Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ka tafi gurin wata kai ka huta
Kasan da baqin cikin duka wannan lamarin da wanda zasu kara mata zai zama ajalinta??

Shi auren bazaa iya hakura dashi ba zuwa gaba ba kodan darajar dan dayake tsakaninku???

Shiru Hakeem yayi sbd yasan ba abune mai yiyuwaba tinda ko yanzu tafiyar nan zuwa Morocco da sukai ta saka aka qarawa auren sati uku yanzu sunyi biyu saura kwanaki kenan daurin auren dan kuwa su acan anacan an fara shagalin bikin tini amarya na cikin lalle an saka.

Rasa abin fada yayi sbd shima duk yanda suke tinanin a fasa auren yanayi yana kuma fada amma bazai taba iya bude baki ya cewa iyayensa aa ba sbd ita fammah ma ana auren daga india idan ya baro Nigeria so yayi ya dauketa su tafi America tare amma gashi lamarin na neman rikice masa.

Bude baki yayi ya bawa Abbun hakuri da tabbatar masa auren bazai saka fammah ta kasa samun kulawansa da kaunarsa ba har abada.

Ganin duk yanda ya fito fili ya roki alfarmar a daga auren daga hakeem bazai yiyuba sbd abinda ya nuna masa bazai taba iya bijirewa iyayensa ba akan komai dan haka Abbu daya rasa abin yi magana yayi da fammah wadda ta gama yanke hakeem daga zuciyarta har abada matiqar zaiyi auren nan da ko rasuwar mahaifiyarta bazai saka a daga mata kafa ba idan bazaa duba yanayinta ba da depression ma tini yake kokarin illata kwakwalwanta.

Abbu kai tsaye ya zabi bin bayan yarsa sbd tako ina yasan anci Amanarta an cutatar da ita an kashe rayuwarta an gama illatata tako ina dan haka babu amfanin zama a cikin mutanen dasukeda tsananin qabilancin da kansu kawai suka sani gwara ta dawo hannunsa kawai ya nema mata lafiyarta data rasa.

Tsayuwa akan raayin fammah da abbu yayi ya saka zancen zama babba har saida su Alh babba suka shigo akaita fama har lamarin ya fara zama babbar matsala me girma,

Sudai jeerahs basu taba hada sunansu da mutuncinsu da komaiba har abada dan haka maganar janye auren Hakeem sam bata taso ba suna dai bada hakurin ayi hkr fammah ta dawo ga mijinta tayi hakuri zasu kula da ita sosai zasu nema mata lafiya kuka bazasu bari hakeem ko kishiyarta su shiga haqqinta ba amma dai ba maganar fasa auren da anacan an fara biki.

Wannan maganar tasu ta sake ciresu daga zuciyar fammah sbd ji da tabbatarda ana can ana bikin ma kenan,
Babu sauran mutunci ko raayin cigaba da zama da hakeem da jeerahs a rayuwarta dan haka a gavan su Alh babba ta dago idanuwanta ta yanke dukkanin wata kauna a tsakaninsu ta maimaita ta gama zama da hakeem da familynsa bata buqatan sake rayuwa a cikinsu har abada.

Mamakinta sosai su Daddyn sukai hakama hakeem mamakinta kashesa yayi yanda iyayensa suka basu hakuri suka rokesu akan komawarta amma ita zuciyarta ta gama bushewan da taurin kai dana zuciya hakama Abbunta ya tsaya cak akan raayin yarsa dan baiga alaman zata samu kwanciyan hankali a tattare dasu ba.

Duk yanda hankalin hakeem ya tashi ya shiga mummunan tsoro da tashin hankali sbd yana tsananin son fammah kaman rayuwarsa bayajin ma zai taba iya rayuwar jin dadi idan bada itaba amma kasa barin girmansa da zafinsa yayi ya zube dan kuwa bayajin shima zai bari ta shimfida masa sharadi ya hau sbd shine yake aurenta ba itace take aurensa ba,

Idan har ta zabi ta rabu dashi sbd auren daya fada mata baso yake ba to shikenan zai bata abinda take son dan kuwa a matsayinsa na cikakken namijin dayake shugaba a dagar yaqi mace bazata juya sa ba ga iyayensa sun roketa da kansu amma ko gezau.

Dagowa yayi ya kafeta da ido daidai nan Ammin cairo ta shigo palon itada SHAKUR babban danta wanda yake balaraben asali ta uwa data uba kaman Fammah din.

Gefen Fammah ya zauna cikeda kulawa ya kalleta yana mata larabci da turanci akan duka abinda yake faruwan sbd lawyer ne babba kuma shine zai zama cikakken lawyer dinta a komai daga yanzu.

Dagowa fammah din tayi da idanuwanta da sukai jajir ta kalli Shakur din tai masa kalma daya tak da labari ya dan gyada kai natse suna maida kallansu kan Alh babba dake magana alama ransa ya fara baci da hukuncin da abbu ya tsaya akai.

Hakeem kuwa da idanuwansa sukai mummunan jajir hatta jijiyoyin kansa sun fito yanayinsa yayi munin gani idanuwansa ya tsayar akan Shakur dake kusa da fammah wadda ta riga ta kafe babu abinda duk duniya yanzu dazai sauya raayinta dan kuwa koda son captain hakeem jeerah zai kasheta ta zabi hakan tafison ta mutu amma ta gama dashi har gaban abada.

Jeerahs basu taba sheda karfi da taurin zuciyar larabawa ba sai a yanxu dan kuwa wata irin zafi da bushewan da suka gani a tattare dasu ya saka lamarin komawa bacin rai da zafin kishin daya rufe idon hakeem sukai fada mara dadin daya sakasa ajiye mata takardar rabuwa da ita kaman yanda ta buqata.

Tsananin zafin juna da wata irin tsanar juna da jin har abada sun gama da juna suka rabu akai wanda iyayensu suma suka rabu akai tareda fizgewa da cire juna a zuciya da rayuwa kwata kwata.

Sun barin qasar suna dawowa da kwana shida aka dauka aurensa da sabuwar matarsa Fadeela.

Aurensa da fadeelan ya karbesa ne a yanzu da hannu bibbiyu sbd zafi da radadin fammah dan haka yake kokarin yin rayuwarsa hankali kwance,

A bangare daya kuma ga fatima da tashin hankalin duniya tana cikinsa na wannan rabuwar data gama sanin ba abu bace me gyaruwa sbd sanin halin Fammah da kakkaifan raayin da babu wanda ya isa ya sauya mata shi.

***Acan fammah kuwa rayuwar tsaya mata tayi cak da zallar baqin ciki da radadin datake jin kaman zai kasheta,
Ta tsani hakeem ta tsani danginsa ta tsani duk wani ahalin jeerah da Nigeria tsana me girman gaske da ita zata mutu tabar duniya,
Tsanar da batajin harta mutu xata dena musu,
Mutum uku ne a duniya dake Nigeria da kawai take kauna da sune kadai suke hana ta tsinewa nigeria da wanda suke cikinta a kowane dare da rana wato Raheem dinta da fatima da nasir.

Mahaifintane yayi waya da fatima ya sanar da ita komai ya kuma qara bata amanar Raheem dan itace uwarsa itace dangin uwarsa kuma itace idonsu da zuciyarsu akansa suma dan fammah bazata nemesa a yanxu kusa ba saita samu lafiyarta da zaa nema mata.

Wannan shine sabon rudanin tashin hankali da damuwan da fatima ta shiga,
Bangaren Fammah suke haryanzu sbd an barwa Raheem bangaren mahaifiyarsa dasu masu renansa,

An sauya musu komai da komai na bangaren an zuba musu sabuwar luxuries tako ina wanda yafi na baya an wadatasu da komai kaman ba rayuwar duniya zasuyiba,

Kullum mahaifinsa na zuwa ya dubasa gashi an yaye su sosai hidimarsu ta qaru akan fatima dan yanxu sunyi wayo koina suna takawo suje da kafafunsu,

Lokacin auren captain yaja sosai tini rayuwarsa ta sauya ta koma wata irin me zafi sbd nutsuwan zuciyarsa daya rasa gabaki daya,
Baida farin ciki baida walwala ya koma cikakken asalin soldier dinsa da bayajin ma yanxu yanada buqatan kowace mace a rayuwarsa kawai aikinsa yake buqata da haka lokaci na sake ja ya tattara ya koma America komawan da baya dawowa sai lokaci mai tsananin tsayi.
Iyayensa da kwata kwata suka rasa Hakeem din baya yanzu soja ne kawai suke tare dashi dan kuwa ko su din yanxu babu sakewa a tsakaninsu dashi yayi nesa da kowa da komai,

Hatta 'dansa RAHEEM daya fara girma babu wata shaquwa a tsakaninsu ko bayyana soyayya sedai kokarin dorasa dayake yi akan rayuwar zama jarumi cikakken namijin fama da zai fuskanci kowace irin danger da rashin tsoro da bugun gaba dan haka ya zama a cikin wainda ake shakka fuskanta a familyn jeerah cikinsu da wajensu.
#MAMUH
#FLEET

GANIN IDO
Mamuhgee
1k
Vip 5k
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

14
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
RAHEEM HAKEEM JEERAH yaron daya taso wani irin miskilin da baa taba yin irinsa ba a zuriar jeerahs shine kuma wanda Allah ya jarabci duk wani jinin jeerah da tsananin kaunarsa da son kulawa dashi hakama jini daya na Rear Admiral da kaf familyn jeerah suke alfahari dashi sbd matsayin da babu wanda ya taba takawa a zuriar jeerah tin ta farko wato Rear Admiral Hakeem Farouk Jeerah.

Duk tsananin kauna da soyayyar da familyn jeerah kewa Raheem bai taba sakewa ko sabo dasu ba sbd yanada wata irin miskilancin da baya ko san rabar mutane kwata kwata,

Bai dauki dangin mahaifinsa da girman daya dauki Maamah dinsa ba wadda ta qarar da kuruciyarta da lokacinta da lafiyarta da zuciyarta a gurin kulawa dashi da mahaifiyarsa wadda bata tareda su sama da shekaru goma a yanxu,

Maamah itace wacce aka ajiye kamar baiwa a jeerah villa dan kawai kulawa dashi tin yana yaronsa har zuwa yanzu daya fara sanin kansa yasan itace uwar da harya mutu bazai sauya matsayinta a gurinsa ba duk da mahaifiyarsa ma tana tareda su a waya bayan shekarun data dauka tana jinyar data cinye mata lokacin rayuwarta dan kuwa jinyar jiki data zuciya data kwakwalwa tayi duka dan kusan saida tayi qaramar hauka sbd damuwa depression da komaima kafin Allah ya saka ta fara dawowa Dr fammah dinta dake kokarin daidai career dinta yanzu sbd sai data koma tayi wani karatun program na shekara biyu kafim ta sake samun damar komawa career dinta data dawo sabuwa.

Maamah bata taba barin kauna da soyayyar mahaifiyarsa da girmanta mai tsanani ya fita daga ransa ba koyaushe a cikin cusa masa kaunarta da girman matsayinta take a gunsa wanda hakan ya kasa ya taso da kauna da tausayin mahaifiyarsa tareda tsantsan son kasancewarta a rayuwarsa daya san haka bame yiyuwa bane har abada sbd wani irin zazzafan raayi da zafin da mahainfinsa yake dashi.

Fatima manyanci yafara hawa kanta sbd wahala data debo tana yi tin a baya duk da yanzu sun girma wahalar ta rage mata amma kuma kaf babu me dawainiyar Raheem idan ba itaba sai kuma dan uwansa rabin jikinsa da kusan shine yanzu yake masa wasu abubuwan duk da komai nasu daya amma sbd shi ya taso tamkar me ciwon damuwa bayada wani walwala ko sakewa bare farin ciki,

Maamah itace uwarsa da babu komai dayake buqata daga uwa har uba amma kuma wannan yanayin da kadaicin na kanada uwa kanada uba amma baka tareda kowane a cikinsu hakama babu wanda ya taba yi masa maganar wani a cikinsu dan kuwa sun goge juna da gaske daga rayuwarsu babu sauran alaqa da fili ko kadan da suka rage a rayuwarsu duk da hakan ya kashe Hakeem gabaki daya ya koma wani sabon mutum.

Nasir shime rabin jikin dan uwansa Raheem da yake tamkar jinin daya da aka haifesu tare,
Shine mafi kusanci da Raheem duk duniya sbd yanda suke jin juna kaman yan biyun da aka yankewa cibiya daya,
Babu ma'aunin da zai iya auna girman kaunar da suke tsananin yiwa juna,
Babu kowace rai dayafi so sama da Nasir dan a yanzu duk da basu wani girma ba ko Maamah bata gane abinda raheem yakeso fiyeda dan uwansa Nasir din,

Nasir ya taso mai karfin hali da naci da qwazo da tsananin son Raheem fiyeda kansa sbd Maamah bata boye masa ko su din waye ba,ta fada masa matsayinsu a gidan da zaman da sukeyi,

Nasir bai damuba baiji komai ba jin koshi da uwarsa waye,
Abu dayane ya sake ninkuwa ya qaru a zuciyarsa da ransa shine kaunar dan uwansa dayake jin zai iya komai da bada rayuwarsa a akansa.

Fatima lokaci yaja itama tasan lokaci yayi daya kamata ta tattara ta koma inda ta fito duk da har lokacin babu labarin ibrahim sedai khalil ne haryanzu yake bibiyarsu akai akai itada Nasir yana jin lafiyarsu.

Babu Alh babba a duniya ya rasu a shekarar data fita sbd ya manta sosai tsufa yazo yayi jinyar watanni kadan Allah ya karbi ransa.

Su Alh husain ma tsufa yazo sosai daddy ne ma yakeda saura,

******Raheem da Nasir nada shekaru goma sha hudu a duniya Dr fammah da Shakur suka nema a basu Raheem bayan komai nata ya dawo daidai ta koma dr fammah dinta ta baya rayuwa ta sauya mata tazama hamshakiyar macenta mai ilimi da da yanci da abun kanta,

Babu wani tashin hankali da akai aka bata damar kasancewa da 'danta wanda zai ringa zama gurinta yana kuma dawowa gurin dangin mahaifinsa.

Tafiyarsa ta farko dr fammah taso a taho da fatima kamar me amma sbd neman Ibrahim mijinta da khalil yakeyi sosai dan tinanin ko baya raye ya saka bata tafi ba dole suka tattara itada Nasir suka koma gida.

Raheem ya shiga mummunan hali sosai bayan rabuwarsa da Maamah da Nasir sbd tinda yake a duniya sune kadai wainda yake tareda su ya rayu dasu baida sabo da shakuwa da kowa bayansu biyun,

Jinya yayi sosai bayan zuwansa Morocco tsawon lokaci kafin ya fara kokarin sabawa da mahaifiyarsa da danginta da suma suke tsananin kaunarsa.

Fatima ta koma gida da Nasir suka fara kokarin fuskantar sabuwar rayuwarsu wadda take tattare da qalubale dan bata wani taho da abubuwan rufin asiri masu yawaba tinda babu kowa a tsakanin Fammah da hakeem da zasu bata dukiya me yawa.

Daddy ne ya bata kudi sosai da motar abinci wadda suka siyar da rabi dan babu gurin da zasu ajiye.

Kadan kadan kudin suka fara shigewa gurin neman Ibrahim da sukeyi ido rife,

Nasir yana ci gaba da zuwa makarantarsa da aka sakasu mai tsananin tsadar gaske shi da Raheem bayan yayi tasa jinyar shima ta rashin dan uwansa.

*****Raheem dauki lokaci sosai a gurin mahaifiyarsa harma yafara karatu yayi nisa a karatun mahaifinsa ya sake dawowa aka dawo dashi Nigeria nan Hakeem da kansa ya aiko aka dauko fatima da nasir suka koma jeerah.

Daga nan rayuwar Raheem ta koma tamkar jeka kadawo baya Nigeria hannun mahaifinsa baya Morocco hannun mahaifiyarsa,

Yanayin rayuwar sai yafara zamar masa wata babbar damuwa data sake saka rayuwarsa abin tausayi dan kuwa karatunsa ma wani wasa ya koma acan da nan,

Da haka suka sake girma babu sauyi ko daya a rayuwar Raheem da iyayensa dan haka mahaifiyarsa ta tattara danta ta karba bata sake barin ya dawo ba,

Barin Raheem rayuwar fatima da nasir suka dawo gida kwata kwata gabaki daya ya saka suka duqufa sanaa kala kala ga khalil nata kokarinsa gurin kulawa dasu da dora Nasir a sanaoi daban daban dan rufawa kai asiri.

Suna waya sosai da fammah amma fatima bata taba yadda ta fada mata halinda suke ciki ba sbd duk wata tana aiko mata kudi masu yawa na karatun Nasir da komai nasa dan ta dauke kowace irin lalurarsa.

Suna gama karatun secondary Dr fammah da suke cewa Dr Mum ta saka ayiwa Nasir takardu da komai dazai dawo hannunta acan Morocco yayi karatu tareda dan uwansa da suke tsananin kewa da mugun son juna sai kwatsam Admiral Hakeem jeerah ya aika Raheem karatun Soja kamarsa America.

***acan Nigeria su fatima sun wayi gari da wata irin gobara me tsananin data saka rayuwarsu sake sauyawa sbd sun rasa komai hadda takardun nasir din da akagama hadawa dan haka komai ya lalace ya dawo baya ta bangare daya kuma sai ga Ibrahim ya dawo gida da kansa cikin yanayi na ciwo baiyi kwana uku da dawowaba ya rasu.

Duk yanda sukaso neman Dr Mum ba dama sbd hatta wayarta da numbern take ciki basu tsira da ita ba bare Raheem da shikenan bazaa taba magana dashiba ko samunsa ba sai ya fito.

Dan gyara khalil yayi musu a gidan suka cigaba da zama kuma ita fatima bazata iya zuwa jeerahs ta sanar dasu ba dan itama batason kowace hulda dasu tinda babu fammah a cikinsu.

Irin zaman da sukeyi ya saka khalil fara tinanin aure dan kawo mace a gidan ya zama ba daga shi sai fatima ne a gidan ba duk da ga Nasir ya zama saurayi sosai aikin security yakeyi a wani babban hotel kafin ya fara karatun dazai cigaba da yi idan admission ya samu kenan.

ZAINAB itace kyakkyawar buzuwar amaryar da khalil ya auro ya kawota gidan suna zaman lafiya da kauna me tsanani tsakaninta da fatima wadda ta zama tamkar uwa a garesu tinda girman ya riga ya hau kanta,

Girmama Maamah fatima sosai zainab keyi kamar uwar data haifeta hakama itace uwar sirrinta,
Bayan Maamah fatima Nasir shine mutum nabiyu dayake tsananin shiri da Zainab din wadda yake cewa momy duk da kananun shekarunta dan iyakacinta tsararsa.

Shiru sukeyi wanda dole tasan rabin jikinsa dan uwansa da babu ranar da baya ambatarsa dan kuwa wani gurbi ne me girma rashin Raheem yabarsa dashi dayakejin kozai mutu gurin aikin wahala zaiyisa ya tara kudin zuwa ga RAHEEM HAKEEM JEERAH.

Shakuwar Momy zainab da Nasir ta saka damuwa da kuncinsu ragewa sosai suka maida hankali a gurin nema da gwagwarmaya da hakura da komai.

Ita kanta momy zainab da ita ake hada kudin Nasir daya sakawa ransa saiyayi aikin soja sbd Dan uwansada sukai alkawarin yin aiki daya a rayuwarsu tin yara.

*******Shekaru sun sake ja sun tafi ayau an wayi gari ADMIRAL HAKEEM JEERAH shine babba mai jagorantar familyn jeerahs kuma wanda ya sake auren wata macen bayan Fadeele ya dawo Nigeria bayan yakai matsayin karshe yayi retire,

Matarsa ta farkon bata taba haihuwaba sai ta biyun ce ta haifar masa wani 'da namijin mai suna ABDULSAMAD JEERAH wanda ya taso a cikin gata da daular arziki da dukkanin jin dadin duniya sbd mahaifinsa yana tareda su a yanzu a Nigeria yana juya manyan qasar yanda yakeso akan tsarinsa sbd kowa dakeson kasancewa tareda ahalin jeerah.
#MAMUH

GANIN IDO
1K
VIP 5K
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

15
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
A shekarar da Nasir ya samu admission daqyar bayan khalil yayita shiga guraren namen alfarma ya samar masa da komai a wannan lokacin ne Raheem yayi fitowan hutun farko daga karatunsa kuma sam Dad dinsa bai bari ya baro America ba acan yayi hutun sbd bayason ya tafi Morocco dan haka yanaji yana gani duk tsananin son dayake yazo yaga dan uwansa bai samu dama ba dan abinda dad din bai saniba shi Nigeria yaso zuwa hutun amma sbd wata irin tsanani da rashin wasa ko sakewan dake tsakaninsu sai baima bada damar hakan ba.

De fammah batama san anyi hutun ba sbd Raheem din da sukai waya bai sanar mata ba dan kada taji ba dadi ko ranta ya baci dan haka har sukai hutun suka gama suka sake komawa ciki bata saniba.

Abu daya daya sake qamar da zuciyar Raheem ga aikinsa da karatunsa shine ya tabbatarda matiqar bai zama abinda mahaifinsa yakeson ya zama ba bazai taba samun rayuwar yanci da mahaifiyarsa da Dan uwansa ba da maamah dan haka baida kowace irin sakewa ko walwala a rayuwarsa a cikin makarantar dako ina bayan tsayar da kansa cak akan abinda yakaisa wanda hakan ya saka ya zama wanda kusan kowa ya sani dan bayan sunan mahaifinsa da matsayinsa daya taka a aikin haryakai matsayin Admiral to shi kansa Raheem kamewansa da rashin fuskansa ko kadan da wani irin karfin halinsa ya saka ya banbanta da abokan karatunsa da yawansu duka suna cikin kulawa da tattalin iyaye biyu tareda kawo ziyara da duk abinda dai ya danganci nuna tsananin so da kewa ga yayansu,
Shi a cikin iyayensa tinda ya taho babu wanda ya taba zuwa bare sakasa a ido sbd kowannensu yana jin bazai taba zuwa ba matiqar zaiga dan uwansa dan kuwa duk inda zasu iya haduwa sun yankesa a rayuwarsu,
Kowannensu a cikin zafi da tsananin baqin cikin juna suke har yanxu bayan duka wannan shekarun,
A familynsa da iyayensa shine wanda ake ikirarin ana yiwa son da baa taba yiwa kowa ba amma kuma sam baida farin ciki da walwala a rayuwarsa dan kuwa ya zama shine yake karban dukkanin hukuncin rabuwar iyayensa tin yana zanin goyonsa haryanzu,
Sun sakasa a tsakiya yana karban baqin cikin da kowannensu yake jefawa juna ta zuci,

Duka wannan ya sake sakawa zuciyarsa bata san komaiba bayan kadaici da rashin sakewa da rashin son rayuwa da kowa bayan kansa shi kadai tinda ya rabu da dan uwansa da shine kadai yake sakewa da walwala a gabansa dan haka ya dage dan kuwa daga ranar daya samu yancin fitowa cikakken navy soldier babu abinda zai sake rabasa da nasir wanda daga garesa kadai yake samun nutsuwa da kwanciyan hankali zai dawo dashi rayuwarsa.

Dad Hakeem jeerah kuwa duk wata kulawa da sakewa ya soketa ne tsakaninsa da Raheem sbd yanason ya zamo namijin da baisan shagala ba ko soyayyarda zata lalata rayuwarsa tin daga kuruciya har tsufa kaman yanda tasa rayuwar ta riga tamutu har abada bazai taba farin cikin daya saniba a baya wanda ya saka zuciyarsa a duhu take babu komai daya sani yanzu bayan doka da order da tsananin zafin doka da wani irin kaifi akan duk sharadi ko umarnin dazai bada wanda a yanxu ahaka duniya tasansa, tsayayyen mutum kaifi daya da babu abinda ya hada da sunansa da mutuncin sunan familynsa da karfin ikon mai nauyi.

Akan Raheem yafi tsaurara Umarninsa da ikonsa wanda hakan keta sake tsayar da Raheem din ga zamowa wani irin miskilin namijin da babu komai a rayuwarsa da zuciyarsa bayan zafi da qwazon aiki dayake ta budesa yana zama wani kakkarfan namijin da lafiyarsa take da karfin gaske dan kuwa bazaka hadasa da Nasir da ko shi idan ya gansa sai yayi mamakin ganin yanda jikinsa yake murdewa sbd azababbun exercises da geamin da bama haka yake ganin sojojin nan ba daya saba ganin gashi shi a tsaye yake baida wani jikin karfi tinda baima taba exercise ba duk da baida rama ko kadan amma kuma baida jiki bare irin wannan na masu geamin.

*****Zainab ta haihu tin kafin samun admission din Nasir harta gamo zaman wanka ta dawo ansamu Al'amin wanda tini ya fara wayo ya saba da Nasir sosai dan idan zai fita baya barin ya gansa maqale masa yake,

Maamah fatima ta samu nutsuwa da rufin asiri sosai ba laifi sbd Baba Khalil ke ciyar da gidan gabaki daya hakama Nasir ranakun da bayada lectures aikinsa yake zuwa yana kuma samu ba laifi dan haka shima yana daukan nauyin gidan.

Dr fammah data kasa samun nutsuwan rashin fatima na shekaru tafara shirin yanda zata iya zuwa Nigeria data dauki alkwarin har abada ta yafe zuwanta duk yanda zasuyi a nemo musu fatima sunyi gashi sun saida gidansu sun sauya anguwan tin bayan gobarar da sukai.

Ga Raheem da shima tasan yasan yana fitowa hutu idan har ya isa Nigeria bazai taba barowa batareda ya nemesu ba dan haka ta sake jiran ya samu hutun wanda kusan fiyeda shekara nawa kenan babu wani hutu kilama bazai fitoba saiya zama cikakken soja dan haka duk ta shiga damuwa da tsananin matsuwan son dauko fatima musamman sbd Nasir datake son yayi karatu anan duk da tasan yanxu kam yana gap da kammala jamia idan ma bai gamaba.

******shekarar da Nasir ke kokarin gama university a shekarar Senior Seaman Raheem jeerah ya sauka a Nigeria tareda Mahaifinsa daya kwana biyu acan suka dawo tare.

Bangaren Mahaifiyarsa da aka sauya kowane tsari da zuba sabuwar dukiya da luxuries din da akasan su ya saba dasu da duk abinda zai buqata aka zuba tareda mai aikinsa Namiji aka ware masa.

Kaf familyn babu wanda baiyi murna da farin cikin zuwansa ba dan sun dauka ma shikenan ya zama na mahaifiyarsa.

Matan mahaifinsa da babu wani sani ko sanayya ko kadan a tsakaninsu suma sun dan nuna murnar ganinsa duk da suna jin wani irin mamaki da dacin yanda kowa familyn ke tsananin kaunarsa fiyeda sauran yaya hakama shi kansa mahaifinsa da baa gane inda ya dosa sunsan yafi kowa da komai tsananin sonsa bai kuma hadasa da komaiba a duniyar nan.

Mummy khadee mahaifiyar Samad kishinsa taji tana yiwa kanta da 'danta sosai har cikin qasan zuciyarta dan bata wani damu da kishin Ummah Fadila ba sbd fahimtar babu wata soyayya a tsakaninta da maigidan nasu ba gwara ita ko dan 'danta data haifa masa ta samu matsayin daya fi na umman dan haka kusan tafi fadilan iyayi da zuba

Please Login or Register in order to submit comment