Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zo."
A sanyaye ta furta." Amma lafiya dai ko?"
Ne ce." Baba Tabawa akan maganar 'barin cikin da na yi ne, shine ya kira shi ya gaya masa don yana zargin zubarwa na yi da gangan.
Sai ta shiga girgiza kanta gabad'aya yanayinta ya nuna alamun damuwa da fargaba ta ce." Haka kawai kuma sai ki zubar da ciki Amina, ai kuna da ilimin addini daidai gwargwado wad'anda ma suke yin sakarcinsu a waje su samu ciki ba su zubar ba sai na sunnah, amma ban ji dadin wannan zargin ba.

Ban ce mata komai ba domin duk bayanin da zan yi mata akan mutumin nan ba zata gane ba. Idan na ce mata shekarun baya na ta'ba yun'kurin zubarwa za ta fara wasu tunanuka marasa kyau akaina kuma bai zama lallai ta fahimci nufina ba tunda ita ai mutuniyar da ce. Akwai tauhidi tare da k'adaita Allah. Shi kam ai ko zan kwana ina rantsuwa ce wa zubewa ya yi babu wata hujja da rantsuwar da zan yi masa ya yarda kan cewa ba hada ba ki muka yi da Hauwa ba.
Hijab na zura a jikina mai fuska har kasa muka fito tare da ita tana ta jadadda maganar har zuwa lokacin Hauwa ba ta fito ba..
Kai tsaye hanyar fita na nufa ita kuma ta nufi kicin babu karsashi da kuzari a tare da ita.

Wuri ne k'ebantace ya ware a gidan domin ganawa da manyan bakinsa na mussaman. Gabad'aya wajen ya fi ko'ina kyau da tsaruwa a gidan. Masu hidima da aikin wajan su kansu na daban ne. Yadda ya sau'ki Baban Saude a sashen ya tabbatar mini da ce wa bai ajiye shi a nesa ba, suna tare domin tun bayan sulhunmu na farko na fara fahimtar abota mai karfi ta shiga tsakaninsu.
Ina dosa kofar da zan shiga falon escort dinshi Sukajiru da Emanuel 'Dahuru sune dai amintattun nasa da basa rabo dashi mussaman ma Sukairaju da duk inda zai tafi tare suke tafiya, bayan wasu jami'ai guda uku da naga ba sa rabo da shi.
ina isa suka fara gaisheni na amsa sama-sama kafin da sauri Sukairaju ya bud'e mini k'ofar na shiga a nutse.
Suna zaune a kujera d'aya hira suke yi cikin faraa da barkwanci tsakiyarsu Loptop ce ta maigidan da alama akwai abinda yake nuna masa a ciki. Center tablet din da yake tsakiyarsu kuwa sha'ke yake da manyan kuloli akwai tazara sosai tsakanina da inda suke tunda girman falon ya shahara sosai. Kafin na kàrasa gabad'aya gwiwata ta sage saboda ban san irin tozarcin da Baban Saude zai yi mini a gaban mutumin nan ba

Cikin nutsuwa na isa wajan da suke zaune na d'an rangwafa kusa dashi kafin na bude baki a nutse na ce." Baban Saude sannu da hanya, fatan duk mutan gidan suna nan lafiya ya su Dada da sauran 'yan uwa."
Ya fuskanceni sosai yana dubana da wani irin yanayin da na kasa tantance shi. Ya ce." Kowa lafiya lau Amina, Dada tana gaisheki ai dana gaya mata cewa zan zo nan wurinki har ta sanya mini rigima wai sai ta biyo ni da k'yar na zame na gudo ba ta sani ba.
Murmushi na yi wanda babu nisha'di ko na miskala zarratin cikin dusheshiyar muryarta da ta ga ji da kuka na ce." Dada kenan ai ba ta ta'ba zuwa ta ga inda nake zaune ba."
Ya sake fuskantata sosai yana fad'in." Tabbas hakane amma ai tana samun labarai a kanki masu dad'i da akasin haka."
Shiru na yi tare da yin kasa da kaina gefe guda Ina ta nazarin manyan mazuban abinci masu daukawar hankali dake jere a saman center tablet din da yake daf da su.
Cikin zuciya na dinga tunanin akan haka. Akwai masu yi masa hidima nau'i daban-daban domin sai na ce duk tsayin zama da shi wasu daga cikin yaransa ma ban san su sosai ba. Amma dai zuciyata ta fi aminta da cewa wannan aikin ba na kowa ba ne face na matarsa da ya rataya fulawar so da k'auna irin ta indiyawa. Momi ce ta yi masa wannan hidimar domin fitar da shi kunya. Ko kad'an hakan bai burge ni ba duk da cewa ta yi ne bisa bin umarinsa amma sai nake zargin babu abinda bai gaya mata ba na abinda ya shafi tsakaninmu da shi. Na sake jin wani irin nauyi da kunci a cikin raina, gabad'aya sabgar mutumin nan ta fice mini daga rai domin kuwa kansa kadai ya sani bai da adalci ko kad'an.

"Ina ita abokiyar zaman naki ai tare nake so na zauna da ku domin tattauna masla'ar da ta kawo gidanki Amina."
Wannan maganar ita ta datse tunanin da na lula na daga kaina cikin kasala da zullumi amma abin da ya ba ni mamaki bai wuce ganin idanuwan maigidan a kaina ba gabad'aya ma hankalinshi na kan 'kafafuna. Har cikin raina kallon ya ta'ba ni domin irin na mutukar 'kurrula ne, nan da nan na fahimci abinda ya assasa hakan bai wuce lallen da ya fito ya zanu radau a kafafuna ba. Da sauri na gyara zaman da na yi na mayar dashi zaman rakuma kafafun suka koma can baya ganin haka ya sanya shi da sauri ya janye idonsa tunda ya fahimci na gan shi sai ya cigaba da duba Loptop din dake gabansa bai ce mana komai ba yana jin Baban Saude yana tambaya Hauwa na kasa ba shi amsa domin kuwa ba na so ko da wasa sunanta ya fito a cikin sha'anina. Hauwa ba ta da wani lefi magani ta ba ni a amtsayinta na ma'aikaciyar lafiya bai yiwuwa saboda yana jin haushinta ya jingina mata lefin da ba ta da hurumi a ciki.

Ya sake maimaita tambayarsa. Sai kawai na rushe da kuka mai tafe da gunji na ce." Baban Saude ita Hauwa ina ruwanta, tsautsayi ne kawai ya faru a matsayinta na ma'aikaciyar lafiya ta bada gudummuwarta amma a ganina bata da lefi a cikin wannan maganar.
Shiru ya yi kawai yana kallona cike da mamakin ganin irin kukan da nake sharba kuma mai tafe da jan majina da shashsheka. Yanayinsa ya d'an nuna sanyi da sasaauci, ganin haka ya sanya na cigaba da rerawa da babban sauti Ina yi ina jan hanci. Wajan in banda sautin kukana babu abinda yake tashi. Baban Saude kawai ya zuba mini ido, shi kuma wanda ya assasa zaman kansa yana dukufe a computr kanzil bai ce mana ba.

Littafin gudun aure na kudi ne kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba sister.

Ya d'an sauke ajiyar zuciya cikin kulawa da da tausayi irin na iyaye a cikin idonsa ya ce. "Amina
ashe kenan ba ni da hurumi ko ban kai abokiyar zamanki ta taso ta gaishe ni ba kenan Amina, ai ni tambayarki ita kawai na yi na ce da ke ina take ai ita din ma 'yata ce kamar ke din ko ba haka ba ne."
Na gyada kaina tare da sanya hannu na ja hanci cikin reshin kuka na ce." To Baban Saude ai ban san me ya gaya maka game da mu ba. Shine dalilin da ya sanya ka ji na ce haka, idan har ba zai iya yadda da kaddara da abinda Allah Ya shiryo ba ai bai kamata ya na hada ni dak.....Ban kàrasa ba ya buga hannun kujerar da yake zauna ya furta." Me ki ka ji na ce miki Amina, wato a gabana din ma kaifin harshe za ki yi, idan shi kin raina shi saboda kuna kwanciya a shimfida da d'aya ai ni ya wuce a ce ki yi mini jayayya bisa umarnina, shin wai ko kin manta wanene a gabanki ne, kuma ai ba mu zauna an ji ta bakin kowa ba tukkuna kada ki 'bata mini rai Amina."
Shiru na yi gabana na bugawa da karfi da karfi, don sasasucin dana hanga a fuskarsa ya 'bace bat ya dawo asalin baban Saude mafada ci.
"Idan na isa ki tashi ki je ki kira wo mini ita."
Ya fad'a cikin sigar bada umarni.
Ban ce komai ba na tashi na kama hanyar fita k'afafuna kamar an doke mini da ta'barya. Allah Ya yi wa Baban Saude wani irin kwarjina da haiba da wata baiwa wadda idan ya yi magana ko babu fad'a a ciki sai mutum ya nutsu. Yanayinsu daya da jarumin film din nan na Hausa (Tahir fagge)
Ina shiga d'akin na sameta ta yi wanka tana cin indomin da Baba ta dafa mata
Ganin yadda na shigo ya sanya ta tsira mini ido har na isa wurin da take zaune. Kafin na furta komai ta riga ni ta hanyar fad'in." Lafiya na ga idonki a kumbure ko mutuwa aka yi ne ban sani ba ina ta baccin asara.''
Na girgiza kaina tare da fad'in." Babu wanda ya mutu Hauwa mijinki ne ya kai 'kararmu wurin Baban Saude."
Ta yi shiru tana maimata sunan baban Saude kafin ta furta." Oh Yayan Mamanku na maiduri ko?"
Na ce." Shi fa, bai jima da sauka ba, yana can sashensa na baki ya ce na kira wo ki muje tare.
Karamin tsaki ta ja kafin ta ce." To akan me Amina ba ki gaya masa cewa zaman idda nake yi ba babu igiyar aure a tsakaninmu, akan me kuma zai sanya ni a cikin abinda ya shafe ku."

"Saboda yana zargin mun had'a baki tare mun zubar masa da ciki. Hauwa musabbabi akan 'barin da na yi kwanaki bai yarda zubewa ya yi da tsautsayi ba. Ga ni yake yi zubar da shi na yi ina sane."
Ta dube ni da mamaki kafin ta ce." To shine me, ai ina ganin ni ba ni da hurumi anan Amina, wallahi kwata-kwata ma ni fa ba na jin dad'in jikina don Allah kada ku sanya ni cikin wannan cakwakiyartaku."
Na ce." Na sani Hauwa, ki ta so dai mu je don Allah idan ya so ni zan gayawa Baban Saude ba ki da lefi, kada ki ce ba za ki je ba, wannan zai sake tabbatar musu da cewa babu gaskiya a tare da mu."
Jim ta yi na sakkoni kafin ta ce."shikkenan mu je to." Ta ajiye plate din indomin wanda dama saura karashe kad'an ta d'auki ruwa ta kurba sannan ta tashi ina tsaye ina kallonta ta d'auko hijabin dake ta salla ta zura sannan ta dube ni. Ban furta komai ba na juya da niyyar fita ta rufo mini baya.
A ka ci sa'a kuwa baba Tabawa ba ta fito ba tana d'akinta.....
'þ
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/3, 8:38 PM] matar mijinta: <Ø2ß<Ø3ß<Ø?ß&þ
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*

A LURA DA WANNAN.
Idan har kina da niyyar biyana hakkina kudin karatu kawai za ki biya kada ki ce mini kina son book3 ko book4 ni dai book1 kadai na bayar a matsayin free peges ba ni na hada doc din 2 3 ba. Ga Details dina nan a sama kisa kudin ki yi karatu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali Allah Ya tsarkake mana zuk'ata ya hane mu tad'e kafafun junanmu ya hana mu dakushe nasarar junanmu. Allah Ya bawa kowa a hannunsa. Allah Ya taimaka mana neman na kanmu ina kara fad'i wannan littafi na kudi ne ki biya mai hakki hakkinta kafin ki karantà. Na gode.

*Wannan littafin na kudi ne vip 1k akan telegram. Normal What'sapp group kuma #700 hanyar da za a biya kudin ita ce wannan...0542382124...Binta Umar gtbank ko kuma 7084653262...Binta Umar Opey bank. 'Yan nijar dala dari katin airtel za ku tura mini bayan kun kankare hoton. A tura da sheda ta wannan lambobin iya What'sapp kawai.*
*07084653262*
*08089965176*
*V-VIP AREWA PEN=ØNÜ*
*98*
Yana cin abinci a lokacin da muka shiga. Cima ce iri iri da snakes tabbacin an shirya sune domin shi akwai wad'anda ma bai bud'e ba suna cikin wamars
Wanda dai yake gabansa farfesu kayan cikin rago ne ya yi kyau sosai da katon bread yana dangwala gefe kuma black tea ne babu madara tunda dama tun asali sanin da na yi masa ba ya shan madara da zuma sai idan ya zama dole, amma ko zaman da na yi a gidansa haka yaransa suke sayo mana madara ta gwangwani duk ranar da suka yi shayi kowa da tasa amma shi haka wadda take da girki zata d'auki tsurar fulas dinsa daban da ba'kin shayinsa a ciki ta kai masa dakinsa.
Cike da nutsuwa Hauwa ta gaishe shi ma ya amsa da kulawa. Wurin ya d'auki shiru tun bayan gaisuwar da suka yi. Sai da ya kammala tukkuna a nutse ya goge bakinsa da tissue ya dube mu gabad'aya kafin ya furta." Hauwa da gaske ke ce ki ka tura Masa'udu direbanku ya sayowa Amina maganin wankin mahaifa?"
Ta dube shi a tsanake ta furta." E, ni ce Baban Saude."
Da d'an mamaki a tare da shi ya ce." Kenan da gaske hade baki ku ka yi ba kwa tsoron Allah dama?"
Murmushin takaici ta yi kafin ta furta.'' Ko daya Baban Saude kaddara ce ta gifta wani lamari mai rikitarwa ya faru a gidan nan gabad'aya muka shiga cikin gigita, to wannan ya assasawa Amina abortion bisa tsautsayi cikinta ya zube . Ganin yadda ya fice ba tare da an samu wata tangarda ba ya sanya na rubuta magani jikin takarda na sanya aka sayo mata domin ya k'ara taimaka mata wurin wanko abinda ya rage a mahaifarta?
Ya ce." A lokacin mai yasa kafin ki yanke hukuncin yin hakan ba ki yi yun'kurin sanar da mijinku ba, ko ko cikin bashi da uba ne?"
Shiru ta yi ta kasa cewa komai sai da ya sake maimaita maganarsa tukkuna ta ce." Wallahi ban san abinda yake tsakaninsu ba domin kuwa na d'auka ita Aminar ta gaya masa shine dalili kuma dai ni kaina ba magana yake yi mini ba a lokacin gaba yake yi da ni."
"Shine dalilin da ya sanya ki kenan yin gaban kanki a matsayinki na ma'aikaciyar lafiya ai kin fi karfin ki yi masa magana dalili yana fushi dake, kamar doka ce babba a kowane asibiti sai da amincewa da sanya hannun mai ruwa da tsaki, ina nufin wanda yake da hurumi akan abu, akan wane dalili zai amince cewa da gaske k'addara ce ba shirya zubarwa kuka yi a tare ba?"
Ta fashe da kuka tana ce wa." To ni dai Allah ne shaidata Baban Saude ni ma cikin ne fa da ni, a ganina kafin na bada goyon bayan wata ta zubar da nata ai ni zan yi yun'kurin zubar da nawa dalilin abinda ya ratsa tsakanina da shi, ai gashinan a zaune yana ji ni ba matarsa ba ce yanzu domin ya sake ni."
Baban Saude ya dube shi da saurin gaske domin maganar Hauwa ta karshe ta kidima shi.
Bai ce komai ba still hankalina na kan computer dake gabansa kuma bai dago ya dubi Baban Sauden ba..
Sai ya juyo gare mu yana fad'in." Ban san da haka ba Hauwa, kuma ni nan ban titsiyeki domin naga iya gudun ruwanki ba. Abinda ya sanya ita Amina muke zarginta da aikatawaa saboda ta ta'ba yun'kurin yin hakan a shekarun baya, abinda ku ka yi ba daidai ba ne, mai yasa a lokacin da za ki aika Masa'udu ya sayu maganin ba ki kira shi kin sanar da shi ba a matsayinsa na jagoranku kuma wanda yake da hakki a kan cikin."
Shiru ta yi ba ta ce komai ba.
Sai ya cigaba da cewa."
ko ni nan babu wata mace da za ta yi mini haka na amince da gaskiyarta. Sannan ya sanar da ni cewa kun had'a kai kun ware d'ayar mutuniyar kirkin cikinku, ai duk macen da mijinta zai zauna ya dinga yabo tare da fad'in kirkinta ita ta amsa sunan mace ba irinku 'yan amshin shata ba, to me ta yi muku, mutuwa ce fa ta raba tsakaninta da mijinta mai rasuwa Alhaji Amadu, kuma ya barwa Amininsa wasiyya akan ya aureta domin cigaba da kula da ita da yaranta. Ban ga matar nan ido da ido ba, amma zaman nan da na yi kaf alheri da kyautatawarta mijinta yake gaya mini, ni ma gashi na ga ni yadda ta sauke ni da hidima daban daban tamkar wani basarake. Ba ku ji kunya ba Hauwa, ita fa macen da ta fi biyayya ga miji itace sarauniyarsa wannan matar ta dame ku ta shanyeku a komai sannan kun yi sake wanda kuke jin haushinta dominsa ya fi sonta kun hade mata kai shi kuma ya had'e kai da ita, ina kara gaya muku kun cika shashasha!"
Tsit! wurin ya dauka bayan yin shirunsa, zuciyata ban da dokawa babu abinda take yi wannan wane irin cin mutunci ne da cin fuska Baban Saude ya shirya yi mini. Menene lefin Hauwa anan da za a sanyata a gaba da cin zarafi haka. Shikkenan a rayuwa mutam ba zai yi kuskure ba.
Wasu hawaye masu d'umi da yaji suka fara simiyowa suna bin kumatuna. Wannan karon hawayen ne kawai suke fita masu zafi da ciwo babu damar yin gunji sai dai ciwon zuciya.
Ya d'auki kofin shayinsa ya kurba kafin ya cigaba da ce wa." Gaskiya ku gyara domin kuwa babu wata gadara da za ku yi a karkashin ikon namiji, mijinku gashi nan yana ji ko shine ya yi ba daidai babu ruwana zan titsiye shi na gaya masa gaskiya ko ta yi masa dadi ko ta yi masa zafi wannan shine zaman tare Alhaji Tajo ba surukina ba ne a yanzu abokina ne, mun yi sha'kuwa ta ban mamaki a sha'aninsa zan yi tsalle na dire a ciki koda kuwa bai shafi Amina ba. kuma za ki koma dakinki Hauwa kin ji ko?"
Tana kuka ta ce." A, a Baban Saude ni kam na ha'kura gaskiya wallahi zuciyata ba za ta iya d'auka ba."
Baban Saude ya yi shiru yana kallonta da mamaki kafin ya ce."Zuciyarki ba za ta iya d'aukar me ba?"
Kafin ta furta wani abu ya rigata ta hanyar fad'in." Ka ji abinda na ke gaya maka ko, gabad'ayansu fa Maryam ta tsone musu idan ba haka ba menene na fad'in wannan maganar, zuciyarta ba za ta iya d'aukar ganin Ina tare da Maryam ba, idan har ina son zama da ita amsar kawai na saki Maryam sai zuciyarta ta d'auka."

Yana ajiye maganarsa na ce. "Baban Saude gabad'aya maganar ba haka take ba zahirin gaskiya bai gaya maka wasu abubuwan da suke faruwa ba. Wanda ya zama lallai ace an zauna a kansu. Wallahi ba mu ware Hajiya Maryam ba illa iyaka shi da ya fifita a kanmu, gashi nan a zaune idan har na yi masa sharri to ni Amina ina ro'kon Allah Ya d'auki raina a yanzu wallahi tallahi zalitarmu yake yi." Na kai karshen maganar muryarta na rawa.
Ya nisa kafin ya ce." Ai dama shari'a ta aure ba za a ce mutum d'aya ne yake da laifi dole ta kowanne b'angare a samu abin fad'a, kuma dama ni ba ni da niyyar rufe wannan mas'alar ba tare dana tambayi kowaccenku ba,
ni babban abinda ya ba ni haushi daku shine yadda kuka had'ewa abokiyar zamanku kai kuka ware ta sannan da ki ka san cikin ya zube mai yasa ba ki gaya masa ba har sai da aka ja lokaci dole ya d'ora alamar tambaya a kanku."
Hauwa tana kuka ta ce." Dukan mu fa yake yi akan ita Hajiya Maryam din a gaban mai'aikinmu Baba Tabawa ko ita sheda ce ya dinga marina ya tunkud'e ni da karfi na fadi har sai da na yi targad'e a hannuna duk da hakan bai ishe shi ya sake ni."
Ta dinga kuka da iyakacin karfinta! Baban Saude jikinsa ya yi sanyi ya dinga maimaita kalmar duka yana kallonsa shi kuma jikinsa duk ya mutu don da alama bai tsammaci faruwar hakan ba.
Baban Saude ya dube ni yana fad'in." Kenan kema sheda ce Amina?"
Na gyada kaina tare da fad'in." I, wallahi ni na shiga tsakaninsu ma." Na fad'a a dan tsorace dalili ina jin tsoron allura ta tono garma ya gaya masa na ta'ba toshe masa hanci da fillo.
Ya ce."To akan me, Allah ya taimakeka dama akwai duka mai illatarwa a cikin shara'din aure kuma mace mai d'auke da yaron ciki, anya akwai imani a nan?"
Fuskarsa ta had'e sosai yana kallonsa da mamaki.
Sai ya kasa daga kansa ya dube shi cikin kame-kame ya ce." Baban Saude yaran nan ba su da kirki ko kad'an ni kuma ban yi mata dukan da zai illatata ba."
Cikin 'yar 'kure baban Saude ya ce." To wane iri ka yi mata?"
Ya furta." Marinta na yi?"
Ya ce." To ai mari karshen tozarci kenan a mari mutum a fuska yanzu tsakani da Allah ko tunkiya ka daure a gidanka ka mare ta, ina lefin ma gabar da kake yi da su duk da itama a shari'a haramun ce, anya kuwa ranka shi dad'e ka shirya sulhunta gidanka kuwa?"
Shiru ya yi bai ce masa komai ba.
Sai ya juyo kaina yana fad'in." Sai me kuma?"
Na ce." Magana ce akan yaranmu da ya kwashe ya kai wa matar tasa, to wannan ma yana daya daga cikin abinda yake mana ciwo koyaushe idan mun yi magana sai ya nuna kamar ya fi mu iko a kansu yana kiranmu da marasa tarbiya komai muka yi ba mu iya ba."
Ya dinga jijjiga kansa kafin ya sake dubansa a karo na kusan hud'u kansa yana kasa bai dago ba tsabar kunya ta hana shi musantawa yadda na lura yana tsoron ya tanka mu sake 'baro wata wata maganar da za ta zama abar tattaunawa tare da nuna masa kuskuransa.
Baban Saude ya ce." Idan kuwa hakane ka takewa yaran nan hakkinsu Alhaji Tajo kasan tsananin so da k'auna da sha'kuwar dake tsakanin uwa da d'anta kuwa? me yasa ka d'auki ga'barar raba sha'kuwa iyaye da 'ya'yansu. Mai yasa ka fifita Maryam a kan su? Idan har gaskiya ne abinda suka fad'a tabbas akwai zama tsakani na dakai na mussaman ko ba mu yi yanzu ba za mu anan gaba wannan ba daidai ba ne bari na gaya maka, ai ka haihu to muddin kana so 'ya'yanka mata su rayu cikin mutunci da kulawa a gidan mazajensu to kada ka zalinci 'ya'yan wasu tare da biyewa son zuciya. Maganar nan fa gaskiya ce da

Please Login or Register in order to submit comment