka nuna hadin kan dake tsakanina da Hauwa baka so saboda ba mu sanya matarka a cikinmu ba har ka gaza ha'kuri ka fitar da maganar duniya."

Ya jima yana kallona cikin tashin hankali kafin ya ce." Ni ko Hajja ban ta'ba gayawa sirrin gidana ba mahaifiyata kenan. Baban Saude shine mutumin da nake ganin zan gayawa matsalar da ta shafe ni ya ba ni shawarwari saboda na yarda da nutsuwa da adalcinsa kuma ki ji tsoron Allah Amina
Idan har za ki yi mini adalci ki fadi gaskiya akaina kada neman fitina ya sanya ki haddasa mini ciwo, ki fadi gaskiyar abinda ki ka sani a kaina na daga da'bia na tabbatar da cewa tsayin zamana dake zaki gane abinda zan aikata da kuma wanda ba zan aikata ba mai zai sanya kawai na zaunar da Maryam na gaya mata abinda ya faru a baya me yasa zan yi haka? Uhm me yasa zan aibata Kamalu a wurin Maryam saboda soyayya ta yi mini dadi."
Ya kai karshen maganar cikin yanayi na damuwa da alhini."
Na ji hawaye sun zubo kumatuna ban goge ba na ce." To a ina ta samu labari idan ba kai ka gaya mata ba, ita kuma ta gayawa yaranta."
Ya yi d'an jim kafin ya furta." A lokacin da abin ya faru ke kan ki fa kin yi dogon rubutu a social media wato fecebook rubutun da ya zagaye kowace kafa ta sadarwa wanda bai san akan wane dalili ki ka yi rubutun akaina ba zai je ya bibiyi ba'asi kin manta da haka? kin manta cewa Salim zai iya cin karo da labarin ke ma fa kin bada gudummuwa wurin 'kara rura wutar lamarin domin dai kin san matsayina rubutunki kuma ya janyo cecekuce da yawa, me yasa za ki d'ora mini lefi?''
Shiru na yi ina kuka domin bakin cikin abinda ya faru ne gabad'aya ya taso mini.
Ya tashi tsaye yana fad'in." Ke duk yadda mutum ya so da ya zauna lafiya dake ba za ki ba shi damar hakan ba, ba ki iya rarrashi da tarairaya ba sai neman fitina."
Ya tafi ya je ya kwanta saman gadona tare da rufe k'afafunsa da bargo. Kuka na ci na koshi yana kallona bai ce mini komai ba. Na shiga bandaki na yi wanka na fito duk idonsa biyu na shirya jikina da kayan bacci.
Abinci na zauna na ci kad'an kafin na kwashe kayan na kai kicin na dawo d'akin yana dai kwance amma bai yi baccin ba.
Gefansa na zauna ina d'an kallonsa gabad'aya ya yi sanyi yanayin damuwa ya bayyana a fuskarsa.
Ban ce komai ba na ra'ba daga gefansa na kwanta ina jin bai fi sau uku ba ya ta'ba kwana a d'akina ba.
Ya mik'a hannu ya kashe fitilar gefan gado kafin ya janyo ni jikinsa sosai ya matse ni a kirjinsa muka sauka ajiyar zuciya kusan a tare jikinsa na dan rawa na ji maganarsa a hankali cikin taushi da rarrashi Yana fad'in." Da zan iya ha'kuri dake Amina da tuni na yi, Allah Ya jarrabe ni da sonki kada ki ga haka ki nemi halaka ni don girman Allah."
Shiru na yi ban ce masa uffan ba ina jin dai yadda hannunsa keta zarya a sassan jikina. yana mika bakinsa wuyana yana sumbata cikin sar'kewar murya yake fad'in." Mu yi soyayya irin wadda na Annabi s.a.w ya koyar Amina kada mu cutar da wani sashe na jikinmu ina buk'atar kulawa a yau ta mussaman kada ki yi mini 'kwange ki marabce ni da zuciya da gangar jikinki."
Na dai yi masa shiru ban tanka ba zuwa lokacin ma na fara bin layinsa. Ya dago fuskata yasa bakinsa yana ta sumbatar kumatuna kafin ya fara ko'karin had'a bakinmu wuri d'aya. Hannayena na sanya a tsakaninsa na janyo shi sosai muka had'e bakinmu cikin wata masifaffiyar runguma wadda take motsa duka ga'bban jiki.

Washe gari da safe kafin ya fita har da yi mini wa'kar soyayya ta Hamusu bireka tun ina daurewa har dai na gaza na dinga kyalkyala dariya ganin yadda yake ta rero wa'kar (Ashe da rai nake sonki jaruma ba da zuciyata ba, komai ruwa da iska akan ki ba za na daina kewa ba, idan na same ki.....) Na tambaye shi a ina ji ya wa'kar har ya haddace baitikan irin haka ya ce a gari ya ji shima. Kai na ci dariya sosai da ya fita na ce lallai na cinye wasan a daran jiya kenan irin wannan wa'ka haka......
'þ
2k complete on telegram via 0542382124...binta Umar gtbank
*07084653262*

A cikin kwanaki biyun da suka kasance na girkina mun yi abin arzi'ki sosai ni da shi ya dinga lalla'ba ni tare da ko'karin ganin wata matsala bata faru ba wadda zata janyo mana k'ananun maganganu . Washe garin ranar da girki ya bar hannuna kafin na sauko daga saman na sake tuntu'barsa maganar zuwa maiduguri ganin d'akin Fadila ya ce ai ya riga ya rantse na yi hakuri har su je su dawo daga asibitin da za su je shi da Momi tunda yanzu abinda ya sanya a gaba kenan idan ya dawo sai ya raka ni mu je maidugurin tare, shima sai ya gaishe da su Dada da sauran 'yan uwana,
Na ce amma maganar yara fa kai tsaye ya ce mini suna tare da Nabila a gidan domin ta d'an kwana biyu da zuwa wurin 'yar uwata, amma ba da ita za a yi tafiyar ba zata zauna ta kula da yaran gabad'aya har da su Salim da Adamu.
Rashin abin fad'a ya sanya ni kawai zuba masa ido, wace irin masifa ce ne wannan jama'a, shin yaushe yaranmu za su dawo hannunmu ne ni Aminatu?"
Ina zaune har ya gama kintsa jikinsa muka sauko tare babu kowa a falon Baba Tabawa ta gama aiki tun da wuri ta shige dakinta. Hauwa ba ta fito ba. Har zai fita sai ya tsaya yana kallona kafin ya ce." Ina Hauwa ne?"
Kai tsaye na ce." Ba kasan inda take ba?"
Ya zura mini ido na 'yan sakkoni kafin ya gyad'a kansa ya kama hanyar fita yana fad'in.'' idan ba ki yi tsiwa ba ai ba sunanki Amina ba."
Ya fice a gaggauce don da alama yana da wani babban uzurin da ya hana shi tsayuwa ma ya karya kummalo.
Ina juyawa da zummar shiga d'akina Hauwa ta fito cikin kayan bacci da alamar ba ta jima da tashi ba hankalinta na wurin cin abinci. Tana hamma ta furta." Wata mashahuriyar yunwa ce ta tashe ni Amina."
Na ce." Ai fa wannan abinda yake cikin naki acici za mu sanya masa Hauwa."
Dariya ta yi tana fad'in." Na dai kusa saukewa na sha ibada wallahi."
Cike da kulawa na ce." Ubangiji Allah Ya sauke ki lafiya, yanzu nan kuwa maigidan da zai fita yake tambayarki."
Ta yi sororo tana kallona. Na gyad'a kaina ina fad'in." A shawarce Hauwa tun kafin manya su ji wannan abin ku shirya tsakaninku don Allah ke ce 'kasa dashi dole ki sauke girman kan ki."
Ta ce." To so ki ke yi na je na ce masa ya yi hakuri ya janye sakin da ya yi mini Amina?"
Na ce." E, mana menene a ciki idan kin ce masa ka yi hakuri."
Ta'be bakinta ta yi ba ta ce komai ba ta nufi wurin da abin kari yake a shirye tana fad'in." Zancen ki ke so Amina."
Na bita da kallon mamaki kafin na girgiza kai na wuce d'akina da tunanin abin a raina. Da alama shi ya fara sakkowa tunda har ya tambayeta na tabbatar da cewa yanzu ya fara neman zaman lafiya a gidansa.

Ranar da za su tafi
har gida ya yi mata jagora domin ta yi mana sallama. Zamanta ke da wuya Hauwa ta yun'kura ta tashi ta shige dakinta. Hakan kuwa bai yi mata dad'i ba, amma dai ba ta ce komai ba, muka d'an ta'ba hira sama-sama kafin ya sauko daga saman suka fita tare. Sosai na yi mata addu'a da fatan alheri ta dinga godiya da murmushin nan nata wanda duk rintsi baya ta'ba d'aukewa daga saman fuskarta.

Bayan tafiyar su da kwana ashirin da shida Hauwa ta haihu. Cikin ikon Allah ta haifi d'anta namiji kama da ubanshi har ta 'baci duk abinda ya kamaci ta yi wa kanta ta yi tunda haihuwar gida ta yi kuma lafiya lau ita da yaron da ta haifa, a matsayinta na ma'aikaciyar lafiya taimakon da muka yi mata kad'an ne. Sai bayan da muka samu nutsuwa gabad'ayanmu ni da ita tukkuna na nemi maigidan da yake koda suka tafi ba kasafai yake kiran waya ba sai dai mu had'u ta whasap to baya jurar typing sai da vedio call. Sai na ajiye masa sa'ko ta whasap din tare da hoton yaron nasan daga zarar ya hau zai gani. Ina idar da sallar la'asar na bud'e sakonshi ya shigo yana online din muka sake gaisawa na tambaye shi mai jiki ya ba ni amsa mai dadi jiki yayi kyau domin a karshen watan da muke ciki ma za su dawo domin an d'orata akan maganguna kuma alhamdulillahi an samu cigaba. Sai ya d'ora da fad'in wai na yi wa yaron hud'uba da sunan Ahmadu domin shine sunan da ya rad'a masa. Rashin abin cewa ya sanya ni yi masa shiru kawai domin tunda Hauwa ta haihu take kiran yaron da sunan mahaifinta wato Ishak, ban san kuma mai zan ce mata ba gaskiyar magana kenan.
Ganin na yi shiru ban ce komai ba ya sanya shi kiran sunana na kalle shi tunda bidiyo call ne ya furta." Ko akwai wata matsala ne domin na karanci damuwa a cikin kwayar Idonki."
Na girgiza kaina a nutse na ce." Babu matsala amma gaskiya ba zan iya gaya Hauwa ga abinda ka yanke ba, mai zai hana kai ka gaya mata naga tare kuka samar da yaron nan ku biyu mai zai sanya ni ka saka ni a tsakiya. Hauwa tunda ta haihu take kiran yaron nan da sunan babanta, to ni mai kake so na ce kuma."
Ya yi shiru yana kallona kafin daga bisani ya ce." Shikkenan zan gaya mata hukuncin dana yanke hakan ya yi ko."
Na gyada kaina ina fad'in." Ya yi shine daidai sai ku tsayar da matsaya a tsakaninku, Allah Ya raya mana shi."
Ya amsa da "Amin. Yana mai zuba mini ido."
Ni ma na zuba masa nawa idon nan na fahimci canzawar da ya yi har da wani kumatu fatar nan ta sake yin fresh duk da bidiyo call yana sanya mutum muni da duhu to shi ban ga hakan ba, kamar ba wanda ya tafi jinyya ba ya yi kama da ango wanda ya tafi yawon sha'katawa da amaryarsa.
Ajiyar zuciya na sauke yayin da nake ko'karin kawar da abinda na ji yana yun'kuro mini a game dashi na ce." Na canza kammanni ne Allah Ya taimaka ka."
Sai ya rausayar da kansa yana ce wa." Sosai kuwa, wata na gani anan asibitin da muke mai kama dake duk sanda na yi ido hud'u da ita sai hankalina ya tashi wallahi yanzu ina cikin tsananin damuwa na yi missing d'inki my love dina."
Na dan bata rai tare da cewa." Matar kuma idan tana da aure fa, kana raya abun da bai dace ba akan matar wani daidai kenan a wurinka."
Kansa ya girgiza kamar karamin yaro ya furta." Ba daidai ba ne, amma ba na tsammanin ai tana da aure budurwa ce, wallahi ba zan munafurceki ba Amina ba na iya d'auke kaina daga kanta domin yanayin hallitar jikinku daya 'yar duma-duma ce mai yawaltaccen kirji da tudun mazaunai."
Dariya maganar ta ba ni na danne ban yi ba domin ganin abin nasa yana nema ya wuce makadi da rawa na ce." To sai ka tuntubeta idan ba ta da aure ka aurota ko?"
Ya girgiza kansa yana ce wa." A'a ai ba musluma ba ce addinin hindu ce."
Na ce." To menene a ciki sai ka musuluntar da ita."
Kansa ya girgiza tare da furta." A a, abinda ya sa ki ka ji ina yi miki maganarta kamar da kuke yi da ita ne ya b'aci da gaske
idan na ganta ina shiga yanayi na buk'atuwa sosai."
Shiru na yi ban ce komai ba. Sai ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya furta." Ina nan dawowa my love za mu sha soyayya ko?"
Na kashe idona tare da fad'in." Sosai ma irin wadda kake so za mu yi."
Sai ya zuba mini idanuwansa babu kiftawa. Na kama dariya ina fad'in." Ka na ji kamar ka d'auko ni daga cikin wayar ko?"
Ya gyada kansa yana lumshe Ido. Hakan ya sake jefa ni a damuwa da sha'awa na sauke ajiyar zuciya a kasalance na furta." Ni ma na yi missing din Baba Yallabai baban soyayya."
Kafin ya ce wani abu kiran da aka yi masa a wayar ya katse video call din. Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefe Ina sauke ajiyar zuciya gabad'aya hirar nan da muka yi ta tayar mini da hankali wani irin nake ji a jikina.
Sai gefin magriba na fito falon daga cikin d'akin Hauwa na ji kukan yaron ya tsananta da saurin gaske na shiga d'akin na same shi kwance cikin net dinshi yana ta wutsil-wutsil towel ya toshe masa hanci. Da azama na zuge net din na d'auko shi fuskarsa ta yi jazur saboda da alama ya jima yana kukan.
Na zauna gefan gadonta ina jijiigashi gabad'aya ya shid'e a tunanina tana bandaki na tashi tsaye dashi a kafad'ata na tsaya kofar band'akin ina kiran sunanta shiru bata amsa ba kuma babu motsin ruwa. Sai kawai na kutsa kaina ciki wayam babu alamunta. Da sauri na fito gabana na dan fad'uwa na tsaya ina rarraba idanuwana a d'akin ban ga alamun komai ba..
Na fita kai tsaye kicin na nufa Baba Tabawa ta kammala abinci dare tana gyara kicin din. Cikin kasala da sagewar gwiwa na furta." Baba ina Hauwa?"
Sai kawai ta tsaya tana kallona kafin daga bisani ta furta." Ba ta dakinta ne Amina?"
Na furta." Kwarai kuwa, fitowata daga d'aki kenan na ji kukan yaron nan koda na shiga d'akinta bata nan."
Ta sanya hannunta ta kar'be shi a sanyaye ta biyo bayana muka tsaya a tsakiyar falon. Ina Hauwa za ta tafi to. Ni nake tambayar zuciyata dalili tunda ta haihu ban ga alamun fitina a tattare da ita ba asalima wani babin annashuwa da farinciki ta bud'e. Baba Tabawa ta sanya babban towel ta goya yaron ni kuma na d'auko hijabina na sanya na fita can harabar gidan. Daga nesa na tsaya ina hangen securitys a bakin gate. Masa'udu ya shigo da mota ya ajiye a wurin da motocin suke ya fito daga motar ganina a tsaye ya sanya shi da sauri ya nufo ni. Ya risina yana gaishe ni na amsa tare da fad'in." Daga ina kake domin kuwa zuciyata ta fara hasashen wani abu......
'þ
*2k complete a kan telegram via 0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *2K Complete ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP 1K...0542382124...BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*109*
Kai tsaye ya furta." Na kai Hajiya k'arama tasha zata bi mota zuwa bauchi don haka na ji tana fad'a a waya kafin mu isa."
Ba tare da na sake cewa komai ba na kad'a kaina na koma ciki gidan raina a masifar b'ace. Anya kuwa Hauwa tana da hankali ta haihu kwana biyu kacal saboda mugun abu ta gudu ta bar jaririn da ta sha dawainiya da wahala a kansa kafin ya zo duniya ta kuma ci kwakwa duk a kansa tare da tsallake siradi. Ga kuma d'aita irin ta haihuwa da rashin kwari a jiki, wannan ba tunani ba ne gaskiyar magana a wannan karon ba ta kyauta ba, shi jariri ina ruwansa kuma hakkinsa kad'ai ba zai bari ta samu nutsuwa ba a duk inda take.
Baba Tabawa ta dinga sallallami tana fad'in." Wannan wane irin sakarci ne Hajiya Amina, to shi wannan din da ta tafi ta bar shi ai hakkinsa ba zai bar ta, ina ruwansa da abinda ya faru."
Ban ce mata komai ba na shige na je na d'auko wayata layinta na dingi kira wayar a kashe na kira ya kai sau goma amma is switch off. Na zube saman kujera ina Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un, wace irin masifa ce wannan ne?
Na jima cikin wannan yanayin kafin na d'auki wayata dake saman cinyata kai tsaye lambar Dr Sailuba na nemo itace tsayayyiyar likitan da take duba ni a duk lokacin da na samu ciki mussaman cikin baby Nana ta taka muhimmiyar rawa kwarai da gaske. Abu na farko da zan yi shine samarwa da yaron abinci matsalar raino wannan mai sau'ki ne. Bayani na yi mata sosai amma ban sanar da ita cewa uwar yaron ce ta ajiye shi ba.
Ba mu yi sallama da ita ba sai da ta tabbatar mini da cewa da kanta za ta shigo ta kawo mini duk abinda ya dace.
Na kashe wayar tare da zubawa Baba Tabawa idanu tana ta faman safa da marwa a katafaran falon duk domin hillatar yaron da yake ta kusurkusur da alamun kuka.
Sai da bacci ya d'auke shi tukkuna ta zo ta zauna a gefana tana fad'in." Ko a tarihi ban ta'ba ganin shashashar uwa irin Hauwa ba Hajiya Amina lallai ta gwadawa wannan yaro rashin Imani."
Shiru na yi Ina nazari kafin daga bisani na furta." Tana so ta huce fushin abinda ubansa ya yi mata shine ta dire shi ta yi tafiyarta. Abin mamaki kuma ita da mijin nata jini guda ne mamansa ta cika nono ta bawa Mamanta wace irin zuciyace wannan."
Kai tsaye ta ce." Zuciyar kafurai ce."
Muka yi shiru cikin alhini kafin ta cigaba da cewa." Ita kanta na tabbatar da cewa wallahi hankalinta ba zai ta'ba kwanciya ba ciwon jiki da ciwon nono ma ya isheta.
Murmushi na yi tare da cewa." Ciwon nono mai sau'ki ne a wurinta tunda likita ce tana da hanyoyin da zata magance abinta ciwon jiki kam zata sha ai haihuwa ba wasa ba ce."
Haka muka kasance cikin zullumi da tararrabi har Dr Sailuba ta zo ta tafi muna zaune a falon cikin wani irin yanayi na mamaki da takaici.
Ba ni da niyyar sanar da kowa wannan lamarin amma dole maigidan ya sani domin duk wanda ya sayi rariya ya san za ta zubar da ruwa, domin duk abinda yake faruwa shine sanadi me ake yi da zuciya irin tasa ta riko da ba'kar gaba, ita dashi duka kanwar ja ce shi ba'kar zuciya da gaba ita girman kai da rashin tsinkaye.
Sai da daddare tukkuna yaron ya gama kiciniyar kukansa Baba Tabawa ta goya shi ya yi bacci sannan na samu sararin bude data.
Na duba shi ta What'sapp din bai jima da sauka ba. Sallama na yi masa tare da barin datar a bud'e na ajiyar wayar na tashi na je na leka d'akin Baba Tabawa tana zagaye a d'akin bayanta goyo da yaron. Tausayinta ya kama ni haka kawai sun sanya tsohuwa wahala lokacin da suka jiyar da junansu dadi har suka samu 'karuwa bata sani ba, yanzu kuma sun haihu sun barwa wasu da raino.
Ta juyo tana kallona a dan sanyaye na ce." Ya yi baccin ne?'
Ta gyada kanta a hankali ta furta." Ya yi da farko dana kwantar da shi shine fa ya tashi na sake mayar dashi na goya."
Na sauke ajiyar zuciya tare da fad'in." Ki yi hakuri Baba an tashe ki a tsaye."
Sai ta yi dariya tana fad'in." To menene a ciki ni na kar'bi ladan Amina duk da ban ta'ba haihuwa ba ai na iya raino an sha kawo mini yara na yaye su ki tambayi Hajiya Sahura ni ce na yaye Yasir kanin Yusura."
Da d'an murmushi na furta." Ai na ga alama duk da haka dai idan ya yi bacci sai ki kwantar da shi kema ki huta da tsayuwa."
Ta furta." Haka za a yi in sha Allahu."
Na juya na fita zuwa d'akina.
Ina d'aukar wayar na duba naga sakon shi voice note ne na buda na saurara yana gaya mini Momi ta samu sau'ki sosai ta ce tana so mu gaisa.
Ban mayar masa ta hanyar murya ba na rubuta masa a rubuce
"Hauwa ta ajiye maka jaririnka ta tafi."
Yana karantawa kuwa sai ya kira ta What'sapp din na daga.
Ya ce." Me ki ka ce?" Na ce." Hauwa ce ta tafi Bauchi ta bar jaririn a gida."
Cike da wani irin yanayi na rikita ya ce." Ta tafi Bauchi ta bar jariri bisa umarnin wa? Me yasa ba ku da hankali ne Amina?"
Da mamaki a tare da ni na ce." Ba mu da hankali kamar yaya? Ni kuma ina ruwa don na gaya maka sai hakan ya zama lefi idan na yi shiru kuma nan ma ya zama lefi."
Ya ce." Da zata ta tafi mai yasa ba ki hana ta ba, ashe ba za ki iya tsaya mini a gidana ba idan ba na nan?"
Dan murmushin takaici na yi kafin na furta." Wallahi ni kaina ban san lokacin da ta tafi ba, kuma tunda ta haihu ban ga alamun fitina a tare da ita ba, sannan da kake cewa na hana ta ni na isa? zaman idda take yi fa tunda duk cikinmu babu wanda ka gayawa ka mayar da ita don ta haihu ta ajiye maka d'anka lefi ne, tun kafin ta haihu kake da dama a hannunka ba ka yi amfani da ita ba."
A d'an raunana ya furta." Ba ki ga lefinta ba kenan Amina tare da hadin bakin ki Hauwa ta yi mini wannan wulakancin."
Na furta." Kada ka d'auki hakkina wallahi ban sani ba, bata kyauta ba ai ko babu komai ta duba yaron ta tafi dashi idan ma ba zata zauna ba."
Ya ce." Yanzu ina yaron yake?"
Kai tsaye na ce." Na aikawa da Nabila shi."
''Kin aikawa da Nabila shi?''
Ya maimaita amsar dana bashi cike da mamaki.
Na ce." Kwarai kuwa sai ta had'a gabad'aya ta ri'ke da 'yan uwansa ko ba haka ba ne tsarinka."
"Ke ba za ki iya ri'ke shi ba kafin na dawo na yanke hukunci.''
Ya fad'a cikin sanyi murya tabbacin ya ji ciwon abin."
Na ce." To ai gani na yi ba ni da nonon da zan ba shi, kuma ban iya raino ba da kula ba shiyasa na aikata mata dashi ta had'a shi ta ri'ke."
Ya furta." Kin so kema ki tozarta ni Amina, na gode bisa wannan abu da kuka hadu ku ka yi mini Allah Ya saka mini."
Bai jira jin abinda zan ce ba ya datse kiran ya ma sauka daga Whasap din gabad'aya.
Na yi kasa'ke da waya hannuna ina dariya wai Allah Ya saka masa ashe da ciwo kenan. Hauwa ta kyauta bata kyauta ba, lallai abinda ta yi ya ta'ba shi ainun ganin bakinsa ya mutu ya rasa abinda zai ce.
Kafin na kwanta sai da na sake zuwa na leka d'akin baba Tabawa yaron ya yi bacci cikin net din sa, itama ta kwanta amma ba ta yi baccin ba tukkuna na tsaya muka d'an yi maganar kad'an kafin mu yi sallama na je na yi shirin kwanciya.
Da safe ina bud'e data sakon shi ya shigo yana gaya mini jiya ya tambayi Nabila ta ce ita yaron baya hannunta. Ina muka kai masa d'ansa.
Dariya na yi kafin na rubuta masa cewa." Gidan marayu muka kai shi."
Yana dubawa kuwa ya kira bidiyo call.
Bai bari ma

Please Login or Register in order to submit comment