Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wanan harkan.
Duk wacce tace zata zauna wallahi ba zugi ba zata koga ba daidai ga maigida.
Balle ke dake da kishiyoyi har uku ina zama ya ganki ai ance in kana da kyau kara da wanka.
Nan dai ta shiga yi min wa,azi da nasiha kan zama da miji har ma da kishiya kan kada na yarda nai aikin da baidace ba ga rayuwa na.
Naji dadin nasihanta don na hango akwai addini sosai tare da ita don sai wanda yasan Allah zai maka wanan nasihan haka.
Tace insha Allahu zan taimaka maki da abinda ya dace wanda ba zaki nakasa ba a gurin mijin ki ki daina tsoron cika bakin kishiya tanayi ne kawai don ta razana ki.
Tace dani ke, ke bashi ruwa yasha ko shi ke sha da kan shi ma,ana ya dauko nace ni ke dauko mai tace ya kwana gidan sauki ai.
Ruwan nan sai ki bude ki juye a cup sai ki karanta bissimillahi kafa dari uku da goma sha uku ciki ki dinga bashi ya sha ko kuma dari bakwai da tamanin da daya kina bashi yana sha har tsawon sau bakwai.
Zaki iya kuma tofa Allahu ya wadudu a ruwa kafa arba,in daya har sau uku ki bashi yasha a ruwan da kika tofe din.
Zaki samu kwalli wanan fari mai dutse ki nika shi ya zama gari sai ki tofa mai (wara fa, anahu man kanan aliyan ) kafa arbain da daya, dinga shafawa a ido duk lokacin da namijin ki ya kalle ki zai ga kin kara mai kyau da sha,awa gare ki.
Zaki samu ruwa na kanzon tuwo sai ki barshi ya kwana a wuri mai kyau amma a fili sai da safe ki dauko shi ki zauna zama irin na bauta ki karanta la,illah ha, illah kafa uku sai li, ilafi quraish kafa uku a cikin sai rabbi ziddini ki fadi sunan mijin ki sau uku ki shanye.
Yana kawo daukaka da farin jini a gurin namiji sosai ba kadan ba a gwada yana da alfanu mata.
Tace wanan ke nan sai kuma wanda yanzu zan baki na amfanin ki kuma.
Kin san kina da kama da kaunata sai naji kawai ina son ki har cikin raina ganin ki nake kamar autar mu wallahi.
Ta jawo wani roba tafito da wani sabulu tace kinga wanan sabulun yana da hadi a cikin shi sai ki samu sabulun wankan ki ki hada dashi ki kwaba kina wanka dashi ko yaushe akwai lalle da majigi da habba da hulba duk a cikin hadin sai abin mallaka da akai amfani dashi ciki.
Ta kara miko min wani turare mai kamshi tace karbi wanan turaren na motsa sha, awa ne shi kafin ki je gun maigida ki tabbatar kin motsutsuke jikin shi dashi sai ki kawo wanda kike amfani dashi ki dora sama don ya kawar da kamshin wanan din kada a gane mudai mukatan mu ko kadan ne ya shaka kawai.
Wanan kuma hayaki ne zaki dinga tsugono an hada shi ne ta igiyar akalar rakumi a cikin sa.
Na dago kai na kalle ta tace kaunata ke nan idan ke baki jashi ba kina kallo sai wata ta jaye maki shi ai.
Wanan abin ba tsafi a ciki bokan ki ne a dakin ki don sai dashi aure yanzu muddin kina son tsufa a dakin ki to sai kin hada da hakan ko.
Kinji ance ki nemi lahiran ki tun aduniya da kuma so da kauna a gurin mijin ki to sune nan babu boka babu malam sai ayoyin da akai fani dasu a gurin hadin.
Tabani gumba tsumi da sauran abubuwa har da wanda zanyi kumshi koda a yatsan hannuwa nane .
Tace naje na gwada su kawai sai wani lokaci idan mun hadu zata bani wani tare da jadda mi cewa ayau fa mace bata kamaluwa idan babu kwaskwarima gare ta don mazan sai da haka ake zaman lafiya.
Keda kada kiyi wanda zaki kaucewa imanin ki ki cutar da miji da kishi amma indon wanda zaki gyara kanki ne malaimai sunce kiyi .
A sanye na sauke ajiyan zuciya na dago kai tare da duban ta nace hajiya nawa zan bada ?
Tace cikin murmushi gaskiya kinci albarkacin yar uwata don gashi na baki harda abinda ban taba ba Zarah irin su ba.
Zarah tace ai mamaki kawai nakeyi wallahi ina jira kigama ne naciki tara.
Tace wanan autar muce ai kin san dole kuma na gyara autar mama ko kada kishiya ta koro muna ita.
Gaskiya ne hajiya inji Zarah .
Na sake cewa na gode hajiya nawa zan bada ?
Tace a gaskiya ita zarah ta san kayana takuma san amfanin su da wata ce Allah sai dubu hamsim zuwa sama zaki bada.
Amma yanzu kibani yadda zaki iya ai yanzu muka fara dake sai nan gaba zan baki har wanda zakiyi nafila dashi.
Nace to haji in na bada ashirin ban so kaina ba da yawa tace babu damuwa kawo goma kawai kaunata ko zan samu ladan zumuci a kan ki don autar mu na baki hakan.
Nai mata godiya mukai mata sallah kan duk yadda naji zamu dawo insha Allahu.
Bayan mun bar gidan ne muka dawo gidan zarah ita tabani abubuwan hadi wasu ma ta hada min na wuce dasu gida nai mata godiya.
Ban shiga dakin anty ba sai da nakai kayan part dina na boye nai wanka sannnan na dawo gaida anty.
Tun daren ranan na fara amfani da wasu daga cikin kayan da ta bani don su girdu a jikina kafin mai gidan ya dawo.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , , ,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI HAKKIN HA,INCI GAREKI, , ,
48

Sannu a hankali nake aiwatar da komai da hajiya mai gyaran harka ta bani.
Sam ban bari kowa a gidan ya fahinci abinda nake yi ba sai na fakaici idon mutane nake yin yadda ta fada min so nake na fahinci gaskiyan al,amarin.
Haka yasa na dage gurin gwada amfanin su ko hakan zai yi wani fa,ida.
Ita ko Hindatu nacan ba zama ba tsayi ta fada nan ta fada can bata gurin bokaye gurin malamai da masu kayan mata.
Burin ta daya shine ta samu kan maigidan ya kasance bai ganin ko wace mace da kima da daraja sai ita.
Gashi duk inda ta tafi sunan Rahama ne dai a bakinta ita dai ai mata aikin da zai dakushe haske Rahama ga mijin su a baki daya takoma ita da babu ita agidan duk daya.
Kudin ka yasha kashi sosai ita kuma tasha kayan kulli da wanka har da shafawa.
Duk ta yo kayan su ira ta tafi hanne yar aikin ta ta tafi mata uwarta taje mata yan uwanta suje mata haka ma aminan ta suje mata duj kan dai abu daya takeyi.
Sai da ta tabbatar ta hadu akan komai yadda take bukata ta sawa kanta sauki da hakkuri hakana.
Jira kawai take maigida ya dawo ta fara aiwatar da nufinta akan shi kamar yadda nima nake jiran ya dawo na gwada kayan mai kayan harka akan shi.
Bani wasa da tashi cikin dare nayi nafila na roki Allah ya kare ni da duk wani sheri da kulli akan duk wacce ta bini da mugun nufi Allah ya mayar mata da aniyan ta akanta.
Sai na gamsu da addua na nakan dan koma na kwanta kafin ai sallah asuba na tashi kuma na kara tilawa.
A bangaren hindatu nasha binne binne da yayafin rubutu a duk inda zan taka.
Allah ya rufa min asiri bana fita daga part dina ko wajen gida sai nayi addua a bakina na neman tsari daga gurin ubangiji na Allah.
Na kuma gode don Allah yai min dauki akan hindu da sherin ta don kar nake kallon ta.
Inda na san akwai magana kaina cikin dare ina part din anty a zaune hira muke a kan Abban ta muna dariya Gajiye bata riga ta rufe kofan baya ba don tana son fita ta kwaso wasu kaya da ta bari a baya .
Haka yaba hanne yar aikin hindatu dama samun shigowa don ta yayafa abinda wani malami ya basu su zuba min a kofa na.
Gajiye na fita ta hango kamar innuwar mutum a gurin yana zuba wani abu da karfi tace waye waye a gurin nan ne ?
Da sauri Hanne ta juya tabar gurin jikin ta na ciri taa gudu zuwa part din su Gajiye tabi bayan ta amma ta saurin shigewa babu kowa a gurin.
Jin ihun ta yasa muka mike muka nufo gurin tace da karfi kada kuzo nan hajiya akwai matsala wallahi.
Cak mukaja muka tsaya tace bari ta haska wuta a gani ta kunna wutan ta Hanne ta kashe mai haska dogon coridor din.
Wani ruwan rubutu ne ko tsimay oho, da wasu bakaken abu a cikin sa.
Gabana ya fadi ras anty tace na shiga uku gajiye waye ya zuba wanan abin anan ta fada muna abinda ya faru.
Anty tace yanzu wake da aikin nan haka Allah ya mayar wa mai shi da aniyar shi don Allah yafi shi.
Gajiye tace ina zuwa ta wuce zuwa baya sai gata da wani abu a wani tsohon roba ta zuba a gurin.
May ye wanan din kike zubawa Gajiye tace hajiya fitsari ne kin san yana kashe dafi da asiri shi.
Bayan ta zuba tasa abin shara ta share tafita dashi takawo moper ta goge gurin tsab gabana sai faduwa yake min.
Anty tace mu koma daga ciki ranan a dakin anty na kwana duk jikin mu yai sanyi sosai kan wanan abin.
Gajiye ke cewa Hanne nake zargi wallahi don babu tantama itace nagani ba wani ba.
Yanzu ai zato muke idan baka iya kama barawo ba sai shi ya kama ka.
Gajiye tace ranan fa da safe koda na fito naga kofan falon mu kamar an tona muna shi sai aka kawo ruwa aka zuba ko ina mutum bai gane komai.
Anty tace shine baki fadi ba Gajiye tace hajiya may fadin zai yi amfani na dai zuba bowli a gurin ma ranan don ban yarda da hakan ba.
To Allah ya kyauta mukace amin baki dayan mu haka yasa na kara kula da kaina sosai nasan da akwai sherin da ake kokarin kulla min.
Haka yasa na kira inna ta na fada mata halin da nake ciki itama hankalinta ya tashi.
Tace zata fadawa maigari halin da ake ciki takuma je ta fadawa Attu ta koma gurin malam Musa ta fada mai.
Yake cewa ta fada min na kwantar da hankalina ba dai ina yin adduoin da ya bani ba da zanzo kuma abinda yai min insha Allahu wani asiri bazaiyi tasiri ba akaina Allah zai kare ni insha Allahu.
Sai da nai kwana uku ban shiga part dina ba ina tsoro itama anty tsoron hakan take ji.
Sai dai takan min sheri muyi ta dariya ga kwana na hudu nagama addua na na fara shiga naji kuma hankalina yai matukar kwantawa sosai.
Kwana biyae sai ga Fatima yar gurin maigari an turo ta guri na da abubuwa daga shi maigari din ya turo min.
Na dawo school na samay ta tazo da murna na tare ta mun dan zauna part din anty muka kwasa muka koma guri na.
Sai da dare muna shirin kwanciya bayan mun rufe part din ne ta fitar da sakon tai min bayanin su dalla dalla.
Banyi sanyi a kafa ba na fara amfani dasu kamae yarda yace min duk na tsari ne kayan.
Naji dadin zuwa Fatima a gurina muna zama muyi hira bata da son jiki kafin na fito ta gyara min part har na anty takan gyara udan aiki yaiwa gajiye yawa.
Anty takan ce wai haka yan garin ku suke ne da saukin kai Rama duk wanda ka gani sai kaga yana da mutunci ji yarinyar nan kamar ba yar kishiyar inna ba komai tsakani da Allah takeyin shi.
Nace daga tarbiya ne anty amma ai akwai marasa mutuncin bamu dai hadu dasu bane kawai.

********* ********* *********
Daddy ya bugo waya next week zasu dawo insha Allahu haka ya kawo ba zama kowa na kokatin gurin gyara a lokacin.
Duk wani abinda hajiya mai gyaran harka tabani banyi wasa dashi ba na maida hankali a gurin yin sa.
Na kwashi yara saura kwana daya ya dawo mukaje gurin gyaran jiki mazan akai masu aski ni da Amira da fatima kuma aka wanke muna kai mukai kitso mai kyau don muna hutu a lokacin.
Sai da muka dawo ne anty taga abinda mukayi don tana barci muka fita gidan bata ma sani ba.
Ga kayan dana sayo masu na taron daddy taji dadin hakan soai da yama na shigo dakin da tsinken kitso da cumb nace ta zauna na gyara mata kan ta.
Don ni bayan kitso an gyara min jiki an min kumshi na sa lallen da mai gyaran harka taban a yatsuna.
Nai matukar kyau sosai har yaran ma anty tace dani kai Rama ni ina zan tsaya yin wani kitso kuma nace haba dai Anty don Allah dai ki bari ko shidda na kwashe maki .
Bataki ba da fada da komai nai mata kitso mai kyau haka yasa fuskanta ya fito da kyau bakin ta yana sheki sosai.
Na zauna kafin magariba na gyara mata yatsun kafan ta da sauran abubuwa tace dani Allah dai yai maki albarka har najini kamar bani ba wallahi ko.
Washe gari munyi aiki sosai irin gyaran part din daddy da girki itama hindatu tayi nata gyaran har girki ta shirya mai bayan mu ya bugo waya ai mai tuwo.
Da yamma suka iso garin take gida ya rude da jin dadin dawowan su lokacin.
Ina part dina da fatima Nasir yazo ya fada min dawowan shi sai da muka dan dauki lokaci na kwashi yaran da muka aha kwalliya mukaje taron shi.
Yana zaune a falon shi shida Bashir muka shigo gaba daya kallon shi ya dawo kan mu har sai da bashir din ya juya yaga may yake kallo haka ne.
Mun karaso muna mashi sannu da zuwa nakuma gaida bashir din suma yaran haka sun gaida abokin baban nasu.
Ina fadin akawo abinci ne sai ga hindatu tashigo dauke da kayan abinci tana ganin mu fara, ar fuskanta ya dauke.
Ta samu guri ta aje abincin tana fadin ga abinci kaci kai wanka ko zakaji dadin jikin ka .
Ina jin haka na mike ina cewa a huta gajiya daddy zamu mu gaida Anty Zulfa itama.
Yace ku kawo min tuwon ko ba ai min bane nace anyi maka daddy yace kawo min tun bashir bai tafi ba muci.
Tace wanan fa dana shirya ma ko may kake nufi da akawo ma wani kuma yaya zanyi da wanan din kuma ?
Yace ai bance ai min ba wanan ra, ayinkine hakan tuwo nace Saade tai min ai.
Yaya za, ayi wanda zaiyi girki daban may kawo tuwo davan kuma ?
Yace bisimillahi hindatu zaki fara kuma ko da dawon mutum bai huta ba zaki saka min bacin rai kuma ?
Tace may ye na bacin rai a nan tunda nice zan yi girki daka tafi ai dakin Saaden ka kwana ko ?
Yace idan hakane kwana nawa nai a gurin ta, ke banson fitina yadda nake so haka za, ayi kinji na fada maki gaskiya.
Wallahi wanan bai yuyuwa haka kawai kan wata can in bari ka danns min hakkina yace indai wanan shine danne hakki tona danne din .
Hakana tsara kuma hakan zanyi ke duk yadda akayi dake ba, a daidaine wai bafa gurin Rahama nace zan sauka ba balle kice zaki min fitina haka.
May ye banbancin Rahama da Saade karshe ma ai munafunci za, ayi ace wai ita Saaden ta yafewa wanan din girkin tunda kun riga da kun shirya.
Ke hindatu kin isheni wallahi ban son rashin hankali wallahi ko addini yabani daman zaben inda zan sauka amma nai haka don a zauna lafiya dai.
Muna fita part din Zulfa muka nufa nida yaran mun samay ta tare da maman ta da yarta a dakinta sun baza kaya sai yan dararakun su sukeyi.
Muka shiga da sallama suka amsa muna sun daure fuskan su a lokaci daya.
Muka gaida ita tare da mata sannu da zuwa ta amsa muna bamu tsaya ba muka fice abin mu.
Tun bamu karasa fitaba naji yarta na fadin kai Zulfa haka yarinyar nan ta koma ashe ?
Tace wallahi nima haka na gani, yar tace jita kamar ma itace tai tafiyan da miji ba ke ba wallahi.
Uwar tace Zulfa koma may ye yarinyar nan ki mata uzuri please tana dai dan kokarinta a kanki.
Yanzu fa ba wanda yazo gaida ke sai ita da yaran kin ga koma may ye ai dai tayi ko da kuwa na munafuncin kishiyace.
Tace gashi itace silar tafiyan ma gaba daya koba komai ki samu abinda kika bata ko ba mai yawa bane inji uwar tace aramawa kura aniyar ta.
Yar tace yaran fa tace ai dole ne inba haka ba tsiya zai shuka min ban ba yara shi komai ba kin san shi bai hada komai da yaran shi ba ai.
Mun koma gun anty tana kallon mu cikin sha, awa tace har kun dawo ko na zauna ina cewa ai har gurin anty Zulfa muke muka gaida ita.
Lalai Rama akwaiki da kalula wallahi ki dai yi a hankali wa yan nan da kike gani basu da tabas wallahi.
Nace ni don yaran kawai naje gaida ita don su saba da hakan don shi yaro ba ruwan shi ki san race nagane hakan ?
Kin yi hikima Rama na fahinci nufinki don yaro ba, a sashi ga zancen kishi yin hakan haukane da batan kai baka san may rike ma yaron ka ba wata rana in babu mutuwa akwai rabuwa mata mu kula don Allah da wanan kishiya bata iya yiwa dan ka komai sai in Allah ya nufa.
Ba,ace ta ka zure ba amma yadda Rahama ta shiga dasu sha tafito shima wani dan hikima na ne na gyaran zaman gida hakan.
Tace kin zauna abinci fa nace may girki takai mashi abinci ko anty shiyasa banyi batun kaiwa ba.
Tace to wata sabuwa ana dai drama a gidan nan wallahi kafin nai magana sai wayan daddy ya shigo mata yana cewa nace wa Rahama ta kawo min abinci mana naji shiru.
Tace dani kinji kuma wai akai may abincin nace dama nasan rigima zasu yi shiyasa muka basu guri ba dadi kullun yara suna ganin irin wanan fitinan haka.
Tace tashi muje da abinci muji may ke faruwa namike na dauko basket din da muka shirya kayan na fara fita dasu anty ma tabini da sauran drinks din da na riga na tofe su da ayan Allah ciki muka kai mai.
Muna shiga tana fitowa a fusace daga falon dagani anyi ba dadi a falon lokaci tace damu muna fukan banza kawai wallahi sai kun gane kun shiga hurumi a gidan nan.
Nikan na jera masu kayan abincin Bashir na ma anty sheri wai uwargida sarautar mata ke saade wai may ye sirin wanan abin ne haka ?
Tace Allah !
Ya ce naga gaskiya ai kan Allah ya barki da besty ki daga inda nake duke nace Amin.
Ina gamawa na mike na bar falon yabini da kallon sha, awa kai mutumin yaya haka kuma wai inji bashir ?
Tace kasan amarya ce fa gata yar shila banga laifin shi ba ai wata nawa rabon shi da ita haka ?
Bashir yace ikon Allah waike saade wata irin mace ce baki ko jin darr a ranki kan yarinyar nan haka wai ?
Tace na fada ma ai Allah ko baka gane ba har yanzu ne abin daga Allah ne fa.
Yanzu dai zuba muna abinci muci na baku guri ni dama an kwadaita min ne na tsaya ci kawai.
Yace a, a barta na zuba muna kada tace kuma bayan ta zai karye yanzu lalaba abina nake don nasan halin kayana sarai.
Shi ya mike ya bude sai kamshi ya daki hancin su yace no warder ka kore kayan shimkafa da miya don nasan shine dai abincin nasu.
Sunci sosai suna hira su uku sai da suka gama ne Bashir yai masu sallama ya tafi anty bata fito ba sai washe gari da safe ni na kwana da yaran a gurina ranan.
Washegari ma nina hads breakfast na hada komai nakai masu saida ta karya tafito ta samay mu zaune ina shirya yaran zasu islamiya don ba boko lokacin.
Nan muka shiga gaida ita ta amsa muna cikin fara,anta nake cewa da ita yanzu nake son wai da na hada maku fruits salad nakai maku gashi kuma kin fito.
Tace kai barshi kawai Rama ki huta kawai sai anjima ni zan ma kwanta ne yanzu bana jin dadi wallahi.
Subbahanallahi may kuma anty ko a dauko maganin ki ki fara sha kafin ki kwata ko ?
Tace kai Rama mutum na shan magani kulun abu jiya wa yau ni na barwa Allah sani ko ma may nene hakan nagaji wallahi Rama.
Mikewa nayi na shiga na hado mata magani tare da ruwa na kawo mata tasha sai dan wani lokaci takoma daki ta kwanta.
A raina nace wai kuwa anya ba jifa ne je damun wanan boyar Allah ba haka mace ba dama ta dan sake da mijin ta sai ciwo ya taso mata haka ?
Tunda ts shiga har muka gama abincin rana bata fito ba haka na daure nakai mata yana gida tare da yan uwan shi na samay shi a falon tun auren na da daddy sau yau naga Ibrahim.
Koda na shiga suna yan dararakun su yana ganina yasha toka na gaidasu na aje abincin ban tsaya ba don ba hijjab ko gyale a jikina a lokacin.
Tun shigowana naga kallon da daddy ya watso min nasha jinin jikina har nakai kofa mubarak ke cewa dani ina Saade ta shige ne baiganta ba tunda ya shigo gidan.
Nace ayya tana kwance bata jin dadin jikin ta ne shiyasa baka ganta ba ai duk suka ce Allah ya bata lafiya a gayar da ita.
Sai bayan la, asar lis daddy ya shigo part din namu inda ya samu dagani sai gajiye da fatima a lokacin mai part din na ciki ta tashi har na shafawa kafanta da tace yai mata nauyi magani.
Nafito daga kitchen ina saye da wando tie da purple da dan riga mai karani ya matukar matse min jikina komai na suran jikina a baiyyane yake din kayan sun matukar daukan jikina sosai.
Sai nai kicibis dashi ya shigo falon bai damu da wai Gajiye na nan ba ko fatima da

Please Login or Register in order to submit comment