Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a cikin kwana biyu da izinin Allah*
*Ni Badiat Ibrahim Mrs Bukhari awar Sabuwan maigogul, Aminiyar Iyabo, uwar Wakin Tani Shanono na gwada na san amfaninshi, kema ar uwa ki kwada zaki bani labari siyan nagari maida kuWi gida.*
*Mun sani yanzu yana da kyau duk abinda zamu siya musan ingancinshi da nagartarshi bawai muita siyan magungunan mata kara zube ba.*
*Wannan kamfanin kayansu babu algus ko almundahana a ciki, da tsoron Allah da warewa gami da gogewa ta sanin* *yadda ake sarrafa magunguna suke aikinsu, cikin nagarta da gangariyar tsabta.*
*Abu mafi sha'awa komai a cikin kwali yake a rufe kirib*
*ga kaWan daga cikin abubuwan da kamfanin yake samarwa*=G<
*Tsumin dadi har Madiga tareda gunbarshi*
*Tsumin no excuse melaabin bita zaizai*
*Gumbar dare daya wanka goma, dana gari da zumarta da tsuminta duk muna dashi*
*Zumar hana bacci gumbarta da garinta*
*Munada Arabian sabaya tare d Sudanese sabaya*
*Da zumarta*
*Sabaya ce dake cuko da a mace duk ramarta, da anjamewarta*
*Itama da zumarta*
*muna da mummuna da aiki*
*Akwai tsumi da gumbar ta da zaune tsaye*
*muna da kogin daWi*
*Abangaren sanyi sun samar ma mata maganin matsolilinsu*
*muna da fitattun maganin sanyin da yake fata_fata d sanyi yayi mishi korar kare*
*Khanzur Rahman herbal formular*
*Sanyi clear syrup*
*7 days for chronic infections flusher*
*Sannan kuma muna da* *Package amarya*
*Package Uwargida*
*Package irin na zawarawan da suke shirin sabon aure*
*Bugu da ari wannan kamfani yana sarrafa magungunan maza ba a iya na mata ya tsaya ba, wannan kamfani magungunan da yake samarwa suna da yawa wannan tsakurene daga cikin kayansu*
*Da sauransu da sauransu wanda bamu ambata ba.*
*Ba fa a iya haka muka tsaya ba muna d cancada cancadan zannuwan Gado da carpet*
*Domin neman arin bayani ku tuntuSeta a kan lambar wayarta kai tsaye*
+2348032089456


*36*
Ta 'bata rai tana ce wa." Matsalata dake taurin kai Amina, kishiyarki wallahi ba a zaune suke ba, babban burinsu ki fice ki bar gidan, kin ga idan ba ki ba ni goyon baya ba sai na yi asarar kudina dubu arba'in na fitar aka ba ni turaran nan da kuma wannan rubutun."
Na cika da mamakin jin kudin da ta bayar har dubu arba'in lallai anti Yagana ta d'auki lamarin nan da girma, ai idan dan ta ni ce wallahi ba wani yawon neman taimako da zan yi a ci kudina a banza. Na tabbata anti Yagana bata ta'ba zuwa wurin wani malami ba sai akan matsalata hakan ne ya sanya na amince zan yi amfani da maganin amma da sharad'in ko da bai kira ba to ba zata kira shi ba domin ta ce mini malamin ya ce idan bai kira ba to sai a kira shi.
Ta amince da abinda na ce ni kuma na kar'bi rubutun da turaran a take a lokacin na fasa daya nasha ba tare da yakini ba.
Da kanta ta je ta hura wuta ta ruru sosai ta shigo da garwashin da yawa a cikin kasko irin na kasa ni dai kallonta kawai nake yi ina mamakin yadda ta d'auki al'amarin.
D'aki ta nufa da rushin wutar kafin ta kwalo mini kira na tashi na je na sameta tana kwance ledar turaran, ta ce." Sai kin cire kayan jikinki tsaf sai ki rufa da wannan zanin, amma idan kin zuba turaran akan wutar sai ki dinga yi kina kiran sunansa.
Fashewa na yi da dariya na fadi saman gado ina kyakyatawa domin duk yadda na kai ga son ganin na danne dariyar kasawa na yi.
Ta yi kasa'ke da ledar maganin a hannunta tana hararata. Ni kuwa Ina dariyar na ce." Wallahi anti Yagana dariya kike ba ni, wani irin turare ne wannan da har sai na yi tum'bur haihuwar uwata, na rantse da Allah malaman nan suna nema su jefa mata a masifa."
Ta sha kunu tana cewa." Kina d'auka abin nan da wasa ko Amina, nema ma ki ke yi ki mayar da ni mahaukaciya saboda baki da mutunci ko ina tsaye akanki amma ki sanya ni a gaba kina yi mini dariya ba za ki fahimci abinda nake nusasheki ba sai ranar da ma'kiya suka kai ki 'kasa tukkuna."
Ganin yadda ranta ya 'baci ya sanya na tashi zaune sosai na kar'bi ledar da turaran yake daure Ina fad'in." Zan yi yadda ki ke so anti Yagana"
Shiru ta yi mini tana cigaba da wurgo mini harara. Babu yadda na iya da ita haka na tashi na fara cire kayan jikina, ya rage daga ni sai rigar mama tana tsaye tana kallona na dubeta tare da cewa." Ko suma din na cire su?"
Ta girgiza kai." Ki bar su kawai ai."
Ban sake cewa komai ba na zuba turaran akan wutar lokaci guda hayakin mai kauri ya tashi na yi sauri na rufa zanin ajikina na dukufa kan wutar ita kuma da sauri ta kama hanyar fita tana fad'in." Kada ki manta ki dinga ambaton sunansa fa."
Na ce." To shikkenan."
Ina jin karar jan kofarta na cillar da zanin na tashi daga kan wutar na matsa gefe ina haki da tari ya sarke ni.
Hayakin ya cigaba da bin iska ina gefe guda. Na ji motsin bude kofarta a guje na d'auki zanin na je na dukufa kan wutar ta leko tana cewa." To kin ga haka ai ya fi, kin shaki hayakin sosai, in sha Allahu da izinin Allah zai kira waya yau din nan sai a daidaita, malamin ma cewa ya yi hakuri zai bayar."
A zuciyata na ce.'' Anti Yagana da tun farko kin k'adaita Allah ba za ki nufi wajan wani malami ba, suma duk hasashe suke yi.
To haka muka yini muna tattauna sha'anin Hadiza da abinda ta aikata, ni ma yanzu na dawo daga rakiyar Ummansu domin ta zama bakin ganga na yarda itace take dorata a gwadabe mara kyau amma duk lokacin da zata kira ni a waya nuna mini take yi itama Hadizan tafi k'arfinta ha'kuri take da halinta a zahiri kenan amma a bad'ini bakinsu d'aya. Na riga na gama fahimtar cewa Hadiza da ni take gasa tun daga kan mutuwar aurena kawowa yanzu burinta itama ta tara arziki har ta kere mini.
Tun bayan sallar Isha'i na lura da anti Yagana jikinta ya yi sanyi duk wani abu da take yi babu kuzari domin abincin dare ma ni na yi mana towon samovita miyar ku'bewa tun yamma take ce mini jikinta yana ciwo dalilin da ya sanya kenan tasha Panadol ta kwanta amma dai karin kasalarta yana da ala'ka da dakon kiran wayar Alhaji Tajo domin yadda na fahimta ta gama aminta da abinda malaminta ya gaya mata.
Muna d'an ta'ba hira sama-sama Babandi ya zo, bai samu wata tar'ba ta arziki ba a wajan matar gidan anti Yagana kenan, ni kaina daurewa kawai na yi nake tanka masa amma duk da haka babu cikakkiyar sakewa kamar yadda muka saba, ina jin hakan da ya fahimta ne ya sanya shi yi mana sallama ba tare da ya shirya tafiyar ba domin idan dai za mu had'u muka shafe sama da awa biyar muna hira ba tare da gajiya ba, yanzu kam ko minti talatin bai yi ba ya kama hanya ya tafi ba karsashi a tare dashi.
Anti Yagana ta rakashi da tsaki da harara duk ina kallonta ban ce mata komai ba.
goma da wani abu Babansu Fadila ya shigo ita lokacin ta shiga d'aki tana kintsawa.
Ya tsaya a falon muna dan ta'ba hira da yake akwai sabo a tsakanimu dukda wani sa'in idan na zo garin har na kare kwanakina bai fi sau biyu muke had'uwa dalili shi din babban direba ne kuma yana da muk'ami a tashar da suke ajiye motocinsu da asuba yake fita sai dare yake dawowa kamar i yanzu.
Ya tsaya yana tsokanata da fad'in." Ranki ya dad'e ina kamun 'kafa fa, a cewa maigidan a irin wad'annan motocin nasa muna neman koda guda d'aya ce wadda za mu dinga lodi daga nan kudu, idan haya ake bayarwa a taimaka a ba mu, idan kuma za a ba mu ne sojan haya zuwa shekara biyu in sha Allahu sai mu mayar da kudin, dama tuntuni nake so na samu dama na bi ta karkashinki, kwanaki an ce mana ya rabawa direbobi biyar kuma uku daga ciki ma an ce kyauta ya basu ba mutum biyu ya kar'ba."

Tsakaninsa da Allah yake gaya mini babu wasa a cikin maganar. Ganin haka ya sanya ni ma na shiga nutsuwata na ce." Aikuwa ban san kana buk'ata ba wallahi tabbas watannin baya na ji yana maganar da wad'anda Allah Ya sa suna da rabo, amma in sha Allahu kuwa zan yi masa maganar idan na koma duk yadda muka yi dashi sai na sanar da kai."
Da farinciki mai yawa ya fara godiya har da kirari kamar wani maroki na dinga dariya ina zolayarsa da cewa sharad'in idan na yi masa hanya ya samu babu shi ba kara aure fad'i yake yi." Na yarda ai tuntuni na gaya mini Yagana ta rufe kofar kece ba ki yarda ba."

Dariya kawai na yi domin nasan yana fad'a ne kawai amma ba har zuciya ba, babu wani namiji da zai so ya rayu ya mutu da mace daya yawancinsu suna ha'kura ne saboda wasu dalilai amma an riga an hallicesu da son mata wannan a jininsu yake akwai ma mazan da suke da tarangahuma sun yarda su tara matan duk abinda ma zai faru sai dai ya faru. To wad'annan sune za mu kira da masu rashin tsinkaye da hangen nesa.

Ki biyaa ni hakkina kafin ki karanta mini littafi yar uwa akwai hakkina akan ki domin littafin nan na kudi ne.

gajiya na yi da tunani na tashi na je na kwanta wanda bacci da k'yar ya d'auke ni. Misalin shida da rabi wayar Hamusu ta tashe ni daga b'ingirewar da na yi bayan sallar asubahi
Muka gaisa sosai dalili mun kwana biyu ba mu gaisa ba kamar yasan maigidan yana adawa da hakan a tsukin ya rage kira na a waya sai dai ya turo mini da voice note ta whasap. Ni ma sai na fi jin dadin hakan. Nan yake gaya mini Gwaggo ce bata da lafiya dalilin da ya sanya ya kira ni domin jikin nata ya fara tsanani.
Cikin kankanin lokaci na ji hawaye ya cika kwarmin idona. Gabad'aya sai na diririce hankalina ya tashi sosai, na ce." Hamusu ina nan maiduguri na zo bikin yaran d'an'uwan Dada, ita Gwaggwon za ta san shi tunda tare suka taso. Amma zan yi kokarin d'auko hanya gobe yadda kake fad'in jikin nata hankalina ya tashi sosai wallahi, ina fatan kun kai ta asibiti.
Ya ce." Kiran da na yi miki kenan, domin babban asibiti nake so mu kaita su bata gado sugar ne da hawan jini, mun je asibitin murtala likita ya dubata ya rubuto magani an Siya kwana biyu an samu sau'ki wallahi jiya kuma sai ta tashi bata iya motsa komai a jikinta, kuma ba damar na yi amfani da kudinki ban gaya miki ba "
Raina ne ya baci jin abinda yake fada. Na ce." Hamusu wannan wace irin magana ce, ashe akwai ranar da za ka iya nuna mini cewa Gwaggwo ba ta haife ni ba, kudin nawa wanene yake juya mini Ina ce kaine jigo har sai ka tambaye don za ka kai Gwaggwo asibiti wallahi baka taba ba ni haushi ba irin yau."
Ya ce." Ki yi hakuri anti Amina ta wani gefan fa Ina da gaskiya, kudi suna iya shiga tsakanin kowa shiyasa sanarwar take da amfani."
Na ce." Ka ga malam maganar ta isheni haka don Allah, ka je daga dubu daya zuwa dubu dari biyar har abinda ya yi sama na amince muddin akan gwaggo ne. Sai ya fara godiya ban jira na saurari sauran maganar ba na datse kiran na fita falo.
Anti Yagana tana kicin tana aikin karin kummalo Fadila tana taimaka mata
Yusi da sauran yaran sun fito bakin famfo suna ta burush da wasa da ruwa.
Na dan jingina a jikin bango a sanyaye na ce." Anti Yagana mun tashi lafiya ya hidima?"
Ta amsa hankalinta yana kan abinda take yi, na ce.'' Ina ganin gobe asubanci zan yi zuwa kano Gwaggo bata da lafiya yanzu nan Hamusu yake gaya mini jikin nata sai a hankali."
Ina dire maganar da take bakina Yusi ya zo ya tsaya da burush dinsa a hannuna.
Anti Yagana cikin alhini ta ce." Allah sarki Gwaggwo ciwon har ya kai ace bata san wanda yake kanta ba, kenan tana asibiti a kwance."
Na ce." Ina fa, tana gida saboda shashancin Hamsu bai gaya mini ba har sai da ciwon ya ci k'arfinta wai ya kaita asibitin murtala da farko yanzu kuma abin yayi tsanani shine fa ya kira ni yake gaya mini da abin haushi wai yana neman izini zai yi amfani da kudina.
Ta ja tsaki tana fad'in." Wauta da rashin hankali shikkenan don ya d'auki Gwaggwo ya kaita asibiti da kudinki sai ki ce masa don me, ya ba ni haushi wallahi."
" Wallahi ni ma ba ki ji yadda raina ya baci ba wannan ai shiririta ce rashin lafiya ya wuce komai, kuma ko dukiyata zata kare akan nemawa Gwaggwo lafiya anti Yagana wallahi ba zan damu ba"
Ya girgiza kai tana cewa." Kwarai kuwa ai Ido ba mudu ba ya san kima."
"Mama wai Gwaggo ce bata da lafiya?"
Na dube shi ya zuba mini ido da yanayi na damuwa a tare dashi.
Na ce." E, itace amma jikin da sauki alhamdulillahi."
A sanyaye ya ce." Mama idan za ki je zan biki don Allah....
'
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/3, 8:38 PM] matar mijinta: *Wannan littafin na kudi ne vip 1k akan telegram. Normal What'sapp group kuma #700 hanyar da za a biya kudin ita ce wannan...0542382124...Binta Umar gtbank ko kuma 7084653262...Binta Umar Opey bank. 'Yan nijar dala dari katin airtel za ku tura mini bayan kun kankare hoton. A tura da sheda ta wannan lambobin iya What'sapp kawai.*
*07084653262*
*08089965176*
*V-VIP AREWA PEN=N*

TEEMAH DATA SERVICES MTN
1GB @550
2GB @950
3GB @1450
4GB @1550
5GB @1700
CHECK CODE *323*4#
VALIDITY 30DAYS
CHAT@08112392177
CALL @08037026306
8037026306 fatima musa ibrahim opay

https://chat.whatsapp.com/K944WIHnBaKHDrZS6snUky

*TALLAH!*
*Albishirinku mata an walisa matan da suka amsa sunansu mata, waWanda suka san sirri da fa'idar gyaran jiki domin ta da komaWar sha'awarsu. To ku matso kusa kuji, wai kuna da labarin shahararren kamfaninnan na awa da awa Waya tamkar da dubu, sha undum, mai suna?*
*DUNIYAR LAFIYA ISLAMIC NATURAL PRODUCT & WOMENS CONSULTATION*
*Daga aunty Fatima Buhari rijiyar lemo 7ano state*
*Cibiyace da tai fice wajen gyaran ma'aurata*
*Wannan kamfanin basu fito ba saida suka shirya tsab domin taimakon mata ta hanyar samar musu da magunguna ingantattu nagartattu wanda aka haWa da natural kaya cikin tsabta da inganci, komai a kwali yake ar uwa cikin tsabta da nutsuwa aka shirya muku*
*ina masu son soma kasuwanci ku matso Anty Fatima tana bada kaya a sari akan farashin da zaki gode mata, tana raba kayanta ga manyan shagunan saida magunguna dake cikin kasuwar kurmi dake kano, tana tura kayanta izuwa gari_gari asa_asa. Kayan sari kona miliyon nawa kike da buata zasu iso hannunki a cikin kwana biyu da izinin Allah*
*Ni Badiat Ibrahim Mrs Bukhari awar Sabuwan maigogul, Aminiyar Iyabo, uwar Wakin Tani Shanono na gwada na san amfaninshi, kema ar uwa ki kwada zaki bani labari siyan nagari maida kuWi gida.*
*Mun sani yanzu yana da kyau duk abinda zamu siya musan ingancinshi da nagartarshi bawai muita siyan magungunan mata kara zube ba.*
*Wannan kamfanin kayansu babu algus ko almundahana a ciki, da tsoron Allah da warewa gami da gogewa ta sanin* *yadda ake sarrafa magunguna suke aikinsu, cikin nagarta da gangariyar tsabta.*
*Abu mafi sha'awa komai a cikin kwali yake a rufe kirib*
*ga kaWan daga cikin abubuwan da kamfanin yake samarwa*=G<
*Tsumin dadi har Madiga tareda gunbarshi*
*Tsumin no excuse melaabin bita zaizai*
*Gumbar dare daya wanka goma, dana gari da zumarta da tsuminta duk muna dashi*
*Zumar hana bacci gumbarta da garinta*
*Munada Arabian sabaya tare d Sudanese sabaya*
*Da zumarta*
*Sabaya ce dake cuko da a mace duk ramarta, da anjamewarta*
*Itama da zumarta*
*muna da mummuna da aiki*
*Akwai tsumi da gumbar ta da zaune tsaye*
*muna da kogin daWi*
*Abangaren sanyi sun samar ma mata maganin matsolilinsu*
*muna da fitattun maganin sanyin da yake fata_fata d sanyi yayi mishi korar kare*
*Khanzur Rahman herbal formular*
*Sanyi clear syrup*
*7 days for chronic infections flusher*
*Sannan kuma muna da* *Package amarya*
*Package Uwargida*
*Package irin na zawarawan da suke shirin sabon aure*
*Bugu da ari wannan kamfani yana sarrafa magungunan maza ba a iya na mata ya tsaya ba, wannan kamfani magungunan da yake samarwa suna da yawa wannan tsakurene daga cikin kayansu*
*Da sauransu da sauransu wanda bamu ambata ba.*
*Ba fa a iya haka muka tsaya ba muna d cancada cancadan zannuwan Gado da carpet*
*Domin neman arin bayani ku tuntuSeta a kan lambar wayarta kai tsaye*
+2348032089456
*41*
"To menene Sahura ciwo fa aka ce, don na duba shi sai ya zama lefi, saboda kawai abin magana bashi da wahala, ke fa da bakinki ki ka ce yana buk'atar taimako, ni kuma ina so idona ya gane mini muddin akwai buk'atar taimako zan taimaka masa wallahi domin ni ma ya taimaka mini ya rike ni da yarana ko yaya ne dole na dubi alherin da ya yi mini a baya."
A dan sanyaye ta ce." Ban'ki ta taki ba sisi, amma kin san ba kowane namiji ne zai yarda da uzurinki ba, kin san kowa da irin fahimtarsa."
Tsaki na ja na ce." Sahura kyale ni don Allah, ba dai akan oganki kike magana ba, yanzu ma rigima muke yi sai mu d'ora da wannan."

"Wace irin rigima kuma sis, ba na son fa sharri mutumin nan na ji labari fa an ce goyaki ne kawai baya yi kuma ba ke ki ke yi masa ladabi shine yake yi miki, har cewa aka yi kin mallaka shi da mahaifiyarsa sai abinda ki ka ce musu a gidan."
Tana dariya ta kai k'arshen maganarta da zolaya.
"Sahura duk wanda ya gaya miki haka ya zalince ni wallahi domin kuwa ni kadai nasan da wanda nake zaune, ba zan iya 'boye miki abinda yake faruwa ba sis, amma wallahi kallon kitse kuke yi rogo, da yawa mutane za su dinga ganin ai kakata ta yanke sa'ka saboda mafiakasari mutane sun amince da cewa kudi sune jin dad'i alhalin ba haka ba ne, na yarda da maganar nan da hausa ke fadi cewa ka auri mai zuciya ba mai dukiya ba, mutumin nan yana da tarin matsaloli wad'anda ya bi ya ninke abinsa ba wanda zai gansu sai wa nda zama ya had'a mussaman ni dai da nake a matsayin matarsa. Akwai ci dasha kula da lafiya da biyan buk'ata ta aure duk akwai wannan to amma kin san wad'annan abubuwan da na zayyano miki idan babu kwanciyar hankali ba za su yi tasiri ba. Idan zan zaga kaf garin nan Ina sukar mutumin nan babu wanda zai yarda da maganata domin ya riga ya siye jama'a da alherinsa."
"Sis ki gaya mini abinda yake faruwa don wallahi ni gabad'aya kin kashe mini jiki, don Allah ki yi hakuri ki zauna a d'akinki."
Murmushi na yi Ina dubanta, itama magiya take yi mini na ha'kura na zauna ko bata fad'a ba na san dalilinta bai wuce irin na Anti Yagana ba.
Na ce." Sahura zaman bashi ne a wahala ba, abokin zaman shine matsala, ni idan ta ni ne wallahi ba ni da matsala dashi amma fa zan gaya miki abinda ba ki sani ba ya sake ni akan wani abu da yake hasashe kuma bashi da hujja akai."
Cikin kad'uwa da tashin hankali ta furta." Saki kamar yaya k'awata, yanzu kina so ki gaya mini cewa babu aure a tsakaninku?"
"Ya sake ni shekaran jiya saboda yana zargina. Duk na kwashe abubuwan da suke faruwa na gaya mata. Jikinta ya yi bala'in mutuwa har da 'yar k'walla a kwarmin idonta ta ce." Wato ita dai 'ya mace rayuwarta ta kan kasance cikin 'kalubale akoyaushe duk abinda ta yi ba zata tsira ba, sis na ga dai harkar social media nan da ki ka yi neman na kanki ki ka yi baki taba aikata wani abin assha ba wanda zai zama tambari na zubewar mutuncinki. Kuma mutumin nan ba yaro ba ne a ganina bai kamata ace yana yi miki munanan zargi irin wannan ba, wallahi a wannan zamanin sis da wasu 'yan matan har gwara zawarawa ban ce duka 'yan matan lalatattu ba ne, amma wasu mazan na yanzu sun gane gwara su auri bazawarar sun san ita suka aura akan su kashe kudi wurin auran budurwa daga baya su gane ba kamila ba ce, kuma mata nawa manzon Allah s.a.w ya aura a matsayin bazawara, ko wannan ya kamata a ce wasu mazan na d'agawa mata kafa. Amma abinda na fi fahimta ga mutumin nan yana da zafin kishi wanda dama haka aka ce na maza ya fi na mata, kuma idan ya yun'kuro masa yakan iya kasa sarrafa kansa, amma ai kishi ba hauka ba ne, zai lalata auransa ne kawai bai sani ba, a wannan ga'bar gaskiya ba na tare dashi."
Na ce." To kin fahimce ni ashe, Sahura a shirye nake akan wannan dalilin wallahi na tsinke auran nan, ban yi abu tunda kuruciya ba akan me yanzu zan yi, har wanda yake aurena ya gaza fahimtata, koyaushe addu'a nake yi Allah ya kare mu daga rudin zamani. Shekaran jiya ya yi sakin jiya da safe ya ce ya mayar da ni. Ai aure ba abin wasa ba ne, ko 'yar tsana ba za a yi mata wannan wulakancin ba, Sahura dole ne na nuna masa nasan abinda nake yi."
" 'Kawata ina bayanki, amma don Allah kada ki zafafa da yawa nasan halinki, ki dubi shekaru da kuma matsayinsa da wad'anda suke k'asansa, dan fa kuskure ya yi kuskure gaskiya."
Na ce." Shi me yasa bai duba shekaru da matsayinsa ba, ai gudun zubewar mutunci yake yi a gari to idan bai yi wasa ba sabuwar jarida zata fita a kansa."
"A a 'kawata kada ki yi abinda duniya zata san me kuke ciki, ki sakaya auranku don Allah, shi dai sannu a hankali ki hukuntashi amma kada ki fitar da sirrinku, ai dan Adam tara yake bai cika goma ba, bai kyauta miki ba amma ki dubi abubuwan alherinsa a gareki ki rangwanta masa.
'Kwafa na yi tare da cewa." Mu bar maganar nan Sahura ta ishe ni wallahi, yanzu ashe yawo ake yi da ni a gari ana cewa juya shi nake yi, mutane basa tsoron Allah."
'Yar dariya ta yi tana fad'in." Wallahi cikin unguwarmu na ji maganar tana yawo, kuma daga gidanku ta fito Ummansu Hadiza ce take gayawa ma'kota ai kin shiga kin fita akansa da Mamansa sai yadda ki ka yi dasu, Hadiza da ta zauna a gidan ta ga irin zaman da ku ke yi.

"Ita Ummansu Hadiza tana d'auka yadda take bin malamai kowa ma haka yake, kin san mai yin abu sai ya dinga zaton wani ma yana yi, ai na gaya miki Sahura wallahi ban ta'ba tsugunawa agaban wani da zummar ya taimaka mini akan mutumin nan ba, kin fi kowa sanin halina. Anti Yagana ce ma da taga abin ya rincabe ta fara biye biye na ce mata ba na so, duk abinda ya tunkaro bawa kawai ya nemi sau'ki a wajan Allah."
"Wannan shine gaskiya 'kawata domin babu wani abu da wani mahaluki zai yi maka face ya kara jefaka a masifa, kuma na ji labarin ma an ce Hadizan bata kasar wai ta tafi dubai saro kaya." Ta kare maganar tana dariya.
Na ce." Ni ma haka na ji Sahura na ce me Hadiza take so ta zama ne, ai mutumin nawa shi ta kira ya bata jarin kudi zaman da ta yi a wajena ta samu kofa a gabana ya ce mata duk lokacin da wata buk'ata ta tashi ta nemeshi. Wallahi Sahura ashe had'a baki suka yi da Ummansu suka shirya karya ciwo ga Fati wai tana da cancer za a yi mata aiki, duk suka daga mana hankali ni dashi a lokacin ya ba su miliyan shida ya kuma bata kofar tambayarsa duk abinda suke so shi ya d'auka da gaske ne sai da anti Yagana ta bincika ta tabbatar da cewa k'arya suke yi. Kuma maganar fa da nake yi miki lokacin da ya tura mata kudin zuwa Dubai din rikici muke yi don har

Please Login or Register in order to submit comment