Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fita suka gaisa da Masa'udu tasan ya yi tafiya zuwa garinsu shine ya gaya mata abinda ya kawo muku."
Na ce." To tunda hakkinta za ta fitar mata ai kamata ya yi ta buk'aci sauran kuma saboda neman magana ni me yasa ba zata gaya mini ba."
Cikin k'osawa ya furta." Ba ni son 'karamar magana ta zama babba Amina kwana biyu abubuwa sun yi sanyi dalili na fahimci kowacce a tsakaninku kada ki girmama lamarin don ta sanar da ni ba wani abu ba ne, ni kuma ai gashi na gaya miki."
Na ce." Munafurci ne kawai idan da yarda babu wani nufi a zuciyarta ai ni ya kamata ta gayawa tana buk'ata tunda tana da lambar wayata."
Ya datse kiran ba tare da ya ba ni amsa ba.
Kicin din na shiga na ce su raba tsarabar nan kashi biyu daidai a bawa Hauwa.
Hadiza dake gyara alayyahu ta ce." A a ai nan kuke da yawa Amina na yi zaman gidan iyali na gani kin san dai Alhaji Halilu matansa biyu ni ce ta uku ko, to duk abinda ya kawo nawa ne kad'an tunda ba ni da yara. Me zai sanya za a yi haka kuma?"
Ina dariya na ce." To Masa'udu garin kaud'insa ya gaya mata ya kawo tsarabar zogale da albasa tare da doya shine tana zuwa gida ta kira maigidan wai tana son zogale.
Taburni ta ce ." Ban da abin Hajiya Hauwa ai ke da ita duk daya ne sai ta gaya miki tana buk'ata ta shigo ta dibi yadda ranta yake so."
Murmushi kawai na yi ban sake tankawa ba Ina jin su suna ta magana. Hadiza na fad'in." Idan an raba an bata biyu ba a yi miki adalci ba."
Anan ne na ce to wannan tsaraba dai ta Masa'udu na neman ta janyo cecekuce ayi dai yadda na ce din idan ma kyautar da su za ta yi shikkenan a bata zogale ne dama yake yi mana wahala don ta doya da albasa wannan ai ba matsalarmu ba ce ko ku raba daidai a had'a mata cikin buhu sai ta aiko ta d'auka."
Na juya na fita daga kicin ina jin maganganunsa akan lamarin.
Yana kuwa shigowa da abinda ya fara kenan na ce an raba kashi biyu ta aiko ta d'auka ko kai ka d'auka ka kai mata.
Yadda na fadi maganar a harzuke shine abinda ya sanya shi tsirawa fuskata ido yadda ya nuna kamar abin ba na tashin hankali ba ne gashi ina ko'karin girmama shi. Ni abinda ya ba ni haushi yadda ta kasa tambayata sai shi zata tambayata tunda ai Masa'udu direbansa kuma shi ya kawo kayan babu buk'atar ta tambayeni wanda yake zaune dominsa shi za ta tambayata ni ban isa ba. Yanayin yadda ya damu da lallai sai an bata tamkar wadda ta bawa umarni.
Haka dai ya dinga kaucewa neman fitinata domin so na yi ya tanka na fad'i abinda yake raina sai ya'ki biye mini ya kira ta a gabana yana fad'in ta turo Ladidi ko yaron dake bawa shokokin gidanta ruwa ya d'aukar mata.
Ya kashe wayarsa. Ya dinga jana da hira a lokacin da nake zaune a gefansa yana aiki a computer na ki biye masa ni ma. Sai ya ja bakinsa ya yi shiru tsayin minti ashirin da biyar ya gama abinda zai yi ya rufe Loptop din Yana kallona ya ce." In banda dole sai an janyo mini tsiya a gidana ya za a yi rigima akan zogale Amina wai don Allah menene yake damunku ne?"
Na dube shi ina fad'in." Halin tsiya ai yana wajanta Allah Ya yi maka mai kyau duniya da lahira ni ai ban ce komai ba, ka ce a dibar mata zogale an yi yadda ka ce din to kuma sai ya zama lefi."
Ya gyad'a kansa still idonsa a tsaye a kaina ya furta." Shine na ce ai kuna nema ku ba ni kunya saboda rashin tsinkaye da tunani ita tana can tana surutai na banza bisa wani zargin da bashi da toshe ke kuma gaki ba ki da fahimta wato cewar da na yi a dibar mata zogalen da Masa'udu ya kawo sai ya zama a lefi a wurinki Amina har ki dinga ko'karin zagi na."
Da sauri na ce." Yaushe na zage ka don Allah?"
Ya nuna kirjinsa da yatsa yana fad'in." Kin san dai ba zan yi miki k'arya ba ko, ai ni ba kurma ba ne na ji lokacin."
Kasa'ke kawai na yi ina kallonsa da mamakin yaushe ya koyi 'karya mai lasisi irin haka. Nasan dai gwani ne shi wurin juya magana idan yana so ya kare kansa ko ya kashe wata rigima yanzu nan zai sar'kafe ya cukurkud'a magana ya kuma dage shine da gaskiya yanzu ma abinda ya shirya yi kenan uana so ya d'aure ni da jijiyar jikina ban zage shi ba amma gashi yana fad'in na zage shi ai ba mahaukaciya ba ce ni.
Ya cigaba da sakin maganganu." Duka kun raina ni wallahi saboda na yi sanyi ina bin kan kowacce da abinda take so babu wadda nake tsoro na yi miki ta bafulatani aradu na d'aga 'kafa ne kawai don ganin yarana suna girma nan da shekaru takwas twins dina sun zama cikakkun 'yan mata 'yan 16years lokacin ko ina raye ko ba na raye Allah ne ka'dai masani."
Ya sassauta maganar cikin alhini tare da 'kura mini ido.
"Hum kawai na ce kafin ajiyar zuciya ta biyo baya na furta." Allah Ya kyauta dai Ina ganin dai ko tsufa muka yi gaskiya da wahala matarka ta canza domin ko kai kasan yadda nake hakuri bisa dabi'unta yanzu don girman Allah menene don ta kira ni ta ce tana son zogale kai ba ka yi tunanin cewa akwai wani abu a zuciyarta ba har yanzu."
Ya gyad'a kansa yana fad'in." Yadda ba zata canza ba haka zalika kema ba za ki janza ba giwa. Na san halin kowacce a cikinku. tunda Ubangiji na ya jarrabeni daku a matsayin abokanan rayuwa dole na yi hakuri mussaman kuma da kuke ha'kuri da ni."
"To yanzu dai idan na fahimta ka goyu da bayan abinda ta yi kenan tunda na ga kamar kana kare ta."
"Ban goyu da bayanta ba Amina na nuna mata cewa tana da ikon shiga kicin dinki ko kuma ta tambayeki ba ni son kumbiya-kumbiya fa wasu lukutan daga cikin dabi'unki na burge ni domin ba ki da rufi kuma ba ki da munafurci na gane shine dalilin da ya sanya idan an yi miki hakan yake yi miki zafi."
Na janye idona daga kansa ba tare da na ce komai ba. Ya saki ajiyar zuciya yana fad'in." Kafin na shigo Sukairaju ya yi mini bayani har results din duka ya nuna mini. Na yi murna na kuma yi addu'a kwarai abinda za a yi yanzu da kaina zan tashi zuwa Kano wajan Baba domin nemo auran hakan ya yi ko?"
Na d'an saki fuskata ganin yadda ya karrama ubana har yana kiransa da Baba na ce hakan ya yi sosai Allah Ya tabbatar da alheri."
Ya amsa da Amin yana fad'in." Idan kuna da idon sanin can garin nasu Sukairaju hakkinku ne domin fad'ad'a bincike a kansa da zuriarsu domin sake gazgata abinda muke hasashe da wanda na sani a kansa."
"Gaskiya ba mu da kowa a garin wallahi, amma komai na Allah ne kuma tunda ka ba da tabbacin akansa da zuriarsu ai ba sai an sake wani binciken ba alheri dai muke ta addu'a akan Allah Ya wanzar musu damu gabad'aya.''
Ya ce." To hakan ya yi in sha Allahu rabbi cikin satin nan zan shirya zuwa Kano kuma babu buk'atar d'aukar dogon lokaci tunda dukkaninsu babu yaro a ciki."

***
To idan Ubangiji na ikonsa babu wani mahaluki da duk iko da shahararsa a duniya da ya isa ya dakatar buwayar Allah domin kuwa rahamominsa suna da yawa. Ni dai ban taba tunanin wai akwai dangantaka ta aure tsakanin Hadiza da Sukairaju ba sai yanzu da Allah ya bankad'a abinda yake rubuce a kudirarsa. Kamar yadda nake wannan tunani da mamakin itama nasan haka take cikin wannan tunanin na kasantuwar auransu da Ubangiji Allah yake shirin tabbatarwa.
Bayan zuwansa wajan Babanmu an samu nutsuwa sosai da fahimtar juna tare da amincewa daga kowane bangare domin kuwa ba su riga ma sun tsayar da maganar d'aurin auran ba sai da kawunan Sukairajun suka zo su biyu daga Zamfara aka yi zaman dasu tare da bada sheda da tabbacin cewa sun kar'ba bisa amana. A take a lokacin ya biya sadakin Hadiza bisa jagorancin kar'bar auran da ya biyo ta hannunsa. Hadiza ta yi goshi dubu dari biyar sadaki suka tsayar da ranar d'aurin aure ranar takutaha ranar da aka haifi manzon Allah s.a.w domin samun falala da dacewa.
A ranan da daddare Ummansu ta kira ni a waya godiya kamar za ta yi kuka har sai da na ji wani iri a raina na dinga tausarta domin dai kukan da ta dinga dannewa sai da ta yi shi a cikin waya da kyar muka to sallama. Na kira anti Yagana a gaban Hadizan na sanar mata da yadda aka yi itama murna kamar ta zuba ruwa a k'asa tasha. Hadiza na gefe sai murmushi take yi domin tunda na gaya mata mun yi waya da maigidan ga yadda ake ciki ta rasa yadda za ta yi da ranta saboda farinciki.
Kwanansa hud'u a kano ya dawo da daddare tare suka je da angon dama. Na tarbe shi sosai tare da yi masa bangajiya da godiya a daran kuwa ya samu tar'ba mai kyau mai tafe da sabon salo wanda bai san shi ba.
Muka shirya tafiya kano kafin zuwan ranar ni da ita da yaran duka tunda an yi musu hutun boko da islamiyya mun shirya walima domin nuna farincikinmu ga Allah anti Yagana ma tana can tana shiri domin ta ce kaf yaranta da su zata zo.
Saura kwana biyu mu tafi Hamusu ya kira ni yana gaya mini Sukairaju ya sanya shi had'a lefe akwati shida tambayata yake yi aure zai yi?"
Hadizan tana zaune a gefena a lokacin da muke yin wayar na gaya masa aure zai yi kuma Hadizar gidanmu ya kuwa shiga farinciki sosai yana ta fad'in ta samu lefe domin milayan shida ya tura ya ce a had'a lefe na kece raini kuma a shagonmu." Lamarin ya yi mini dadi sosai na juya ina kallonta tana murmushi bayan mun yi sallama da shi na dube ta kafin ma na yi magana ta furta." Kudin ya ce zai ba ni sai kawai na ce ya yi magana da Hamusu ya kuma tura masa shi zai had'a komai."
Da murmushi a tare da ni na furta." Na taya ki murna Hadizan gidanmu ta yi goshi kin zama bazawara mai kafasiti yanzu abinda ya rage muna dira kano a yi gyaran jiki sannan na kai ki gidan GARKUWAR MATA ta had'a mini ke da kyau!
Ta kuwa fashe da dariya sai ka ce wata shashasha. Na shiga taya ta sai muka zama kamar sakarkaru rayuwa kenan bayan wucewar kalubale mabambamta da 'kin jinin juna tare da 'kyama ashe akwai ranar da Hadiza za ta k'aunaci cigabana duk son kud'inta sai ta ce a a gwara a yi sayayya a wurina saboda na cigaba. Lallai bahaushe ya yi gaskiya da yake fadin ranar naka sai naka.............
'
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 3:03 PM] Hauwa Galadima: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*172*
Duk abinda ya kamaci Hadiza na gyaran jiki ni na d'auki nauyi don har tana cewa za ta gayawa angon ya bata kudin gyaran jikin na ce a a kada lalacewar ta yi yawa yadda ya fitar da kudi masu kauri domin yi mata lefe irin na budurwa mai jini a jika bai kamata a ce ya bada wasu kudin ba. Sosai na yaba masa dangane da abinda ya yi mata duk a kokarinsa na ganin ya dakusar mata da damuwa kuma da alama yadda Allah Ya jarrabeta da sonsa haka shima yake k'aunarta domin matar so ai ake yi wannan hidimar a matsayin dai Sukairaju tsayayyan namiji mai suffa da mazantaka ina da tabbacin ba zai rasa 'yan mata da suke kawo masa caffa ba. Amma shi so babu ruwansa Hadiza ya hango cikin dubbanin 'yan mata da zawarawan da suke a wannan duniya.
Anti Yagana ta riga mu zuwa domin da muka isa kanon a gidana na sharad'a muka sauka sannan gari yana wayewa muka yi gidan GARKUWAR MATA yini muka yi a tare da ita ta sabunta ni ta kuma sabunta Hadiza da ciccibi tare da dahuwar 'yan shilla aure biyu da duk wani abinda ya kamata.
Kuma Koda muka gama da ita gidana muka sake komawa sai da gari ya waye bayan mun kintsa muka nufi can gidan na mu gabad'aya ni da ita da Baba Tabawa domin tare muka zo da ita saboda yaran Mairo da Taburni suna gida Abuja muka bar su.
Gidan an yi masa sabon fenti ciki da waje har da ties a tsakargidan da d'akunansu wannan aikin Usaini ne ya gyara gidan sosai bayan wanda na yi musu ya yi musu sabbin d'inkuna Babanmu tsaf da shi cikin manyan kaya ya sake murmurewa. Sosai hankalina ya kwanta ganin yadda aka samu daidaito tsakanin matan gidan duka sun daina abinda suke yi Ummansu Saminu ta fito ana ta hidima da ita yayin da 'yan uwan Ummansu Hadiza suka cika gidan zuwa na ya sake bud'e babin gaisuwa har da rige-rige a tsakaninsu lamarin nan dai ya tabbata da ake cewa kudi suna sayan girma kuma suna kankaro mutunci. Ma'kotan gidanmu da ada suke yin surutu a kaina a duk lokacin da Ummansu Hadiza ta yi musu gulmata sai na zama abar fadanci da gurfana tamkar wata basarakiya.
Ranar da aka d'aura auran da daddare ya kira ni yana gaya mini bai tafi ba sai gobe don haka Ayuba zai zo ya d'auke ni da yaran mu kwana can gidana na sharad'a.
Na ce masa ya bari gari ya waye domin duk mun gaji har yaran su Hassan ma sun yi bacci tun d'azu. Ya ce a a mu Ayuba zai zo. Haka na kintsa ina gayawa anti Yagana yadda muka yi da shi ta ce mu tafi din kawai tunda hakan ya bukata.
Wajan tara da arba'in Ayuba ya zo ya kwashe mu a mota amma banda amaryar tukkuna dole za ta yi sallama sosai da mahaifiyarta.
Kwanciyar aure zai yi da ni a daran ashe shine dalilin da ya matsanta lallai sai mun dawo dalili matar da yake d'an ragewa da ita tana can saudia basu dawo ba shi ya gaya mini tare ya biya musu da mahaifiyarta da kuma Kawunta da ya zo ya yi musu sulhu wattanin baya. Daga lokacin na gane dalilin da ya sanya ta sassauto har take taka kyasa da k'arfi ganin ta fara samun kansa kyautar umara ya yi wa iyayenta biyu wannan kuma shine karo na biyu tsakaninta da Inna Uwanin a shekarun baya tun kafin ya kai k'arfin haka ya ba su kujerar ita da Hajja da Samira duk su hudun suka je lokacin suna soyayya kafin auransu.
Ya yi yadda yake so ban hana shi ba dalili nasan ya jure tunda kusan kwanaki biyar kenan rabon da mu had'u da safe yake gaya mini gidan da ya mallakawa Sukairaju amma ba a cikin estate din da muke ba ya d'an yi gaba da mu. Ya nuna mini shi a waya maidaidaci ne plate wanda aka yi wa ginin zamani daidai gwargwado kuma ya ja kudi sabo ne kuma na yi masa murna sosai ya kuma tabbatar mini da cewa a shirye gidan yake shiga kawai za su yi.
Yini guda muka yi da shi a d'aki yana ta maimaita abu daya don a k'alla sai da ya neme ni sau uku bayan wayewar gari da safe bayan mun karya da azuhur ya yi sallah sai kuma da yamma wanda shi ya yi bala'in gabalabaitar da ni na yi kwance a gado ina nishi wai lallai sai an samu ciki bayan shi kansa ya san yawan yin wannan abu ba shine yake bada ciki ba. K'addara ma a samu d'in amma ai ba mu da hurumin nunawa Allah abinda muke so idonsa gabad'aya ya rufe har na rasa inda tunaninsa yake har da cewa yana ganin a shekarar nan zai mutu shiyasa ya damu da ganin na sake haihuwa.
Baba Tabawa ita ta dinga hidima da yaran gabad'aya domin ban sauko ba sai bayan biyar da rabi a gajiya tubis ga gajiyar bikin Hadiza ga wadda ya tara mini
Ta yi abinci tsaf ta gama shirya ko'ina da yaran gabad'aya suna zaune a falo suna kallon cartoon Hasan na wasa a kusa da ita shi kuma Usaini na dafa kujera yana mi'kewa tsaye Sultan na ri'ke hannunsa.
Na zauna cikinsu zamana kuwa ke da wuya suka rufe ni kowa da abinda yake fad'i mussaman Minal duk ta kanainaye ni ta ko'ina.
Yana dawowa daga sallar magriba yake gaya mini rasuwar Malam D'aha a lokacin ne Malam Rabi'u abokinsa ya kira shi a waya ya sanar da shi amai da gudawa ya yi kwana daya don asibitin zana ya rasu.
Na kadu sosai da rasuwar malamin jikina ya mutu na zauna ina Kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un babu babu shakka maza sun tafi Allah Ya kar'bi ayyukan alherin da aka yi dominsa.
Da sassafe mu ka dauki hanya ni da shi domin samun ta'aziyya a daran dama na kira Usaini na ce cikin hikima ya san yadda zai sanar da Hajara domin kuwa tsohon ciki ne da ita haihuwa ko yau ko gobe ya tabbatar mini da cewa da wuri za su tafi shi da ita inshallah.
Aikuwa a can muka same su gidan Malam ya kacame unguwar ma gabad'aya motocin manyan mutane ta ko'ina da yake karkara ce akwai filaye sosai da aka samu damar ajiye motacin.
Hajja ma can muka same ta lokacin an gama shirya gawar za a fito da ita domin a sallace ta.
Sai bayan da aka d'auke shi zuwa gidan sa na gaskiya tukkuna na samu sararin bin dakunan matan gidan ina yi musu gaisuwa da yaransa mata aurarru Hajara na cikinsu sun yi kuka har sun gaji na yi musu gaisuwa sosai kafin na koma na zauna wurin da Hajja take a killace muka sake gaisuwa tare da yi wa juna ta'aziyya. Wajan biyu na rana Babanmu anti Yagana Hadiza da su Fati da Ummansu Saminu suka zo Ummansu Hadiza """"""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""""#kawai a ka bari a gidan Saminu da Ashiru duka tare suke Hajara da kanta ta dinga bi da su d'akuna suna yin ta'aziyya sannan mazan suka fita waje su kuma su anti Yagana muka zauna a tare a wuri d'aya.
Hajja can muka barta da za mu tafi ta ce ba zata iya wannan kai kawon ba sai anyi addu'ar uku tukkuna. Amma ni da shi haka muka dinga wannan kai kawon muje mu dawo har sai da aka yi addu'ar uku tukkuna. Ranar sadakar bakwai kuma shi kadai ya tafi bai ce na shirya ba sai ya dawo tukkuna yake gaya mini tare suka je da Hajja.
Kwanaki goma da rasuwar Malam D'aha muka shirya komawa abuja lokacin Hauwa ta kwana kusan shida da dawowa kira shi a waya babu adadi ya kuma gaya mata babban rashin da aka yi ba wai jin dad'i ne ya zaunar da shi ba don a ganinta tunda muna tare wata'kila ni na hana shi dawowa bayan kwanakin da ta yi a saudia ya kamata a ce ya yi d'okinta.
Ranar da muka koma kuwa a gidanta ya kwana domin hura masa wuta ta yi babu kintsi ya tafi ba cikin dad'in rai ba.
Hadiza a can muka bar ta. Sai bayan sati daya tukkuna angon ya je ya daukota kai tsaye kuma gidanta ta sauka sai da ta kwana biyu da tarewa tukkuna na je na ga gidan alhamdulillahi Hadiza ta 'yantu ta yi gida gayun nan da ake ta nema yanzu ya samu an ci ado da kwalliya irin na amare abin dai gwanin burgewa da sha'awa nan take gaya mini Ummansu ta ce bayan ta dan yi wattani sai su shirya zuwa ganin d'aki dangin babamu da danginta na ce hakan ya yi Allah Ya sanya alheri.

Kwanaki talatin da uku da rasuwar Malam D'aha Hajara ta haihu mace tun daga haihuwar aka ce mini an yi mini takwara dole haka na shirya tafiya da gudumawar kayan baby kwanaki uku kacal na yi a daddafe domin da 'kyar ma ya bari na dawo gida tunda ba taron suna aka yi ba saboda rasuwar mahaifinta. Amma alhamdulillahi ta haihu lafiya lau ita da baby suna cikin koshin lafiya yarinya kamar Usaini ya yi kaki ya tofa saboda tsananin kammani.


Na kudi ne littafin kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba.


****
Bayan wata hud'u zaman namu ni da Hauwa yana ta tafiya a waskace babu tsari sai dai zangon 'kasa da kuma bita da 'kulli tunda nake kafata bata ta'ba taka gidan Nusaiba ba wallahi don wasu lukutan har kunyarta nake ji yarinyar har ta gaji da tambayata yaushe zan zo nakan ce mata ina tafe in sha Allahu amma Hauwa ta riga ni saboda gulma tana cin ko'kon ranta kawai yarinyar ta kira ni a waya tana gaya mini wai Hauwa ta je mata ta yini har ta kai mata mayafai biyu da hijabai irin wanda ta zo da su daga makka har tana gaya mata cewa Hadiza ba tsaran auran Sukairaju ba ce dalili karuwa ce kuma 'yar kungiyar shan jini an cutar da shi kuma ta girme shi nesa ba kusa ba wataran za a wayi gari babu shi ta nemi wani sassa na jikinsa domin alamu sun nuna zaman da ta yi gidan gyaran hali bai koya mata darasi ba don haka dole za ta matsantawa maigidan ya dawo mata da yaranta saboda tana jin tsoro kada a wayi gari babu daya daga ciki mun had'a baki mun bawa dodon tsafi tunda ni kishiyartace kuma ba ni k'aunarta zan iya yin komai domin ganin bayanta da yaranta saboda ni da 'ya'yana mu gaje dukiya.
Wallahi bakina mutuwa ya yi na rasa abinda zan cewa yarinyar kaina ya yi bala'in d'aurewa wata'kila fahimtar hakan ta yi daga wajena yasa ta shiga ba ni ha'kuri tana fad'in ba ta san hankalina zai tashi ba kuma ta yi rantsuwa da Allah ba ta ta'ba gazgata maganarta ba domin ni din ma na fiye mata ita sau dubu.
Har muka yi sallama ban iya ce mata komai ba saboda mamaki lallai wannan al'amari ya daga mini hankalina ba kad'an ba. Duk wasu kaidi da sharri Hauwa ta yi mini na jure saboda dalilai masu yawan gaske amma ina ganin wannan kam ba zan iya ha'kura ba dalilin da ya sanya kenan yana shigowa ban ma bari ya huta ba saboda da abin na yini shima ganina a hargitse cikin rashin nutsuwa ya shiga hankalinsa na shiga gaya masa abinda kunne na ya ji wanda nake da tabbacin cewa yarinyar nan Nusaiba ba za ta yi mini karya ba.
Ya shiga mamaki kwarai shima jikinsa ya yi sanyi mussaman yadda ya ga hankalina ya tashi ina kuma sake jaddada masa cewa shari'a ce zata raba tsakanina da ita idan kuma bai yadda da hakan ba ya zama dole ya za'bi zama da ni ko'ita domin ba za a cigaba da tafiya a haka da ni ba ya zame mini dole na nemi mafita.
Kwanan rarrashi ya yi duk da girkinta ne sai ya kashe wayarsa ma gabad'aya domin kada ta kira shi ya rufe dakin da key ya boye shi saboda kada na fita rarrashina ya dinga yi sosai lamarin na sa'barsa shi kansa yanzu yadda yake nunawa lamarin Hauwa ya kai shi ma'kura akwai dalilan da ya sanya yake daga mata kafa wanda ni ma su nake duba mussaman yaranta Khalil dai biyayyar da yake yi mini kwatankwancinta ba ta samu ba ga Minal da take jarabar kulafucina uwa uba kuma ina duba Hajja domin duk lalacewarta tata ce idan na yi tutsu abubuwa da yawa marasa dad'i za su faru wanda za su sanya kunci da zubar hawaye a idanuwan yaran.
Wallahi kwana cur ba mu rintsa ba har sai da ya karya mini lagona

Please Login or Register in order to submit comment