Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

komaiba na ci ko sha drip ne da allurai kawai ake bata ba bata lokaci.

Raheem ma a hannun fatima take ganinsa wanda shima ake cikin tashin hankalin yunwar dayake ciki dan kuwa kuka yakeyi sosai ida yatashi.

Yanayin halinda Raheem yake ciki ya sake daga hankalin jeerahs da ita kanta fatima da mahaifin fammah wanda abubuwan sukai masa yawa ga Amminta a kwance gata a kwance babu me sauki a cikinsu.

Shi kansa hakeem dayake can sabon tashin hankalin ya shiga duk da har lokacin baa sanar dashi komaiba na abinda ya samu din me tada hankali.

Likitocin yara manya aka nema suka zo suka dubasa suka bada shawarwarin abinda ya kamata take aka siyo duk abinda sukace da madara kaman zaa bude shagonta.

Fatima aka nunawa komai da bayanin komai na yanda zata ringa basa har lokacin basu bawa tata haihuwan mahimmancin daya kamata suyi tinanin abin zai mata yawa ba.

Ita kanta fammah dake kwance tana dan fahimta da jin wasu abubuwan tausayin fatima tafara yi ganin irin wahala da dawainiyar datake fama da ita a cikin kwanakin da suke tafiya na jinyarta da fama da jarirai guda biyu dama kuma ita kanta da jegon takeyi amma ba wanda ya tina da hakan.

*****wata irin jinya me nauyi da azaba da mawuyacin hali fammah takeyi da babu sauki a cikinta,

Babu daren da bata wani irin kuka mara sauti da taba zuciyar me kallo dan hakanne itada fatiman suke zaunawa suyisa a tare zuciya da gangar jikin kowannensu tana quna,

Fatima rayuwa tayi mata wani irin nauyi a dan lokacin sbd itama lafiyar neman gagararta takeyi sbd jikinta dayake danye amma wahala da dawainiya babu wadda bata yi.

Fammah na cikin mummunan qunci da baqin ciki da dacin zuciyar da takejin kaman zata mutu ne tabar duniya,

Iyayenta na can a cikin mummunan halin jinyar Amminta datakejin kaman bazasu hadu ba hakama mahaifinta tasan yana gap da kwanciyar shima matiqar jikin mahaifiyarta na sake rikicewa a kowane lokaci hakama nata jikin,

Koyaushe ya kirasu kwarin gwiwa yake bata yana danne dacin halinda yake ciki yana tabbatar mata da indai fatima na tareda ita hankalinsu zaici gaba da kwanciya suyi jinyar Ammin dakyau.

Hakeem ma fatima ce wadda ke saka zuciyarsa dan samun qanqanuwr nutsuwa akan fammah wadda a yanxu ta sallama ta cire rai daya rayuwa kwata kwata mutuwar kawai take jira.

A lokacinda akaiwa RAHEEM HAKEEM JEERAH nadin sunansa a tare da dan fatima akai musu yanka da komai akai musu yankan ragunan suna da shanu akai sadakarsu gabaki daya.

Tinda akai yankan sunan babu wata hidimar sunan da zaayi sbd jikin fammah dake kwance har lokacin.

Satinta uku a asibiti harda kwana hudu anata fama jinya ba sauki kafin aka sallamota tareda shawarwarin likitoci akan kada a fita da ita wajen da akeson fiddata a yanzu sbd yin tafiya da ita zai iya janyo matsalar da zaa iya rasata ayi hakuri ayi jinyar a hankali idan tayi healing ko yaya ne sai a fita da ita.

Wannan shawarar dole aka dauka aka dawo da ita gida aka bude babin jinyar da baa gane komai sbd tinda fammah tasan abinda ya gama samunta a ranar ciwonta dawowa yayi sabo sbd tashin hankalin da kowa ya shiga sai data sake kwana biyu a kwance bata san inda kanta yakeba tukuna ta farfado.

Farfadowanta sabo ya dawowa da fatima jinyarta sbd ko ruwa ake bata dawowa sukeyi,

Fammah dake rashin lafiyar da fatima dake jinyar a tare suke wata irin mummunan rama da bushewa da tsiyayewa sbd halinda kowannensu yake ciki,

Fatima ga nata rashin lafiyar dake cinta,ga jarirai biyu da dawainiyarsu ta tsayar da rayuwarta cak guri daya musamman Raheem da har lokacin ya kasa sabo da shan madarar kuka da wuya yake a cikinta wadda tafara sakasa rashin lafiya mai karfi,
Sannan ga jinyar fammah da itace wanketa itace shiryata itace bata abinci duka a kwance ga damuwan rayuwarta datake ciki da danta dama ta fammah duka.

Ta fige ta lalace ta zama kaman me qanjamau babu sauran kowane jin dadi a rayuwarta.
#MAMUH

GANIN IDO 2026
Mamuhgee
1k
Vip 5k
0022419171 AccessBank maryam sani gummiGANIN IDO 2026
Mamuhgee

11
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
Ahankali ahankali suke tafiyar da rayuwarsu cikin damuwa da dacin jinyar da a yanzu wata uku ake magana kuma har lokacin fammah na jinya sosai sedai ta samu sauki tinda tana zama yanzu hakama tana cin abinci batareda ya dawo ba kuma tana magana sosai sedai babu karfi a tattare da ita da kuzari har lokacin,

Raheem ya koma mara lafiyar kwata kwata shima sbd yunwa data kamasa anyi yawon likitoci dashi har an gaji sam ya kasa zama cikakken lafiyayye dan haka ne aka dawo da kokarin ganin ko zai samu nono ne daga mahaifiyarsa amma a banza sbd koya samu din baida wani amfani sbd kadan ne kuma ita batada lafiyar samun kuzarin shayarwa.

Gabaki daya farin cikin samun Magajin jeerah komawa ciki yake kokarin yi sbd ganin halinda Raheem din yake ciki dan haka suka duqufa nemawa uwarsa lafiya dan ta samu dama da lafiyar shayar dashi.

Suna shiga wata na hudu Hakeem jeerah ya dawo Nigeria garesu dawowan da zai jima bai komaba kuma dawowan da zai jira kiran qarin matsayinsa da zai qarasa sauya rayuwarsa gabaki daya kuma ya qarawa ahalinsa suna da matsayi a idon duniya.

Fatima tafi kowa farin cikin dawowansa sbd halinda fammah take ciki da suke cire rai koyaushe daga tashin kowace safiya.

Dawowan hakeem ya saka fammah fasa kuka a gaban wani karan farko idan ba fatima ta rokesa ya kaita qasarta gaban iyayenta tayi jinya idanma batada rabon tashi ta cika a hannun iyayenta.

Shi kansa ya girgiza da mummunan ganin da yayi mata da mummunan labarin daya tadda wanda ya saka ya rasa ina zai saka kansa ga Raheem ma sai ahankali.

Irin yanda ta daga hankalinta da son komawa gida jinya ya sakasa fara tinanin amincewa amma ganin Raheem, ai iya rasa ya saka ya raba tinaninsa biyu iyayensa kuwa take suka kasa aminta da hakan.

Ita kanta a lokacin tana tsananin tausayin Raheem dan haka ta yanke hukuncin daya girgiza fatima da hakeem a lokacinda ta fada musu buqatarta.

Fatima dataji zancen kaman a mafarki zubawa fammah idanuwanta tayi shi kansa Captain Hakeem kafe fammah yayi da idanuwansa fararen da suka sauya yana mata kallan tausayi sbd tsoron ko ciwon ya taba kwakwalwanta ne.

Hawaye ne masu zafi suka gangaro mata batareda jin komai ko shakka ko fargaba saima kara jin yadda da hakan datake yi sbd tasan ko bata rayu ba Raheem dinta bazaiyi maraicin uwa ba matiqar fatima na raye dan hakanne ma ta yanke shawaran bawa fatima Raheem ta shayar mata dashi nononta.

Kasa yadda da hakan Hakeem yake kokarin yi amma yanda ta gama kashe masa jiki da wani irin kuka da maganganun da suka sakasa tsoro ya saka ya kalli fatima wadda idanuwanta sukai jajir batada zabi sai wanda suka zabar mata.

Hakeem dinne ya kalleta da nutsuwa da qasqantar da kai dan bata haqqinta na raayin zatayi ko bazatayi ba ya roketa hakan.

Fammah ma zuba mata ido tayi cikeda tsananin kaunar ta kasance wadda zata shayar mata da Raheem kada ya rasa ransa.

Batada zabin daya wuce yin duk abinda zai kawo sassauci da abinda akeso a rayuwar fammah da Raheem dan haka ta amince.

Amincewanta ta kawo sauyi me girma a rayuwar Raheem da iyayen nasa harma da Familyn jeerahs da babu wanda yasan abinda yake faruwa sbd daga fammah sai mahaifinta da Hakeem ne kadai suka san fatima na shayar da Raheem da Nasir a lokaci daya sedai kawai aka ga Raheem na samun lafiya yana warwarewa yana jiki yana zama babyn da suka jima suna tsananin son ganin yana zama.

Kulawa sosai Hakeem yake bawa fatima da fammah sbd dukansu suna buqatar kulawan.

Lokaci yaja samun lafiyar Raheem da fara wayonsa ya saka Zuciyar Mahaifiyarsa samun nutsuwa da amincin data kasa samu tin haihuwansa sbd tsoron rasasa,

Hakama samun lafiyarsa ya saka walwala da farin cikin ahalin jeerahs dawowa gabaki daya anata hidimarsa da nuna masa zallan gata da kaunar daya saka yanxu mahaifinsa ake tsananin tausayi ya qare a gurin jinya da kulawa da matarsa baida walwala baida farin ciki masu aiki ne da fatima ke kulawa dashi abinda bai kamata ba sam dan haka kai tsaye kaman saukan aradu iyayensa suka nemasa suka basa umarnin sake aure sbd samun mai kulawa dashi yanda ya kamata kafin samun dawowan fammah daidai tinda lokaci yaja sosai babu wani cigaba.

Da farko tashin hankalin maganar yaji amma daga baya saiya fahimtar dasu sam baya buqatan hakan musamman tinda shi din ba mazauni bane kada ya tarasu ya tafi ya barsu.

Sam Alh babba Ahmed bai yadda da hakan ba sbd babu wani uzurin daya wuce ya auro wadda ba iya shi kadai zata taimakawa ba hadda ita kanta fammah din.

Kasa fadawa kowa maganar yayi sbd yasan qarin aure garesa a yanxu ba abinda yake a tsarinsa bane tukuna musamman a yanzu da fammah ke jinya irim wannan amma yasan bazai kuma iya kauce hukunci idan iyayensa suka yanke ba.

*****Maganar qarin aurensa ta saka yaji yana son kai fammah din gida yanzu sbd kadama taji kota sani gwara ta tafi daga baya idan ta samu lafiya zai sanar mata sbd lafiyarta.

Su kuwa iyayen nasa babu bata lokaci aka fara shirin hadasa aure da daya daga cikin yan uwansa amma kowacensu nada maneminta kuma suna son juna dan haka aka ba bata lokaci kuwa aka hadasa da yar Ambassador Nuhu Sultan.

Auren gata da gata ne zaayi musu dan haka tin a gurin neman auren maganar ta fara bayyana a duniya tana yaduwa.

Fammah da fatima duka basusan abinda yake faruwa ba anata hidima da shirin yin auren wanda Sam ba wata hayaniya zaayiba sbd kada a tada hankalin fammah.

Tinda kwanakin bikin suka matso fammah ta fara rasa gane kanta sbd zuciyarta da lafiyarta dataji suna nauyi dan haka tayi sanyi ta rage kuzari sosai.

Fatima ma da tini ta zama uwar yan biyu ganin yanayin fammah sai ta dauka jikin ne ya dawo tinda yanzu haka yakeyi gashi a lokacin su Raheem din sun wuce shekara daya sosai biyu suke neman cikewa dan haka yayesu daga nono take kokarin yi har lokacin babu wanda yasan Raheem na shan nono.

Ana saura sati daya daurin auren Hakeem daya rasa inda zai saka rayuwarsa gurin sanar da fammah sai gashi kwatsam ta samu labarin daga bakin mai aikinta ta amanarsu itada fatima wato saratu.

Fammah sam bata yadda ba sbd tasan abune da bazai taba yiyuwa ba daga Hakeem dinta da bazai taba mata kishiyaba sbd sanin baa yimusu kishi hakama a daidai lokacinda take cikin wannan mummunan halin na jinya me wuya sama da shekara ga mahaifiyarta data rasa har abada itada haihuwa sedai kallo.

Kati da duk abubuwan bikin dake trending saratu ta nuna mata a waya ta zubawa wayar ido zuciyarta na kasa yadda har lokacin daga karshe ma jintane da ganinta suka dauke dan haka da gaggawa Fatima da itama ta kasa yadda ta kira hakeem din.

Kafin hakeem ya iso gidan daga inda yake nesa sosai mummunan kiran daya qarasa dakatar da rayuwar fammah cak ya shigo wayarta Na rasuwar Mahaifiyarta Ammi.

Mummunan halinda ta shiga dole akai gaggawar kiran ambulance wadda dole itace zata iya kaita asibi sbd ta sanqame.

Duk inda ake shiga tashin hankali fatima ta shiga ta firgita ta rasa inda zata saka kanta.

Kowa ya shiga fargaba da tashin hankalin ganin halinda fammah ta shiga dan haka aka fara gaggawan hada tafiya da ita Morocco din.

Shi kansa hakeem tashin hankali da damuwa kashi kashi yake ciki dan haka ya matsu yaga ta farfado.

Fatima dai bata wani shiga cikin ahalim jeerahs dinba tana gefe da Nasir da Raheem da baya wani yadda da kowa idan ba ita ba sai mahaifiyarsa da baima san itace cikakkiyar uwar data haifesa ba.

Fammah jikinta yayi nauyin da bata farka ba sai washe gari kuma tana bude idanuwanta akan Hakeem suka sauka wani abu yaxo ya danne maqoshinta da kirjinta sedai rashin uwarta datai a yanzu shine abinda yake gabanta dan kuwa ta rasa duniyarta kenan.

Bata cewa hakeem komaiba ko kalma daya bata iya furta masa ba abu daya ta nema daga iyayensa da kanta shine tafiya gida a cikin wannan halin datake ciki taji ta gani.

Iyayen nasa sun tausaya mata sun kuma jajanta rashin mahaifiyarta.

Babu wanda tayiwa maganar auren Hakeem kaman yanda bata bawa kowa damar yi mata maganar auren ba har iyayensa kuwa.

Da zatai tafiyar akace tabar Hakeem tinda ya isa yayewa kuma daman ba wani sosai yake shan nonon nata ba sbd yanayinta da kuma jinyar da zatai ga rasuwan Amminta.

Wani nauyi ne mai tsananin gaske ya sake danne kirjinta kaman zuciyarta zata kama da wuta haka take ji dan haka bazata iya hayaniya ba tinda ba lafiya a tattare da ita kwata kwata.

Fasa tafiya da fatima tayi tace ta zauna da Raheem a matsayin yar rainansa tukuna.

Fatima ta shiga tashin hankali sbd tsoron abinda take gani a zuciya da idanuwan fammah akan duka abinda yake faruwa amma batada zabi haka ta zauna aka tafi da fammah tabar mata 'danta RAHEEM wanda zatai zaman renansa a jeerah a matsayin Nanny.

A daren da zasu tafi sai a wannan daren ne fammah ta fasa wani irin kukan daya saka fatima sauke kai itama tana tayata kukan datake jin yana ratsa dakin da tsananin tsima.

Washe gari da asuba jirginsu ya daga da fammah da Hakeem dama su Daddy da ummah da zasuje gaisuwa dukansu.
#MAMUH
#FLEET RAHEEM JEERAH
#MUHAMMAD NASIR IBRAHIM
#S.A.N.A.H

GANIN IDO 2026
Mamuhgee
1k
Vip 5k
0022419171 AccessBank maryam sani gummi
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

12
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
Bayan tafiyar Fammah daga Nigeria fatima jin tayi tana rasa nutsuwarta da kanta dan kuwa kadaici ne ya sakota gaba da kewa da damuwa,

Babu wanda aka bari a tareda ita a bangaren daga ita saisu Raheem da nasir sai kuma saratu,

Babu me zuwa bangaren kwata kwata sedai duk safiya idan tayiwa su Raheem din wanka suka sha nono ta hada musu da cereal da sukesha zata kai Raheem can gurin su Ummah sbd abinda akace mata kenan.
Acan zai dan wuni saiya gaji yayi bacci a dawo dashi sai kuma washe gari ta sake kaisa.
tin tafiyar batai nisa ba rayuwar ta sauya mata kwata kwata musamman da duka su biyun qyuya ne dasu basa wani yadda da mutane ko Raheem dinma daga baya yadda da kowa a cikin familyn bayan Mamma dinsu fatima da ita suka sani.

***Isar su Dr fammah qasar Morocco har lokacin babu wanda tacewa komai dan kuwa kwata kwata idanuwanta a rufe suke ma ruf babu alaman idonta biyu dan hakane kowa ya qyaleta ta samu dan rintsawar sbd tana buqata ko dan yanayinta dakuma damuwar rashin mahaifiya.

Hakeem dake zaune a kusa da ita ya san idanuwanta biyu dan kuwa yanada tabbacin babu baccin da zai dauketa a rayuwar dasuke kai yanzu,

Duk yanda yaso mata magana ganin suna tareda iyayensu yayi shiru shima dan kuwa ko jirgin dasuke cikinsa zai juye dasu yayi fata fata bazata taba tankasa a yanda yasan zuciyarta.

Kallanta yakeyi a kai akai harya hakura ya dena kallanta ya kama nasa girman sbd kada ya zamana kaman yana shakkarta ne.

Ita dai a nata bangaren batajin akwai wani a cikinsu dama danginsu dake gida da suka rage da kowace qima ko daya a idanuwanta jinsu takeyi tamkar wainda zama guri daya dasu yana danne numfashinta.

Motocin da familyn Jeerahs din suka tanada ne suka taho airport suka daukesu guda uku na alfarma kai tsaye gidan iyayenta suka nufa.

Suna isa koda fammah ta hada ido da mahaifinta wata irin rawa jikinta yafara ahankali kafafunta na kasa daukanta sbd sama da shekaru uku kenan bata sakasu a idanuwanta ba tin wani zuwan datai ganin gida ta koma,

Kasa iya daga kafafunta tayi ta sauke kanta ahankali wasu irin hawaye masu tsananin zafi suna gangaro mata abbun da kansa ya taso ya iso gareta daidai Hakeem ya miqa hannu zai kamata sbd har lokacin daman bata iya tafiya ita kadai da kanta sai an taimaka mata.

Abbunta ne shima ya miqo mata hannunsa ta kama a sanyaye batareda ma tako kalli inda Hakeem yake bare ta nuna tasan da mutum,

Kuka ne mai karfin gaske ya taho mata take mahaifinta ya rungumeta yana lumshe ido tareda sauke ajiyan zuciya.

Ciki sukai gabaki dayansu zuwa palon Abbun da babu mutane sbd basa zaman gaisuwa tinda akai janaizar ta aka kaita kowa yayi gaisuwansa ya watse dan haka koda aka kwana zuwa yau babu kowa duk anyi gaisuwan an watse sai iya qanwar Ammin data taho daga Cairo da babban 'danta.

Zama akai tsakanin Abbu da familyn jeerahs sukai gaisuwa tareda jajantawa da nuna kulawa kafin suka tafi masauki bayan sun dan jima sosai a gidan.

Tinda suka taho ciki akai da fammah dan haka har suka tafi basu sake ganinta ba Hakeem dake tsananin son ganinta da magana da ita haka yaga babu alaman ma zai iya maganarta dan haka suka tafi.

Kukan dukkanin baqin ciki da kunci da kadaicin dake cike zagaye da rayuwarta fammah ta sake tana jin rayuwa ta gama juya mata bangare mara dadi sbd a yanzu batasan tayaya zata fuskanci wannan masifar rayuwar ba babu Amminta,Amminta ta tafi tabarta a rayuwar da babu komai sai son zuciya da son kai tareda zalinci,

Irin kukan datakeyi da yanayinta da suka gani mai muni da tada dukkanin gashin jiki ya saka duk karfin halin mahaifinta da manyancinsa fasa wani irin kuka yana jin tsananin dacin mutuwar rayuwar yarsa daya tak hakama yana jin gwara da Allah bai nunawa Amminta ita ba a wannan mummunan yanayin data koma kamar wadda take dauke da qanjamau dan kuwa hatta haske da lafiyar farar fatarta duk sun tafi koina qashi ne a jikinta kawai yake gani.

Ita kanta qanwar Amminta Anne kuka ta fasa tana rerawa jikinta nawata irin rawar tashin hankalin ganin Fammah a hakan ma wai tana aure a familyn da suke billionaires a can qasar.

Ayau da suka ga yar Ammin a gabansu suke asalin kukan rashinta a cikin mummunan yanayi.

Kukan mahaifinta shine abinda ya qarawa yanayin muni da tashin hankali.

Kwana sukai a cikin damuwa me nauyi da qunci babu kowace irin farin ciki a gidan da mutanen gidan ga damuwar Raheem da aka baro data saka mahaifinta jin kaman ma zuciyarsa zata buga dan haka washe saida shima aka kawo masa likita ya dubasa.

Jeerahs washe gari ma sun sake zuwa suka wuni a gidan zaman gaisuwan da babu kowane sakewa a yanayin dan Abbu ba lafiya bai iya fitowa ba haka sukai zamansu suka tafi ko fammah bata fitoba sbd sunsan yanayinta.

Hakeem ne ya shiga har can ciki dakin Amminta ya dubota tana zaune ta dunqule guri daya idanuwata sunyi jajir sun kumbura ba kyan gani.

Duk yanda yayi magana da nuna mata kulawa ko kadan bata iya juyowa ta kallesa ba dan kuwa a duk lokacinda zai wanzu a guri zuciyarta da idanuwanta tareda jinta dauke mata sukeyi dan haka har yayi maganganunsa ya gaji ya miqe ya fice babu abinda taji bare juyawa ta kallesa.

Bayan tafiyarsu ranar saida suka kwana biyu basu sake zuwa ba gidan banda Hakeem da kullum yana gidan amma sam ko Abbun bai samun ganin fammah din kawai yake gani sai masu aikin gidan itama tin yana jin karfin gwiwa harya rasa abin fada mata sbd batama responding bare yasan akan matakin datake na ta fahimci abinda yakeson fada mata.

Sati biyu suka share a qasar suka tattara zasu koma suka tafi gidan sukai musu bankwana dan Abbun ya fito sun tattauna akan zasu tafi da Fammah daga nan zaa wuce da ita india ne asibiti.

Abbu bai musu ba ya amince musu da fatar allah yasa a dace dan bayason hayaniya a yanzu da rayuwarsa data yarsa suke cikin duhun damuwa da kadaici.

Bayan tafiyar su Alh babba masauki Hakeem ya shiga har ciki ya samu fammah ya sanar mata maganar tafiyarsu a jibi.

Dagowa tayi a karan farko ta kallesa da idanuwanta da suke jajir a bushe kaman yanda takejin ko zuciyarta ta bushe babu abinda takeji.

Kallansa datai ya sakasa sauke numfashi da ajiyan zuciya sbd yasan lokacin maganarta yayi.

Bude baki tayi a natse da sanyi tace

'Aure zakayi HAKEEM?

zuba mata ido yayi yana kasa bata amsa sbd bayason sakata a wani mummunan halin.

Bata dauke idanuwanta akansa ba ta maimaita tambayarta da cewa

'Hakeem wata macen zaka kuma aura bayan ni??
Hakeem sbd rayuwata ta lalace ne bazan iya sake haihuwaba zaka sake aure?
Hakeem bazaka iya hakurin na samu lafiyar dana rasa ba?
Hakeem menene saurin da kukeyi?
Hakeem menene amfanin rayuwata a cikin familynka????

Dakatar da ita yayi da cewa

'Karki saka a ranki cewan sbd kin rasa lafiyarki ko haihuwa ya saka zaayi wannan auren Fammah sbd kinsan kece soulmate dina,bazan taba son kowace mace ba a duniya bayan ke,
Kece ni fammah,wannan auren aurene kawai na umarnin da bazan iya kaucewaba....

Fammah bata girgiza ko jin kalamansa ko dayaba a jiki da zuciyarta saima wani dacinsu dataji yana ratsata dan haka kai tsaye ta sake kallansa da jajayen idanuwanta tace

'Ka fada musu bazaka iyaba,
Bazaka iya hada matarka da kowa,
Bazaka iya auren kowace macen ba,
Bakada raayin kara auren kowace mace har karshen rayuwarka,
Bazaka iya cika wannan umarninba ka fada musu sbd idan ka fada babu wanda zai maka dole tinda kai ba yaro bane shekarunka sunkai har sun wuce...

Da mamaki ya kalleta yanda take maganar kai tsaye cikin kaifin harshen daya hango matakin datake tsaye akai kenan.

'Iyayena ne ake magana anan kina tina hakan ko??

Wani numfashi me zafi ta fidda tana sake riqe nutsuwanta sbd kwakwalwanta dake neman bugawa da abinda take ji tace

'Hakeem jeerah ni fammah wallahi tallahi matikar zakai wannan auren nabarka na bar aurenka har abada bana fatar sake ci gaba da zaman aure da kai da familynka......

Da tsananin mamaki ya kalleta yana shiga shock da bugawan zuciya ya kafe idawanta dake bushe da kallo sunyi jajir shima nasa jan sukai ya bude baki yace

'Fammah,kinsan me kike fada kuwa?
Kin rasa hankalinki ne ko me?
Akan wani auren kike cewa kin gama naki auren?
Idan nayi auren zai raba mu ne kokuwa zai rage soyayyar dake tsakaninmu??

Lumshe idanuwanta tayi ahankali kalamansa na ratsata sbd auren dai yi zaiyi bazai fasa ba ko maganar dakatawa ta samu lafiya ba da futa quncin rashin mahaifiyarta data rasa ba.

Miqewa takeson yi a hankali tabar masa gurin amma ta kasa tashi hannuwanta na wata irin rawa ta boyesu a cikin jikinta tana jin zuciyarta kaman zata fashe.

Duk maganganun dayake yi cikin tashin hankali baiga alaman tana jinsa ba sbd idanuwanta da alamar sun bushe batareda yasan zuciyarta wani irin kuna da kuka takeyi ba me tsananin abinda yake shirin yi mata ba na zabar auren wata ba a cikin wannan halin datake ciki datake tsananin buqatarsa fiyeda koyaushe ba na rayuwar aurensu.

Miqewa yayi ya fice daga dakin ko gani sosai bayayi ya nufi gurin Abbu muryansa harta fara shaqewa ya zauna gabansa ido jajir yafara jero masa abinda yake faruwa wanda ya saka Abbun zuba masa ido bako kyaftawa sbd baimasan da maganar aurenba dan fammah bata fada musu ba.
#MAMUH
#JEERAHS
#DR MUM FAMMAH
#BROTHERS
#RAHEEM HAKEEM JEERAH
#MUHAMMAD NASIR IBRAHIM

GANIN IDO 2026
Mamuhgee
1k
Vip 5k
0022419171
AccessBank maryam sani gummiGANIN IDO 2026
Mamuhgee

13
*_HARGITSI_*
By
*_TALATU ZAKI_*
+201031621512
*Duk maaboci kuma masoyin karatun littafin Hausa to karya wuce labarin nan bai karantasa ba sbd duk wani tsari da labari yake buqata to akwaisa tattare a cikin labarin HARGITSI Na TALATU ZAKI*🔥
https://chat.whatsapp.com/ERrtA3G4obwBQzBTiJUad3?mode=gi_t

*********
Abbu har a cikin zuciyarsa wani irin zazzafan kishin yarsa da bacin rai ne ya rufesaai tsananin daya kasa dauke idanuwansa daga hakeem dayake kallansa yana fada sbd zai qara aure fammah na cewa zata rabu dashi.

Numfashi me sanyi da mutuwar jiki Abbu ya sake yana jin nauyin kirjinsa na qaruwa ciwonsa na son tasowa amma cikin karfin hali ya bude baki yana kallan hakeem din yace

'To kai Hakeem da gaske auren zaka kara a yanxu da iyalinka batada lafiya sosai ko tafiya fa kanaga bata iyayi sai an riqeta,
Batada cikakkiyar lafiyar komai da komai harma da kwakwalwa dan kuwa ayanzu datake cikin ciwon da fiyeda shekaru biyu tana jinya a kwance komai sai anmata ga mahaifiyarta ta rasa ga danta kun rabata dashi kuma zaka iya aure

Please Login or Register in order to submit comment