Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ashe dama kin tura yar kice don taje tai CID a can to kinji abinda ranki ya baci duk irin kokarin da akaiwa yaran ki amma baki gode ba yace ni na riga na aje zancen ki ko wallahi ba yau ba tunda baki da tunane.
Ya kuma samu Amira da Ihisan yai masu tas yace masu munafukai ai sunyiwa kan su don ba zasu kara zuwa ko ina ba.
Yaran sunyi kuka sosai sun kuma yi da sun sani da basu fadawa iyayyen nasu komai ba da suka gani acan Amira harda karya ta hada wuriin fadin zancen ta.

********* ********* *********
An bugo min cewa mahaifina baida lafiya hakan ne yasa na shirya zuwa gida don a yadda aka bugo min ma sai nake ganin kamar baida raine.
Tare da daddy muka tafi lokacin cikina yana da wata hudu a jikina amma ba a ganewa don in ba kayan aiki ke a jikina ba to kuwa baka rabani da hijjabi ajiki na.
Da dare muka sauka ban shiga wurin kowa ba tunda ni da nai tafiya ba wance tazo taro na sai duk suka share ni kamar ba zuwa nayi ba.
Sai washe gari da safe har mun shirya zuwa kauyen mu naga ba zan iiya share anty ba hakana ko banza nice kasa gareta ai.
Na shiga wurin ta mu gaisa tunda nai sallama tana karyawa ta dago kai muka hada ido gabanta yai wanii irin mugun faduwa don gaba daya na sake mata na canza kamar ba Raman da taa saani ba nata a baya.
Komai nawa ya koma na wayyayin mata ba sakin fuska nima a idona na gaida ita ta amsa min a gadarance.
Nai mata yaya gida cikin rashin damu yarona yana tafiya yana saye da dogon wando da riga mai dogon hannu da takalman shi masu tsada sai kamshi yakeyi gashi fari kwal dashi sai gashin kanshi mai zubin na fulani.
Ina rike da hannun shi ban sake shi ba don kada yai mata wani abin kuma nace zan shiga gida don baba ne baida lafiya mukazo.
Allah ya sauwa tace dani muka fice tabini da kallon harara takke ta dauko wayan ta ta buga wa yar uwar cin mushen ta tace wai Rahana kin koga abinda nagani kuwa ?
Nan dai take bata labari tace wallahi ki matse mata kada ki bata kafa kikuma fada mata ta tuna da asalin ta kada ta manta daa bazanki take rawa har yanzu.
Falon daddy na shiga iinda tun kan na karasa kamshina ya sanar dana ciki ina tafe falon suna ciki da matan shi duk su biyun a lokacin sai dai kamar magana sukeyi dashi.
Baba na ganin mahaifin shi ya fisge a hannuna ya nufi wurin shi ya dane jikin uban yana fadin daddy cikin gwalancin yara take uban ya gane mai yake nufi.
Nai masu sallama tare da gaishe suy ban damu da ko su karba min ba sai dai alama ya nuna sunyi mutuwar zaune a wurin.
Na juya nace cikin dan hausan na daya koma na yan Abuja yanzu daddy mun shirya muna son mu tafi ke nan.
Yace a, a Rahama ina tare zamu tafi ki dan bani minti biyar na fito please don ina son in shiga na dduba shi kinn san damun koma ni tafiya zanyi nace ok sai ka fito ina waje.
Har na juya naji hindatu tace da daya layan wuya inda an haihu da yawa aiko mijin bamu gani ma saui dai labari a haka dai za, a dawama da da daya kamar laya.
Kamar na wuce sai na juyo nace nagode maa Allah Allah yasa mashi albarka amma kila gado nayi na haihuwan da dasyan yadda naga wasu sunyi.
Ke wallahi kama kan ki kada kiga an rike maki maciji kina wasa da bindin shi bakifi kowa ba don kkowa ma yasan hanyan bin miji idann ya tashi ba sai an hada da yaudara ba da cin amana.
Bin miji ai isane duuk waccee ta shirya tazo mu tafi don ni nayi gaba , a, a Rahama kudai tsaya kuyi abinku amma kada ki sani a ciki.
Nace Anty Zulfa da wanda yai magana ai nakeyi ba dake ba daga haka nafice abina na barta nan tana kumfar baki a falon.
Bai dade ba sai gashi ya fito muka dauki hanya shi ke jan mu nii dashi ne a gaba yaran suna baya.
Sai da muka kusa fita garin kano naji yace watau ku mata halinku daya wurin hauka keda kikazo duba mara lafiya ina ke ina tsayawa hauka haka.
Nace cikin bacin rai daddy abin matan nan ya isheni ne wallahi mace haka da bakin son fita ko yaushe daga zuwa na jiya jiya zata hauni da balai wallahi a shirye nake da kowan su don nagaji da hakkuri hakana.
Bai kara magana ba muka dauki hanyar kaauyen mu a can ya barmu zamuyi kwana biyu mu dawo mu wuce mun samu jikin baba din yayi sauki sosai.
Yai masu goma na arziki yai muna sallama ya dawo ya barmu a can zamu ga yan uwa kowa sai fadin canzawan mu yakeyi.
Nai mamaki kwarai yadda innata ta fahinci ina da ciki ajikina haka da sauri abinda kowa bai gane ba sai ita don sai najii tace dani.
Amma tun kan ki yaye yaton nan kika samu ciki ko gabana ya fadi nadago klai nace hakanane inna tace Allah ya inganta ya rabaku lafiya nace amin.
Wanan katon na kwana a giidan mun mun sha hira da mahaifina kamar bashi ba munci mun sha daga nauin abincin kauye da muka dade bamu samu ba.
Amarya baba ta haihu sai haba haba take dani ta rasa inda zata sani ranan don daukaka da na samu ta haihu tana goyon diya mace itama.
A yadda na fahinta ciwon sugar ne ya kama mahaifina sai dai ban tabbatar ba na dai ce idan na koma sai su shigo asibitin mu a auna ashi a gani.
Bai so zuwaa amma da kyat na samu ya amince da zaizo naa saya mai kayan abinci na masu sugar nace ya fara ci mu ganii.
Kwanaan mu biyu hamza yazo ya dauke mu mun sha gata sosai a gida muka dawo kano da yamma na samu gida ya rikice don matan daddy sunce sai suma yaje dasu Abuja din don basu yarda ba case din daa na samu anayi ke nan don tun a mota Hamza ya fara kyankyasa min labarin halin da ake ciki.
Yace daddy ya haukace masu donn yace idan sukai tsiya ko kin gama ma bazaki dawo ba a raina nace dama hakan ne ai don nasan da wuya asibintin da nake su sake ni.
Ban bi ta kan kowa ba na shige part dina da mutane na gajiye tanata faman dawainiya damu cikin rashin gajiya don harda helen mukazo garin.
Sai washe gari da rana na shirya tsab zan tafi na gaida iyayyen mijina da yan uwan shi, kafinn in fita na leka anty a part din ta mun gaisa ta tambayi mai jiki nace ya samu sauki.
Nace zan tafi na leko su Hajiya har furin Abba zan shiga don kada taji naje yazama min matsala kuma a tsakanin mu duk da yanzu ban gudun shi idona ya bude ko.
Na juya nakai kofa tace dani Rahama sai na dakata don jin yadda ta kirani sunan da ya dade banji shi a bakin ta ba haka yasa na fahinci tana da magana mai girma ke nan.
Najuyo ina fuskantar ta batare dana koma na zauna ba tace ke yanzu kina ganin wanan cin amanan da kuka dauko yi muna keda maigidan shinee daidai komay ?
Bafa ke kadai bace matar shi yaran nan da suka dawo sun fada min duk abinda kike a can ban yarda ba sosai sai yanzu da idona ya gane min nagani.
Nace ashe dama ba hutun arziki su kaje min ba leken asiri ne yakaisu ke nan ?
Tace aiko sunyi bai baci ba don dukiyan uban su ne suke ci bana wani ba kuma don ke baki da hasara da daya ke gareki a gidaan shi yasa kiika sa uban su gaba da wawaso ko ?
Murmushi nayi nace dayan ma na gode da Allah yabani nima na kada nawa a cikin naku kinga suyi zumunci da yan uwan shi don nabar tarihi nima.
Au lallai naga kuwa kije abuja kada ki manta cewa duk abinda kike takama yanzu dashi nice dai din nan silar shi.
Nace ban taba manta halarci ba komai kankantar shi damani shiya nake shanye duk wani dacin da kike zuba min don ni ba butulu bace.
Yaushe kuma?
Butulci yafi wanan da kike min kuma ai ya baci nai maki rana kin min dare kina son rabani da miji ki kuma rabashi da diyan shi.
Nace cikin girgiza kai Anty tare na ganku har diyan ku don haka ni Rahama ban taba tunanen wanan kalman ba a raina don ni ba azzaluma bace kuma nasan ya kamata ako ina.
Wuyan ki ya isa yanka komai yanzu zaki iya fada min ai don kina ganin kin kai, ddon kina takama miji yana a hannun ki.
Nace cikin dan murmushi kamar maganan bai zafe ni ba babu inda nake don har gobe a karkashin ki nake.
Don nabu abinda nake maki a baya wanda na fasa yin shi ayanzu, na fannin biyayya sai wanda naga baki ra, ayin shi nake dainawa don haka girman ki da kimarki yana zaune daram a zuciya na ko yaushe.
Miji kuma ni a suwa da ya zama nawa in samu mutm da iyalin shi ince zan shige gaban su ni har yaushe na shigo cikin ku ne ma ?
Tace Zamu zuba tunda abinda kika zaba ke nan nace mu zuba alherin nan da kika saba yi min ina maki Allah ya kare mu daga sherin shedan.
Ban tsaya sauraren ta ba na juya na fara tafiya sai naji tace takamar ki dai da dayan da kika jefa a cikin mu shine kadaran ki waike kin haifi namiji ko ?
Akara haihuwan mu gani iin haihuwan ya zama banza ke nan a gidan kowa ta kwaso sharan ta tace sai anan zata juye shi a cika muna gida da diya barkatai.
Maganan yaci min rai sai kuma na tuna da abindake ciki na a yanzu wanda kowa bai san dashi ba sai ni da Zarah da ubangijin mu kawai.
Nai murmushi nakai hannuna ga cikina take ko naji cikin ya wani dan harbawa don tun ranan da mukai tafiyan nan mai nisa naji ya fara dan min motsi kadan kadan.
Ina fita mukai kicibis da Zulfa tace ashe kun dawo nace eh anty ya baby traana lafiya tace dani sai dai Rahama gaskiya ki mayar da hankalin ki akan abinda ke shirin faruwa a gidan nan bawai nai magana bane don wani abu a, a ni kawai dai nasan kowa kan shi ya sani.
Nace naa gode sai na dawo tace a dawo lafiya na samu yara na jirana a waje nan muka samu Jinior da Nasir sukace zasu bimu nace dasu mu tafi.
Duk da nasan fita dasu zai kawoo matsala gidan su daddy muka fara kai gaisuwa naji dadin yadda Hajiyan dadi ta karbe ni tana kuma yi min nasiha akan hakkuri da jama,a tace duk abindda zanji nayi hakkuri naci gaba da biyayyana don mai hakkuri yana dafa dutse yaci.
Shima Alhajin shi yai min nasiha akan rayuwa mai kama da wa,azi kan zaman takewa naji dadin fadan su a gare ni sai gidan mama laraba don ba nisa da gidan su daddy din.
Abban anty nakai mai shadda da turare da zuma ya nuna jin dadin shi da ganin mu sosaii yai min fatan alheri da saka min albarka tare da kara rokona nai hakuri da yar shi.
Har gidan Aisha da Fatima muka shiga daga can muka wuce zuwa gidan Zarah can muka bata lokacin mu gurin hira tare muka fito zuwa gidan Anty Amina da hajiyan harka na sada zumunta.
Mun shigo gida tun a get maigadi kewa Nasir kabi hajiya uwarka bata sani ba har anyi tashin hankali tsakanin ta da Alhaji a gidan nan.
Nace ai a gaban Amira muka tafi don haka ansan fitan mu dasu muna shiga gidan ba a dade ba sai na ji ihun yaran yana tashi sai dai ina ganin jinior ne ta samu gamin shi.
Ban shiga bada hakkuri ba sai fatan Allah ya sauwaka nayi na shareta ina jiran tazo tai min magana kan fitan da nayi dasu din amma sai naji shiru kwanan mu shidda ran na bakwai tunda safe muka bar garin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , ,

72
A wahale muka isa don gaba daya na ragwabe a motar da kyat naga an kai don tun ina jurewa har yakai bana iya jurewa sai dai daddy yana ganin kamar gajiye ne kawai ke damuna.
Tun shiga na daki ban fito ba na watsa ruwa a jikina na kwanta ranan ko wurin daddy ban samu zuwa ba a dakina na kwana.
Washegari har ya fita na kasa tashi sai bayan fitan shi ne kawata tazo gidan tai treatment din na har na danji sauki.
Ban samu kaina ba sai yamma jikin ya dan sake min na fito falo wurin mutane sai dai duk da haka a kwance nake.
Dadi ya dawo daga office mukai mai sannu da zuwa sai su Aisha suka mike ina kokarin mikewa zaune ne naji yace dani wai ke duk gajiyan hanya ne haka ko kuma kewan antyn ki ne ke damun ki ?
Murmushi nayi nace ai anty na wanan karon ba mu kwasa da dadi ba da ita don ta fada min magana na fada mata sai daga baya abin ke min ciwo da na biye mata har muka kai ga haka da ita.
Yace abinda kuke son kai gayi ke nan ni na kasa fahintar may nene matsalan ku ga wanan halin da kuka tsiro yi.
Shiru nayi har ya gama fadan shi ya bar falin inda ni dai banga laifina ba don duk yadda ake ai nayi wa anty halarci.
Satin mu daya da dawo daddy ya shirya yabar kasan zuwa Spain don wani businesses da suke hassashen yi na karafuna a can.
Tun da daddy ya tafi na samu sakewa a gidan don dama a takure nake dashi don ina jin kunyan yadda zai gane cewa akwai ciki a jikina tun kan na yaye goyona.
Tun tafiyan daddy ba mai jin motsin kowa tsakanina da su anty nace a raina watan sai idan yana gatin me dama matsala yake yanzu da bai kasan shiru babu ruwan wani da wani.
Sannu a hankali nake bussines dina inda nake saro kayan da zasu shiga na tura dasu kano wurin Zarah da mai kayan harka da yake mata na shiga wurin ta nan danan zakaji tace min a karo wasu sun shige ta turo min da kudina.
Rana wirin yawon shige shigen, Hindatu sai gata gidan mai kayan harka wata kawar ta takaita wurin ta bayan sun dada ta wurin iya hada mace.
Ta shiga Mai gyaran harka tagane ta amma ita ba san ta sanni ba na ta sake tana fada mata komai akaina tace.
Wallahi wata hatsabibiyar kishiya muka samu gata yarinyar karama kuma yar kauye ce amma shigowan ta gidan gaba daya ta kwace muna miji.
So nake yadda ake yabaki din nan ki hadani don Allah yadda mai gidan zai rikice akaina ya bar wacan gajar yarinyar yaji ba kowa a gaban shi sai ni cikin mu hudu.
Wallahi ni ban ki ace duk sufice su barni da gani sai shi ba a rayuwan mu na tsani kishiya a rayuwa na gashi kuma Allah ya bani su har mu hudu ne kuma ina son mijina don ban iya rabuwa dashi.
Sai da maigyaran harka ta gama saurarenta tace ai ba haka yakamata kice ba kedai kawai abaki abinda idan kuna tare yaji ba wata bayan ke.
Tace haka nake so ashe dai ke yar hannu ce sosai kinga daga haka ai zan samu kanshi ya tunkudo waccan shigiyar data koma Abuja da zama ta dawo gida ni in dane.
Yarinya kamar hatsabibiya ba duk abinda nayi mata tankar taki nake zubawa akan ta shigiya ko gezau sai naga kamar aiki zaici amma kwana biyu sai abu ya koma fiye da farko.
Tace da ita su bata kwana biyu su dawo idan ta gama mata hadi duk da kudin da ta tsala masu amma haka hindatu ta lale ta biyata kudin ta kai tsaye.
Suna fita wayana dake gefe na yai kara na daga da kyat don a kwance nake tun safe da yake yau ban fita aikin sai da dare.
Ina dauka muka gaisa tace Rahama kin san may nace a, a tace wallahi yanzu wanan kishiyar taki tazo guna yau.
Nan dai take fada min yadda sukayi da irin zagin da ta dinga min sai dariya nake nace kai Allah na gode ma wallahi Allah ka kara rufa min asiri dama nan suna yawan jifana duk kan su Allah ne dai ke kareni wallahi don ba imani ne dasu ba akan mijin su.
Tace ni dai yanzu na bata kwana biyu ta dawo idan kuma ta dawo zan mayar mata da kudin ta ne don ba zan iya mata komai ba.
Nace a, a hajiya kadai ki haka don Allah kefa akasuwa kike don haka na rokeki da duk abinda kika san na amfanine tsakanin miji da mata ki bata ni a gareni babu komai wallahi ai zaman lafiya zai sa a tsakanin su Allah kuma yasa ta gane gaskiya.
Waiko kina da hankali kuwa Rahama kishiya har kike fadin nabawa abin amfani taji dadi da miji ko may ?
Nace yo hajiya sai may jikinta daban nawa daban ai bashine zaisa tafini ba kema ai zakiji tsoron Allah ya tambaye ki akan yi mata kissa da kikayi idan baki bata mai kyau ba.
Tace kai lalai ma Rahama halinki daban ne wallahi da zasu gane natabbatar ba karamin zaman lafiya zakuyi dasu ba amma kishi ya rufe masu idanuwan su.
Mun dan kai wani lokaci da ita muna hira daga karshe mukai sallama da ita tabarni ina tunanen irin hakin na kushiyoyina naga maganan maigyaran harka gaskiya ne datace na kar mikewa na nemi tsarin jikina da na yarona.
Haka na wuni da zancen lafazin hindatu akaina nasan Allah ne ke tsare ni bawai iyawa na ko wani abin ba da na keyi.
Sai dare na shirya nai masu sallama nafice zuwa asibiti inda zanyi night duty dina tun shigana na shiga na shiga aiyukana na manta da zancen wata hindatu can a raina don aiki da yai muna yawa a gany don matsalan mata da yai yawa yanzu.
Sosai nake kula da kaina ban wasa da duk abinda zai kawo min kuzari ajikina na masu ciki tunda na sani ba sai wani ya fada min ba.
Ranan na shiga wurin aikin mu nan nasamu sauran likitoci mata yan uwa na suna hiran aka rayuwan duniya kowa tana fadin nata matsalolin.
Ina sauraren su banyi magana ba sai da sukaji ni bance kala ba sai wata hadiza ke cewa dani ke kan doctor Rahama kin huta ke kadai ce a gun mijin ki kin huta da matsalan rayuwa.
Murmushi kawai nai mata nace a ganin ki ke nan doctor hadiza ni jinku kawai nake don nafi ku matsala idan da zakuji sai kice ashe ke naki dan mali ne.
Tace kajiki da wani zance matar dake zaune daga ita sai mijinta ke har may kika sani akan halin wani zaman takewa haka ?
Nace doctor hadiza nice ta hudu a gun mijin mu ba yadda kike tunane bane din a lokaci daya suke hada baki wurin cewa what nace hakane namike ina tattara takatdin dana gama dubawa na wata mace da aka kawo a cikin dare ciki ne idan ta samu sai yaki zama a jikin ta har sai yafita asamu lafiya.
Nafice duk suka bini da kallon mamaki dayar tace kai ina ban yarda ba wallahi ta dai fadi ne kawai don muce itama din ai tana da nata matsalan.
Amma mai kishiyoyi ne zata zauna haka ko yaushe hankali a kwance bata cikin wani damuwa ko kadan.
Basu yarda ba nima ban kara masu bayani komai ba muka bar zancen a haka a tsakanin mu bandai masu bayani ba.
Sai kuma kamar sati uku na shigo na samu abokiyar aikina tana waya cikin tashin hankali sai na fahinci da mahaifiyar ta take wayan.
Tana fada mata rikicin da suke da mijin ta da kushiyar ta har takai gayin kuka nasan uwar tace ta nemi tsarin jikin ta ne sai naji tace mama nida ke nan a ina zan samu wanan ?
Sai dai ke ki sama min don Allah dai mama daga ni har yaran da zaran Nafisa ta shigo garin nan bamu da sauran kwamciyan hankali har sai ta bar garin nan zamu zauna lafiya dashi.
Har ta karasa wayan bata daina kukan da takeyi ba nai ajiyan zuciya nace da ita kiyi hakkuri hakana don Allah.
Shi alamarin namiji sai idan kana sakawa a ranka ne zai damay ka tunda har kin san inda matsalar take maku da zaran matar shi ta shigo gari ki rungumi yaran ki kifita zancen su har lokacin da ta tafi ya dawo maku.
Idan yaga kina damuwa da alamarin maimakon kiga sauki sai dai kiga ma yana kara tula maki haushe ga hakan yadda ranki zai kara baci ga banza.
Mafita dai daya ke nan mama ta fada maki shine kidai tsare jikin ki dana yaran ki don kariya daga duk wani manufa nata akanki.
Don idan kin fahinta sai kiga bayin kan shi bane hakan shuumanci ne irin namu na mata take kara ingiza shi akai don ranki ya dinga baci kawai idan tazo garin.
Tace doctor Rahama don baki da kishiya ce yasa kike fadin haka wallahi a yanzu nayi dana sanin auren Abdul a rayuwa na.
Haba dai don Allah kice astangafurullah mutun da kuka haihu har biyu dashi zaki tsaya fadin haka kuma akan shi.
Tace doctor kishiya fa ba abin yarda bace walkahi nasani nace mata don ma sai nace ni nafiki sani don ni nan da kike ganina kishiya tai sanadiyar aure da mijin mu na zama ta hudu amma kuma yanzu nice babban makiyiyyarta a duniya don halin kishi kawai.
Da sauri ta dago kai tana kallona a cikin mamaki nace kwarai kuwa nan nafara bata labarina har zuwa wanda hajiyan harka ta jiyo min din ga hindatu.
Nisawa tayi bayan tagama saurare na tace amma kan matsalar ki yafi nawa gaskiya ni ina zan iya zama cikin mata uku na zama ta hudu ai sai su caza min kaina dayan ma yaya na gama da ita balle har na zama ta hudu.
Nan dai muka yanke shawara tare zamu tura wa mahaifiyanta kudi ta taimaka muna

Please Login or Register in order to submit comment