Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jin kamahin girki na tashi a gidan sai da nai sallah la, asar na fito daga daki na samay ta tafito daga kitchen din nake cewa ashekina ciki bata ko kalli inda nake ba tace eh kawai ta shige.
Na koma daki abina ban jima da shiga ba yaran suka shigo gida sai ga su sun samu bakuwa a gidan Ihisan kan da murnan ta ta fada a jikin uwarta.
Tace wa yaran ku halan kunyi bakin ciki da ganina ne naga kunyi wani cirko cirko kuna kallona kamar kun ga bakuwa.
Jinior baiko bi ta ianta bw sai cewa yake ina little mum din mu take helen da ta kwaso shayi ta daka mata tsawa tace ke yar aiki kizo ki kwashi kayan nan ki wanke.
Sai yarinyar tace anty bata bari na wanke masu kaya ita ke wankewa ko Aisha tace to ni ba antyn bace maza zoki kwashe su.
Kamar nasan sunayi sai gani na fito daga daki naga helen tana wanke kayan abincin namu nace da ita helen yaya haka bana hanaki ba ashe ?
Tace wanan bakuwar anty ce tace na wanke mata na fada mata tace sai na wanke kafin in magana sai najita daga baya na tana fadin eh nice nan nasa ta wanke muna su.
Nace amma ni bani bari ta wanke muna kayan ibadan mu don ba musulma bace ko kin manta watan azumi muke watan ibada ne.
Na manta kin san bani azumi ne sai yanzu danaji daga bakin ki dai na tuna kallon mamaki nai mata kawai nace helen bar kayan na wanke su shige dakin ki.
Sai cewa tayi dama nasan akwai tsiya akan yaran nan dake don dama naji komai gamay dasu to ki sani duk wace tazo cin arzikin mu ba zan barta ba.
Sai lokacin na juyo nace da ita wasu ko wasu kan ai kina ganin su dole ki barsu inda kika gansu din.
Tace haka kika ce ko nace kwarai kuwa ai kema kina da ya da ar aiki sai ki saka su don ban saka naki ba.
Na wuce abina na barta a tsaye ta fara haushin ta data saba don ba yau ne farkon ganin ta ba a gare ni nasan ta nasan halin ta tun a baya.
Ina shiga daki sai ga Nasir da Jinior Nasir ke cewa dani little mum wai may wanan matar tazo yine a gidan nan yaushe ne kuma zata koma ta barmu please da zuwan ta tafara wa mutane fada a gida haka.

********* ********* *********
An sha ruwa kowa yana dakin shi gidan ya koma shiru ranan daga hindatu sai daddy ne a zaune a falon ga abinci dafa duka data dafa ya saka a gaban shi tun cibi daya daya diba ya hade shi da kyat bai sake iya kara na biyu ba.
Don yaji da kaurin kuna dake tashi ga abincin ga ba magi ko mai naiji ba wai shi may azumi zai yi buda baki dashi.
Sai faman surutu take zuba mai yana dai amsawa da kyat da eh a, a don biye mata kada ranta ya baci.
Na fito daga dakina dauke da Haidar na samay su zaune a hakan na gayar dashi da shan ruwa ya amsa da fara,ar shi yanawa haidar wasa.
Ban saukr yaron ba na juya abina na wuce zuwa kitchen don Nasir ne ya fito dani nai mashi abinda zaici ba zai iya cin wanan abincin ba.
Miya na hada dole a cikin daren nan na zuba shinkafa a rice cooker na dafa masu shine yaran gaba daya sukaci suka kwanta niko na sha tea kawai.
Washegari abinci ne tule an barta dashi a kitchen ta fara fada da masifa don taga tunkuyar da naiwa yaran abinci da shi.
Ta kwasa fuu taje ta fadawa maigidan harda zancen helen da yadda mukayi a jiya din sai da ta fada mai komai.
Ina jiran yai min magana sai banji yayi ba haka ta zubar da abinci mai yawa tunda ba almajiri ko wani mabukacin da zata iya ba anan.
Yau da zata dora ina dakina tun safe barci nake kwasa abina can baba ya tayar dani da kuka nasan yunwa yake ji na fito indan dama mai cooker orth yasha ko zai muna shiru.
Na samu ta fito daga kitchen tace yauwa dama naso fitowan ki yanzu.
Don naji naga jiya kun hada kai da yara sunki cin abincin dana dafa yau dafa dukan taliya zan masu sai naga shegen da zaice baici kuma.
Murmushi nayi mata kawai na shige abina tabiyoni kamar tana zargina har na dora abinda zanyi nagama na fita na dawo falo na zauna nakira Aisha ta kawo yaron.
Sai da Aisha ta fito da yaron har sun zauna nace ta fifita mai yai sanyi a bashi sai naji tace amma wanan da kika damawa yaronki kin dai san na baban su ne ko idan ya kare fa ?
Nace sai ya sawo wani dama ai dan shi ne yasha ba dan wani ba kuma tare suke sha da uban dama.
Ai bashi kadai ya haifa ba ba zan yarda da son kai din nan ba kowa ma ai shi ya haife shi ba wanda ya tsinto a bola cikin su .
Kin ga sai ki dama kowa yasha tunda ko banza gaki a kitchen ai ko abu mai sauki kankana.
Rahama wuyan ki fa na lura tun jiya ya fara kauri to bari kiji bakin cikin ki da tashin hankalin ki za a katse maki jin dadin rayuwan ki anzo an gwamatse ku to sai dai ki mutu.
Nace kai ji wani magana kuma nan wanan kuma ai sai Allah dayayini ya isa ya katse min jin dadi ba mutum banza ba irin ki.
Ranta yai mugun baci tace nine banzan zan gwada maki wallahi ni hindatu ba banza bace a gidan nan sai na lahira yafiki jin dadi angaji an koma kauye inda akafi wayo dama kwashe kwashen Saade ne yakaimu ga haka itama din kin mata halin ku na yan adam kin rabata da mijin ta.
Nace koke baki fi karfin hakan ba a gare ni nace dadin abin dai ina da asali ba cirani nazo yi ba garin mutane balle ace ba a san sunan kauyen mu ba.
Aiko sai zagi ta uwa ta uba kamar ba azumi takeyi ba nace ni bani zagin ki don nasan hukuncin zagi ga Allah kuma ina ibadana ke kinyi kadan ki rusa min ibadana.
Haka muka sha ruwa tana rusa muna fitina har magariba kowa ya shige muka barta a wurin.
Tun dawowan shi gidan ya fahinci akwai matsala don maigadi ke cewa dashi tun waje oga bakuwar nan fa tana da masifa tana matsawa uwar dakin mu yau fitina suka wuni yi.
Yace dashi sharf ita ma bakuwar matatace kamar yadda uwar dakin naka take matana don haka mind your self ya wuce shi fuu yana bashi hakkuri.
Ran shi a bace yafito daga dakin shi bayan ya sauya kayan jikin shi zuwa na shan iska yana zama sai ga Jinior ya fito yana cewa daddy I can't eat this food.
Ya dakawa yaron tsawa ya juya rai a bace ya fice daga falon sai gata tafito ta zauna a gefen shi bata dade da zama ba Nasir ya fito zai fita daga gidan uban ya hango shi.
Yace ina zaka yanzu da daren nan soja yaron ya tsaya ya dan juyo yace zan fita na samo wani abu a waje ne don bama iya cin abincin nan gaskiya.
Ya juya gareta yace hindatu wani irin abinci kika dafa ne yaran sun kasa ci tai wani irin shuumin dariya tace sun kasa ci ko makirci dai.
Dafa dukan taliya ne nayi masu shine za, ace sun kasa ci ni duk iskancin yaro dashi da wanda ke turo shi ai ina iya shi wallahi.
Kafin yai magana sai ga Ihisan ta fito tace mama nifa bana iya cin wanan abincin ya yi yaji da yawa ba haka little mum ke muna abinci ba ko Aisha.
Yace you see,
Ita kuma wanan din waya kulla mata makirci da tazo da wanan maganan bafa yau ba ina maki wanan complain din kan abinci akwai komai amma ai abinci ba test ba komai.
Tace a hasale yadda na iya nakeyi bakuma wanda zai sani nayi abinda ban tashi yi ba ehe,
Ina sawa yarona parmpers naji yana kirana na fito da yaton a hannu na a zatona fadan dazun ne zai yi magana a kan shi.
Sai da nai mai barka da shan ruwa na samu wuri na zauna ina sauraren shi inji may zaice dani.
Yace ga danki can daki yanzu ya fito zai fita na tambaye shi ina zai tafi wai zaije ya samo abinda zaici baya iya cin wanda aka dafa masu.
Nace subbahanallahi Nasir a Abuja da daren nan ina zaka haka karami dakai yace gasu nan har jinior shiyazo ya fara samu na sai ihisan kuma sai ki sama masu abinda zasuci yanzu.
Dama haka kike so yar iska shine plan din da kika shiryawa yaran tun ian nazo nai murmushi na sabala dana a kafada nace basu saba cin kazanta ba tun wurin uwar su yanzu ko ba yadda za, ayi su iya cin jagwalgwalen ki sai a koma kitchen a koyi girki don an wuce wurin.
Ke ke ke hindatu may na fada maki tun farko bana son irin wanan jidalin kikace min bazakiyi ba yau kwanan ki nawa da zuwa da har zaki fara muna fitina haka tun jiya kike complain ke anyi maki abukaza.
Yanzu ina dawowa aka tare ni tun waje kun wuni kuna jidali a gidan nan bayana wallahi duk ina kwasan ku ku koma kano gaba dayan ku ko.
Na ce yafi nono fari a wurina ai can ma gida ne ba wani matsala ko can tace karya ne munafuka don ki min bakin ciki ko to ba inda zan tafi nazo ke nan zama daram.
Nace gaki ga gidan ai na shige gurin yara suna kwance kowa a cikin damuwa na zauna bakin gado Nasir ya dago kai yana kallona yace little mum barka da shan ruwa nace kunci abinci sai sukai shiru nace tambayan ku nake kun yi shiru mana.
Wallahi mum abincin ba dadi kuma yana wani wari wari nace yanzun may zakuci, da kuka zauna daki bakuyi magana ba ?
Jinior yace naje gun daddy ya koro ni nace kaima da gangan yanzu dai ba wanan ba ku tashi muje kitchen muga may zamu dafa mai sauki.
Da saurin su suka mike muka fito daga dakin nan muka wuce zuwa kitchen tare da yaran cikin sauki na hada masu abinci mai sauki sai gasu sun fito suna dariya harda ihisan na zubawa na kira Aisha ta dauki namu zuwa part din mu.
Nan suka zauna wurin uban nasu suka zauna suna hira suna cin abinci cikin jin dadi da walwala har suka gama suka dan yi hira suka mike zuwa dakin su.
Ni dai muna dakina da Aisha, da Atika sai helen dake biye damu nadauko ta ba dama na kore ta cikin mu kuma.
Anan da yake barcin azumi ne har barci ya kwashe su ban tada su ba na barsu nan sai asuba muka falka don yin sahur na riga na tanadar masu abin buda baki na dauka nakaiwa yaran nasu sai dana tabbatar da sun tashi sun shiga brush na bar dakin nasu.
Ban kwanta ba na shiga dan zirgazirga kafin ai kiran sallah na gama na zauna saida nai sallah na tayar da yaran suma sukayi suka fara shirin zuwa school.
Barci na nayi sosai koda na tashi na samu Aisha ta gama duk wani abinda ya dace ayi shi.
Wanka na fada ban damu da son zuwa gaida daddy ba don nasan baya gidan a lokacin don goma da wani abu a lokacin.
Gidan tsit sai kace ba kowa a cikin sa kowa na dakin shi yana barcin azumi a lokacin wanka nayi na fito don sama ma yaran da basu azumi abinda zasu ci.
Ina kitchen ina karainiya naji kamar motsi a falon ban tsaya juyowa ba naci gaba da abinda nakeyi a kitchen din.
Can dai na sake jin motsi sai na dan leka hindatu ce naga tafito kamar daga backyard din mu da alaman rashin gaskiya a tare da ita.
Na lafe don karta san ina kitchen din a lokacin da sauri ta shige dakin ta tana waige waigen bayan ta.
A hankali naci gaba da aiki ba tare da na damu da abinda nagani a gare ta ba don zargi ta nakeyi kawai nagama na kwashe a kula ina fito daidai ta sake fito sai naga ta dan kadu tace ashe kin tashi nace da ita eh har ta fara tafiya take cewa tun dazun kike nan ne ?
Nace yanzu na fito in samawa yaran nan abinda zasu dan ci tace oho yayi sai ta juya ta koma dakin ta nikan na wuce zuwa dakina .
Ance zance baizo maka sai kana tsaka da sallah shedan ya dinga rudin ka da zantutuka barkatai a zuciyar ka.
Irin hakane yazo min kan na duba backyard dinan naga may matar nan take boye min Aisha nasawa kira tashigo nace ta matso kusa da inda nake zaune saman sallayana.
Cikin rada nai mata bayanin abinda nake son tai min tace ba matsala ta fice daga dakin.
Takai min ti ashirin sai gata ta dawo dakin take cewa dani naga ni anty a razane nace wai da gaske tace Allah ko.
Nan muka bar zancen har zuwa dare nasan Aisha zata iya aiwatar da komai yadda ya dace.
Mun fito muka dora girkin abinda za ai buda baki a ranan tunda mu zamuyi duty .
Yi wana dora wancan sauke wanan har muka kamala komai da za aci na jera shi inda muke zama ai buda baki.
Tunda nake aikin nake ganin tafita takoma haka taitayi nace da Aisha ta saka ido idan naje sallah akan matar nan .
Bayan kiran sallah saiga yaran sun fito sun taru a falo nan mukai buda baki na tura yarta tace tazo tasha ruwa.
Sai gata tafito dakin tana ganin yadda muka taru ana raha kowa na farin ciki yana shan fruit da drinks din dana hada a wurin.
Sai ta bata rai ta juya zata wuce bata zauna ba nace bissimillah mana ga abin buda baki nan an aje tace barshi kawai har anjima ta juya ta koma dakin ta.
Mun gama muka shiga sallah amma Atika na gurun ta kasa ta tsare sai gata tafito tana tambayan Atika ke baki zuwa sallah ne kowa ya tafi tace sai anty Aisha tafito zan shiga taso yiwa yarinyar jan ido sai taga bazata gusa ba nan da can dole ta barta an bata mata plain din ta.
Sai bayan sallah ya shigo gidan ina daki Atika tazo ta kirani wai nazo daddy ya dawo ban dade ba na fito nai mashi sannu da zuwa ya karba ya shige dakin shi don ya sauya kayan jikin shi zuwa masu sauki.
Ruwa na hada mai yai wanka ya fito falo ina daki tare da yaran ban fito wurin su ba don naji muryan su a falon tare.
Ihisan ce ta shigo take fada min daddy yana kirana falo na karaso ina kara gaidashi da shan ruwa tana zaune gaf dashi tana tsiya ruwan juice din abarba a cup.
Ya dago ya kalle ni lokacin da nake zama saman kujera yace kin shige daki kin zauna da yara bayan kin san cewa nafito kuma .
Nace na dauka ba wani abinda kake bukata don na aje ma komai da zaka bukata wurin.
Yace baki zoba waye zai zuba min abincin nacu sai na dan kalli inda take zaune ina nufin bagata ba a wurin ta zuba mai.
Nadai sauko na zuba mai komai yadda ya dace na fara kwashe sauran zan shige dasu kitchen tace ina kuma zaki dasu ni ban ci ba ?
Nace ba tare na zuba maku dashi ba na mu yana can sama table ajiye nai saurin kwashewa na bar wurin da kayan zuwa kitchen tabishi da kallo ko zaiyi magana.
Na riga da na shirya amsan bata a lokacin koda zaiyi magana kan hakan sai baiyi ba din har nakai na aje.
Na fito naso nq shige sai naji a jikina ni daddy yake kallo sai dai naki yarda na dago na kalle su.
Yace Rahama daidai na dan juya na amsa naam daddy yace yaran ki sun ci abinci ko ?
Sunci tun dazun daddy yanzu fruits salad suke sha kafin su kwanta yace yayi kyau.
Na fahinci daddy yana da wata manufa akaina ranan don haka naki bada fuska yadda zai samay ni da sauki hakana.
Yana gamawa na fara kwashe kayan hindatu dake zaune ta cika fan don ko magana batayi ranta ya baci dani.
Ban koma wurin su ba na shige daki abina na samu yaran sun watse sai Aisha ke gyara wurin da suka bata.
Wanka nayi na shirya na haye gadona na mimike abina ina waya da zarah sai dana gama Aisha ke cewa dani anty na dauko fa nace abune aciki tace wallahi helen nasa ta ciro yana can mun boye shi a wani gyrin mun mai fitsari a razane nace Aisha kina da hankali idan wani ayan Allah ne fa ?
Tace a, a wani abune kamar tsoka da gashi an sosoka mai allura a jikin shi kamar mutum mutumi.
Nace wa iyazu billahi injin kun jefar tace helen ta fita dashi can bayan gida sai da muka wargaza shi gaba daya muka fitar dashi takardan dake ciki muka boye kawai.
Muna nan muna magana akan zancen daddy ya shigo dakin sai Aisha ta gaidashi tafice daga dakin ta bar mu a ciki nida shi.
Kallona yake ni kuma naki dago kai mu hada idanuwan mu ni dashi yace humm kawai tare da karasowa inda nake.
Rahama wai har yanzu fushin ne kike baki daina ba ko may ?
Nace fushi ni bani fushi da kowa ai da ina fushi aida ba haka ba ba yanzu nafito wurinka ba can fallo inda kuke zama daine banayi har a soka min magana tunda ni banje na takurawa mutum ba.
Yace naso ace tun kan hindatu tazo ta fahinci halin da muke ciki kin daina wanan fushin haka na don Allah ki sake jikin ki ki bar wanan fushin hakana.
Nace na huce indai nice yace koke fa in ba haka ba ko yaran ki abin zai iya shafa ai.
Ya juya yana fadin ina jiran ki a dakina ban tanka shi ba ya fice daga dakin nabishi da harara kawai har ya fice.
Har sha daya da wani abu ban je gun shi ba sai ga wayan shi ya shigo min na dauka lokacin har na soma barci.
Yace wai kin manta da nine anan komay may ke damun ki ne haka wai Rahama may kike son bullowa dashi ne a tsakanin mu ?
Ina ce mun riga mun yi magana kin ce komai ya wuce yaya kike son nayi da raina ne please.
Ban yi magana ba sai mikewa da nayi na gyara shiri na fice daga dakin inda na samu yana kwance ban bata lokaci ba na kwanta nima.
Ya sauke ajiyan zuciya tare da birginowa inda nake a kwance yakai hannun shi a jikina.
Abin mamaki ranan duk yadda daddy yaso yakai a gare ni sai ya kasa duk kokarin shi a kaina abin yaki sai ya koma tankar mace a guna.
Ya koma yana sauke nunfashi gefe daya tare da wani irin tartso zufa a jikin shi ni dai ina kwance lamo nima mamakin hakan nakeyi yau a gare mu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , ,

79
Wanan matsalan da ya faru tsakani na da daddy sai ban dauke shi komai ba a raina ko banza ma acikin watan mai arbarka muke watan kara kusantar bawa ga ubangijin shi.
Ban sa abin a raina ba don ban dauke shi wani babban matsala bane a wurina sai na samu daman yin ibaduna yadda nake so.
Yau shine karo na uku da abu daya ke ta maimaita kan shi sai ya kusan kaiwa gare ni sai wasa ya canza sallo aiki.
A bu daya dake ci min rai shine rashin walwalan da naga daddy baya ciki a yan kwanakin nan.
Don zai zauna yayi tagumi da gani akwai abinda yake tunane a ranshi tun abin na damuna har na fitar da damun a raina tunda bai fada min komai ba.
Na fito falo daga dakina don in danyi hira da yaran dake gida yau weekend ba su zuwa school a gida zamu wuni tare dasu don haka nakan yi na zauna da su na wani dan lokaci muna hira a tsakanin mu.
Hiran mu muke kwasa ga tv na aikin shi sai faman dariya muke a tsakanin mu banji sallaman shi ba sai ganin shi mukayi a tsakiyan falon ya shigo gidan.
Nan yaran har ni muka shiga yi mashi sannu da zuwa ya samu daya daga cikin kujerun falon ya zauna akai tare da dafe goshin shi da hannuwan shi.
Sai duk muka bishi da kallo Nasir ne ya fara mikewa zai shige sai daddy ya bude idanuwan shi da sukai ja yace No zauna abinka mana kuyi hiran ku.
Yaron ya koma ya zauna inda ya tashi sauran ma sai suka zauna baiyi magana duk zaman da yayi sai lumshe idanuwan shi da yayi.
Nace dashi daddy yau lafiya kake kuwa naga ka dawo wanan lokacin ya dan bude idon shi ya sauke su gare ni yace inaga dai azumi ne yasa min jin ciwon kai yau don ni ban faye saurin yin ciwo ba haka.
Sannu muka fara yi mashi yana amsawa can ya dan dago yace Nasir ina Ihisan take banganta ba nan cikin ku.
Kafin Nasir yai magana sai jinior yace da uban tunda mum din ta tazo ai ta daina zama tare damu ko school muka tafi sai ta dinga muna abinda taga dama yanzu ma saboda ita late mukeyi zuwa schoool da safe.
Daddy yace may yasa baku fada min ba tunda ta fara hakan yace kira min ita dakin nasu sai yaron ya mike tafi gun kiran ta.
Tare da uwarta suka fito falon inda uwar kecewa dashi kadawo ashe yace eh kawai ya juya kan ihisan yana cewa may yasa kowa na falo a na hira kika shige daki ke ?
Yanzu nake jin duk kwanakin nan bakya fitowa da wuri sai kin sa yan uwan ki yin late a school daga yau kada na sake jin haka daga gareki.
Sai uwar take cewa wata sabuwa yau kuma Ihisan ce akaiwa kulli bani ba babu dai yadda zakuyi damu gani nan bari nan wallahi.
Yace ke dakata wani irin magana ne

Please Login or Register in order to submit comment