Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ashe duk mata ke kingani da idon ki ba labari aka baki ba ko yake cewa anty hakan ?
Ya juya zai fice daga dakin nace ai ita tasan halina bazatai min hukuncin da bashi ba akaina.
Anty tace ana magana kuma ka juya zaka wuce ba akai karshe ba.
Yace may kike son nace mata kuma bayan kinji magana tun farko zagine bani so ko ita ai nai mata magann haka.
Daga haka ya juya abin shi ya fice anty tace kin gani kinga galin maza ke nan shifa bawai ya rike maganan bane fa yayi a lokacin kuma ya wuce gareshi.
Nace ya wuce mana tunda ita an mata yadda take so taji dadi tai dariya tace anya Rama ba kishi kika fara yi ba kuwa ?
Nace anty aiko kishi nake ba zan so na jawa wani halaka ba a rayuwa su dai da suke kishina zan bar masu miin su a huta.
Don Annabi yace kasowa dan uwan ka abinda kakeso wa kan ka ba zan yarda don ni ki zauna ana bata maki ba haka.
Tace to ni dai na baki hakkuri kiwa Allah kibar zancen nan hakana don Allah dai ya wuce hakan ma da kikayi ya isa.
Don ko ba komai gobe idan wani abu ya faru a tsaya ayi bincike kafin a farwa mutum daya.
Don Allah kiyi hakkuri ki koma normal kamar yadda kik da farkko da kowa kinga ko yaran ki yanzu da sun fara damuwa da rashin ki.
Ta mike tace na barki lafiya komai ma ya wuce don Allah ban son a kara tayar da zancen kuma.

********* ********* *********
Ranan da zan karbi girki nayi komai sai dai kafin ya dawo masalaci har na jera komai na dawo dakina na zauna don nasan idan anty ta fahinci wani abu zatai min magana.
Ko da daddy ya dawo daga sallah ya samu abincin shi a falo sai dai bani a cikin falon kamar yadda na saba idan nakai na zauna sai yaci na kwashe kayan.
Haka ya zauna zuciyar shi a vunkushe ba dadi ko kadan ya dan taba kadan ya bari duk da abincin yayi dadi kuma yasan nina girka shi da kaina.
Shiru shiru baiga na shigo ba yanayi yana kallon agogon falon har gooma saura ya mike ranshi a bace zuwa cikin gida.
Part din anty ya biya bani ciki sai yara dake kallo ya shiga gurinta yai mata saida safe ya fito.
Direct part dina ya nufa kofan yana a rufe ya murda sai yaji shi abude yake ban riga da na rufe ba ko.
Ina zaune a kasa nayi rigingine da kaina a saman kujera idon a rufe ina karatun kur,ani da kai ina dan juya kafana daya dake a dage.
Yashigo har yai tsaye a kaina ban sani ba sai kamshi shi danaji yasani gane yana dakin.
Na dan bude idanuwa na a hakali na gan shi a tsaye akaina na maryan na rufe tare da kai aya na sadakallahul azeem.
Yana tsaye dai ya kura min ido baiyi magana ba sai yakai zaune saman kujera.
A hankali ya mika hannun shi ya dan rugumoni na jaye jikina sai ya dan sauko ya kama yatsun kafana a hankali yana dan ja cikin tsigar wasa.
Ina jin hakan har cikin raina sai na dake kawai ban yarda na sa a raina ba balle abin yai tasiri a jikina.
Ganin ban bada wani reaction ba yasa naji yace humm Rahama ashe haka kike da riko ban sani ba.
Yana batun rugumoni na ware idanuwa na nace please daddy stop nace daddy ina ganin kimar ka da darajan ka sosai dakai da matar ka shiyasa nake rage wani abu.
Ni ba yar kowa bace kuma ba yar birni bace face yar kauye fakiriya kamar ko wace yar tallaka.
Yana jin abinda na fadi naga ya mike ya koma saman kujera ya zauna yai shiru can naji yace.
Rahamaa zauna da kyau muyi magana dake bani son irin wanan rayuwan da matana sam.
Jin abinda ya fadi yasa na dan kara gyara zamana don girmamawa gare shi.
Yace nasan kin san dai aure mukayi wanda ake ganin a bisa kaddara mukayi shi ni dake.
Amma iyanzu dani dake mun san aure ne na so da kauna mu Allah ya tabbatar muna akan mu.
To dan may kike kokarin son tarwatsa muna farin cikin mu a hakan da kikeyi yanzu ?
Wanan abin da kikeyi zai sa dani dake dama antyn ki ai muna dariya don idan tayine daniyar fanshe haushi to haushin ta kara akaii.
Duk macen da kika gani a gidan nan nasan halin kowa a cikin ku dakuma haka nake zama da kowan ku.
Yadda na dauki kowa a gidan nan haka kema na dauke ki don a matsayi daya kuke gare ni.
Idan naa kyale ki har kika saba da zagin iyayye irin na Hindatu haka zaki saba dayi kema baki jin nauyi da kunyan yin haka ga kowa.
Amma ni magana ta nayi shine akan gaskiya sai dai ku kun kasa fahinta saboda akidar ku na mata.
Koda ban gurin kukai fadan nasan wa zai fara zagi a cikin ku amma sai na fifiita ki nai maki fada don ki gyara tunda ita nayi nayi ta daina ta kasa bari ya zama mata hali zagi a bakin ta ba komai bane ita a wurin ta.
Nace amma daddy shine zaka hada har da anty kai mata tas matar dake iya kokarin ta akaina akan may zan zauna ana bata mata rai sabodani ko yaushe bayan tana fama da kanta.
Yace nafa san abinda nakeyi Rahama ita saade da tasan halina aikin ga bata dauki abinda zafi yadda kika dauka ba ke.
Daddy ni banin son har wata rana magana ya kai ga hajiyan ka tazo tai min yadda naga tawa anty kaga kawai ka sauwake min kowa ya huta tun ba, aje ko ina ba.
Tun yaushee hajiya taji zancen ai sai dai kada akara kawai amma tun ranan mahaifiyar hindatu tai mata waya.
Nace daddy kagani don Allah kayi hakkuri hakana don gudun abinda kaje ya dawo kuma don kaga laifin zai dawo ne ya taru akan anty daga baya.
May kike nufi da hakane wai Rama kekina tunanen zan iya rabuwa dake ne ko may a yanzu ni sakin mace baya a cikin tsarina ko yana ciki bake ba kuma.
Wai ma may kika dauki aure ne ke kina daukan aure abin wasa nagani ko ?
Daga yau ki cire irin wanan zancen na zaki bar gida a ranki don ba a gida na ake wanan maganan ba.
Nai haukane da zan samu zukekiyar mace kamar ki na saka akan dan maganan da bai taka kara ya karya ba.
Don haka ki cire komai a ranki ki tashi muje ki bani hakkina dake kanki kada ki cuta min da yawa.
Kin hana ni ganin fuskan ki kwana biyu kin boye min wanan surar da nake gani naji sanyi a raina yanzu kuma zakice abinda Allah ya halsata min ma zaki min rowan shi to ba zan iya jure wanan ba gaskiya.
Don ya fita ya barni sai kawai na saka mai kuka wiwi maimakon ya tashi sai ma daukana yayi cak zuwa cikin bedroom dina Allah ya taimake ni tsab nake don bai kyale ni ba duk da kukan da nake sai da ya samu gamsuwa a gareni.
Ranan anan dakina ya kwana sai safe warwas yafito duk matan gidan sun fahinci komai ni abangarena koba komai na gwadawa hindu nima din mace ce kamar kowa duk da ni diyar tallkawane da take gani.
Washe gari ban fito da wuri ba kuma ba zuwa school don haka na baje nai hutun gajiya nai ta barci abina sai sha daya na tashi don banda damuwa nasan anty zata bashi abin karyawa idan ya nema.
Na tashi nai wanka na shirya na nufi gurin anty mu gaisa yaran na gida su suka fara tarona.
Nashiga daki tana zaune tana waya na samu guri a gefe na zauna har tagama wayan ta juyo gareni tana fadin kin tashi Rama ?
Nace ina kwana anty tace kin dai huce naga alama yau sai dai ashe haka kike baki ita turewa Rama ?
Murmushi nayi na dukar da kaina kasa nace anty ba hakana bane tace to komai mutum zaiyi idan an bashi hakkuri ana son ya sake yabar anin don gaba.
Nace nagode anty tace may ye na godiya Rama yanzun dai ki tashi ki batun ba mijin ki abinci na bashi na safe saura ki na rana don bazan daukar maki ba.
Na juya ina dariya nace kai anty ki dai cika ladan ki mana tace dayake baki da tausayi ba.
Zama nayi falo muka dan yi shirmay mu da yara hiran game ne muka taba karshe nace kowa ya kawo min haddan da akai masu atare dasu muke biyawa.
Haka uwar tafito ta samay mu muna karatu tace Rama rana fa yayi kin san yau weekend ne da wuri may gidan zan shigo gida.
Nace yanzu zan tashi ta koma tana kallon mu yadda nake ma yaran gyara karatun boko ne bamu samu yi ba nace sai da yamma zamuyi shi.
Namike ina fadin oya Amira taso muje kitchen muyi girki shima Nasir ya mike yace little mum nima dani za, a nace mu tafi shima jinior ya biyo mu.
Abinci lafiyye na hada kamar ranan za, ai wani bako ne sai biyu muka kammala komai a gurguje naje nai sallah nai wanka na shirya cikin dogon rigar material mai ruwan dark blue da kore.
Dinkin shi mai dogon hannu ta hannuwa an mai stly ya baje haka kasan rigar ma free stly akai min.
Kamshi kawai ke tashi ban dade da fitowa ba sai ga daddy ya shigo nan aka shiga gaidashi kunya da nauyin shi nake ji na kasa dago ido na kalle shi.
Yace akai masu abincin shi saida ya fita da yan mintoci na mike nace oya azo muje mukaiwa daddy anbici yau weekend ne muyi hira da daddy suka mike cikin jin dadi mukarbar anty da Gajiye kawai.
Yana zaune da waya magana yake a hasale koda muka shigo ya dago idanuwan shi da suka nuna akwai bacin rai a cikin su ya sauke a kaina.
Simi simi na fara aje kayan tare da gyara wurin sai naga duk falin ya hargitse min kwana biyun da nayi.
Ban zauna ba na juya na dauko abin gyara na gyara komai tsab na har ya gama waya na dawo gurin su.
Hira yake da dariya sosai da shirmay da suke zuba mai kowa na fada mai abinda zaiyi idan ya girma.
Da Amira ya fara tace ita idan ta girma police zatayi ta tare hanya da bindiga nace kai Amir police kuma tace eh mum bakiga police din hanyan school ba na tsaya a hanya duk wanda yazo na harbe shi Nasir yace karya kike yi ko mummy nine sojan little mum na harbe kowa har da maman ihisan dake sa little mun kuka.
Cikin harshen turamci daddy yace you see what you people are course to my children they start hetting people with dis eges.
Sai yace kai Nasir soja ai ba halbi yake yadda yaga dama ba yace daddy ni dai soja zanyi bakaji little mum na kirana da sojan ta ba.
Nan ya shiga jero muna haukan wa yanda zai halba in ya zama soja sai dariya uban keyi yana tambayan shi may zai sa ya halbe su ?
Yana fada mai laifin da sukai mai yace Amira tace har da gajiye zamu halbe idan bamu tashi barci ba sai taita dukan mu ko in zata muna wankan safe tai ta zagin mu a bathroom.
Nasir cikin halin nan na shi yace eh da ita zan harba first ranan kin manta ta doke ni wai na balla buttle din uniform dina.
Banji dadi ba yadda suke maganan abinda gajiye ke masu haka shima uban sai naga ya lumshe idon shi.
Hindatu ce ta shigo falon ta samay mu cikin raha haka da yaran ta ce ashe ka shigo yace eh, tace tana son zuwa unguwa ne dama.
Wai ke hindatu shi fitan nan kullun sai anyi shi ne jiya kin fita fa yau kuma kice fita zakiyi kowa na gida da yaron shi yana weekend.
Bin yaran tayi da kallo tace eh ai na gani tunda ga yaran so an tara ma a gaba sai dariyan ka akeji tun a waje suko wa yanda ba, a so su mutu.
Ni bance ba in ma sun mutu kwanan su ne ya kare tace ana dai makirci a gidan nan wallahi.
Idona na dan rintse kamar na bata amsa sai na daure muryan daddy ne kecewa makircin may kuma akayi ?
Tace ai dai akwai Allah don ko wani dama haihuwan shi akayi baga dalilin ware wasu ba anan kana hira dasu.
Yace kin bari yar ki tana hurda da yan uwanta ne ko tazo ne aka kore ta nan din tace tazo nan yin may cikin ku ta gane may anzauna ana maka wani kilibibi haka.
Yace dakata ya isa haka na idan shi ya kawo ki kaman hanya ki fice min uguwa dai ne ba kuma yau ba ba mai fita gidan nan yau.
Eh da yake mune ba amma wa yanda ake so ai su ko yaushe fitan su sukeyi ko ba tambaya.
Yace bako a gidan nan ba yanzu duk macen da zata fita dole sai da izinina idan kuma mutum ya isa ya fita ga kofa a bude ai.
Ko bani gari kuma mace ta fita bada sanina ba nace ban yafe ba fakat abinda ba, a yafe ba ai yawa garesu gidan nan tunda wasu don milki da isa har dakin su ake binsy akwana can.
Yace na kwana ina dakin matana na kwana ba dakin farka ba dai ko gida nane ina da right din da zanyi abinda nake so.
Wata fi a gidan ita da kake kokarin fifitata haka yace ya ishe ki haka kifice min da fitinar ki da baki da aiki sai tsegumin tsiya kullum.
Tsegumi kan ai kowa nayin shi bani kadai ba in ma kayi ne don ka gyara ma ta rai saboda ita yar gwal ce tayi fushi to ka sani yadda ka kwana da ita dakin ta kowa ma sai ka kwana a dakin shi.
Yace to ki jirani nazo kwana dakin naki get out from here mara tunane kawai ke kullun da sabon fitinan da zaki bullowa mutane dashi.
Ba sai ka koreni ba ai fita zanyi dama ba zama nazo yi ba ra, ayina ne na fada ta juya tafice tana fada har ta bace yai tsuki ni kuma na sauke ajiyan zuciya inda nake.
Amira ne tace kai maman ihisan fada fada da duka ranan ma akan ihisan ta daki jinior wai ya ciji ihsan kuma fa daddy ihsan ce ta shanye mai swwet din da little mum ta ba mu.
Amira bana hanaki yawan surutu ba hakana tace tana kama bakin ta na bari little mum.
Yace ai ki barta ta fadi anyi ne tunda kikaji sun fada tayi ne don bata da kai, ko kadan.
Ina kwashw kayan da sukaci abinci sai ga Zulfa ta shigo tana ya mutsan fuska ta samu guri ta zauna saman kujera.
Tace zan tare da bin kowa da kallon sai ta sauke ajiyan zuciya tace dan fita ne nazo fada ma.
Yace ba fita yau ko ina yanzu hindatu tazo na fada mata hakan ita don haka ku barni in huta please.
Inda yaran suke suna wasannin su takai ido ta bi su da kallo cikin takaici ni dai ina daga bayan kujera na tsaya tare da dafa makarai yan kujeran ta baya daidai saitin daddy din.
Batai min magana ba nima ban mata magana ba ta dan yi jim kamar zatai magana sai kuma ta mike ta fice rai bace.
Na sauke ajiyan zuciya a hankali na ce a rai na gidan danger ke na wanan gida kowa da tashi kalar fitinan.
Mun dade tare da daddy da yaran da alama yaji dadin samun lokacin da ya danyi dasu.
Ina ganin uku da rabi nace dasu oya muje mubar daddy zaiyi sallah muma zamuyi sallah.
Suka fita da murnan su muka kwashe kaya zuwa cikin part din anty nakai kitchen idan na idar da sallah nazo na wanke su.
Bayan na idar da sallah ne na dan zauna da casbi a hannuna ina ja a hankali cikin lumshe idanuwa na daga inda nake zaune.
Tunanen rayuwan gidan ne ya tsaya min a rai na sosai nace wanan indan mutum bai yi da gaske ba sai ciwon tunane ma ya kama mutum.
Da dare sai ga kiran wayan daddy akan duk muzo mu falon shi yana neman mu.
Nice ta kusan karshen shiga don ina bayan anty tana gabana mun samu su saraki matan gida a zaune a kusa dashi.
Na kula haka sukeyi idan ya kiramu gaba dayan mu sai suyi saurin fitowa don kawai su zauna a kusa dashi.
Ni dai ina zuwa na zauna kasa a gefen kujeran da anty na take zaune a kan shi daidai saitin kafan ta.
Yana ta aiki a cikin system din shi bai kula kowa ba a cikin mu har tsawon wani dan lokaci.
Sai can ya dan sauke numfashi tare da dago kai yana kokarin rufe laptop din nashi a hankali tare da fadin yaiwa kun zo ko.
Ya fara da bissimillah yana cewa dama nace a kira ku ne don ni tafiya ya kamani zuwa Australia.
Don haka nake son naji wace keda tafiya a cikin ku dan ina ganin zanyi wata uku ko hudu ban dawo ba.
A take gurin yai tsit bakajin motsin komai sai na na,uran da suke aiki a lokacin.
Kowa tana sakan zuci sai anty ne tai magana farko tace badani ba cikin wanan tafiyan gaskiya.
Nidai ina zaune karatu ma nake a cikin wayana ba sauraren su sosai na keyi ba.
Daddy yace nasani amma dole ne abaki hakkin ki akai ai.
Sai shiru ya biyo baya can dayaji shirun yai yawa yace ku nake saurare fa.
A lokaci daya suka hada baki gurin cewa dani zaka, sai yace to ban fahince ku ba dai ?
Wanan tace da ita wanan tace da ita yana jin su ya lumshe idanuwan shi sai da suka ishe shi yace a tsawace stop .
Kada kuyi min hauka anan ba shi na kira ku ba don Allah duk baku da tunane da adalcin gava dayan ku dakuke wanan haukan haka ?
Inda ku masu adalcine da sanin ya kamata bazakuce naje daku ba sai dai kuce na dauki Rahama mu tafi da ita.
Nima ba don uzuri ba babu wani tambaya da zan tsaya yi don nasan ita ya dace naje da ita din yanzu.
Hindatu tace tunda tafi mu ko may ko kuma mu bamu da hakkin zuwa ne daba za, a damu ba?
Zulfa tace nasan hakane ya kamata amma sai tun farko banji ka fadi hakan ba shiyasa nai shiru.
Yace naso zuwa da Rahama sai dai karatun da take yi bai son wasa acikin sa wanan uzirin ne yasa ba batun zuwa wani guri da ita a yanzu.
Amma ku sani nan gaba inda halin hakan za, a maimaita tafiyan idan hakan ya taso.
Don haka daga cikin ku ina son naji wacce za, a tafi da ita din ?
Sai kuma gardama ya kaure masu basu ko tsaya batun jinda sukayi yace nan gaba za, a maimaita tafiyan dani ba.
Nice na dago kai ina cewa amma sai naga kamar tafiya da anty Zulfa zaifi don taje ta samu kara ganin likita a can don lalurar ta.
Ke muna fuka waya saka bakin ki yar bakin ciki ni zakiwa bakin ciki ko bukulu ?
Ta na gargade ki da kiyi gagawan fitar da bakin ki cikin maganan nan don babu sa,ar ki anan kaji min yarinya karama da iskanci.
Nace wallahi yarinya na bayar uwarta daga fadin gaskiya sai ki dinga fadar magana wa mutum kamar kin haifi mutum ?
Magana ce ta gaskiya ake so shina fada amma idan nayi laifi kiyi hakkuri don Allah ?
Kaji kilibabba ki gama nuna min kiyayya yanzu a filin Allah kuma ki dawo kina wani yin hakkuri.
Ni dama can nasan babu mai kaunata a cikin ku da kike cewa aje da Zulfa may Zulfa ta fini da za,a da ita ko kuma may zata je ta tsinana mai a can.
Muryan shi ce yace Zulfa dama nima tunane akanki yake sai ki shirya mu tafi aje a duba lafiyan ki dana baby a can.
Shi ke nan kuna iya tafiya har anty na batun mikewa yace na tuna dakata sai ta koma ta zauna kawai bata dai yi magana ba ita.
Yace Rahama shiga ki dauko min briefcase dina a ciki wana ashh colour din, zaki dauki min nace to tare da mikewa zuwa daukowa.
Bayan na dauko ne na mika mai cikin girmawa ya bude tare da kirga kudi ya ce zo karbi ki mikawa antyn ki wanan tare da ci gaba da kirga wani.
Ina mika mata na samu wuri na zauna ya kirgo ya mikowa Zulfa nata dake kusa da ita sai hindatu.
Nice ya kirgo yaba a karshe ina karba hindatu na fadin kamar daidai ka bamu da ita nake gani ?
Yace ita wa wai tace wanan yarinyar da bata da kowa a tare da ita muko ga yara ga yan aiki da sauranvsu.
Yace eh daidai na baku ma ita ba mamata bace ko may ?
Tamike tsaye a fusace tana fadi kai kai ana dai rashin adalci kan agidan nan yanzu wacce bata da kowa za, a bawa komai daidai damu ?
Yace ashe da nake baki daidai da sauran abaya hainci nakeyi ke nan tun wanan lokacin ko yanzu ne rashin adalcin ya soma akan ita Rahaman.
To shi naga zan bayar kudin ki ko nawa ko wani abin kikafita dashi ke naga baki son azauna lafiya wallahi duk kika kara cewa tak a gurin nan sai ranki ya baci yace ku tashi ku tafi nagama daku ke nan.
Gaba daya muka mike zamu bar falon yace ke Rahama zo ki mayar min da wanan jakkar daki.
Na juyo na koma na dauka na mayar daki inda na dauko da farko na fito na zo zan wuce yace dani idan kin shiga turo min anty ki.
Kwana uku suka shirya suka tafi bayan mun sha nasiha mai kama da gargadi a gare shi kan fitina da kuma fita ba bisa kaida ba.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA

Please Login or Register in order to submit comment