Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da gasken gaske yakeyi ga kuma fammah ga kuma duniya bayyanar cikin kawai zatashi batareda tinawa ma aurenba bare asan cikin na waye kuma dai koba komai ciki kafin a karba aure da tarewa? Ina zasu saka kansu da duka wannan tashin hankalin wanda basu taba tsammanin zuwansa babban fatan yanzu dai Allah yasa babu abinda ya hada SANAAH da ciki a yanxu.

SANAAH da kanta ke juyawa sosai tsabar shock da tashin hankali kasa daukanta kafafunta sukai ta zame zata zube qasa safiya ta riqota tana kallan Mommyn a tsorace da fargaba tace

"Mommy bafa ta da komai"

Wani kallo mommyn tayi mata tana maida kallanta akan SANAAH din tace

"Allah yasa hakan ne sbd babu wanda ya shiryawa hakan"

Sake shiga mummunan tashin hankali SANAAH tayi tana rasa tinaninta ko daya dazai bata ikon tinanin ma a wane babin take dan haka da qyar su mommyn suka kaita daki tana kwantawa wani mugun zazzabi mai karfin gaske ya rufeta wanda dole ya saka Safiya kwana dakin tareda su sbd amai ta ringa yi cikin daren kafin safe tayi wani mugun laushi ta firgice gabaki daya.

Maamah ta aiko safiya ta kawo mata wayarta da Raheem din ya kira yana nemanta bata iya wata magana ba tana jin muryansa kuka ta fasa masa ahankali sosai kawai.

Shiru yayi tsigar jikinsa na tashi gabaki daya daga inda yake dan haka ya miqe tsaye daga zaunen dayake a hankali tareda isa bakin windown dakinsa dayake Miami iska ta ringa ratsosa tana rage wani zafi da zufan dayaji yana tsatsafo masa a take.

Cikin wata sauti mai nutsuwa data ratsata ya kira sunanta sukai shiru su duka biyun tsawon seconds kafin ya sake ambatar sunanya yana cewa

"Are you okay?
Lafiya dai?
Akwai matsala ne?
Me yake faruwa?
Bakida lafiya ne?

Shiru tayi tana kasa cew komai hawayenta na tsananta gudu jin hakan ya sakasa bude baki baki yace

"Ina famma?

Sai a lokacin ta iya bude baki da rashin karfi tace

"Tana can bangaren"

"Ok bara na kirata naji abinda yake faruwa"

Katsesa tayi ahankali da cewa

"Bata saniba fa,kuma babu komai banda lafiya ne kawai"

"Kawai???? Yayi maimaicin kalman tata ta karshe yana fidda wani numfashin dataji sa har cikin wayar ya riqe kansa dan ba qaramin tabasa kukanta yayi ba yace

"Ok shikenan ki huta Dr zatazo gidan ta dubaki"

Bai jira gardaman da zatai masa ba ya kashe wayar yana jefarwa akan sofa da saka hannuwansa duka biyu aljihun wandonsa yana sake tsayuwa a gaban iskan datake ratsosa sbd basa daidaici.

Imran ne ya shigo batareda ya juyoba ya katsesa a natse daga abinda ya shigo fada masa yace

"A nemi Dr bushrat taje yanzu ta duba abinda yake damun Baby SANAAH"

Gyada kai Imran yayi yana cewa ok ya juya ya fice yana daga wayarsa dan neman Numbern Dr Bushrat din dayasan yayi saving a waya tin last time.


SANAAH kuwa jin abinda ya fada ya saka hankalinta sake tashi gashi ta kasa iya barin Dr Mum ta dubata ta tsaya akan mura ce ke damunta sosai hakan sbd batason a dubata kaman yanda Mommy ma take shakkar a dubata din.

Kokarin nuna ta warke tafara yi duk da jikin yana qin yadda da hakan sam gashi ta kauracewa Mum da fammah sosai da dr mum zaman daki takeyi sbd tsoron abinda zasu iya gani a tattare da ita kasancewansu duka likitoci.

Fammah tsananin mamaki da tausayin SANAAH din takeji ganin yanda take fama fashi sam taqi yadda kowa ya dubata hakama taqi zuwa asibitin da Fammah ta matsa sai sun tafi din.

Mommy da safiya da ita ne a cikin wata irin fargaba wadda duk suka rasa sukuninsu Mum kuwa kwata kwata hankalinta ya karkata akan mijinta da yanzu take jin kaman suna nisa dan haka ta sauya shawaran tattarawa tabar fammah ta samesa a Miami dan kuwa hadda tsananin kewansa tana ji da buqatansa dan haka hankalinta baya kan SANAAH da ciwonta sam tanata kokarin nemawa kanta tafiya zuwa Miami batareda sanin kowaba.

SANAAH duk inda tashin hankali yake tana ciki wanda ahankali su Maamah suka fara ganewa musamman mutane da batason shiga sam da a tsarge take gidan tako ina sbd manyan dake zagaye da ita.

Yau tinda yace zai aiko a dubata ya sakata shiga muguwan damuwa da fargaba dan haka daga karshe kasa jiran zuwan Dr bushrat tayi zata sameta asibiti ta dubata acan inda babu kowa dan haka tin kafin fammah ta shigo bangaren batareda sanin kowaba tabar gidan itada safiya itace mai tuqa motar wadda daga ita har safiya a cikin fargaba suke sbd safiya tsoro da tashin hankalin datake ciki shine Mum din fammah zata iya kashe SANAAH akan hakan batareda kowane tinani ba sbd silar tsananin tsanar datake tsakaninta da Hajiyar samad yanzu sbd maganar kishiya ne kadai gashinan ta tsaneta babu balai da masifar da bata kirawa hajiyar sbd hakan wanda tasani da zata samu dama ko kan hajiyar zata iya bi da mota sbd kadai tayi maganar Fleet da qarin aure.

Ko mommy da suka baro gida a cikin zullumi take tana fatar allah dai ya saka ba ciki ne da SANAAH ba kafin tarewanta ko Dad batasan da wane idon zasu kallesaba ga tashin hankalin Meenah da basuma san daga ina lamarin zai fara ba gwara ace babu komai har sai an sanarwa meenah anyi tarewa.

Suna isa Dr bushrat din na fitowa harabar asibitin zata nufi motarta ta tafi JEERAHsV din sbd kiran da Imran yayi mata akan sakon Fleet.

Parking sukai kusa da motarta tana ganin bumbern da sunan jeerahs ta dakata saida SANAAH din ta bude motar ta fito a natse sanyeda dogon hijabi har qasa idanuwanta sanyeda glasses data hana bayyanarda kumburin idanuwanta data sha kuka gurin waya dashi din.

Da kulawa da sakewa tareda girmamawa Dr ta kalleta tana cewa

"Patient din tawa ce ta taho da kanta bayan can nayi gurin dubaki,
Yaya jikin?
Mu shiga daga ciki to"

Ciki sikai SANAAH na dan bude baki da sanyi tace

"Alhamdllh naji dan sauki"

Office din Dr bushrat din suka nufa tana kokarin sake tambayar jikin SANAAH din da dan karantar yanayinta tin daga nan dan haka suna shiga ruwan sanyi ba sosaiba ta dauko mata daga fridge tazo ta zauna suna fuskantar juna tace

"Menene matsalan?
Gashinan dai i can see you look pale and anxious when last kika samu period naki??

Qarasa mutuwa jikin SANAAH yayi da tsananin gaske ta dan dago idanuwanta da sukai jajir ta kalli dr din ta bude baki tace

"I cant remember"

Numfashi dr bushrat ta sauke tana cewa

"Taso muje na duba wani abu"

Miqewa SANAAH tayi daqyar gabobinta ba karfi ko kadan tabi bayanta.

Anan suka bar safiya tsawon mintina masu tsayi sosai kafin suka dawo office din suka zauna idanuwanta sun sake fadawa da sauyawa tayi wani irin sanyi koina jikinta cikin damuwa mai tsananin gaske take ciki dr ta kalleta cikin lura da yanayinta dan haka sai batai wani dabbakawa ba tace

"SANAAH ciki ne dake kusan wata biyu da kwanaki"
#MAMUH
09033181070
[13/06, 2:08 pm] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

114
Wani amai ne ya taho mata da karfi da tsananin sauri dr tayi toilet din cikin office din da ita tafara yinsa cikin galabaita da tashin hankali.

Daqyar ya dakata suka fito jikin SANAAH din na dan rawa.

Ruwa da wani dan magani ta dauko ta bata tasha ta danji sauki sauki ta kasa cewa komai itama dr din kasa cewa komai tayi sukai shiru safiya ma zuru tayi.

Dr ce ta yanke shirun da cewa

"Kada ki saka damuwan komai a ranki fa sbd Kinga yanayinki a yanxu sakawa ranka fargaba ko tashin hankalin koma menene zai iya saka cikin a hadari harma dake so pls be very very cautious"

Magani ta dauko mata na masu ciki su folic cid da sauransu ta bawa Safiya ledan ta rakosu har mota.

Tana barin asibitin Dr Bushrat da sukai alkawarin duk abinda ya samu SANAAH zata sanar masa tin wancan lokacin daukan wayarta tayi kawai tai masa sending sakamakon da scanning datai mata.

SANAAH kuwa kai tsaye gida ta nufa zazzabi me karfi na rufeta driving dinma cikin tsananin karfin hali tayisa suna isa ko parking batai daidaiba ta tsaya daidai nan motar hajiyar Samad tayi parking a gefen tata motar suka fito kusan a tare hajiyar na waya idanuwanta suka sauka akan SANAAH wani mummunan shock ya shigeta ta tabbata kenan SANAAH dince ta gani a asibiti tareda Dr bushrat sun shiga dakin scanning ita kuma taje duba wata yar kaninta data samu miscarriage.

Rikicewa tayi a take sbd kallo daya tayiwa SANAAH din wadda suke kusa batama tsaya lura da hajiyarba ta wuce ta ga alaman mai ciki a tattare da ita kanta yai mugun sarawa zufa ya keto mata dan kuwa wlh bazata yadda da Raheem ya amsa auren SANAAH ba bare ciki sedai idan wani gurin akayo matashi wanda wlh saita tona duniya taji idan kuma na Raheem ne wlh sai duniya taji shima batasan lokacinda a rikice bakinta ya furta

"Yanzu SANAAH dince da ciki kokuwa gane gane nakeyi na shiga uku"

Samad da kaman saukar tsawa yaji zancen jin yayi kansa ya dauke wuta dip ya bude baki muryansa na sarkewa da shock din da bai taba shigaba a rayuwarsa yace

"SANAAH danake jira ce da ciki ko kuwa wata SANAAH din???

A rikice hankalinta na sake tashi tace

"Allah yasa cikin shege ne a jikinta dan idan na Raheem ne bugawa zuciyata zatai na shiga uku"

Kashe wayarta tayi tana sake shiga tsananin mamaki da rikicewa tayi cikin gida.

SANAAH kuwa sbd sanin kowa yana palon su mommy ya sakata juyawa ta nufi bangarensu Fammah ta nufi dakinsu ta zare takardun asibitin daga jakarta ta saka a cikin wata qaramar jakarta ta maida cikin kayanta ta ajiye ta fito nufi bangaren suna shigowa kuwa fammah ta amsa jakarta tana dubawa da tsokanar inda taje.

Bata iya cewa komaiba ta wuce ciki tana dan boye damuwanta.

Daki suka nufa fammah na biye da ita tana magana kai tsaye bathroom ta shige.

Tubewa tayi ta sakarwa kanta ruwa tareda fashewa da wani irin kuka tsawon lokaci kafin ta fito.

Safiya ce ta kawo mata abinci a tray ta ajiye mata tareda juyawa da maganin data shigo dashi bata ajiyeba ganin fammah a zaune.

Zaunawa tayi bayan ta shirya ta kasa cin abincin da aka ajiye tareda kasa kallan fammah tai shiru tana dan kwantawa kadan bayan tayi sallah.

Kasa hakuri fammah tayi ta kalleta da bada dukkanin nutsuwa tace

"Akwai abinda yake faruwa dake wanda bansan menene kike kasa fada mun ba,
Akwai wani abin ne?
Menene matsalan?
Can you pls tell me right now sbd dai duk kin sakani damuwa wlh"

Girgiza kai tayi tana sake kasa iya kallan famman.

Shiru sikai daga nan fammah ta miqe ta fice daga dakin.

Tana fita mommy na shigowa kallo daya tayi mata ta nemi guri ta zauna bata ce kala ba dan a fuskan SANAAH din komai dai ya bayyana.

A daki ta wuni har dare bata kuma fitowaba sai da daddaren harta kwanta ta dauki wayar Mommy a karan farko rayuwanta ta saka kiransa kaman bazaa dagaba sai aka daga kiran tana jin muryansa ta fasa masa wani lafiyayyan kuka tana cewa

"Ni mutuwa ma zanyi sbd bansan ya zanyi da rayuwata ba"

Kalamanta suka sakasa yin shiru sbd tin dazu sun kasa samun wayar Dr bushrat dan haka miqewa tsaye ya sake yi kansa na balain sarawa da abinda ta furta masan ya bude baki zaiyi magana sai kuma kawai ta kashe wayar gabaki daya dan ko magana bataso.

Bin wayar yayi da kira yaji shiru dan haka ya saka kiran Imran yana dauka kai tsaye yace ya siya tickets din tafiyarsu.

SANAAH kuwa kwana tayi kukan gaske koda gari ya waye da wani sabon ciwon ta tashi wanda ya saka Mommy yanke shawaran sanar dasu Dr Mum dan haka kai tsaye dakinta ta nufa.

Hajiyar Samad ma da babbban tashin hankali ta tashi kaman zata dora hannu akai ta zunduma ihu sbd Samad ya haukace a lokaci daya ya zare ya siya ticket din dawowa.

Batajin zata iya barin ya dawo yayi abinda zaa aikasa lahira tsakanin ubansa da Raheem dan haka gwara ta tada balai a gidan dazai hana a abinda samad zai dawo yi fitowa dan haka bangaren Ms Meenah ta isa tinda tanata kiran Samad din tin cikin dare bata samu ta tabbatarda yana hanya kowane lokacin jirginsa zai iya dawowa.

Tana isa bangaren bata tadda Meenah ba fammah data fito daga bedroom dinta tafara gani cikin sakewa da nuna hankalinta a kwance yake tace

"Aa fammah kece kadai kika tashi?
Ina SANAAH da Mum dinki basu farka bane?
Jiya ma ko dana ga SANAAH a asibiti gurin masu awon ciki na dauka tare kuke ashe ita da Safiya ne ko ganina basuyiba Allah yasa dai lafiya?
Meya kaisu gurin masu ciki?
Waye ba lafiya??

Da mamaki fammah ta dago ta kalleta tana ma kasa daukan bayananta dan haka sai kawai ta gaidata tace ai Mum bata fitoba.

Wani zancen ta kuma kwatsawa cikin nutsuwa da rashin nuna damuwa da hikima kafin ta juya ta fice tana cewa daman zuwa tayi su gaisa da Meenah tinda suka dawo basu gaisaba.

Tana fita bin bayanta da kallo fammah tayi tana mamakinta da maganganunta marasa lissafi.

Ficewa taso yi zuwa bangaren su mommy amma kuma sai zuciyarta ta sakata juyawa dan dubo katin asibitin SANAAH dayake dakin cikin wata jakarta qarama dan ganin yana nan ko asibitin sukaje da gasken batareda ta fada mata zataje ba tinda kusan tare suke komai.
#MAMUH
09033181070
[15/06, 9:55 am] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

115
Mommy na isa kofar dakin Dr mum sauke ajiyan zuciya tayi a natse tareda dan bugawa kafin ta bude kai tsaye tana shiga da sallama a bakinta ta nufo tsakiyar dakin daidai lokacin Maamah data biya ta sanar da tanada magana dasu ta iso dakin na dr mum itama ta shigo tana kallan mommyn kafin ta isa ta zauna akan sofa Dr Mum na zaune akan bakin gado ta gama waya kenan da Abbu ta bisu da kallo su dika biyun tana cewa

"Lafiya dai na ganku haka a jere kaman jiki a mace"

Maamah data zauna ce ta bude baki tace

"Zainab ce tace da akwai maganar dazatai damu"

Kallan mommyn sukai duka wadda ta qaraso ta zauna a kan sofa itama tana sauke ajiyan zuciya babu batawa kowa da kanta dayake cikin nauyi lokaci ta bude baki tana dan kasa kallansu su dukan tace

"SANAAH taje asibiti yau akan ciwon datake fama dashi dashi ance ciki ne da ita tsawon wata biyu da satika"

Da wani irin azababben sauri su dukan suka kalleta Maamah dake kusa da ita dafata tayi da sauri hannunta na dan rawa tsabar rudewan jin zancen kaman daga sama abinda suka gama cirewa rai har abada dan haka kokarin bude baki tayi zatai magana sai kuma tama rasa abin fada ta kalli Dr Mum wadda tayi mutuwan zaune cikeda wani irin shock itama dan kuwa kaman bata gama yadda ba sbd Allah kwata kwata bai bata tinanin hakan ba da duba SANAAH din sosai dan haka zubawa Mommy idanuwanta tayi tsawon lokaci kafin Maamah ta yanke shirun da cewa

"Ciki dai cikin haihuwa??
Wani 'dan Raheem zan sake gani a duniya??
Ya Allah kasa ba mafarki nake ba"

Mommy Numfashi ta sauke tareda bude baki a dan sake da jiki sbd ba wai farin cikine batayiba abinda zai biyo bayan bayyanar cikin ne tashin hankalinta tace

"Yaya zaayi da cikin Sbd Meenah da batasan da aurenba haryanzu tukuna???

Wani kallo Dr Mum tayi mata batada energy sam sbd yanda zancen cikin ya daketa ta bude baki tana kallan mommyn da kyau tace

"Yaya zaayi kikace zainab?
To kodai kema bakida lissafin ne kaman Meenah da har kike iya tambayar yaya zaayi,
Yanxu dai ni ina buqatan son duba SANAAH da kaina da kyau na tabbatarda zaman cikin tukuna na fadawa Meenah da kaina dan gwara ta sani dan renan ciki kam ya zama dole a bayyane ba kowace boyo"

Wayarta Mommy kasa tayi da kanta tana yin shiru har Maamah ta miqe tana jin wani irin tsallen da kirjinta ke yi da zuciyarta ke bugawa tana fatan itama ayiwa SANAAH din sabuwar dubawa su tabbatarda idanuwansu ko zata samu jin abinda ya tsayar mata da komai cak ya watse cikin tsantsar godewa Allah da asalin farin cikin da suke jin ba iya dan SANAAH da Raheem bane hadda kaman dan Nasir ne suke ganin kaman zasu gani sbd mutane biyu dayafi so ne a kaf duniya zasu haifar masa 'da ko yar da dayana duniya zaifi kowa so.

Fitowa Mommy tayi tabaro dakin tana komawa dakinta inda ta tadda SANAAH da safiya dake kokarin hada mata dan tea cikin kulawa da tsananin tausayi da mutuwan jiki ga dukansu itama guri ta nema ta zauna a dakin batareda tace musu komaiba ta dauki wayarta tana saka kiran Al'amin da basu taba boyewa juna komaiba tana tinanin fada masa ko kuma barinsa yaci gaba da aikinsa cikin nutsuwa kada ta damar dashi duk da tasan bazaiji komaiba tinda an nuna masa shi cewan SANAAH din ta jima da tarewa sbd hanasa damuwan zamanta gida har lokacin.


*******fammah kuwa tana shiga dakinsu inda jakunkunansu suke a jere ta nufa ta fara duba jakar SANAAH din datasan takardunta suna ciki taga bata ganta ba dan haka ta dan dakata tana tinanin da gaske hajiyar uncle Samad din take kenan SANAAH taje asibiti ko me??

Wani irin nauyi kirjinta yayi kanta ya sara da dan karfi ta fitarta wani numfashi mai dumi da fitarda kowace irin tinanin yadda da kowace maganar kowane dan adam mara kyau akan SANAAH dan haka tayi kokarin yakice tinanin a kanta ta juya ta fice daga dakin tana jin takaicin Hajiyan Samad din dataso saka mata wani mahaukacin rashin tinanin wai SANAAH a gurin awon ciki.

Tana isa bangaren su Mommyn kai tsaye dakin mommy datasan SANAAH na ciki ta nufa.

Tana shigowa dagowa Mommy tayi ta kalleta tana dan kokarin sakewa da faraarta tana amsa gaisuwanta tana tambayar Mum dinta.

Gurin SANAAH din fammah ta kalla wadda ta dago ahankali ta kalli fammah din jikinta babu kuzari ko daya idanuwanta suka si cikowa da wasu irin hawayen data kasa riqewa ta sauke kanta daga kallan Famman tana dan lumshe idanuwanta ta rufe.

Mutuwa jikin fammah yayi itama taji duk damuwa da haushin kanta ya rufeta data iya bin maganar Hajiya harta je bincika dan haka ahankali ta tako ta iso gurin SANAAH din ta zauna a gefenta tareda kwantawa jikinta ahankali tana cewa

"Allah ya baki lafiya My Baby SANAAH"

Wani irin nauyi da damuwa ce ta sake dirowa SANAAH din ta sake rufe idanuwanta tana dan kwantawa jikin fammah din itama batareda ta iya cewa komaiba.

Fammah dataji wani irin zafin zazzabin dayake jikin SANAAH din mai tsanani qara rungumeta tayi tana shafa bayanta ahankali tana mata sannu.

Safiya ficewa tayi daga dakin tana barinsu ta nufi kitchen inda ta tadda mommy tana aiki ta saka hannu suna aiki kowannensu shiru ga abin farin ciki amma tsoro ya hanasu bayyana hakan kuma tsoronsu duka akan abinda zai samu SANAAH ne da bazasu so komaiba.

Suna dakin Dr mum ta shigo duba SANAAH din tana binta da wani irin kallan dayake bayyane da wata irin sabuwar kaunar data kasa boyuwa a idanuwanta taji idanuwanta itama kaman zasu ciko da hawayen data hanasu fitowa dan kuwa ayau indai da gaske ciki ne a jikin SANAAH burinta dana mahaifiyarta zasu cika na samun wata haihuwan a jininsu dasu Allah bai basu ba,
Mahaifiyarta ita kadai ta haifa hakama itama shi kadai Raheem din ta haifa shima sun riga sun fidda ran sun gama yadda da Fammah ce kadai kwansa a duniya da zasu gani wadda ita mace ce wani gidan zata tafi aure ta haifa musu yayan acan wainda ba nasu bane ashe sunada rabon shedar da wani tsatson nasu faga Raheem.

Irin kallan da dr mum kewa SANAAH din ya saka Fammah juyowa ahankali ta kalli SANAAH wadda tai qasa da kanta jikinta na kuma mutuwa sosai.

Kallan Fammah dr mum tayi da kulawa da kaunar datake jin tana mata da ita sa cikin SANAAH din tace

"Fammah ki bawa Rabin ran taki dan dama kadan na dan je wani guri da ita kinji,yanzu zamu dawo ba jinawa"

Kallan SANAAH din tayi da dan boye mamakinta ta saki murmushi kadan tace

"Ok Dr Mum saikun dawo Allah yasa asibiti zakuje a dubata sbd jikin nata dai lafiya taqi kuma koni naso dubata amma taqi yadda"

Murmushi Dr mum din tayi tana maida kallanta akan SANAAH tace

"Ganin takeyi kila kauna bazata bari ki dubata da kyauba"

Dariya famman ta dan yi kafin ta taimakawa SANAAH din ta saka doguwan hijab suka fice.

Suna fita Driver ne yaja su a mota sai asibitin da rabonta da ita sama da shekaru batasan iyaka ba dan kuwa asibiti ce tin asalin farko an ginata ne sbd ita sbd tayi aikinta a cikinta wadda aka sauyata gabaki daya dan kusan an rusata anyi sabon ginin da akai akai ake sauyasa komai a tsare da kyau kaman baa qasar Nigeria ba.

Kai tsaye office din Dr Akin data kira tin kafin su iso ta nufa da SANAAH din wanda shima tinda ta kira ya fito hanyar office din dan tarbanta sbd tin a shekarun baya shine likitan dayake karkashinta gashi yanxu shine babba anan din gabaki daya sai Dr bushrat a mata dan haka akwai sanayya sosai tsakaninta da Dr Akin din.

Yana ganinta da girmamawa da farin cikin ganinta ya iso ya tarbeta suna wucewa kai tsaye office dinsa.

Bayan gaisawa da yan maganganunsu na likitoci kai tsaye abinda tazo yi suka fada wato duba SANAAH din da kanta dan haka waya yayi aka kawo masa scanning machine har office dinsa anan Dr Mum din ta nutsuwa ta zauna da kanta taiwa SANAAH din scanning ta duba komai tana gamawa wani lafiyayyan numfashi mai asalin nutsuwa da mutuwan jiki ta sake zuciyarta na cikuwa da dukkanin farin cikin da rayuwarta ke nema da buqata dan kuwa daga karshe dai zata samu qarin zuriarta datake jin ba iya nan zuriarta zata tsaya ba SANAAH zata basu farin cikin da zai cika zuriarsu insha Allah.

Bataji nauyi ko wata iyakancewaba rungume SANAAH din tayi ahankali tareda kissing tsakiyar kanta tana mata addua da wata irin kauna mai tsananin tsananin karfi ga cikin ta gasken gaske.

SANAAH data sake shiga kunya da tsaka me wuya bata iya warwareba saima jin datai zazzabinta ya qaru dan haka koda suka dawo gida shigewa tayi tai sallah daqyar ta kwanta tana dunqulewa.

Maamah kuwa da Dr Mum ta bata tabbacin cikin Sallah tayi ta nafila ta ringa yiwa Allah godia ranta fes dan haka suka shiga wata walwala da farin ciki abinsu wanda Mum ma data shigo taga alaman ana cikin farin ciki sai itama tahau farin ciki a sake tana jin nata farin cikin itama na tafiyan datake kokarin tabbatuwa tata zuwa ga mijinta.

Fammah data fara shiga rudu akan abinda yake faruwa kasa riqe kanta tayi zuciyarta nata shiga tinanin abinda yake faruwan data kasa ganewa dan haka ta zauna a tareda SANAAH wadda bata samu dan sauki ba sai yamma sosai tayi wanka Maamah ta kawo mata abinci da kanta ta sakata taci kadan ta bata magani wanda fammah bata gani da kyauba amma ta tabbatarda kaman su folic Acid ta gani dan haka kirjinta yayi wani mummunan faduwan data kasa dauke idanuwanta daga kan Maamah din harta fice da maganin a hannunta bata bari ta ajiyeba.

Kasa juyowa Fammah din tayi sbd tsananin nauyin da kowace gaban jikinta tai mata ta bude baki tace

"SANAAH meyake faruwa?
Menene ciwon dayake damunki??
#MAMUH
09033181070
[15/06, 12:37 pm] Dasoo: GANIN IDO 2026
Mamuhgee

116
*_NOOR COLLECTION_*
09035841194
07044204680
Yar uwa kina neman inda zaki siya best,classy and luxury
ABAYA'S
JALLABIYAs
SNEAKER'S
KAYAN YARA
NEW BORN BABIES ITEMS
MAYAFAI (veils)
da idan kika saka sai kallake an tabbatarda kin saka luxury kuma kayan alfarma unique da basu zama ruwan dare a koina ba,
To ki tabbatadda a gurin NOOR COLLECTION luxury shop kika siyawa kanki da maigidanki da yaranki komai 100% tested and trusted.
Ana iya turo orders din wasu abubuwan idan anaso NOOR COLLECTION zasu nemo su kawo muku babu banbanci a saukin kudi ma kudai kawai ku riqe NOOR COLLECTION bazakuyi dana saniba.
EGYPTIAN ADDRESS: NEW CAIRO.
NIGERIAN ADDRESS: Zaria

**********
Shiru SANAAH tayi tareda kasa cewa komai duk da zuciyarta na tsananin son sanar da fammah laifin datai mata amma bakinta ya kasa furtawa dan haka ta sauke numfashi mai sanyi tareda kallan fammah din wadda ta juyo ta kalleta da dukkanin idanuwanta tace

"Ba komai"

Shiru sukai su dukan wanda ya sake saka zuciyar fammah cikin wani irin nauyi da jin rashin sukuni da nutsuwa taji tana kasa hana kanta fara dawo da maganar hajiyan samad cikin kanta dan

Please Login or Register in order to submit comment