Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da Gwaggo da Baba Hamusu."
Yusi ya riko hannunsa ya tashi tsaye muryarsa sanyi kalau ya ce." Wallahi ban san da tafiyar ba sai yanzu ka yi hakuri d'an uwa, idan har za ka je sai mu je ai babu damuwa."
Da farinciki a fuskarsa ya furta " Zan je mana bari na sanar da Momi kai kun yi sallama ko?"
Yusi ya girgiza kansa a hankali ya ce." Zan shigo yanzu na yi mata sallama.
Adam na fita ni ma na kama hanyar fita zuciyata cike da zullumi da nazari nasan ba karamin gagarimin rikici ne zai 'balle a gidan ba dalilin wannan matakin da na d'auka. Amma a shirye nake da tarar komai daga maigidan koda kuwa ta rabuwa ce. Ai an yi abinda aka yi, Allah Ya shige mini gaba.
Muna fita harabar gidan Masa'udu shine babban direbanmu da ya ajiye mana domin zurga-zurga dukda ba kasafai muke fita ba amma tun farko dama ya hana mu tu'ka mota a wasu lukutan ma ya gwammace shi da kansa ya ja akan wata daga cikinmu ta ja
Ya taso da sauri tare da risinawa yana gaishe ni na amsa a gurguje domin ba na so Adam ya sake shigowa ya same mu ban san mai zan ce masa ba.
Cike da girmamawa ya ce." Hajiya za a fito da mota ne?"
Kaina na girgiza a takaice na ce." A a.'' Ya biyo bayanmu da sauri Yana fad'in." Hajiya ki yi hakuri na kai ku don Allah" Ya k'arasa maganar a raunane. Na Dan dube shi sai ya ba ni tausayi sosai suke ko'karin ganin sun ri'ke aikinsu sam ba sa son abinda zai 'batawa ogonsu rai ko su sa'ba umarninsa.
Na ce." Yi sauri to." Da dan gudu ya nufi wurin da motocin suke ya fito da daya da gaggawa har zuwa wurin da muke tsaye.
Kamalu ya bude mini na shiga na zauna kafin ya dubi Yusi cike da tsare gira ya ce." Malam shiga mota.'' Ya shiga ba tare da ya ce masa komai ba sai da akwai da 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~muwa Mai yawa a tattare dashi don sai waige-waige yake yi.
Sai da muka hau titi sosai hankalina ya kwanta domin ni kaina ina jin nauyi da kunyar yaron ina kuma fargabar ya zo ya riskemu ba zan iya ce masa tafiyar ba zata yiwu dashi ba.
"Hajiya Ina muka nufa..... Muryar Masa'udu ta katse tunanin da nake yi.....
'
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/3, 8:38 PM] matar mijinta: *Wannan littafin na kudi ne vip 1k akan telegram. Normal What'sapp group kuma #700 hanyar da za a biya kudin ita ce wannan...0542382124...Binta Umar gtbank ko kuma 7084653262...Binta Umar Opey bank. 'Yan nijar dala dari katin airtel za ku tura mini bayan kun kankare hoton. A tura da sheda ta wannan lambobin iya What'sapp kawai.*
*07084653262*
*08089965176*
*V-VIP AREWA PEN=N*

*TALLAH!*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/BieW3hHvRNIJLFNloG2CDl

Momyn Hajara GHT supplements

Muna da kayan gyara jiki na maza da mata munada magungunan matsalolin ma'aurata munada magungunan kowacce irin matsala in sha Allah

Hadin Amare
Hadin Ango
Hadin jego
Hadin uwar gida
Hadin babbar mace
Hadin maida tsohuwa yarinya


Muna da Maganin sanyi kowanne iri
Muna da maganin ulcer
Muna da maganin Asthma
Muna da maganin ciwon zuciya
Muna da maganin ciwon Hanta
Muna da Maganin hawan jini
Muna da Maganin ciwon Ido
Muna da Maganin rashin haihuwa
Muna da Maganin skeler
Muna da Maganin kowacce irin cuta da yardar Allah

Sannan kowa zai iyayin register da campanynmu maitarin albarka kasari kaya kasiyar kaci riba sannan Kuma campany yadunga biyanka albashi Duk watan da kayi aiki
Saida kaya shine aikin da zakayi campany ya biya
07012621175
Register 8000 ne kachal=L
*87*
Muryar Masa'udu ta katse tunanin da nake yi. na sauke ajiyar zuciya a hankali na ce." Kai mu jabi park."
Cike da bin umarni ya ce." An gama.
Motar ta yi shiru ni da yaran duka muna cike da zullumi mussaman Yusi da nake hankalce dashi yana goge hawaye a fakaice. Ban tsawatar masa ba domin kuwa ban san mai yake ji a zuciyarsa ba, amma zahiri wannan shine iya gatan da nake ganin zan yi musu a duniya. Ba zai yiwu a ce koyaushe rayuwarsu ta kasance cikin kyara da hantara ba. Sun fara kaiwa munzali na girma a wannan lokacin ya kamata ace mun had'u ni dasu mun gina gobe dalili watarana za su yi aure su tara iyali suma. Sannan zuciyata ba za ta iya cigaba da jurar ganinsu cikin kaskanci ba, arziki Allah ne yake bayarwa su fita su nema kowa ya tsaya da k'afafunsa.
Cikin ikon Allah motar dana sanya su ta yi lodi saura bai fi mutum hud'u ba. Cike da dauriya da ko'karin kara musu kwarin gwiwa muka yi sallama na ce lallai idan sun sauka Kamalu ya kira ni tunda da waya a hannunsu.
Ban gushe daga wurin ba har sai da na tabbatar da tashin motarsu sannan na sauke ajiyar zuciya na gyara zaman nikab din da yake fuskata tunda ban fito ba sai da na sunkufe jikina ta ko'ina dalili ba na so a gane wata ala'ka da za a yi yamadidi da ni, kuma safiya ce tashar babu wadatar mutane da yawa sosai.
Kai tsaye na nufi wajan da Masa'udu ya ajiye mota.
Yana ganina ya taso daga inda yake ya bud'e mini na shiga na zauna sai a lokacin na ji wasu gagariman hawaye masu radad'i sun k'wace mini. Wato ni kuma haka kaddarata take, ina ro'kon Allah Ya ba ni ikon cinyeta ya kuma saukakawa yaran nan rayuwa ya basu hakurin maraici.
Ina komawa gidan na samu Hauwa da Momi zaune a falo, amma babu cikakkiyar sakewa a tsakaninsu Hauwa ta yi zaman gadara da ki ce kule na ce miki cass domin kuwa fuskarta tamkar kunun tsamiyar da ya kwana a rufe. Kusan a tare suka amsa sallamata.
Kwarai da gaske na yi kokarin danne abinda nake ji a zuciyata game da al'amuran dake faruwa. Na nemi wuri na zauna babu yabo babu fallasa nake kallonta ina sake nazari akan al'amuranta. Ta tsuke sosai ta yi fayau abinka da mara jiki da gasken ne bata da lafiyar domin alamu sun nuna babu wani kuzari da karsashi a tare da ita.
Ita ta fara gaishe ni a tsanake na amsa ido na a kanta ina sauraran abinda take tafe dashi ta gyara zamanta kad'an tana kallona sai ta sauke ajiyar zuciya a hankali
Ta ce." Amina na shigo nan ne saboda ke domin mu tattauna abubuwan dake faruwa da yaranmu, Allah Ya ga zuciyata ban shigo cikin rayuwarku da wata niyya ta cutarwa ba, kuma ban had'a kai da Salim domin ya ci mutuncin Kamalu ba, asali ma abinda yake aikatawa ba ni da masaniya sai bayan ya aikata din nake samun labarin." Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya a karo na biyu kafin ta cigaba da cewa."
Yana da kyau a matsayinki na uwa mai hankali ki yi nazari mai kyau Amina idan hankali ya 'bata fa nutsuwa da dattako ake sanyawa domin nemansa bai kamata ace kin d'auki munanan shawarwarin da ba za su zama silar gyar........Hauwa ta katse ta cikin fusata." tana fad'in "Ai dama ban ce kin shigo gidan nan domin ni ba Maryam, ko kuma kin ji na ce miki kin shigo ne da mummunar niyya. Kin tsargu ashe ai shi mara gaskiya dama kullum cikin zullumi Hajajju ki dube ni da kyau ki ga ni, a waye nake k'warai babu wata kinaya da za ki yi mini kafin ki san Amina da yaranta ni na santa na kuma zauna da ita. Idan har mijinki ya gaya miki cewa da hannuna wurin matakin da Kamalu ya d'auka bai yi miki k'arya ba, ga ni a zaune ai ina jiran hukunci tunda ku kun iya take gaskiya da gangan."
Cikin rashin sukuni na ce." Hauwa menene don Allah, duk cikinmu nan babu yaro karami tunda har ta shigo domin mu tattauna magana dan samun daidaito bai kamata wasu maganganu mara dad'i su biyo baya ba kuma."

Ta ja dogon tsaki tana fadin
"Kina jin irin jirwayen da take yi mini ai, ai mu 'yan iska ne marasa 'yancin kai tunda mijinta haka ya nuna mata ba mu da mutunci da kima sannan ba mu da sirri komai muka yi a tambad'e ita nata sirri koyaushe cikin danda'be shi yake baya so kowa ya ji. Bazan jure d'aukar cin kashi daga 'bangaranta ba wallahi tallahi."
A nutse ta ce." Ba halina ba ne raina mutum Hauwa, kuma kamar yadda ki ke hasashe hakane maigidan ya gaya mini komai ke ce ki ke ko'karin ganin lallai sai an yi 'batacciya domin kuwa abinda muke ta bunnewa dalilin gudun rikici mai muni ke ki ka gayawa mahafiyar yaron nan, kuma ki ka cire nauyi da kunya ki ka dubi tsabar idon yaron nan Kamalu ki ka gaya masa to kin fad'a kin ji dadi kuma in sha Allahu abinda ki ke fata ba zai faru ba da izinin Allah."

Hauwa ta mike tsaye tana huci ta ce." Kin yarda yaronki mahassadi ne, kuma sharri ya yi wa Kamalu ko ba ki yarda ba, ke yanzu don girman Allah ba ki ji kunya da nauyi ba
ai ita karya fure take bata 'ya'ya wallahi ni dai Hauwa Maryam ba ki isa ki siye ni da kudi da abin duniya ba. Wannan gingimeman sharri da d'anki ya alak'anta marayan Allah dashi saboda rashin adalci da son zuciyarku sai ku ja baki ku yi shiru babu wani mataki da ku ka d'auka. Sannan kuce ba za a yi magana ba, to ni na sayi rikicin don girman Allah ki d'auki mataki a kaina. Kenan wannan ya nuna kun sake bawa yaron lasisin ci gaba da aikata abinda yake yi dalili kun nuna masa akan daidai yake, ke da mijinki kun daure masa gindi saboda kun tara abin duniya kuna ganin kun fi karfin hukuma ko? to ku d'aukaka k'ara don Allah allura ce zata tono garma menene ba mu sa ni ba Maryam na fad'a din idan ta yi miki zafi ki kaini 'kara ko kisa tsinken tsire ki tsire ni!"

Na tashi tsaye da sauri
na tare ta tare da mayar da ita kan kujera na zaunar sai huci take yi tabbacin a fusace take kuma a shirye take da duk abinda zai faru.
Hayaniya ta fito da Baba Tabawa daga kicin tana fad'in." Mai yake faruwa ne don Allah ku yi aiki da hankali da girman shekarunku kada hayaniyarku ta d'auki hankalin yaranku k'ananu har su fahimci abinda yake faruwa, kun san dai yaro da ri'ke abu a zuciyarsa...

Littafin gudun aure na kudi ne, don Allah kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba.

Cikin numfasawa Hauwa ta koma ta zauna tana huci! ita kuma Momi ta yi 'kasa da kanta k'walla cike a kwarmin idonta. Alamu sun nuna cewa ba ta iya fad'a na cacar baki ba koda fad'ansu ya yi tsayi da Hauwa ita za ta kaita kasa.
Har cikin zuciyata ban ji dad'in abinda ta yi mata ba duk da cewa duka su biyun ban san menene a cikin zuciyoyinsu ba don haka ba daidai ba ne abinda ta yi tsinka na k'asa da kai ma tozarci ne ballantana wanda yake sama da kai ashekaru. Ni da ita duka haihuwa ce ta janyo mana domin kuwa da yara ba su had'a ba ina ganin babu wani dalili da zai sanya na yi sa'insa da ita akan namijin da ba shi da wani tabbas. Tun farko itama Hauwan da ta d'auki shawarata abinda yake yi akan matarsa ba zai dameta ba tunda ta san tafi amfanarshi fiye da ita ko a wurin tarayya ta aure ne. Kuma ita ce uwar mai sunan mahaifinsa Ibrahim Khalil, uwa uba kuma 'yar uwarsa ta jini. Hauwa ba ta fi ni kishi ba wallahi kawai na fita ha'kuri da juriya ne dalilin gwagwarmayar da na yi a rayuwa ita ba ta yi irinta ba.
BabaTabawa ta koma kicin jikinta duk a sanyaye bayan cikin hikima irin ta manya ta yi mana nasiha aka ci sa'a kuma Hauwa bata k'alubalanceta ba.
Falon ya yi shiru bayan gushewar baba Tabawa daga wurin babu wanda ya sake magana. Ita Momi din tunda ta sunkuyar da kanta kasa ba ta sake d'agowa ba tabbatacin ta ji ciwon irin tijarar da Hauwa ta yi mata.
'Dagowar da za ta yi kuwa sai ya yi daidai da kwaranyowar ruwan hawaye a dakalin fuskarta. Ba ta yi yun'kurin gogewa ba sai ta kalleni ta fara magana cikin karaya da zullumi." Amina ni na haifi Salim amma wallahi ba na goyon bayansa akan irin abubuwan da yake aikatawa na rashin kyautatawa. sannan na sake jadadda miki babu yawuna ka haifi d'a ne kawai amma ba ka haifi halinsa b..... Hauwa ta yi saurin cewa." Kuka ai yanzu ki ka soma in sha Allahu rabbi Hajiya kina
fama da gagararan d'anki da ki ka kasa sarrafawa ina ke ina iya yi wa yaran wasu tarbiya wallahi ki ji tsoron Allah da Annabi, ga shi dai da bakin ki kin fad'a cewa Salim baya jin maganar ki, sannan nan Nusaiba ta shigo har gida ta yi mana rashin kunya, ina tarbiya anan kina so ki lalata mana yaranmu ne, ko kuma kina so su yi koyi da abinda yaranki suke yi duk a had'u a yi mutuwar kasko gabad'aya ko ba haka ba ne."
Shiru ta yi ba ta ce mata komai ba. Na dube Hauwa da ta kasa zaune a kan kujera sai zabura take yi kamar ta yi tsalle a gabanta ta rufe ta da duka.
Gyada kaina na yi ban ce komai ba na mayar da hankalina kanta domin sauraran abinda take cewa." Na nunawa Salim takaici da 'bacin raina na kuma gargade shi akan kada ya kuskura abu mafi muni ya sake faruwa irin haka. Ina kwance cikin ciwo jiya na samu labarin doki-in-doka da ya shiga tsakaninsu. Wannan shine abinda ya fi tayar mini da hankali na ce kina ina har hakan ta faru. Ban haifi Kamalu da Yusi ba, amma yau zan gaya miki wani abu da nake ji game da yaran nan a zuciyata wallahi ina sonsu fiye da yadda ki ke tsammani. Yadda nake jin yaranku gabad'aya a raina haka nake jin wanda na haifa. Ina rokonki da Allah da annabi kada ki yanke kyakykyawar ala'kar dake tsakaninmu. Kada ki yi yun'kurin datse k'akkarfan zumuncin da yake tsakanin Adamu da Yusuf domin kuwa d'azu Adam ya je mini cikin damuwa cewa kin tura yaran nan kano, ki yi hakuri yara su dawo mu cigaba da rayuwa cikin aminci na yi miki alkawari wani abu makamancin wannan ba zai sake faruwa ba. Kuma in sha Allahu Salim zai shigo ya baki ha'kuri komai ya shige da izinin Allah."

Ta gama maganar tana sanya hannu domin share hawayen da yake ta tsiyaya a fuskarta. A nutse na ce." Ki yi hakuri ki daina kuka akan wannan lamari Momi wallahi ban k'ullaceki ba, kuma ni har abada akan yara ba zan yi rigima dake ba, amma ina so ki sani ce wa muddin Kamalu da Salim na tare a Inuwa daya to sa'bani ba zai daina giftawa a tsakaninsu ba. Abinda ba na fatan ya sake faruwa. Ba wai ba ki isa ba ne, kin fi karfin komai a wurina domin ban mance alherinki ba, ki yi hakuri yara dai har abada sun bar nan in sha Allahu suna can hannun dangin Babansu sai dai su zo da ziyara. kuma ban isa na yanke zumuci da ala'ka ba tunda ai ba ni na had'a ba......
'
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/3, 8:38 PM] matar mijinta: *Wannan littafin na kudi ne vip 1k akan telegram. Normal What'sapp group kuma #700 hanyar da za a biya kudin ita ce wannan...0542382124...Binta Umar gtbank ko kuma 7084653262...Binta Umar Opey bank. 'Yan nijar dala dari katin airtel za ku tura mini bayan kun kankare hoton. A tura da sheda ta wannan lambobin iya What'sapp kawai.*
*07084653262*
*08089965176*
*V-VIP AREWA PEN=N*

*TALLAH!*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/BieW3hHvRNIJLFNloG2CDl

Momyn Hajara GHT supplements

Muna da kayan gyara jiki na maza da mata munada magungunan matsalolin ma'aurata munada magungunan kowacce irin matsala in sha Allah

Hadin Amare
Hadin Ango
Hadin jego
Hadin uwar gida
Hadin babbar mace
Hadin maida tsohuwa yarinya


Muna da Maganin sanyi kowanne iri
Muna da maganin ulcer
Muna da maganin Asthma
Muna da maganin ciwon zuciya
Muna da maganin ciwon Hanta
Muna da Maganin hawan jini
Muna da Maganin ciwon Ido
Muna da Maganin rashin haihuwa
Muna da Maganin skeler
Muna da Maganin kowacce irin cuta da yardar Allah

Sannan kowa zai iyayin register da campanynmu maitarin albarka kasari kaya kasiyar kaci riba sannan Kuma campany yadunga biyanka albashi Duk watan da kayi aiki
Saida kaya shine aikin da zakayi campany ya biya
07012621175
Register 8000 ne kachal=L
*88*
Ta yi shiru tana gyad'a kanta kafin daga bisani ta yi wani murmushi da babu annashuwa ta ce." Shikkenan ba zan karya miki rantsuwarki ba Amina tunda har kin rantse amma ya za a yi da kayansu akwai takardun Yusi na makaranta shi ma Kamalu akwai wanda na sanya aka yi masa domin na gama shiri tsaf za su tafi jami'ar musulunci ta Madina makarantar da Salim ya kammala domin samun horo fannin addini da al'kur'ani tare da hadisan Annabi Muhammadu S.a.w."
A nutse na ce." Babu damuwa duk abinda ya danganci nasu ne za ki iya aiko mini dashi sai nasa a mota a kai musu in sha Allahu rabbi, na gode sosai Allah Ya saka miki da alheri."
A sanyaye ta amsa da "Amin." Kafin ta yun'kura da kyar ta tashi tana gyara madaidaicin hijab din da yake wuyanta ta ce." Zan shiga gida, Allah Ya ba mu alheri."
Ni kadai na amsa mata. Hauwa kam uffan ba ta ce mana ba har muka 'kare maganarmu. Ta kama hanyar fita jikinta a sanyaye.
Gabad'aya muka bi ta da kallo tana tafiya a hankali da rashi kuzari.
Sai bayan da ta fita ne Hauwa ta ja tsaki tana fad'in." Sai ta d'an ban tausayi wallahi."
Na dubeta a hankali na ce." Hauwa zan gaya miki gaskiya abinda ki ka yi wa matar nan ba daidai ba ne, don Allah ko don gaba kada ki sake kwatantawa ko so kike ki krasa gawar da ba ta ki ba. Kina kallon fa a yanayin da take ciki amma sai tsalle ki ke kina han'karo kamar za ki kai mata duka. Takaici abinda ki ka yi mata ne fa ya sanyata kuka. Ki duba shekaru da kuma d'awainiyar da take yi da yara don Allah."
Dan murmushi ta yi sai kuma ta ja tsaki a karon da babu adadi ta ce." Ta yi kukan jini ma, ni ina ruwana, sau nawa a sanadinta ana sanya ni kuka, munafukar banza kawai duk abinda take yi wallahi da niyya take yi ai sanin zuciyar mutum sai Allah."
Na gyad'a kai ina sake ce wa." Magana dai ta mutu Hauwa don Allah ni dai kada hakan ta sake faruwa kin ji."

Ta'be baki ta yi tare da furta." Haba ko yanzu na buga na bada ruwa wallahi zuciyata wasai nake jin ta. Murmushi takaici kawai na yi na yun'kura na tashi cikin zuciyata nake fad'in ba za ki ta'ba canzawa ba Hauwa, ba ki takali rigimar kina jin dad'i ba abinda zai biyo baya shine damuwar domin kuwa nasan akwai rikici akwance a tsakaninmu da shi uban gayyar. Shiga ta d'aki da kamar minti ashirin na fara jin hayaniya na tashi falo. Murya Hauwa a sama da wata murya da na kasa tantance ko ta wacece. Cike da zullumi da fargaba na fito falon na same su a tsaye cirko cirko har da yaranmu k'ananu a tsaye kusa da baba Tabawa dake ko'karin shiga tsakani.
Nabila ce 'kanwar Momi mutuniyata ce sosai kuma tun lokacin rasuwar Alhaji Amadu muka kulla zumunci don har musayar lamba muka yi. Sai ta d'an ja baya da ni ta rage kiran wayata bayan auran 'yar uwarta da maigidan. Ni kuma ban ta'ba nuna mata komai ba don wasu lukutan har magana nake yi mata idan na ga ta d'ora status a Whasap amma dai duk da hakan ta kasa sakin jikinta kamar lukutan baya.

Tana tsaye cikin shiga ta alfarma dama can 'yar gayu ce tunda itama tana taba kasuwancin irin na 'yar uwarta business take yi sosai zannuwan gado takalma da dogayen riguna har dashi take yi irin na manya maza da mata tunda ina gani a wasu lukutan tana dorawa a status dinta tana juya kudi itama yaranta biyu kacal duk maza tunda auranta ya mutu ta famtsa duniya itama har 'kasashen waje take zuwa sarin kaya..

"Ba ku isa ku kashe Momi da bakincinku ba Hauwa. Idan ba zata iya ba, ni zan kar'bi rigimar akan me? me ta yi muku da za ku tisa ta a gaba, masifar yau daban ta gobe daban tunda ta auri mijinku kuke yi mata bita da 'kulli kun had'e mata kai me ya yi zafi
mace tana sonku da zaman lafiya, tana d'awainiya da yaranku amma kuna cin dunduniyarta. Idan kun had'e mata kai sai me? Mijinta yana sonta fa, ai duk maccan da ta samu soyayyar namiji itace mowa kowa ya iya allonsa ya wanke
kuma ita alheri a jininta yake, wallahi ba za mu lamunta ba, za mu iya d'aukar kowane irin mataki akan abinda kuke yi."

Ido na zuba mata kawai kaina ya gama d'aurewa da maganganunta amma ba zan ce mata komai ba Hauwa kadai ta isheta tunda dama mai neman kuka ce.
Aikuwa ta bugi kirji har tana had'awa da tsalle tana fad'in." Karya banza da wofi an had'e mata kan don Allah ku d'auki mataki, matsafa masu kauce hanya domin neman duniya menene ba mu sani ba, dube ki don Allah sai kace tsohuwar karuwa tunda ki ka shigo falon nan ya game da 'karni da warin zunubi, kuna haura kan dutse fa ai ba abin mamaki ba ne don 'yar uwarki ta zama mowa a gidan nan, mun san komai mun ji labari
asalin dukiyar da uwar guzumar taku ta tara daga majiya mai tushe cewa kudin tsafi ne uwarku da ubanku ta bawa gumaka suka shanye jininsu. Sannan 'dan uwanku da aka tsinci gawarsa an kwakule masa Ido tare da cire masa 'ya'yan maraina haka aka ce da sanya hannunta. Tun a wancan lokacin kowa ya sheda matsafiya ce shine yanzu ta fake da gina gidan marayu taimakawa mabukata da sadaka domin yi wa Allah a dubara, in sha Allahu ba za ta yi karshe mai kyau ba
Har mu za a zo a yi wa wata burga, ko kuwa mun ce ta yi dawainiya da yaranmu ne? Ita taga zata iya. Mu dai in sha Allahu ba zamu rayu da kudin haram ba. Ba zamu fake da Allah da addini mu ciyar mu tufatar da kudin jinin mutane ba."
Nan da nan Nabila ta rikici sai ta fara rawar murya idanuwanta suka ciko da ruwan hawaye ta ce." Wallahi tallahi Hauwa sai mun yi shari'a dake sai kin tsaya a gaban alkali kin bada sheda akan abinda ki ka fad'a akan 'yar uwarmu wallahi ba zamu bar wannan maganar ba
ba za mu yarda."

Ta ce." Ashe babu dadi k'azafi ko. Mai yasa kuka take gaskiya da gangan, yanzu ke Nabila har kina da bakin da za ki zo ki tsaya a gabanmu da wata banzar magana. Ki je ki tambayi 'yar uwar ki irin zaman da muke yi da ita a gidan. Ai ba a banza ta ri'ke mana yara ba. A shirye nake ki kalleni da kyau babu wata 'yar iska da ta isa na ji tsoronta wallahi."
Nabila ta kasa cewa komai domin ta yi mutukar k'aduwa da jin maganganun da suka fito daga bakin Hauwa. Duk yadda ta dinga kokarin hana kanta kuka hakan bai samu ba cikin gaggawa ta kama hanyar fita ba tare da ta iya mayar da martani ba.

Cike da mutuwar jiki na dubi Hauwa da take ta numfarfashi na ce." Tsakani da Allah Hauwa idan rai ya 'baci yana da kyau a sanya hankali da tunani. Yanzu ke don Allah a ina ki ka ji wannan maganar kada fa ki d'auri kanki Hauwa mai ya yi zafi ne, ni dai idan har a kaina ki ke wannan balo'kokon to don Allah ya isa haka, yaran da suka asassa wannan rikicin na d'auke su da gidan fakat mu zauna lafiya, babu ruwanki da matar

Please Login or Register in order to submit comment