Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da mota da wata crazy reverse aka bude motar da sauri imran ya fita security dinsu daya ya fada yaja da gudun gaske suna bi bayan su Dad.

Imran Maamah da Mommy aka saka masa a wata motar tareda safiya data fada motar itama yaja suka fice da nasu gudun gasken.

A lokacin ne samad ya juya da gudu shima zai dauko key Meenah dake tsaye tayi mutuwan tsaye tana kallan abinda yake faruwa ta kasa motsawa idanuwanta a kafe kan Fleet din da bata taba saninsa ba jininta ya daskare tareda gangar jikinta bin Samad tayi da kallo a zuciyarta tana jin tafasa da tsantsar kunan abinda ya saka jinin jeerahs su uku suke tsananin son SANAAH tsakanin Dad,Fleet da Samad.

Hajiyar Samad din daga ita sai rigar baccin dake jikinta ba zani akai kafafunta na hadewa tabi bayan samad tana sake rikicewa da tashin hankali da ihun kiran sunansa yana shiga ta fada palonsa ta zare key ta fito da sauri ta dannawa kofar key ta baro gurin da gudunta tana jin kaman ta dora hannu akai tayita ihu sbd yanda baqin ciki yake neman kasheta a take da abinda danta ya tashi yi da yanda Dad jeerah yau ya kasa riqe Dad jeerah dinsa HAKEEM JEERAH dinsa na asali ya bayyana.

Fammah da duk ta fice hayyacinta itama tashi tayi daga qasan data fadi sbd watsin da Dad dinta yayi dasu ta nufi gurin Mum dinta dake tsaye daidai lokacin firefighters motocinsu suka iso suna shigowa harabar gidan ta kama hannunta dayake tsananin rawa tafara janta dukansu kafafunsu rawa sukeyi tabar gurin da ita zuwa bangarensu suna shiga ta rufe kofar mum ta xame a gurin qasa ta fasa wani masifaffen kukan daya saka fammah tsayawa cak daga inda take tana durqusawa batareda ta juyoba ta saka kanta a kafafunta ta fasa wani irin kukan itama.

Kuka sosai mai tsananin karfi da jijjiga jiki Mum din keyi tana jin wani irin azababben radadin da duk duniya babu abinda yakaisa zafi da radadi a kirjinta tana qanqame kirjinta da dafe kanta da kaman zai tarwatse.

Sun jima a wannan yanayin tana wannan kukan fammah na yin nata na tausayin iyayen nata duka biyu da damuwan rayuwan da suka samu kansu rana tsaka ta tarwatsewan zama duk da ta kasa kama kowane tinani akan iyayen nata harma da kananninta da SANAAH batasan me zata kama ba me zatai tinani akansa sbd dai auren andaura kuma maauratan sun karbi junansu hakama kakanninta sun aminta suna kuma son auren ga mahaifiyarta bata yadda da ko daya ba a cikin hakan to ita batada kowace tinanin kamawa bayan jin kaman rayuwan tana isarta.
#MAMUH
09033181070
[17/06, 1:53 pm] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

123
Asibiti kuwa tin kafin su isa Imran ya dannawa Dr Akin waya ya sanar dashi Fleet suna hanya wanda tini suka fito harabar asibitin da nurses da masu daukan patients din da zaa iso dasu din suna jiransu a shiry cikin gaggawa.

Motar Dad tin daga nesa Mr Sideeq ya buga wani mahaukacin horn din daya saka maigadi wangale makeken gate din suna isowa haka suka wuce da gudu ciki suna parking ko bude kofar basuyiba motar fleet dayafi Mr Sideeq wani irin gudu tayi parking kai tsaye kaman baby Fleet ya fito da SANAAH dake jikinsa ya nufosu aka tarbesa tin bai isoba da stretcher ta asibiti aka dorata tareda yin ciki da ita lokacin aka tura dr mum itama saiga su Imran suma su Maamah akai ciki dasu gurin ya dauki tsit babu me iya magana ko zama babu wanda yayi a tsaye suke kaf dinsu jijiyan kai dana hannuwan Fleet sun wani irin fitowa manya manya dashi fuskansa da hannuwansa sunyi wani irin jajir.

Dad kuwa katuwar jacket mai tsayi da kauri Mr Sideeq ya kawo masa ya dora akan kayan baccin dake jikinsa masu kauri da hular sanyi sbd wani sanyi dayake ratsowa tsakiyar daren duk da suna wani lafiyayyan kebantattacen daki da aka kaisu.

Babu wanda ya fito daga dakin emergency din sai bayan dan lokaci dr Akin ne ma ya shigo da dr bushrat sai dr Nafeeu suka kalli su fleet din da Dad kafin Dr akin ya fara bayanin dukansu babu abinda ya samesu numfashinsu ma ya dawo daidai hakama babu konuwa ko daya a jikin kowannensu kawai dai zafi ne mai tsanani ya bugesu da hayaqi dan haka zuwa safe ko asuba ma zasu iya farfado insha Allah.

Imran ne yayi masa godia yana dan magana sbd fleet kwata kwata babu maganar da zata iya fitowa daga garesa yanxu kila sai zuwa goben hakama Dad shiga yayi ya dubasu tukuna ya fito aka koma gida dasu guraren asubar ma kenan sbd yana buqatan ganin likitan shima a duba bp dinsa daya riga ya sauka daga hanya saiya kwana biyu ana daidaita sa.

Fleet kuwa a asibitin sukai asuba saida gari ya fara haske saiga Maamah ta fara tashi tukuna Mommy sai Dr Mum daga baya dan haka ajiyan zuciya ya sauke a natse idanuwansa da fuskansa har lokacin jajir baiyi cewa komaiba daqyar sautin muryansa data toshe ya furta musu sannu da tambayar babu abinda sukeji suka tabbatar masa da basa jin komai.

SANAAH ce bata farka ba haka aka kwasosu a ambulance suka dawo gida inda kai tsaye bangarensa aka kai SANAAH su Mum kuwa bangarensu na farko da Meenah din take ciki aka kaisu tana dakinta bata fitoba batama san andawo dasu ba sbd fammah ta rufeta a ciki ta waje sbd kada ta sake wani abin.

Fammah ce ta isa dakin da Dr Mum take ta dubota wadda tayi weak sosai bata iya magana doguwa ta qaraso gurinta ta zauna ahankali tareda bude baki tai mata ya jiki.

Zuba mata idanuwanta Dr Mum din tayi cikeda wata irin tausayi da tsananin kauna sbd tana ganin damuwa da kunci bayyane kwance a cikin idanuwan Fammah din dan haka ta gyada kai ahankali tareda dan ware hannunta daya ta rungumeta tana sauke ajiyan zuciya.

Daga gurin Dr mum dayan dakin taje ta dubo Maamah da Mommy kafin ta fito ta koma dakinta ta zauna ahankali tana kasa fita zuwa dubo Dad dinta da SANAAH wadda kai tsaye tasan tana can bangarensa.

Dr kuwa likita biyu ne suka taho kansa aka dubasa sbd ba qaramin hawa da rikicewa bp dinsa yayi ba amma duk da hakan saida ya tafi har bangaren ya duba Dr Mum wadda yana shigowa har dakin dago idanuwanta tayi tana daga kwance bayan ta danyi wanka ta shirya taci abinci kadan da maganin itama jininta daya dan hau ta kallesa ahankali tana sauke masa idanuwanta da wani irin sanyin dataji na Allah bai dauki rantaba ayanxu batareda ta sake ganinsa ba sbd sunfi kwanaki yana fushi dasu basu haduba sai a asibitin shekaran jiya da cikin SANAAH ya zube sai kuma a daren jiyan da harta cire rai daga rayuwa.

Shi kansa wani numfashi mai sanyi da babu sauti ya sake yana bude baki kai tsaye ya mata ya jiki tana amsawa bai iya cewa komaiba ya juya ya fice su Maamah da mommy a palo fammah ta kirawo masa su suka fito ya musu ya jiki ya fice daga bangaren.

Yana isa bangarensa umma datake zaune tana jiransa dan yana fita tana shigowa kallansa tai da idanuwanta da sukai jajir tana sauke wani numfashi mai sanyi kafin ta bude baki tai masa ya jiki ya kalleta da idanuwansa da sukai jajir wani daci da nauyi yana toshe da maqoshinsa ya bude baki ya amsa yana kasa ce mata komai itama sbd wutar bacin rai da baqin cikin dayake cin jini da kirjinsa.

Ciki ya wuce bedroom dinsa kai tsaye ya daga wayarsa ya kira Mr Sideeq ya sanar dashi yaje da kansa babbar asibitin mahaukatan garin a taho masa da manyan likitocinsu da motar daukan mahaukatansu yana buqatan miqa musu Meenah a fara duba masa kwakwalwanta a tabbatar masa da idan tanada hauka ko babu sbd yasan hukuncin yankewa.

Mr Sideeq kuwa da daman yasan abinda zai faru kenan dan haka kai tsaye ya buga mota da kansa tareda securities biyu ya nufi asibitin.

Ummah ganin yanayinsa tasan babu sauki ko kadan a kone yake da tsantsar bacin rai da fushi mai tsananin dan haka ta lallaba tabar bangaren ta koma nata tana jin kaman zuciyarta zata zazzago qasa sbd baqin cikin datake diba na shekaru a wannan auren da bata ganewa komaiba.

Mr Sideeq na isa asibitin ga mamakinsa daya daga cikin motocin Fleet ya gani a bangaren tarban manyan baqi na asibitin wadda ya kalla da mamaki yana shiga ciki saiga Imran wanda shugaban asibitin gabaki daya da kansa ya fito ya tarbesa yana masa iso dan haka da tsantsar mamaki Mr Sideeq ya iso ya kalli imran wanda ya baice masa komaiba dole yabi bayansa tinda abu dayane ya kawo su shine buqatan babban likitan asibitin kwararre akan mahaukatan.
#MAMUH
09033181070
[17/06, 1:54 pm] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

124
Tinda ya dawo da ita daga asibitin ya kwantar a tsakiyar gadon dakinsa ya rabata da kayan jikinta ya goge mata jikinta da towel sabo da ruwan dumi ya saka mata rigarsa mai kauri sosai tareda rufeta ya zuba mata ido yana mata wani kallan dayake tafiya da kowace bugawan da zuciyarsa keyi da tsantsar zafi da wuta.

Miqewa yayi ya fada bathroom din ya sakarwa kansa ruwan sanyin gaske idanuwansa a bude ruwan na shiga har cikin idanuwansa suna sauka kansa.

Har lokacin jajir idanuwansa da fuskansa suke hakama jijiyoyin jikinsa da kansa basu koma ba.

Yana fitowa kaya masu dan kauri ya saka a lokacin ne ta farka ta bude idanuwanta ahankali tareda wani kasalallen tarin daya sakasa jiyowa da wani irin kallo ya sauke mata idanuwansa data kalla ahankali tana sauke ajiyan zuciya ahankali batareda ta motsa ba.

Gabanta ya iso a cikin sanyi da rashin karfi ko kadan da shock din daya shiga da tsananin tsoron da bai taba shigaba a rayuwarsa ta fuskantar rashinsu dazaiyi akan idanuwansa ya zauna ahankali bakin gadon datake kwancen yana kasa dauke idanuwansa daga kanta ya saka hannuwansa biyu duka ya dagota ahankali bai tsaya komaiba ya sakata cikin jikinsa ya mata wata irin kyakkyawar rungumar data sakata rintse idanuwanta tana jin yanda hannuwansa dasuka zagayeta suna wata irin rawar data bayyanarda shock din daya shiga na matakin karshe.

Ahankali taji jikinta yayi sanyi zuciyarta datake cikin tsananin damuwa da qunci tana cikewa da tausayin kansu ta rufe idanuwanta hawaye masu sanyi suka gangaro daga cikin suka saike ajiyan mai sanyi da tsananin kasala a tare.

Tsawon mintina suka dauka ahakan yana rungume da ita a cikin jikinsa kafin ya saketa a natse ya sake zuba mata idanuwansa da tanajin tsananin zafin tension dinsu har a jikinta ya kama hannuwanta duka biyu a cikin nasa ya bude baki muryansa datai wata kauri da tsantsar shaqan dayayi yace

"How are you feeling now??
Kina jin any discomfort?
Yaya kike ji?
Akwai inda yake miki zafi??

Dagowa tayi ta kallesa da idanuwanta ahankali kafin ta dan girgiza kai tana bude baki ahankali tace

"No"

Dagata yayi gabaki daya ya nufi bathroom da ita yakaita har gaban ruwan zafi daya tara mata a bathtub ya tayata cire kayan jikinta ta shiga ahankali tana dan kamasa ta zauna ciki ahankali tareda sauke numfashi mai sanyi ahankali kafin tace yaje zata iya da kanta.

Fita yayi ya fitar mata da kayansa da zata saka harta gama ta fito ahankali daure da towel ya kamota jikinsa a natse yana tayata goge jikinta ya taimaka mata ta saka komai ya zaunar da ita a bakin gadon ya fice yaje palo ya dauko breakfast din safiya ta kawo ya dauko mata.

Yana shigowa dakin Zaunawa yayi a bakin gadon tareda ajiyewa ya dauki tea cup din mai dan zafi yakai bakinta yabata tasha ahankali tana kallansa da idanuwanta da suke sake shiga tsabanin damuwa.

Ms Meenah kuwa babu wanda ya nemeta dan kuwa babu wanda yakejin bai gama da itaba musamman dr mum da bata buqatan sakata a idanuwanta kwata kwata dan haka koda Fammah budeta ta fito da ita takai ta dining duka ba kowa tsit kakeji sbd da safe an dan shigo dubasu Mum din daga sauran bangarorin villah din.

Abinci ta hadawa mum din da kanta tareda bude baki tace

"Mum dan Allah ya isa haka,
Kiyi hakuri mu taru mu dauki kaddara wlh bazan iya rayuwa ina kallanku a cikin wannan halinba ke da Dad,
Ya dauki fushin da bamusan wane mataki zai iya dauka ba akan wannan babban tashin hankalin Mum rayuka hudu kika so dauka ki rabasu da duniya
Mum ni kaina wlh na kasa yadda da wannan abin"

Dagowa Mum din tayi ta kalli Fammah din da wani irin jajayen idanuwanta kafin ta bude baki tace

"Akwai wanda bai cancanci mutuwan wulaqanci bane a cikinsu?
Akwai wanda ba azzalumi ba maci amana a cikinsu?
Akwai wanda baici amanar rayuwataba har abada a cikinsu?

Rintse ido fammah tayi tace

"Ko me sukai Mum basu cancanci kisa ba a hannunki,
Kisan rai fa Mum?
Kashewa fa?
Mum pls"

Wani baqin ciki ne mai tsanani ya tasowa meenah din tai wani irin watsi da duka kayan gabanta dake table din tana dakawa famman tsawan gaske jikinta na rawa tace

"Idan nice na haifeki bazaki taba sake saka bakiba akan wannan maganar,
Idan nice nayi naqudanki ban yafe ki kuma saka bakinkiba ko shiga sbd bazan taba yafewa abinda akaimun ba sbd kabilanci da cin amana datake a jininsu,
Ita Dr mum data zabi aci amanata da ita ta manta cewan ba dadi tinda ita da akai mata tattarawa tayi ta bar auren
Abinda bazan taba yiwa kowaba a duniya shine barwa kowace macen Fleet,na zabi zama komaima amma wlh saita bar min mijina kota bar duniyar."

Miqewa tayi tabar gurin ta ficewa daga bangaren gabaki daya ta nufi bangarensa idanuwanta a rufe,
Fammah kasa motsawa tayi daga inda take zaune tinanin na toshewa gabaki daya akan Mum din tata.

Tana isa bangaren nasa daidai lokacin motocin asibitin mahaukatan na shigowa harabar gidan tareda doctors dinsu guda biyu da masu daurewa sbd tinanin haukar tuburan take.

tana bude kofar palon kai tsaye kitchen ta nufa ta dauko wuqa sabuwa dal mai kaifin gaske tana nufar dakinsa idanuwanta a rife hankalinta na sake gushewa gabaki daya.

Tana isa palonsa bata tsayaba bedroom dinsa ta isa ta bude kofar da kofar tana boye wuqar bayanta ta sako kai tareda tsayawa cak kafafunta na wata irin zufa da rawa sbd abinda idanuwanta suka ganar mata yana zaune da SANAAH din a cikin jikinsa ya mata wata nutsatsiyar runguma da shigarwa jikinsa sunyi shiru kowa da damuwa da tinanin dayake kirjinsa.

Dagowa yayi ya sauke idanuwansa akan kofar kallo daya yayi mata ya rintse idanuwansa ahankali yana kokarin riqe kansa daga makashin dayake jin zai iya zama
SANAAH kuwa zare jikinta tayi a cikin nasa da dan sauri ba karfi sosai a jikinta tana qasa da kanta da sauri jikinta na dan rawa.

Miqewa yayi tsaye idanuwansa jajir hannuwansa na fara wata rawar da fushinsa da zafinsa ke kokarin fin karfin control dinsa ya nufota tana ganin hakan tayi kan SANAAH da wuqar da tsananin gudu tana jin kanta na kamawa da wata wuta.

Bata isaba ya saka hannunsa daya yayiwa wuqar wata damqar data yankesa sosai jininsa ya zuba har a fuskan SANAAH din wadda ta zuba ihu da karfi.

Kama Meenah din yayi tareda juyota ya dauketa da wani mahaukacin marin da take hakoranta biyu na gefe suka futa a take,kunnuwanta suka dauke wuta sai wani jiniyar da suka dauka hakama idonta daya take jini ya kwanta masa taji kaman an daga Caterpillar an buga mata akai take ta kife a gurin idanuwanta basa ganin komai da rarrafe baya hayyacinta ta fito tana isowa waje ta saki ihu mai karfi ta zube a gurin.

Yarta ce kawai ta fito a rikice tayo kanta daidai lokacin Likitocin suka iso kanta zata tafi da ita dan dubawa fammah ta riqeta da karfi tana girgiza masu kai cinin tsananin tashin hankali.

SANAAH da jikinta ya dauki rawa sosai saukowa tayi gadonsa tana isowa gurinsa da tsananin tsoro da rikicewa sbd jinin dayake fita hannunsa sosai.

Fammah ce ta shigo cikin tashin hankali dan sanar dashi abinda yake faruwa a waje amma tana ganinsu ta tsaya cak tareda maida kallanta akan Hannun Dad din dayake zubarta jini sosai tayo kansa da tsananin sauri tana ambatar sunansa.

Itada SANAAH din suka dora hannunsu akan nasa suna hana jinin fita kafin fammah a rikice tace SANAAH ta dafe bara ta dauko first aid box.

SANAAH fitowa tayi dashi yana kallanta da ganin yanda ta rikice ya janye hannunsa yana miqewa zai fita ta riqosa da sauri tana zata bude baki ya katseta da wani yanayi mai tsananin bayyanarda wuta ce take cin jininsa yace

"I'm ok"

Sake binsa SANAAH tayi daidai fammah na dawowa da box din sbd har lokacin jini fita yakeyi ga hankalinta na rabuwa biyu da Mum dinta da aka tafi da ita wadda takejin zuwa yanzu kaman akwai abinda yake damun Mum din kodai shock din ya taba kwakwalwanta dan haka zata bisu asibitin tasamu sanin menene matsalar mahaifiyarta.
#MAMUH
09033181070
[18/06, 10:18 am] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

125
Da sauri fammah din ta kama hannun Dad din nata daya suka isa kujera SANAAH ta zaunar dashi tana miqawa fammah hannunsa mai zubar da jinin tana kallan fuskansa datake babu rahama ko daya zafi ne yake cikeda kirjinsa ta dan sauke numfashi ahankali mara sauti hankalinta itama dik baa kwanceba ta koma gefensa daya tana dora hannuwanta duka biyu akan hannunsa daya daya dan juyo ya kalleta da idanuwansa da suke jajir tai masa wani kallan da tashin hankalinta yake a bayyane ya hade yatsunsu guri daya yana maida kallansa akan fammah datake dressing din hannun nasa daya jikinta duk yana rawa da tsananin tashin hankali da wani irin quncin datake ji mai tsananin dayake neman buga kirjinta akan abinda ya sake faruwa din da Mum.

Hannun nasa mai yankar yai amfani dashi ya kama hannunta cikin nasa itama tareda dagowa da jajayen idanuwansa ya kalleta itama shi din ta dago ta kalla take wani iri kuka mai tsananin karfi ya taho mata koina jikinta na sake daukan rawa ta rintse idanuwanta tana kukan sosai.

Rungumeta yayi a cikin jikinsa da hannun daya yana kissing tsakiyar kanta ahankali batareda ya iya furta komaiba sbd zuciyar data gama cinyesa babu kalman dazata fito masa.

Sakinsa tayi tareda kama hannun ta gama dressing dinsa kafin ta dago idanuwanta da sukai jajir harma da kumbara ta kalli hannunsa daya dayake sarqe dana SANAAH wadda take kallan fammah din tin dazu jikinta a tsananin mace zuciyarta na cikin wani irin kunci da damuwa.

Dauke idanuwanta tayi ahankali daga hannuwan nasu wanda sai lokacin SANAAH ta lura da kallan ta zare hannunta da sauri a cikin nasa tana miqewa tsaye ahankali hawaye na cikowa idanuwanta.

Shi kuwa miqewa yayi ya nufi bedroom dinsa dan sauyo kayansa da duka suka lalace da jini.

Yana barin gurin Fammah ta miqe tsaye tana juyawa zata fice SANAAH data kasa hakuri da riqe kanta da wani irin sauri da tsananin damuwan datake jin kaman zata kasheta ta isa bayan fammah din ta bayanta ta rungumeta da karfi tana fasa kuka mai tsananin ratsa zuciya tana qanqameta da bude baki tana cewa

"Ki yafemun fammah bazan iya daukan fushinki ba da rabuwa dake dan Allah kiyi hkr,
I'm very sorry"

Rintse idanuwa fammah tayi tana jin wani nauyi da radadi a kirjinta wanda ita kanta tasan zata cutu matiqar gaske rabuwa da SANAAH din amma bazata iya kallantaba a yanzu bayan duka wannan abin dayake faruwa wanda tin farko da ko ita an sanarwa zata iya sanar da mum dinta cikin fahimta da sanin yanda zata fuskanci komai amma itama SANAAH ta zabi soyayya akan amintarsu da kusancinsu,
Ta tambayeta ta kuma tambayarta akan ta fada mata meke faruwa amma ta zabi boye mata sai yanzu da komai ya lalace aka kai gabar da auren iyayenta ma tasan bame rayuwa bane matacce ne dan kuwa a yanxu da Mum ta kusan kashe uwar data haifesa da uwar da bai hadata da kowa ba tayaya zai iya cigaba da zaman da ita.

Wasu zafafan hawaye ne suka gangaro mata daga idanuwanta da har radadi sukeyi tanajin kukan SANAAH din wadda takeyi sosai kaman ranta zai fita saima yanzu ne ta samu yin kukan da tinda komai lalace batai irinsa ba dan kuwa jikinta har rawa yakeyi tana kukan mai tsananin karfi.

Itama famman kukan ne ta kasa riqewa tafara yinsa mai karfi tana qanqame jikinta da SANAAH ke rungume da ita har lokacin ta baya.

Sun jima ahakan kafin fammah ta zare jikinta ta fice daga palon tana isa bangarensu dakinta ta wuce ta fada ta rife tana zamewa kasa ta cusa kanta cikin kafafunta.

SANAAH dinma fitowa taso yi ta bita amma babu wasu kayan arziki a jikinta ta juya da sauri dan zuwa dakinsa ta samo abin rufa amma tana shiga ya gama shiryawa janyota kawai yayi ya zauna da ita tareda rungumeta yana hanata fita koina da taqaitacciyar maganar da sam bayason yi dan ko fita sosai muryansa bata yi.

Dr Mum da sukasan SANAAH na can bangaren hakan yafi musu kwanciyan hankali duk da sunsan an tafi da Meenah din wadda gabaki daya saida kowa yasan zaa tafi da ita sbd haukan data ringa zubawa tana kwacewa amma babu wanda yabi ta kanta aka tafi da ita ko fuskan kowa bata gani ba sai Hajiyar Samad wadda itama bata bayyana ba gabaki daya tana dai addua da fatan Allah yasa ana zuwa a banka mata allurar mahaukata ta qarasa haukacewa batareda ta dawo hayyacinta ba bare ta samu fadawa mijinta Samad yace SANAAH tasa ce kokuma ma yasan Samad ya taba saninta.

Ana tafiya da ita kuwa tin a mota suka daureta a gadon da zaa isa da ita tana wani irin ihun da fizge fizge daga karshe allura sukai mata wadda ta saka jikinta sakewa a take tana rufe idanuwanta ahankali daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba.

SANAAH komawa taso yi gurinsu Dr Mum amma sam bai bari ba duk rigimar dataso yi duk da batada karfin rigimar karshe dai anan su Dr Mum din sukazo suka dubata anan ne suka san abinda ya faru duk da bawai SANAAH din ta fada bane ganinsa da hannu a daure yasaka Maamah tambayan abinda ya samesa.

Jin hakan data faru din ya saka Maamah jin gwara zaman SANAAH din a gurinsa for now tinda a bangaren Meenah din suke yanzu.

Da daddare zazzabi ne ya taso mata jikinta yayi zafi sosai kuka da damuwan datake ciki dan haka magani ya bata bayan taci abinci tukuna sukai shirin bacci suka kwanta tana cikin jikinsa yana rungume da ita sukai bacci yana jin zafin jikinta na shigar jikinsa har kusan tsakar dare sosai tukuna zazzabin ya sauka dan haka ya dan qara musu Ac kadan suka samu bacci mai nutsuwa ya daukesu.

Washe gari da Safe da kansa ya nemi Fammah wadda ta tashi da shirin zuwa asibiti sbd jiyan ma taje amma bata samu ganin Mum dinba.

SANAAH na bacci bata tashi ba dan haka daga shi sai Fammah dinne a palonsa ya riqe hannunta cikin nasa yayi magana da ita sosai cikin kaunarta mai girma datake ransa da jininsa ya kuma fahimtar da ita abubuwa da dama akan lamarin tareda bata tabbacin yana yiwa SANAAH So daya kai tsaye da bazai taba iya rabuwa da itaba batareda boye mata ba sbd bayason kowace irin tinani shiga kanta koda daga bayane dazai hana zuciyarta da tinaninta sukuni.

Shiru tayi jikinta yayi sanyi sosai taji gabaki daya tana buqatan break daga kowa da komai zuwa gaba idan kanta da zuciyarta sunyi digesting komai dan haka kai tsaye ta shiga jikinsa ya rungumeta ta bude baki tace

"I need a break from all this Dad ina fatan zan samu wannan daman"

Numfashi mai sanyi ya sauke tareda sake rungumeta yana kissing tsakiyar kanta yace

"Imran will arrange everything"

Bude baki tayi cikin tsananin sanyin jiki da radadin dayake tsananin cinta tace

"Dad nasan akwai hukuncin daka tanadarwa Mum akan abinda tayi,
Dad kayi hakuri ka sassauta mata sbd ba haka take ba a baya,
Dad ina rokon mahaifiyata taci albarkacina idan har a hukuncinka akwai na kasa cigaba da zama da ita ka maidata kasarta acikin rashin hayaniyar da zata taba mutuncinku Dad,
Kayi hakuri dan Allah ka yafe mata Dad"

Shiru yayi batateda yace komaiba saima wani ja da idanuwansa sukai sbd irin kauna da son dayakewa yarsa yana jin radadin abinda takeji a tareda nasa radadin na abinda uwarta tai masa.

Baice komaiba shafa kanta kawai yayi ta miqe

Please Login or Register in order to submit comment