Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jiki da fuskanta datai laushi sosai kaman babyn data sha kuka.

Zaunawa yayi akan sofa din dake facing gadon ya jinginar da bayansa a jikin kujeran yana dora kafansa daya akan daya cikin nutsuwa yana cigaba da kallanta da rashin kowace motsi,

Akwai yanayi dayake jin kansa a ciki na rashin iya bude baki sam ya furta kowace kalma idanuwansa kaman suna kamuwa da wata obsession ne da baitaba sanin yaya yake ba akan kallanta da baisan me hakan ne nufi ba.

Bacci tsawon awa biyu tayi ta farka sbd zazzabin daya sauko mata a cikin baccin dan haka tana bude idanuwanta akansa suka sauka yana zaune a inda suke facin juna idanuwansa a lumshe fuskansa tayi wani irin haske tana fidda wani sanyayyan kwarjini da sirrintaccen kyau da class da wata irin kamewansa dake bayyane.

Lips dinsa da sukai wani irin light ta kalla wanda duk wanda ya kallesu zai iya fahimtar abinda suka ringa yi ne,

Rufe idanuwanta tayi ahankali cikin kasala da gabalaita tana jin yanayinsu da suka ringa sauka a kowane sako na jikinta taji zazzabinta ya qara karfi da fargaba.

Tashi tayi zaune ahankali cikin sanyi da rashin hayaniyan dogon motsi ta ziro kafafunta qasa tana miqewa tsaye wani zafi taji ya ratsa tsakiyarta ta rintse idanuwanta da karfi tana dan komawa ta zauna kadan tana hana hawayenta sauka cikin karfin hali.

Miqewa ta sake yi tana gyara rigarsa dake jikinta da dogon wandon kayanta ba bacci da rigar ta tashi aiki ta daga kafarta daya tana kokarin fara takawa bataji motsinsa ba sai jin hannuwansa tayi sun zagayota daya baya zuwa gabanta ya hade kirjinsa da bayanta yana sauke wata ajiyan zuciya mai zafi a bayan wuyanta da kakkauran muryansa mai dakar zuciya ya furta

"How are you feeling???

Rintse idanuwanta tayi ahankali tareda budesu tana jin hankalinta na sake tashi da yanda zata fuskanci iyayenta.

Zamewa tayi tana son sake takawa yayiwa tafiyan tata wani kallo kafin ya saka hannuwansa biyu ya dagata jikinsa yayi sama da ita yana nufar kofa yace

"Ina ne zaki??

Kallansa tayi da wani irin damuwa ta bude baki daqyar tace

"Zan tafi"

Kallanta yayi ta dauke idanuwanta daga kallansa.
##MAMUH
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

85
Kallanta yayi a natse da kyau kafin ya nufi hanyar bedroom dinsa da ita wanda yake a yanda suka hargitsasa.

Sauketa yayi a natse kafin ya dauko wayarsa ya kunna datake a kashen tin juyan ya nemo numbern Maamah wadda take bacci ta dauka a natse tareda ambatar sunansa ya bude baki kai tsaye yace

"Good morning Maamah,pls a turo Maid dinta yanzu ta kawo mata something hot and light,thank you"

"Ok ba damuwa" Maamah tace ya kashe wayarsa yana kallanta da ajiye wayar ya zaunar da ita a gefensa tana dunqulewa sbd zazzabi sosai.

Jikinsa yaso shigar da ita amma taqi yadda ya kyaleta yana jin wayarsa na vibration na shigowan kira amma bai dubaba sbd ba lokacin wayarsa bane yanxu.

Babu bata dogon lokaci safiya ta iso bangaren dauke da tray har palonsa ta ajiye sai a lokacin ya fito da SANAAH din wadda ta dane cikin azaba tana hana safiya datai qasa da kanta barin ta gane tafiyarta ko yanayin fuskanta daman jiran datai tazo sbd ta taimaka mata su koma tare dan bazata iya doguwan tafiyar ita dayaba.

Miqewa safiya tayi tana ajiyewa ta gaidasa da girmamawa mai girma kanta a qasa ta juya zata fice SANAAH ta bude baki daqyar ba karfi a muryanta tace ta jirata.

Cikin tilas tasha madaran da aka dafa mai kauri da zuma da kayan qamshi bada yawaba duk da zafinta daya ratsa cikinta taji dadin hakan sosai sbd karfinta ya dan karu da kuzarinta dan haka komai bata iya ci ba tafara hawayen son tafiya dole yabarta ta fice ya bita da kallo a tsanake harta fice batateda ta waiwayoba tana tafiyar da itace idanuwansa ke kasa iya dena kalla.

Tana fitowa babban palon Safiya dake can kofa tsaye tana jira dagowa tayi ta kalleta da kulawa sosai ta dan dawo gurinta dan bata daman jin saukin dataga babu shi a tattare da ita zuciyarta cikeda tinani kala kala dana farin ciki dana tsoro dana fargaba dan kuwa daga yanzu ta tabbata kishiyar Ms meemah amma dai ko menene tinda SANAAH ta samu zama cikakkiyar mata itama hakan yayi mata dan kaman yan uwan jini suka dauketa tintini kaman yanda itama ta daukesu sbd a yanxu daga mommy sai SANAAH ne nata sbd maraici.

Fitowa sukai babu kowa har lokacin babu wanda ya tashi suka nufi bangarensu mommyn suna isa babu kowa dan basu tashi ba dan haka ta tsaya cak tsakiyar palon cikin tsananin damuwa fargaban batasan dakin wa zata nufa ba dan a cikin iyayen nata ukun mata babu wanda take fatan yaganta ya iya gane halinda take.

Jajir idanuwanta sukai damuwa mai tsanani da mutuwan jiki na rufeta hawaye masu zafi suna ciko idanuwanta,

Safiya ce ta bude baki tace
"muje dakin Mommy"

Can suka nufa suka shige mommyn na bacci SANAAH din ta iso bakin gadon ta haye ta shige bargon jikinta na dan rawar sanyi.

Safiya fita tayi taje kitchen ta sake hado mata tea mai zafi da kauri sosai ba suga daga zallan madaran gari saita ruwa da condensed kadan ta kawo mata ta bata tasha itama kadan tace ya isheta ta dunqule safiyan ta fice.

Zazzabi mai karfin gaske ne ya sake taso mata ta ringa rawan sanyi tsawon lokaci kafin bacci ya dauketa.

Mommy ko data farka ta ganta kwance a gadon fuskanta ta kalla taga yanda ta kumbura tayi ja sai ta tashi zaune a hankali ta kalleta da kyau tana zuba mata idon taga ko a cikin baccin kaman a galabaice take yinsa sbd zazzabin daya sake sakata laushi sosai.

Dauke kai Mommyn tayi daga kallanta da sauri tana jin kirjinta ya buga kadan ta sauko gadon tana qin sake kallan SANAAH din ta fada toilet.

Bata sake bi ta kallanta ba harta gama duk shirinta bayan ta fito wanka ta fito palo tana nufar dakin Maamah wadda itama ta farka harta yi wankanta tana waya a natse.

Gaidata tayi kafin ta fito ta nufi dakin dr mum itama ta gaidata ta dawo ta wuce kitchen dan duba breakfast idan baa kammalaba.

A dining safiya ta gama komai ta jere dan haka Mommy sauran su drinks ta qarasa jerawa saiga su Maamah da dr mum din duka sun fito zuwa dining din.

Zama sukai a natse suna firarsu hankali kwance suna cin abincinsu banda mommy da hankalinta yaketa neman rabuwa biyu amma ta tattara ta watsar ta danne tana cigaba da firarta.

Sai da Safiya ta wuce dauke da tray na wani breakfast din daban zata nufi dakin Mommy maamah ta kalleta tace

"Ina zaki kai abinci safiya??

"Maamah SANAAH zan kawai batajin dadi ne tana dakin mommy"

Shiru mommy tayi tana ci gaba da cin abincinta ita kuwa maamah cikin kulawa tace

"Subhnallah,muran ce ko me? Amma ba sosai ba ko?

Gyada kai safiya tayi tana juyawa ta wuce

Dr Mum kuwa bata ce komaiba tana gamawa ta miqe tana cewa bara ta duba SANAAH din ko zata sauya mata maganin muran.


Koda Dr Mum ta isa daki SANAAH na toilet ta jima a ciki kafin ta fito daure da babban towel tana tafiya ahankali tana ganin Dr Mum ta gyara tafiyarta da sauri tana dan bawa kanta karfi da kuzari harda dan sakewa kadan tana daukan wani babban towel din ta rufe jikinta da bude baki tace

"Ina kwana Mum"

Amsawa Dr Mum tayi tana kallanta da kyau da ganin SANAAH din ta kasa dagowa ta kalleta ko kadan.

"Yaya jikinki? Muran ce?
Kin gama shanye maganin dana rubuta miki last time??

Gyada kai tayi ahankali tana dan bude baki tace

"Naji sauki dan zazzabi ne kadan kawai amma yanzu komai banaji ma"

Gyada kai Dr Mum din tayi tana sake kallanta kafin tace

"To ki huta zuwa anjima mugani idan bai dawoba zazzabin"

Miqewa tayi ta fice daidai nan Maamah ta shigo wadda kallo daya tayiwa SANAAH taji tinaninta ya tsaya cak sbd koda ta shigo SANAAH na tafiya zuwa gaban dauko kayan da zata saka.

Kallanta tayi da dan sauri da jin wata kauna da kulawa ta qaraso tana cewa

"Ki kula tinda bakyajin dadi ki zauna safiya tashi ki dauko mata abinda take buqata.

Miqewa safiya tayi tana isa gurin kayan ita kuma SANAAH din ta zauna sbd Maamah dake dakin kada ta gan tafiyanta.

Koda ta shirya cikin kaya marasa nauyi tana cin abincin kadan amansa tayi gabaki daya sai dai aka kuma bata abu mai ruwa tasha ta sake komawa bacci jikinta da wani irin zafi sosai.

Wasa wasa sai ciwo ya zama nata dan kuwa wuni tayi a kwance zazzabi mai Karfin yaqi sakinta babu gabar jikinta da bata mata wani irin tsami da ciwo dan haka dole mommy ta ringa kulawa da ita.

Har dare tana daki daga toilet sai gado,
Maamah ma itace ta hada mata abinci har so biyu amma babu wanda ya zauna cikinta dan haka dole dr mum tace zata mata dubawan likitoci dan sanin meyake damunta dan itace kadai bata gane asalin halinda SANAAH din take ciki ba.
#MAMUH
09033181070GANIN IDO 2026
Mamuhgee

86
Kiran Dad ne ya shigo wayarta bayan sallar ishai datake kokarin zuwa duba SANAAH din.

Kaman ba zata dauka ba sai kuma ta daga kai tsaye nemanta ya furta yana yi yanzun nan.

Shiru tayi da mamakin isarsa da ikon dayake nuna mata amma tinawa da matakin da suke akai na tashin hankalin dayake neman jefasu akan auren SANAAH din ya sakata saka slippers masu kauri ta nufi bangaren nasa dan daman doguwan abaya ce a jikinta da mayafinta tinda sune kayanta.

Ko data isa a kofar shiga bangaren taga Imran a tsaye yana waya take ta san RAHEEM yana ciki kenan shima dan haka fargaba taso kamata amma ta fuska tareda kame fuskanta.

A zaune Raheem yake a palon farko wanda sanyin qamshinsa ya doke na mahaifinsa ya kame niimar palon gabaki daya.

Qarasowa tayi ta zata wuce ciki a natse tareda kallan RAHEEM din kadan tana amsa gaisuwan daya mata a tsanake a kame duk da waya yake amsawa cikin iko.

Tana shiga palon da Dad din yake zauna ta qaraso ta zauna ta dan dago ta kallesa tana dan bude baki ta gaidasa shima ya amsa fuskansa a daure sosai ya bude baki bayan ta zauna tana sauraransa yace

"Likita kina sane da inada maganar jiran takardar sakin SANAAH amma kika aikata 'dan ki ya dora mata iddarsa??
Me kuka maidani?
Me kuke nufi da hakan?
Menene amfanin hakan bayan bai gama amincewa da bata matsayin matarsaba?
Rainani kukayi da maganata batada mahimmci ko me?

Da mamaki mai girma dr mum ta dago ta kallesa tana jin zancen kaman saukan haihuwa ta ji wani sanyi ya ratsa zuciyarta da kwanciyan hankali tareda tsananin tausayin SANAAH din wadda kenan halinda take ciki ne yau.

Murmushi ne ya kufcewa dr mum din wanda ya sake kular da Dad ya daidai nan RAHEEM din ya shigo palon da sallamarsa mai bayyanarda kamewa da nutsuwarsa ya qaraso ya zauna Dad daya gama yanke hukuncinsa sbd tabbas maida SANAAH macensa da RAHEEM yayi ba shine samun yancinta na zamowa cikakkiyar matarsa me yanci ba tinda matarsa haryanzu bata saniba kuma duka sun kasa sanar da ita yayita basu lokacin hakan amma basu cika ba sai kawai yaxo ya maida masa 'ya cikakkiyar mace wadda dagashi ubanta har ita basusan cikakkiyar makomar aurenba da yanxu kam ta tashi daga budurwa...wannan ne ke sake cin ransa dan haka ya maida kallansa cikakke akan RAHEEM din ya bude baki babu sauki ko rahama a sautinsa yace

"Fleet admiral a yanxu anan nake baka umarnin bani sakamakon auren SANAAH"

Dagowa RAHEEM din yayi ya saukewa Dad din idanuwansa cikin nutsuwa da kwanciyan hankali tareda kamewa da mamakin yanda koyaushe iyayensa basa gajiya da zama akan magana daya tin asalinsu farko hakan suke haryanzu bayan sunsan shi sam baa zama daya ayi biyu ayi na uku dashi duka akan magana daya sbd baida time din batawa akan abu daya koyaushe amma a wannan karan suna neman wuce huruminsu da Allah ya basu akansa.

Dr Mum kallo daya tayiwa yanayin RAHEEM din tayi shiru dan tasan nasa hukuncin zai fada wanda take fatan taji abinda bazai sakata samun bugawan zuciya ba.

Dad kuwa kallan RAHEEM din ya sake zai sake maimaita maganarsa a zafafe
Kalaman Fleet din suka ratsa shirun palon da cewa

"Tana dauke da aurena haryanzu akanta da i don't know wani sakamon da ake jira da hakan Dad,
She is my wife,
She still is,
She will still will be,
Tana dauke da igiya ukun auren da aka daura,
Tana amsa sunan iyalina,
Tanada matsayin iyalina,
Na kirata sa kalman iyalina akwai wani sakamon daya rage bayan hakanne??

Dr Mum da ita kanta kalamansa suka sakata kafesa da ido maida kallanta tayi kan Dad da dan sauri sbd tanaji a jikinta irin tafasar dayake yi da yanda kalaman suka zafafesa dan kuwa babu abinda yaji wanda yakeson ji kafin ya bude baki yayi wata maganar sbd a yanzu ma ya fasa kowane sassaucin dayake da niyar yi RAHEEM ya miqe tsaye tareda sake bude baki a natse kaman bai taba furta komaiba yace

"Nagode Allah ya qara lafiya ya saka da khairan"

Juyawa yayi ya nufi kofa Dad da zuciyar sojoji ta gama ciyosa ya dago idanuwansa jajir zai furta kalamansa Dr Mum tayi saurin dawowa gurinsa tana miqa hannunta bakinsa zata dora cikin mantawa da matsayinsu sai kuma ta dakata cak batareda hannun ya qarasa sauka akan bakinsa ba sedai yana dap dan kuwa hatta saukan numfashinsa mai zafi tana ji a fatar tafin hannunta ta dago da idanuwanta da a karan farko suka shiga cikin nasa gap da gap ya saka idanuwansa da suka sauya sbd bacin ran dayake ciki a cikin nata yana jin asalin qamshinta tin na shekarun kuruciya suna shigarsa direct da tareda numfashin bugawan zuciyarta.

Janyewa tayi baya cikin nutsuwa da dan kamewa da qin sake kallansa ta bude baki tace

"Dan Allah tinda ta riga ta zama matarsa ka kyalesa yayi yanda zaiyi"

Kafeta da idanuwansa yayi yana qin furta kalma ko daya sbd da yawa sun bace daga kansa da bakinsa a yanxu dai.

Juyawa tayi tabar palon tana jin itama gabaki daya kalamanta sun bace mata.

Tana komawa bangarensu bata iya fuskantar kowaba sai data shiga dakinta ta nutsuwa ta dawo daidai tukuna ta nufi gurin SANAAH wadda Maamah ta rufe ido ta sake gasata dakyau da abubuwa tana kuka tana jin kaman zata mutu sbd kunya harta galabaita tayi bacci gwanin tausayi.

Yaso nemanta sosai sbd yanayin lafiyarta amma ba wayar hakan hakama iyayen nasa yasan idan har bata warware ba zasu bata kulawa dan haka ya barta kawai ko bangaren bai sake zuwaba sbd ganinta zai iya basa matsalar rashin jinta din dan haka kwata kwata babu wanda ya sake ganinsa.

Washe gari ba laifi ta tashi sbd ta samu sauki sosai dan ba qaramin gasuwa tayiba hakama dr bushrat ta sake zuwa dubata,

Wani tattali da kulawa take samu daga Maamah da Dr mum mommynta ta kawo ido ta saka kawai.

A waya fammah tasan batada lafiya sosai dan haka ta ringa tarairayanta a wayan mum kam anyi busy bata wani bawa rashin lafiyar mahimmanci sosaiba ta bari idan taxo tukuna.

Bata fitowa palo koyaushe tana bedroom sbd batason tsautsayi yasa ya shigo tana palon ta gansa dan kaman bazata taba iya sanin kallansaba take ji.

Dad ma ya dauki mugun zafin da shi kansa Raheem din zuwa yanxu ya shedar da hakan sbd dai da gaske auren zai rana dan haka ya hana kowa daman ganinsa a cikin iyayensa kaf dan su Dr Mum ma hankalinsu ya tashi yanzu kam.

Imran dayake shirin tafiyarsu Morocco ya gama kammalata amma dayake akwai sauran kusan sati kafin tafiyar sai bai siya ticket ba ya sanar da Fleet din komai ya kammala batareda ya dago ya kallesaba ya bude baki a natse yace

"A siya tickets gobe koman dare zuwa gobe da safe zamu wuce"

"Aiit Done fleet" Imran ya fada yana daga wayarsa yabar gurin yana fara aikinsa kawai.

Imran na fita wayarsa dake gefensa tana fidda hasken shigowan kira ya dauka yana decline na call din ya saka kiran Maamah wadda take zaune tareda Dr Mum sun gama magana da Abbu a wayarta taga kiran Raheem din ta dauka a tsanake.

"Maamah da asuba insha Allah zan wuce Morocco maid ta shirya mata komai"

Ajiyan zuciya Maamah ta sake tana cewa

"Zan hada mata da kaina insha Allah"

Kashe wayar yayi yana kashewa gabaki daya ya aje ya miqe ya shige bedroom dinsa.

Dr Mum maamah ta fadawa wadda itama wani nauyi ne taji ya sauka kirjinta sbd zuwa yanzu sun gama shiga tsaka me wuyar HAKEEM JEERAH dan da shi kansa Raheem din bai hango sauki ba ko kadan.

Maamah ce ta miqe taje dan kiran safiya ta hado mata kayan SANAAH din ita zata hada sauran duk da ba wasu kayan zaa daukan mata ba acan ayi siyayyar wasu yafi sauki.

Dr Mum kuwa batajin zata iya barin Dad ya sani gwara dan haka zata tabbatarda bata bar SANAAH taje masa sallama ba tinda tasan yasan da tafiyar batasan tashin hankalin da ake ciki ba sam sam ita.
#MAMUH
09033181070Mamuhgee

87
Dr Mum ce ta samu SANAAH din har dakin Maamah data koma da zama ta kalleta da kulawa tana zaune cikin kujera ta dan kwanta kadan tana sauraron Safiya dake mata firar nishadi sosai tana murmushi tana sauraronta da kallanta.

Ganin Dr Mum din ya sakata dan tashi zaune a natse tana gaidata da cewa

"Sannu da zuwa Dr Mum"

Zaunawa tayi gefenta kafin ta amsa da kulawa tana dan sake fuskanta da murmushi mai tsananin kyau daya bayyanar da kamannin fleet a fuskanta tace

"Fira safiya kike bawa Yata take wannan murmushin da jin dadinsa"

Dariya safiya tayi tana kallan SANAAH din wadda itama murmushin ta sake yi tana dan kasa kallan Dr Mum din sosai.

"Yaya jikinki Baby?
Yanxu bakya jin kowace rashin jin dadi dai right??

Gyada kai tayi tana cewa "eh thank you Dr Mum"

Murmushi dr mum din tayi tana maida kallanta kan safiya tace

"Ai Maamah ta fada miki zaki hadawa SANAAH wasu daga kayanta yau da Asuba ne tafiyarsu Morocco an dawo da ita kusa"

Da jin dadi Safiya tace
"Eh zanje yanxu na hado mata su"

SANAAH kuwa dagowa tayi ahankali da yar faduwan gaba da shakka ta kalli Dr Mum din kadan sbd bata gama jin tafiyar ma ta kamata kwata kwata ba gashi ana maganar yau da asuba,

Wani numfashin tashin hankali da rashin jin dadi ta sake na abubuwa da dama da suka bata son tafiyar kwata kwata bata kaunar yinta,
Batasan tayaya zata iya hada idanuwa da Fammah dinta da Mum ba dik da babu wanda yasan abinda yake tsakaninta da Dad din famman amma hakanan take jin tsananin nauyi da kunyar kai kanta gabansa ta iya kallansu musamman fammah datake jin tafi jinta a cikin zuciya da kirjinta,

Hakama batasan tayaya zata kasar da babu wanda zata iya sakewa dashiba a cikin yare da al'adar da ba nata ba ga uwa uba shi wanda bazata iya sake hada idanuwanta da nasa ba sbd har yau basu taba sake ganin junaba bata kuma shiryawa sake hada fuskanta da nasa ba ko a kusa.

Dr Mum ta lura da yanayin nata daya sauya jikinta yayi wani irin sanyi da nuna batada raayin tafiyar dan haka tai kaman bata gane ba sam ko fahimta sbd tafiyar itace maslahar datake fata idan ba hakan ba Hakeem bazai taba dena daga musu hankalin raba aurenba dan haka tafi farin cikin Raheem din ya tafi da SANAAH din kafin dawowansu zata samu ta lallaba Hakeem din yabar maganar.

Dafa SANAAH din tayi da kulawa da kauna mara sirki tace

"Kada ki damar da kanki tinda kinsan baki gama warwareba hakama kada ki takura kanki idan kinje ki saki jikinki tinda ga Raheem nan you'll feel safe ga kuma fammah da itama zata kula dake sosai na sani,
Dad dinki yasan da tafiyar tini kin sani dan haka ba lallai ki samu ganinsa ba yanxu dare yayi hakama da asubanma ba ganinsa zakiyiba ki bari idan kun isa saiki kirasa nima da safe zan masa bayanin kinso ganinsa tinda yasan da tafiyar da wucewan naku"

Shiru SANAAH tayi tanajin jikinta na sake sanyi ta dan sauke numfashi mai sanyi tana gyada kai ahankali wanda ya saka Dr mum sake murmushi tana sake dan dafa hannuwanta da kulawa da jin dadi tace

"Thats my Baby"

Safiya da itama hakan ya mata dadi sosai tana kallan SANAAH da dariyarta da fatan ma kada ta dawo shikenan Dad din fammah ya tafi da ita miqewa tayi ta fice dan hado mata luggage din tafiyan.

Dr Mum cigaba da kwantarwa da SANAAH hankali tayi da wata irin kulawa da kaunar data saka SANAAH jin ta karbi tafiyan a zuciyarta da nutsuwa.

Dr Mum na barin dakin Maamah ta shigo tareda wasu LV suitcases guda biyu marasa girma sosai ta tura gefe tana qarasowa gurin SANAAH din Safiya na bayanta dauke da tray dayake dauke da wani maganin daban da Maamah din ta hadawa SANAAH datake hada mata kullum dan yanayin jikin nata.

Bata tayi tana cewa ta karba tin yanada dumi ta shanye.

Jiki a mace ta karba tana dan bata fuska ta fara sha ahankali maamah din da safiya na mata fira dan hanata shiga damuwan barin gida tin yanzu.

Sun dan jima sosai kafin safiya tai musu saida safe ta fice ta wuce dakinta.

Maamah ma shirin bacci tayi ta kwanta tabarta lafe a kujera tana son yin waya sosai amma ba daman hakan sbd Maamah ce ta karba wayanta wanda da alama kilan ya fada mata hukuncinsa ne.

Dad takeson kira sosai ta masa sallama amma ba daman hakan haka ta miqe ta shiga bathroom ta fito tayi shirin bacci ta kwanta jikinta duk yayi dumin da koyaushe kwana biyun haka yake dan dumi sbd yanayin maganin da ake bata sai ya zamana jikinta baya sanyi ko kadan koyaushe a dan dumi yake.

Da asuba Maamah ce ta tada ita tai wanka da ruwan zafi tana fitowa har Safiya ta dan hado mata light breakfast wanda chips ne da plain egg.

Sallah tafara yi kafin taci abincin kadan wanda Maamah ta sakata ci kafin ta bata magani a cup mai dumi ta sha kadan amma maamah ta sakata shanyewa.

Dr Mum ce ta fito itama ta iso dakin lokacin tini maamah ta gama sakata shiryawa...

Gaida dr mum tayi da sanyin jiki tana qarasa saka ipad dinta a handbag dinta dake gefenta ajiye.

Miqewa tayi ta nufi dakin Mommy wadda bata fitoba tana zaune tana lazimi.

Tana shiga gaidata tayi kai tsaye tana qarasa ta zauna kan sofa tana daukan wayar mommyn dake aje gurin ta nemo numbern Dad ta saka kira kai tsaye.

Bata shiga ba ta kuma sake saka kiran still bata shiga,
Shiru tayi kafin ta sake danna kira babu alaman ma wayar na kashe dan haka ta fara neman numbern Mr Sideeq daidai nan Maamah ta shigo tace tafito Raheem ya kira motocinsu are ready.

Faduwa gabanta yayi da wani irin karfin daya saka jikinta sanyi daga sunansa kadai da Maamah din ta ambata.

Mommy hannu ta miqa ta karbi wayarta tana qarasa adduarta ta kalleta tace

"Ki tashi mana kada ki barsu suna jira,
Allah ya tsare yakai lafiya a dawo lafiya"

Dago idanuwanta da suka sauya take tayi ta kalli Mommyn kafin ta miqe tsaye ta bude baki tace

"Amin" da qaramin sauti a taqaice tukuna ta juya ta nufi kofa ta fice.

Safiya ce ta ja suitcases nata ta fita dasu tin daga nesa security daya ya qaraso ya karbi kayan daga safiya sbd bazata samu daman qarasawa har gurin motocinba dan Fleet din yana ciki already dan haka daga nan ta tsaya cak Maamah ce ta qarasa har kusan gurin mota da ita tin kafin su qaraso aka budewa SANAAH din motar da Fleet yake ciki a zaune cikin wasu fitinannun brown Armanis marasa kauri sosai da suka maidasa kaman saurayi.

A natse ta shiga aka rufe kofar take aka ja motocin suka nufi babbar gate din ficewa wanda tin daga nesa aka wangale musu shi suka fara ficewa da wani irin speed.

Airport suka nufa kai tsaye sai a lokacin da suka hau titin dayake tsit ba mutane sosai sbd duhun asubar taja wani numfashi mara sauti ko kadan na zuciyarta data sauya bugawa tinda lokacinda ta sako kafarta motar zuwa zaunawanta qamshinsa daya gama kama cikin motar gabaki daya ya shigeta take kokuwa da riqe bugun zuciyarta dayake bugawan da ta sani ba nata bane...

Hadiye numfashin tayi tana sake riqe nutsuwa da kamun kanta da rashin hayaniyarta ta bude baki da wani irin sauti mai

Please Login or Register in order to submit comment