Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

akai a qanqanin lokaci sukai duk da basu san waye mijin ba sundai san yau ne daurin auren Yarsa SANAAH wadda kowa ke girmamawa a cikinsu sbd zamanta 'yar da Sir jeerah da kansa yake kauna.

Umma ce ta fara jin daurin auren daga garesa bayan data taho bayan ya gama hutawa bayan dawowan tasa hankalinsa kwance zuciyarsa fes da wani natsatsen farin cikin bayana shekaru masu yawa yau dai ya nuna nasa ikon akan 'dansa shima,
Ikon da daga 'dan har uwarsa basu isa su sauya ba ko nuna rashin jin dadinsu sbd sanin tinda ya daura ko mutuwar Raheem din ce kadai zata raba auren amma ba dan adam ba ko waye kuwa,

Hakama a yanzu ne yakeda cikakkiyar sani da nutsuwan 'dansa yayi aure
Auren daya daura masa a matsayinsa na ubansa ba wanda uwarsa mace ta daura masa.

Ummah kasa motsawa tayi tsabar mamaki shock din jin auren da idan taji daidai Fleet Raheem jeerah aka daurawa da kuma SANAAH,
Auren da kila mahaifiyarsa zatafison ace wani balain ne ya fado masa yayi jinya ya warke akan yayi aure hakama matarsa da zata iya ransa ma tsabar wani masifaffen kishi akan ace yayi aure musamman yanxu datake ganin sun zama manya yarsu ta zama budurwar dake shirin zama likita amma ace yayi aure aurenma da saar yarsa wadda zatafi baqin cikin hakan dik ranar da Allah ya kaddareta da ji dan kuwa su dai har abada bazata taba ji ba a bakinsu sbd kadama ayi balain dasu idan an tashi dan tabbas lokacin fuskantar juna tsakanin Jeerah da dr fammah yayi tinda daga karshe danta yayi abinda duk duniya ta tsana ko jin sunansa wato qarin aure kuma da yar asalin Nigeria gaba da baya wainda ta tsana.

Rasa abin fada Umma tayi sai kawai tabi auren da adduar Allah ya sanya alkhairi.

A bangare daya kuma dadin hakan taji sosai sbd baqin cikin da Samad da uwarsa zasu shiga da wanda ita kanta Meenah wahab zata shiga sbd bata taba daukansu da mahimmanci ba bare basu girman daya kamata a matsayinsu na matan uban mijinta dan haka hakan ya mata dadi sosai dan tasan tako ina baqin ciki da tashin hankali ne zaaita zubawa wanda zai saka da dama wasu samun sallama.

Tana baro bangaren Dad samun kanta tayi da wucewa kai tsaye bangaren Hajiyar Samad wadda ta rasa sukuninta da kwanciyan hankali a cikin kwanakin a tsorace da fargaba take sbd shirun Dad ba alkhairi bane ko kadan.

Tana ganin Ummah ta danne baqin cikin datake ciki da damuwa ta dan sake tana nuna hankalinta kwance yake da walwala ta mata sannu da zuwa.

Da walwala sosai itama Umma ta gaisa da ita tana kin zaka daga tsaye tace

"Ba sai na zauna ba zan wuce nace bara na sanar miki kije kiyiwa Alh barka da arziki da taya murna Yau aka daura auren 'yarsa SANAAH da Fleet RAHEEM dan kila baki sani ba"

Shiru hajiyar Samad tayi kaman bata fahimta ba sai data juya zancen taga ta kasa ganewa kafin ta dago ta kalli Umman tana dan neman rikicewa da kuma kasa boye rikicewanta tace

"Wane Raheem din?
Da kuma wace Sanaar??

Umma da bazata iya doguwar hayaniyar tashin hankalinba juyawa tayi tana cewa

"Fleet admiral RAHEEM JEERAH"

Tana saka kai Samad na shigowa ko gaidata bai iya yiba sbd jin abinda ta fada ya qaraso cikin palon yana kallan hajiyarsa ya bude baki yana zama yace

"Godfather naji ana ambata"

Tsabar rikicewa hajiyarsa bata san lokacin datace

"Aurensa aka daura da SANAAH dinka ayau mun shiga uku wace sabuwar masifar ce wannan?
Wlh tarko aka nada maka wanda zai kasheka da gaggawa....hada kayanka ka tafi tin a.........

Kallanta yakeyi da duka idanuwansa batareda ya motsaba sbd bai yadda ko kusa da wannan zancen ba da har abada bazai taba yiyuwaba wai Godfather dinsa da aure a irin tsarin rayuwarsa da babu gurin shigar kowane irin mutum ma sbd ahalinsa basason yawa su kansu bare qarin aure.

Tayaya ma?mutanen da basa wani son wani ma yazo cikinsu ya zauna yayi rayuwa bayan iya su to ta ina zai iya kallan wata macen bare qarin aure,

Hakama tayaya SANAAH datake saar yarsa aure zai yiyu a tsakaninsu....

Dauke kansa yayi daga kallan hajiyar yana miqewa tsaye zai fice sbd gabaki daya ta rasa kanta tinda abin ya faru a kwanakin kullum cikin tinani da zullumi kala kala take.

Riqosa tayi da karfin gaske tana kallansa tace

"Bakaji abinda na fada bane?
Kanajin Auren da aka daura?
Wlh ba aure ne ba kai akaiwa tarko wannan auren,
Baka jina ne???

Wani mummunan daci da baqin cikin kalmar auren datake furtawa ya hadiye sbd da ace wani ne yake maimaita kalman an daurawa SANAAH aure da zai iya hallakasa da hannuwansa amma hajiyarsa dan haka ya sake hadiye wani dacin mai karfi ya kalleta da idanuwansa da suka sauya yace

"Hajiya babu auren da zaa daurawa Godfather da kowa a duniya bama wai SANAAH ba,
Babu aure a yanzu kuma babu shi har abada dan haka ki dena wannan tinanin yayi nauyin dama yake kaman haramun"

Kallansa takeyi da tsananin takaici itama da baqin cikin data rasa abin fada amma itama tanason tabbatarwa dan haka ta wucesa ta fita tana dan gyaran mayafin tsadaddiyar abayar dake jikinta ta nufi bangarensu SANAAH sbd tasan bazata iya zuwa bangaren Dad ba kai tsaye ko hauka ce ta haifeta.

Tana isa bangaren ga mamakinta Umma na bangaren tana taya mommy murna wadda take amsawa cikeda farin ciki da sakewa da walwala tana godiya hankali kwance.

Ganin yanayinsu ya saka hajiyar itama tattaro karfin hali da danne tashin hankalinta da baqin cikinsu da takaicinsu ta dan saki fuska cikin karfin hali tana gaisawa da Mommyn kafin ta bude baki tace

"Sai mukaji abinda yake faruwa,
An daura auren ne ko zaa daura ne?
Allah ya nuna mana"

Umma data gama karantar halin datake ciki murmushi mai sanyi da nutsuwa ta sake kafin hankali kwance tace

"An daura tin dazu bayan jumaa sedai fatar Allah ya nuna mana tarewa lafiya idan lokaci yayi"

Miqewa tayi tanawa mommy sai anjima ta fice.

Hajiya datai mutuwar zaune tana kasa yadda har lokacin sake bude baki tayi ta tambayi mommy itama mommyn ta tabbatar mata da an daura.

Bata san lokacin data miqe ba ta fice batareda cewa komaiba mommy ta bita da kallan mamaki da fatar Allah yasa kada ta sake zuwar mata.

Tana baro can bangaren tsabar rikicewa da rudun tashin hankali kai tsaye bangaren Dad ta nufa tana zuwa yana palonsa na kurya zaune cikin hutawa yana waya da wanda aka daurawa auren yau dan sanar dashi sai gata.

Kokarin tinkaro inda yake takeyi ya daga mata hannu ya dakatar da ita cikin wani irin umarni da kaifin daya saka kafafunta tsayawa cak ba shiri ta bude bakinta dayake rawa tace

"Alh Auren FLEET RAHEEM da SANAAH aka daura ayau????

Maganar a kunnen wanda ake waya dashi ta sauka kai tsaye cikin wani irin direct da slow yaji saukanta a cikin kunnuwansa da suke karban kowane zance da nutsuwa da kamewa yana zaune a palonsa dayake saman cikin gidansa matarsa tana zaune gefensa hannunsa na sarqe cikin nata tana jiran ya gama yaci fruits din data hado masa masu tsafta da sanyi.

Dago fararen idanuwansa masu tsananin kwarjini yayi daga qasa a lokacin daya ji zancen ya ratso wayar batareda ya motsaba.

Dad kuwa bude baki yayi cikin kaifi daya da zafi mai tsananin dayake tattare da sautinsa da hukuncinsa yace

"Kije ki shirya komai naki gobe zaa bude miki bangaren dayake kusa dana su SANAAH zaki koma can"

Sarewa kafafun hajiyar sukai ta kifa qasa da karfi jikinta na rawa ta dago kai ta kallesa da sauri idanuwanta na yin ja a take ta bude baki zatai magana ya dakatar da ita yana cewa ta fice kuma dan ta yana wayuwar garin gobe a qasar Nigeria bama a cikin gidan ba bazata sake jinsa ko ganinsa ba sai takusa manta kamanninsa.

Zarewa taji tana neman yi dan haka a rikice ta juya tabar bangaren zuciyarta ne neman dakatawa daga bugawa ta nufi bangaren Samad din bataji bata ganin komai daman tafiyarsa a goben ne amma yace ya fasa.

Ko data shiga bangarensa yana palo yana waya ganinta ya sakasa kashe wayar yana kallanta.

A haukace da tashin hankali ta kama hannunsa ta turasa hanyar bedroom dinsa tana cewa

"Ka hada komai naka ka shirya a cikin daren nan zaka wuce airport kafin asuba lokacin tashin jirgin da zaka bi,
Wlh tallahi Dad dinka ya daurawa SANAAH aure da Godfather dinka kuma daga yanzu zuwa gobe ya baka kabar qasar,
Ka taimakeni Samad ka tattara ka tafi dan Allah ka taimakeni ka tafi kada ka bari yayi maka hukuncin da bazamu iya dashiba."

Mutuwan tsaye Samad din yayi yana jin jiri na dibansa idanuwansa na wani irin duhu da dauke gani kafin ta sake wata magana ya yanke jiki ya fadi a gurin.

Ihu ta kwalla tana kamosa da kiran sunansa da karfi jikinta na rawa tashin hankalinta na daduwa.

*****Acan palon Dad kuwa bayan ficewanta shiru Yayi na seconds kafin ya bude bakinsa cikin girman matsayin dayake dashi akan Raheem din da ikonsa akansa na mahaifin daya haifesa da nutsuwa da kamewan datake cike da isar da umarnin daya riga ya zartar ba neman shawara ba ko tausasa ya ce

"Kaman yanda ka riga kaji zancen daya fito daga bakin hajiya khadija a yanzu shine sakon dazan isar maka daman na ayau na Daura maka aure wata 'yata datake da matsayi me girma a cikin ahalina,
Inason ka fara sanin darajar datake dashi mai girma a gurina ne ya saka na baka aurenta,
Ban nema shawaranka ba akan hakanne ba sbd ita din bana buqatan shawara da kowa akan duk lamarin daya shafeta dan haka ayau ni mahaifinka ina sanar dakai na sake daura maka aure da wata matar bayan wadda kake da ita ina kuma fatan zaka girmama wannan hukuncin dayake hade da umarnin nawa"
#MAMUH
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

43
*ZUZEAM VENTURES*
08144015291
https://wa.link/l1gcz8
ASSALAMU ALAIKUM
Mata masu abun duniya🔥🔥🔥
*Zuzeam ventures* takawo muku babbar gara basa Duka akan 7k ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki Garabasa gara basa, Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 7k na
1. Sashen kaza
2. Ciccibi
3. Gumba madara da chocolate
4. Gari 7in1
5. Tsimi mallaka 5. Tsimin matar minister
6. Women coffee 3in1 sunada kyauta abubuwa kamar haka:Matsin ba a Fira da wando 1k,Matsin maganin infection 1k,Dripping pills 1k,Turaren mallaka 2k
Total total gift 5k
Kiyi kokari ki kasance aciki Garabasa kan garabasa Da 7k dinki ki mallaki kayan da ko 16k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah 08144015291 Maman yasmeen takuce For more information say hi
Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam ventures tashirya tsaff dominku muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu
*DAHUWAR KAZA*
Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt Akwai kyauta mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya
MASU JEGO DA AMARE
Karku bari wannan dama ta wuceku
Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 2000 kacal.
Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd
Infection set
Sabon budurci set
Niima set
Basir set
Matsi mallaka
Amarya set
Uwar gıda set
Mai jego set.

*******
Wani irin shiru ne mai tattare da nutsuwa da kamewan manyan mutane biyu ya ratsa yanayi da wayar wadda sukeyi batareda kowannensu ya bayarda wani motsi ko hayaniya ba wayar....


FLEET ADMIRAL RAHEEM HAKEEM JEERAH shiru ne ya ratsa bangarensa wanda baiyi kowane irin motsiba ko bada reaction bare bayyanarda kowane irin yanayin dazai bayyanarda halinda zuciya da kunnuwansa suka shiga bayan jin kakkausan umarnin da bai taba tsammanin ji ba ko a lokacin dayake da samartakan kara aure ba sai yanzu da baisan ma yanda zai iya kallan kowace mace da sunan mace da namiji zai buqaci kulawa ba bare aure,
Bai taba saka ran aure ba koda yayi aurensa na farko ba,
Bai taba tsammanin bawa mace wani space na rayuwarsa da zuciyarsaba saida yayi aurensa wanda haryanzu yake struggling na yanda zai bata cikakkiyar iko da zuciyarsa,
Haryanzu zuciyarsa da rayuwarsa suna kokari ne sosai gurin bawa mace daya dake rayuwarsa dukkanin dama da haqqinta da farin cikinta daya rataya a wuyansa ba,
A duniyarsa da rayuwarsa mata uku ne zuciyarsa da rayuwarsa basa iya yaqi da yanda zai basu duka sonsa da kaunarsa ba sune iyayensa biyu mata sai 'yarsa amma ko matarsa duk yanda yake sonta da bata kaunarsa duka hakanan yake jin kaman yana tilasta kansa ne sbd kada ya tauyeta da bata duka sonsa,

To a yanzu da Mahaifinsa yazo da umarnin daya riga ya yankesa a garesa baida kowane space a zuciyarsa da familynsa da gidansa da zai iya bawa kowace mace da sunan baqunta ma bare zaman rayuwa,

Ba hayaniya a gidansa da rayuwarsa,
Ba kowace irin damuwa ko buqatan bayani ko tsarin dokar kowane farin ciki da walwala a haka suke rayuwarsu da babu komai a cikinta sai zallan wayewa da asalin daula da kwanciyan hankali da kauna me karfi da soyayya mara sirki Babu ma macen da zata iya rayuwa a cikinsu,
Babu macen da suka zasu iya rayuwa da ita dan haka wannan aure ne da mahaifinsa yayi kawai sbd dawo dashi qasar Nigeria da zuwa akai akai kuma indai hakan ne baida kowace kalma ta fada akan hakan sbd a kalaman dayake bayyanar masa bin bayan daurin auren shine wulaqanta auren na nufin wulaqantasa.

Bai taba iya hayaniya ba da kowa bare mahainfinsa da babu kowace sakewa a tsakaninsu bayan umarnin daman da order tin yarinta hakama shima tin yarinyar haryanzu da manyancin yaxo bai tana daga ido ya kalli Hukunci ko umarnin mahaifinsa ba akansa dan haka a natse ya dan sake dago idanuwansa da suka dan sauya a take da wani mafi girman nauyin umarnin da baa taba basa ba irin yau koda kuwa na aikinsa ne tinda yake kuwa.

Bude baki yayi a natse da deep voice dinsa mai kaurin dake tada tsigar yawancin duk wanda ya fara jinta for the first time yace

"Nagode Allah ya saka da khairan ya qara nisan kwana da lafiya"

Hakan daya fada ya saka Dad saka masa albarka shima tukuna sukai sallama batareda kowace sabuwar magana ba.

Shima a natse ya ajiye wayarsa gefensa idanuwansa a sauye sosai Ms Meenah na gefensa bata lura da yanayinsa ba ta fara kokarin yi masa magana akan taso gaisawa da Dad itama a wayar.

Baice mata komaiba saima dagowa da yayi da wani kamewa yayi mata kallo daya da idanuwansa da suka mugun sauyawa take tsigar jikinta suka tashi sbd yanda kallan ya ratseta tajisa har tsakiyar kanta,
Fleet Raheem jeerah bai taba mata kallan da batajinsa ba har acikin kwakwalwanta ba koda kuwa na fushi ne idan sunyi fada sbd ita dai Allah ya jarabceta da komai nasa.

Dauke idanuwansa yayi daga kanta yana sanar mata yana buqatan silent time.

Bata damu ba sam da tambayar meya samesa ko meya faru a gida ko kuma dad dinne ba lafiya sbd ba dabiarta bace sam ita dai bata damu da kowa nasaba da komai dashi kansa indai akan abinda taga kaman sauyi ne kawai ita shi take so a kowace hali dan sam bai saba da samun kulawan tambaya ba ko karantar yanayi wanda shima baisan da hakan ba sbd sabon data basa na rashin karantar yanayi ko tambayar wanda hakan ya saka bata san abubuwa da dama ba gameda shi ko familynsa dake Nigeria ba ko mahaifinsa koma gurin aikinsa ba.


*****lokacin hajiyar Samad taga balain neman rasa danta ganin idonta hankali tashe ta kira Mr S ta sanar masa shine ya sanar da Dad wanda a hakan ya saka aka tattara komai na Samad din na tafiya yace akaisa airport idan ya farfado acan jirgi kawai zaibi.

Hajiyar Samad din qarasa yankewa tayi daga kowace sauki daga Dad din dan kuwa tsoro lamarin ya fara bata,

Ba imani haka aka kwashesu har airport itace ta hada kayan Samad din komai da komai aka tafi dasu.

Cikin daren suna isa aka saka securities suka tsaresu a mota har sai lokacin tafiyarsa yayi,

Koda ya farfado baima damu da inda ya gansu ba da halinda suke ciki jin yayi ya rasa kansa gabaki daya,
Wata muguwar rawa da jikinsa yakeyi zuciyarsa da tinaninsa sun bace bat dan haka hajiyarsa ta ringa kokarin dawo dashi daidai amma lamarin yayi munin da kuka kawai ta fasa ta fara yi wiwi tana rungumesa jikinta tareda ringa tsinewa auren da da wainda aka daurawa auren da fatar kada auren ya bawa kowa farin ciki har abada.

Samad kuwa baya hayyacinsa sam gashi an hanasu matsawa koina a wannan halin suka kai asuba aka fito da Samad din kaman wani qaramin yaro sbd baya hayyacinsa sam aka wuce dashi.

Haka akai masa kowai batareda ya dawo hayyacinsa ba aka wuce dashi hajiyarsa na airport din tana wani kukan baqin ciki cikin mota har saida jirginsu ya daga tabar Airport din aka dawo da ita gida.

Sabon tashin hankalin data fuskanta shine koda ta iso gidan guraren 8 na safe har an bude mata inda zata koma an saka sabbin furnitures masu tsada da kyau da tsari ba cutatarwa.

Bangare ne daya kusa dap danasu SANAAH hakama komai iri daya ne da nasu wanda yake shima babu abinda ya rasa na tsarin jin dadin duniya da daular gaske kawai dai hakan da yayi mata yana nufin ba sauran aure a tsakaninsu kenan tinda babu inda zata anriga an manyata an tsufa.

Baqin ciki da abinda taji ya danne kirjinta kwantawa ciwo tayi tana fatar Allah ya dauki ran Dad din ma ya mutu tin kafin asan da ya gama da ita kowama ya rasa a huta.

Komawanta bangaren sabo ya saka Umma jin dadin hakan sosai sbd hajiyar Samad itace fitinar gidan da kuma me isa da tinkahon itace me 'da a gidan tinda Raheem ya shafe kaman babu kowace 'da a gurin Sir jeerah sai Samad sbd Fleet Raheem jeerah yafi kama da business partner na jeerahs than a son dan shine yakeda babban hannun jari a businesses nasu da dukiyarda takeda karfin gaske.

SANAAH kuwa washe gari Dad da kansa ya kirata taxo ta samesa ya zaunar da ita ya sake mata nasihu masu ratsa jiki da suka bawa zuciyarta nutsuwa da kwanciyan hankali sbd ya bata tabbacin yanda ya daura auren nan bazai taba barin kowa a duniyar nan ya nuna mata rashin daraja ba ko waye kuwa.

Hakama Sabuwar mota dal data narke miliyoyan kudi masu yawan gaske ya mata kyauta a matsayin tukuicin biyayyarta da rayuwar da zata fara ta cikakkiyar budurwar datake da power a yanzu bama yanci da gata kadai ba.

Hajiyar Samad jinya tayi ta kwana biyu ta asalin zallar baqin ciki amma babu wanda yabi ta kanta taci baqin cikinta ta cinye ta miqe da tsanar kowama a gidan hadda uban gayyar wato Dad.

Su mommy kuwa yanzu da SANAAH takeda aure akanta hankalinsu kwantawa yayi batareda sun damu da Samad yana nan ko bayanan ba sun maida hankali akan hutawa da jin dadi kawai,

Dad ya budewa SANAAH sabon babin rayuwa me kyau da jin dadi dan kuwa komai saida aka sauya aka ninka mata aka zuba mata kudi masu lafiya a acct sbd yin duk abinda take so ga sabuwar motarta da aka dauki lokaci aka ware aka koya mata harta qware itace take ja takai kanta makaranta da duk inda take so.

*******Rayuwa ta sauya sosai sbd lokaci yaja sosai shekaru sun qara tafiya wanda a ciki ne Yaya Al'amin ya gama karatunsa harya fara koyan aiki acan batareda ya dawo ba sbd son tsayuwa da kafafunsa da nasa sunan hakama yazo ya gansu ya musu hutu har so biyu amma sam baa jeerahs ya sauka ba a hotel mai kyau da tsada yake sauka ya gama hutunsa ya komawarsa.

SANAAH KHALIL rayuwarta tafi sauyawa akan ta kowa sbd a yanzu ba iya Sanah bace Ms SANAAH KHALIL ce wadda kyanta,tsarinta,class dinta da wata irin ilimin daya ratseta daban yake,
Hutu da gata yayi mata ratsar da komai nata fizgan hankalin duk wanda zai kalleta yakeyi,

Gata da daular datake zubawa ba iya Nigeria kadai ba take zaune suna fita kasashe sbd ko gurin yaya Al'amin zuwanta kusan uku hakama umrah ma suna zuwa itada mommy wani lokacin ma da ita da mommy da Ummah.

Kauna da tsananin biyayyar dake tsananinta da Dad sun dake karfi sosai dan kuwa babu daren da ba itace mai kai masa tea da snacks ba ta gaidasa dan da dare ne ma ya koma lokacin zuwa gaidasa,

Karatunta yayi nisan datake gap da kammalawa sbd dan tana final year dinta,

Hajiyar Samad itace wadda ta bayyanarda tsanarta a fili a kanta wanda ya saka sam bata ma shiga ko bangarenta kwata kwata iyakacinta da ita gaisuwa idan sun hadu ko a hanya ko a harabar da kowa zai shiga motarsa ya fita.

A daidai wannan lokacin aurenta dayake kanta data manta dashi kwata kwata a rayuwarta sbd tin daga lokacinda akaisa baa sake maganarsa ba har ayau dayake kusan shekara uku zuwa hudu bata taba damuwa ba sbd hakan ma shine daidai a gunta bata buqatan kowane namiji a rayuwanta haka tafi mata.

Yaya Al'amin da mommy ne sukaso su damu amma suma ganin karatu takeyi hakama hankalinsu su duka a kwamce sai suka aje damuwar sukaci gaba da rayuwarsu a walwala.

A daidai wannan lokacin ne Allah ya hadata da wani sabon lecturer dinsu dayazo program na shekara daya a qasar daga Srilanka amma mahaifinsa dan Nigeria ne.

Da farko basama wani shiri sbd yawan zuwanta late daga baya kuma rashin shirin ya koma mutunci da shiri daga karshe ya kamu da wata irin sonta mai zafin gaske da kuma tsananin son aurenta.

Bai bayyana mata soyayyarsa ba sbd kai tsaye aurenta yakeso kuma batareda jan lokaci ba dan haka mahaifinsa ne ya nemi Dad dinta kai tsaye wato Sir jeerah da nemawa dansa aurenta.

maganar ta girgiza Dad sosai anan ya gane irin kuskuren watsi da maganar auren da sukai su duka dan haka kai tsaye ya basu hakuri da sanar musu tanada aure akanta already da wannan ne kuma cikin bacin rai da zafin daya cikasa akan maganar auren da Duk shekarun nan Raheem bai taba masa ba ya dauki wayarsa ya kirasa kiran da baya buqatan komai sai son sanin matsayin auren.
DAWOWA LABARI.
#MAMUH
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

44
*ZUZEAM VENTURES*
08144015291
https://wa.link/l1gcz8
ASSALAMU ALAIKUM
Mata masu abun duniya🔥🔥🔥
*Zuzeam ventures* takawo muku babbar gara basa Duka akan 7k ki daure ki mallaki naki kar dama ta wuceki  Garabasa gara basa, Mutun goman farko da goman 2 Zuwa goban 3 da suka siya promo dimmu na 7k na
1. Sashen kaza
2. Ciccibi
3. Gumba madara da chocolate
4. Gari 7in1
5. Tsimi mallaka 5. Tsimin matar minister
6. Women coffee 3in1 sunada kyauta abubuwa kamar haka:Matsin ba a Fira da wando 1k,Matsin maganin infection 1k,Dripping pills 1k,Turaren mallaka 2k
Total total gift 5k
Kiyi kokari ki kasance aciki  Garabasa kan garabasa Da 7k dinki ki mallaki kayan da ko 16k Bata bakisu zakisha dadinki oga ya more har kyauta saikin samu insha Allah 08144015291 Maman yasmeen takuce  For more information say hi
Ina uwar gida da Amaren bayan sallah zuzeam ventures tashirya tsaff dominku muna gyaran ciki muna saida kayan gyaran jiki dilka sabulu dadai sauransu
*DAHUWAR KAZA*
Kin taba cin *DAHUWAR KAZA 5in1* wato Ni’ima, Matsi, Chikowa, MAllaka, da Karin soyayya Duk me buqata TAYIMUN magana ta Pvt Akwai kyauta mai tsoka ga mutun 5 da suka fara siya
MASU JEGO DA AMARE
Karku bari wannan dama ta wuceku
Mata ga wani sirri mai abun mamaki amma mata aji tsoron Allah kada ayi amfani da wannan dama kijuya mai gidanki yanda bai kamata ba amfaninshi shine a tafin kafar ki kawai zaki shafa lokacin kwanciya zakiga daukar hankali wurin mai gida amman don Allah karki juyashi yanda bai kamataba amana ce na baki 2000 kacal.
Munada kaya kala kala wanda bazasu faduba kedai kidau number kimin magana ngd
Infection set
Sabon budurci set
Niima set
Basir set
Matsi mallaka
Amarya set
Uwar gıda set
Mai jego set.

******
Sun dauki dan time a maqabartar kafin ya gama adduoinsa ga makwancin dan uwansa rabin jikinsa da bayan shekaru sai yau ya kawo masa ziyarar daya kamata

Please Login or Register in order to submit comment