Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Biyar da yan mintina ta falka taganni a hakan yadda nake kwance tausayina ne ya kamata a gurin.
A hankali take kiran sunana na falka zubur ina cewa anty kin tashi nw tace eh ina son in dan kewaya ne bandaki ga lokacin sallah ma yayi.
Na gyara inda zata mike ta yunkura da kyat ta tashi zaune harta dan sako kafanta zata mike sai kuma naga ta koma ta zauna can ta mike da kyat ina tsaye ina kallon ta da kyat take cira kafa tana tafiya zuwa ban dakin.
Naji tace Rama zo ki kamani jiri nake ji sosai na zo da sauri na kamata zuwa bandakin sai da naga ta zauna saman toilet na fito daga waje sai da taga ta doro alwala sai tace nazo na kamata.
Har lokacin da alama tana jin jirin nakaita bakin gado ta dan zauna na shimfida na shimfida mata salaya ta zauna a zaune tai sallah ranan duk kokarin da take dashi gurin yin sallah a tsaye ga halin da take ciki.
Nima alwala nayo nan na zo nai sallah ina addua naji tace Rama don Allah ki rufe ni sanyi nake ji jiikin ta rawa sosai a lokacin.
Da sauri na dauko bargo na rufeta dashi sai sharking jikinta ke faman yi duk na rude na rasa abinyi a lokacin.
Can dabara ya fado min a raina da sauri na nufi inda wayan ta yake na fara duba lamban mijin ta.
Naga ta rubuta mai Heart Beat na danna kira duk da babban waya ne gareta amma na gane yadda zan kira dashi.
Kira daya na biyu naji an daga wayan da sauri yake cewa heart beat yaya dai sai dana daure nake cewa daddy nine anty ce jikin ba dadi bata samu barci ba tun dare.
Yace subbahanallahi Rahama shine baku kirani ba muje asibiti nace harta dan samu sauki ne da farko shiyasa ban kira ba.
Naji ya kashe wayan nashi nakoma inda take kwance a kasa saman salaya tana rawan sanyi cikin bargo.
Baifi minti shidda ba ya fado dakin a rikice dashi idanuwan shi a kansa yana kallonta da saurin shi ya karasa gurin da take ya dan yaye bargon a hankali.
Idon ta yana rufe ya kai hannayen shi yana dan taba jikin ta naga ya mike zubur da sauri yacewa shiryata mu tafi asibiti yanzu da ita.
Na mike jikina min rawa na sauri dauko wata doguwar riga na samu ta mike da kyat tasaka na kamata zuwa hanyan waje duk nauyin ta a kaina yake sai gashi da saurin shi ya kama min ita muka fice daga gidan ban ko tsaya kallon inda mama tashiga ba ashe tana bandaki.
Nan dai muka kama hanya sai asibiti take aka karbe ta sai dakin likita aka shiga dubanta an fada muna cewa, tana fama da rashin lafiyan masu ciki yashigo mata kuma.
Gado aka bata za, a kara mata ruwa da allurori idan ma har da bukata harda niji zaa saka mata likita ya fadi.
Hankalin mijinta yai matukar tashi yake cewa ai mata duk wani abinda ya dace a taimaka mata dashi don Allah.
Dakin da za, a kwantar da ita aka kaimu nan dai aka fara mata duk abinda ya dace muna waje zaune cikin damuwa dagani har mijin nata kowa hankalin shi a tashe yake lokacin.
Ba adauki lokaci ba barci mai karfi ya dauke ta sai lokacin aka bari muka shiga gurinta tana barci sai dai kana gani kasan tana cikin wahala sosai.
Lokacin ne yaran suka fado min a raina na sauke ajiyan zuciya nake cewa ina son nakoma na shirya yara a gida saina sanar da mama halin da ake ciki.
Nan ya dan dago kanshi daga inda yake zaune yana dan buga kafanshi a cikin damuwa yace zaki gane gidane idan kin fita nace insha Allahu zan gane.
Bussimillah yace dani tare da mayar da hankalinshi gareta na fice daga dakin na nufi hanyan fita daga asibitin.
Tafiya nakeyi a cikin damuwa yanayina yake ina tafe babu abin hawa a lokacin sosai duk wanda nagani a cike yake da mutane can naji anata faman horn a bayana ban juyaba don ban zaci da ni akewa horm sai da naji horn din ya matsa ne na dan daga kaina mijin anty ne na gani yana min horn din yace shigo na saukeki nima zan shirya ne.
A tare muka dawo gidan muna tafe ina kallon hanyan don in gane kada na bata idan zan dawo asibitin, ina shiga gida na samu mama a cikin damuwa tana ganina take cewa ina kuka shiga nafito ban samay ku ba nace cikin wani yanayi mama asibiti aka kai anty an bata gado tana can kwance nake mata bayanin komai.
Na nufi gurin yaran da sauri na samu sun falka sai dai suna kwance da sauri na shirya su nai masu indomie kawai ranan sun dan makara zuwa makaranta.
Na shiryawa Anty breakfast koda ta tashi tana son cin abinci abinci mai sauki na hada mata jeloup da vegetables sai anta da nai amfani dashi a cikin wani littafi na karanta yadda ake hada shi don mara lafiya na zuba ruwa a flask da sauran abubuwan bukata da za, a nema acan.
Nafito na hadu da zulfa tana shigowa main falon na gidan nai mata ina kwana ta amsa a dakile ta wucce abinta.
Allah ya taimake ni don droup na dauka sai asibitin mijin na waje yana magana a waya ya hangoni tafe da kaya.
Waya yake amma yadan kalloni na wuce shi tare da dan dukawa nagaidashi na shige ciki.
Har lokacin tana barci mai nauyi ga drip din da aka samata da allurai acikin sa ya canza launin ruwan.
Mama na zaune saman kujera na shiga da sallama tadago tana cewa kin dawo Rahama na amsa da ehmama ina aje kayan a gefe tana ganin nazo da carpet da filo don zama tace Allah dai yai maki albarka Rahama don zama saman kujeran ba dadi.
Na karasa bakin gadon ina cewa har yanzu bata falkaba ne ?
Bata falkaba likitan yacs abarta ta samu barci don shima cikin lafiyan ne haka, wanan yar dai Allah ya tausaya mata yabata lafiya amna tana wahala wallahi.

****** ********* ******

Zuwan Jatau gidan mu gurin biko yafi a kirga wanan lokacin ganin mama ba zata sauki ba yanemi sulhu gareta.
Kudin data yanka mai dole ya fitar yaba da shine suka dan hada ma Lawisa kayan aiki da dan gado madaidaici da sauran abubuwa.
Sai dai Lawisa takafe bazata koma ba gidan nan dai sani Allah sani Annabi aka samu suka shawo kanta aka mayar da ita gidan da kuka dakomai bafon ransu yaso hakan ba har mama din.
Zuwa wanan lokacin hankalin baba ya dan dawo gareshi don ya fahinci rashina da mahaifiyana a gidan ba karamin kuskure yayi ba.
Don gidan gaba daya ya sauya ba dadi gare shi ga cin mutunci ga mama kaman an kara mata hakan ne bata tunanen mutuwa ko kadan a rayuwan ta.
Haka yasa ya nemi aminin shi suje ai mai bikon Inna ko zata dawo dakinta.
Amma inna tace har abada tagama zama a gidan shi don ita yanzu hankalinta a kwance yake mata.
Duk yadda yaso Inna taki daawowa gidan hankalinshi yai matukar tashi ga gida ba dadi ko ga diyanshi agaban shi yaro sai yai abin fitsara ba su dauke shi komaiba garesu.
Lawisa na komawa matan gidan suka hade mata kai kan sai an raba girki ta fara tace ita baza tayi ba tace da Jatau ai Rahama da tai aure a gidan garbati marigayi bata girki da matan shi don su suna da iyali sai itace za, ace ta shiga cikin manyan mata tai girki.
Jatau dai ya fahinci tana da kaifi irin na uwarta na ya fara shiga da fice yana neman magani ya kafeta a gidan.
Yai nasara cikin kwana biyu aiki ya haukanta sai gata tafara yin komai na gidan tukunyane babba duk ranan girkin mace ita zata tukeshi da tuwo.
Ba wani cima na kwarai a gidan dare da rana tuwone miyan kadi dasafe ma sai mutum ya danyi dabara neman na karyawa don dimamay akeci sai rana za, a girka abinci kowa yaci.
Wani lokaci ma idan yan tsiyan nashi na akai sai dare za, a girka abinda za, aci a gidan irin dai mugun rayuwan mutanen kauye.
Cikin dan kankanin lokaci tafara fita hayacinta ta ramay tayi baki sosai da ita ga matan gidan da ita babu dadin zama ko kadan.
Komai sai su ware ta ai mata wullakanci ba matan ba ba yaran su ba gashi ita ba sana, a sai zaman baza ga Jatau bai kwantuwa ko kadan amma akwai shi da auki kwana da mace kamar ba tsoho ba.
Har gudun ranan girkinta yazo rakeyi don bakin kwazaba irin nashi bai da sauki gurin yin harka da mace gashi gidan shi mata basu fita kasafai sai tsawon wani lokaci.
Abindai babu dadi gashi sam yanzu bata son abinda zai fitar da ita gidan duk da bakin wahalan da take sha aikin gida kamar zai kasheta.
Sai Rukaiyyane kan da tafi gurinta wani lokaci ta dan taimaka mata da abinda ke hannun ta don ta samu na tabawa don mijin baya kwantuwa.
Idan ta koshi sosai sai ranan girkinta amma idan kishiyoyinta suka tuka dan kadan ake zuba mata a kwano ace abincine bai kaiba kowa haka yasamu.
Ranan da abin ya isheta ta dauki abincin ta nufi gurin wace ta raba ta gwanmace ko kashe ta zasuyi yau sai tai magana kan hakan.
Tana zuwa tace maman Abu wanan abincin da aka zuba min aiko loma uku bazai kai ba dubifa yawan shi ki gani.
Matar ta dago kai ra kalleta sama da kasa tace tunda uwarki ta tuka min ba sai kisa na cika maki kwano ba tunda kinfi kowa agidan ne.
Wani irin takaici ne ya kama lawisa jin harda zagin uwarta daga magana kan abinci iya hakkuri dai tayi shi a gidan nan duk irin cin fuskan da ake mata tana daurewa don magani na aiki a kanta lokacin.
Cikin zafin zuciya tace wallahi ba dai uwata ba sai dai na wanda ya zaga cikin mamaki matar ra wawuro ido waje tana kallon Lawisa da mamaki.
Tace lalai ma yarinya baki san wuta ba sai kin taka kina nufin uwata ke nan komay ?
Tace ni dai wanda ya zageni dashi nake ai tana yowa kan Lawisa ita kuma tasa kafa tai shuri da abincin da miyan da matar ta cika kwanon ta dashi nata dana diyan ta abincin ya zube a kasa .
Haushi yakama matar cikin wata bakar zuciya jikake kiff takaiwa lawisa duka da karfi Allah.
Tabita ta hada ta tukwanen dake gurin da kyat Lawisa ta iya mikewa matar ta kara kai mata duka cikin zafin rai da hasala jin zafin da lawisa tayi yasa itama tai kokarin ramawa ai nan dambe ya kaure masu.
Abinka da sabon jini lawisa tafi hanne karfi sai ga hanne a kasa tabita ta taushe ta akasa .
Kafin mutanen gidan su fito duk sun sha wiyan junan su a gurin yaran Hanne na ganin haka sukayo kan Lawisa suka taya uwar su fada.
Sun dake ta sosai sai da suka barta kwance a kasa suna fadin shegiya gobe ki kara cewa zakiyi fada da uwar mu ki gani.
Da kyat lawisa ta daga daga kwace cikin karfin hali rake cewa wallahi ko gobe aka zuba min abinci kamar nazo bara bazan kyale ba.
To mu zuba dake mugani mara mutunci kawai in ma ba abin baba ba wazai kwashe ki haka ragowan kwararo dake kawai tace oho nadai ji haka ubanku ke zaune dani kuna jin haushi na.
Dariya da shewa suka saka mata suna fadin andaiji kunya wallahi an kare da auren tsoho.
Haka taja kafata zuwa daki ga yunwa na damunta babu abinda zataci a dakin gashi gurin rashin hakkurinta ta zubar da dan abincin da aka bata.
Tana kwance ta rasa dubara ga bakin ciki da yunwa na addaban ta a lokaci daya mikewa tayi ta suri hijjabinta ta saka sai gidan su.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI ALLAH YA GANKI, , ,

22
Tun da safe mukaji ana dukan kofan shigowa part din mu ina kitchen ina hada abincin yan makaranta wanda kullun da nauin abincin da nake girka masu.
Da sauri na fito zuwa kofan ina budewa naga wata mata tana da matukar kama da hajiyan mijin su anty.
Nai ma matar ina kwana ta amsa tana kokarin wucewa ciki tana fadin lafiya kuka kwana ko ?
Na bata amsa da lafiya kalau mama sannu da zuwa ta wuce tana fadin ina dakin Saaden yake na nuna mata dakin na koma kicin abina naci gaba da aikina.
Daidai na kanmmala ne kuma stil naji ana sallama muryan namiji ne da sauri na fito ina karba sallaman na shi yana tsaye daga kofan mu na gaidashi yace ina maihaihuwan take nace tana ciki yace fada mata ga Bashir yazo.
Najuya na shiga dakin suna zaune har wanan bakuwar tana dauke da yaro na sanar da ita zuwan bashir din tace nace ya shigo daga ciki.
Na juya na fada mai na koma kitchen don na kawo mata abin karyawan ta.
Ina shiga naji mutumin na fadin tun dare ya damay ni da kira sai nazo naga halin da kike ciki ko za, a tafi asibiti ne ashe ke Allah ya kawo maki saukin haihuwa haka ?
Matar da ta fara shigowa tace ni ai wallahi Alhaji karami ya tayar min da hankali da kyat naga gari ya waye min wallahi.
Tace mata gidan sun san da haihuwan kuwa don ban ji duriyan su ba ko da na shigo sai shi namijin yace anya Yusuf bai fada masu ba.
Matar tace bari ai yanzu na shiga na fada masu naji idan basu ji bane amma ai haihuwa da ciwo ya kau da komai da suke ji a ransu cin tuwon kishiya ranko.
Mama Altine dake zaune gefe ne take cewa banda yaran nan sun dauki kishi da zafi wallahi ace ko gaisuwa na musulunci babu shi a tsakanin ka da dan uwa balle in yana cikin wani hali ka sani.
Ko kwana ki data kwanta asibiti bance matan sunyiwa yarinyar nan sannu ba har ta dawo gidan nan ban gan su ba gaskiya.
Matar tace daurin gidin hakan suka samu daga yaya amma ta yaya zan bar gidan dana yana ci da wuta har na mara ma abin naya don son kai.
Yanzu cikin su ukun nan waye bare a cikin su tunda duk abu guda suke ma zama sai a zauna a sulhunta komai kowa ya tsaya maysayin shi amma ba ayin hakan.
Yanzu ba don Allah ya kawo wa yarinyar nan dabara dauko yan uwanta kusa da ita ba yaya ke nan ga yadda haihuwan yazo mata haka a gida.
Bashir yace ai ina ga abinda ke tayarwa Yusuf da hankali ke nan don ma yana jajirce ma akidar tasu ai da abin yafi nan.
Mata sam basu da tausayi akan kishi wallahi in bashi ba may ye a cikin hakane wai kazo ka samu mutum da mijin shi suna zaman lafiya da rufawa juna asiri kace ina suka fito kai dole sai naka akidar zaka kawo a cikin gida.
Bayan sun san auren su dashi auren kaddarane haka Allah ya nufa dashi don yana mai bin umurnin iyayye akayi shi ai da basu isa ba wallahi.
Muryana ne nake cewa anty ki tashi kici abincin kada yai sanyi.
Ta dan dago daga inda take tana fadin Ramana abinci kikai min tunda safe haka ?
Matar tace to ai shine kyau shine jegin asali kaci a binci sai jikin ka yai kyau da sauri ba wanan shaye shayen zamanin da mata keyi ba.
Tashi ki karya kin san jikin ki ko banza ba lafiya ne da shi ba ki daure kina ci koba dadi yafi jikinnki yai kyau sosai.
Sallama su anty Aisha ne kannen maigidan su biyu suka shigo suma dau nasan daddy ne ya rudasu suzo suga matar nashi take dakin ya cika da jama, a.
Ina ganin haka na sa a raina yau ba fita school gareni ke nan don ga baki a shiyan mu tab.
Matar data shigo da farko naji sun kira da mama laraba ashe kina nan tace ba dole ba dana ya hanani barcin dare sai nazo na duba mai matarshi naga halin da take ciki.
Su anty Aisha sukace tun da asuba ya bugo muna waya wai tunda na karata nurse nazo na duba jikin ta na gani.
Mama laraba tace ai Alhamdullahi yadda yake zaton abin ba hakana bane da sauki gaskiya bari naje gurin wa yan can marasa hankalin naji may ya hana su shigowa har yanzu su duba yar uwar su da tai gwajin arziki .
Kai mama ai da kin kyale su inji anty hadiye da suka shigo tace ni banga abin damuwa da lamarin su ba wallahi tunda Allah ya sauke ta lafiya ita da baby a kyalesu kawai shi yafi.
Bari tace inji Aisha basu da kirki wallahi kwanaki sai da nai ma hindatu tas akan Saade ta dauki bakin ciki da hassada ta dora kan wanan cikin a ranta.
Wai kullun tace bata da lafiya amma ta iya shigewa daki tai ciki da namiji su masu lafiyan ma an ki basu cikin ji min maganan hauka anan .
Wallahi ban san lokacin da idona ya rufe ba nai mata tas a gurin sai da ta raina kanta.
Take cewa wai ai dama saade duk ta asirce mu hajiya ce kawai tafi karfin ta cikin mu.
Nace ni na san batai muna komai ba halinta dai a gare mu ne ya asirce mu ba asiri ba.
Basu da hankali kin san halin yaran yanzu ne su shigo gida su samay ka da matar ka suce sai sun rabaka da ita ko ta halin kaka don bakin kishin tsiya da hauka ai kishiya abokiyar zamane.
Hadiye tace inda sun zauna lafiya da anty saade ai ba karamin karuwa zasuyi ba da ita mutumin da bai dauki duniya da girma ba ai dadin zamane dashi.
Mama laraba ta fice daga dakin tana jaddadawa anty ta ci abinci sosai ta bar tsakura
Anty ta ce ni dai wallahi Rama yau kin ja min cin abincin safe haka yarinya da shegen akidan tsofaffi haka ina ni ina cin abinci mai nauyi haka da safe ?
Aisha tace ai wanan sister din naki wallahi tayi ranan ta tafi tabar ni da sha, awan ta sai data gyara min gida na tsab ta dawo gidan nan.
Duk taron matan nan an rasa wace zata daga tsintsiya ta gyara guri haka muke zaune cikin kazanta sai zuwan ta wallahi ta taimaka min ba karamin dadi naji ba.
Jifa part dinki kamar ba a haihuba kimai neat dashi gwanin ban sha,awa wallahi.
Antyna tace Rama akwai tsabta ai bata son kazanta ga ta da sanin ya kamata kinganta nan tun zuwan ta wallahi ban taba nuna mata yi min kaza ba itace tasan ya kamata bakiji na daina zancen neman mai aiki ba yanzu.
Sai dai yanzu data fara karatu dole na samu mai aiki amma ban son yar birni kauye nake son a samo min yar ma daidaiciya yadda zan iya controling din ta.
Aike dai anty da yar birnin da yar kauyen sai dace yanzu duk abin daya ne ai inji anty hadiye.
Nan dai sukai ta hiran su a tsakanin su suna raha Bashir yace shi zai koma don zai tafi aiki ne yai masu sallama ya fita tare da cewa matan shi zata zo in an jima.
Mama Laraba a dakin Zulfa ta fara shiga tana zaune da kayan barci a jikin ta shiyan nata sai wani tsami yakeyi wanda ma bataji ko rabin shi ba a dakin mai haihuwa daya dace ace can akaji wanan abin.
Tana ganin mama tace mama kece da safen nan injin dai lafiya nagan ki gidan yau kuma da safe haka ?
Au bani da ikon zuwa ke nan gidan lokacin da naga dama sai anzaba min ke nan ko ?
Shiru tayi tasan maganan da taiwa maman yaci mata rai ke nan tabata amsa da hakan don Zulfa bata son taga suna shigowa gidan ko yaushe shiyasa ma da suka fahinci gidan yanzu ba kamar da can da anty take ita kadai bane da suke zuwa gurin maigidan ko ita sukawo koken su garesu kuma ya taimaka masu koma bai nan anty zata iya taimakawa da dan abinda ke gareta.
Amma zuwan yaran nan biyu gidan yasa kowa ya jaye daga shiga gidan tun zuwa da wata daga cikin yan uwa tayi Zulfa tace ana yawan damun su da zuwa kullun sai wani yazo kuma rokone su ba, a bari yai masu hidima yadda ya dace sai dangi.
Take labatin ya bazu ga dangi kowa ya kama kan shi yanzu basu zuwa suma basu zuwa inda suke zumunci na batun lalacewa.
Nan dai take cewa to ni ba wani abu nazo yi ba baki da labarin yar uwar ku ta sauka ne tunda dare halan ?
Sai da ta ya mutse fuska take cewa ya bugo min amma ai naga gida daya muke ita bata fada muna ta haihu ba sai shi dake wata kasan zai bugo muna waya.
Mama Laraba tace lalai Zulfa kinyi nisa shi mijin naku bai isa ba ke nan ya fada maku kubi sai naki ra, ayin ko anya zulfa kin wa kanki shimfidan arziki kuwa ?
Kada ki manta yadda kukai tabin mu keda uwar ki akan akama kafa ai auren nan a tsakanin ku yanzu kina ganin kin samu shiga shine kike fito da kalar ki kina hura hanci ko?
To kiyiwa kanki kiyamallaini tun yaron nan baidawo ba naki ya samay ki gidan nan wai ke baki tunanen mutuwa ne arayuwan ki komay ?
Ran Zulfa ya baci don mama laraba na yar mahaifiyarta ne data fada mata magana sai dai duk da haka tace mama ai ko ba, a kama kafa ya aure ni ba Allah yayi aure a tsakani da shi dama yaya za, ayi tunda Allah yayi shiga kima daram ba fita.
Zulfa ni kike fadawa haka to ki sani ni ko uwarki bata kallon idona ta fada min magana haka kai tsaye don akwai mutum biyu a tsakani na da ita.
Ki sani ni tallaka ne cikin dakin mu amma ban dogara da abin wani ba nawa nake mikewa na bida don haka babu mai kallon idona ya fada min maganan akan abin shi.
Nasiha ne nai maki ba lalai bane sai kin dauka indan zaki gyara ki gyara Alhaji karami ne kin san halin shi tun baki shigo ba.
Idan zaki sauke girman kai ki rufawa kanki asiri kije ki gaida yar uwar ki ki mata barka da arziki daya fi maki.
Zulfa tace mama laraba da kece kika haifeni nake cikin wanan daulan bazaki ce najeyiwa matar da bata kaunan farin cikina barka ba.
Amma yanzu nagane zumuncin baki wasu keyi wa yan uwan su ba har zuciba saade dai kishiya tace matar mijina

Please Login or Register in order to submit comment