Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su.Da sauri ta lea ta windo don idanunta su fita da shakkun kayan da ta saka za ta etare wata asa a matsayin ta na matar aure.

Haka ta wuni sukuku daga kallo sai kwanciya tunna ba masu gidan da za ta yi musu girki.Da daddare sai ta kasa bacci saboda ita kaWai ne sai masu gadi,Baba in ta gama ayyukanta gida take tafiya saboda ba ta da nisa sosai da gidan.

Kasa bacci ta yi ta na ta juye-juye girman gidan yake matuar tsorata ta, sai take ganin kamar wani zai shigo ga ihun karnikan gidan da suka hana kunninta saat!

Da ga arshe ma tashi ta yi ta Wauro alwala ta yi sallah sannan ta Wauki alkur'ani ta na karatun suratul Ali imran don ta samu ta yi bacci.

A alla mutane gidan sai da suka yi sati biyu ba su dawo ba.A.m ya fara dawowa ranar talata da rana dama tun da safe Zainab ta kira Juwairiya ta gaya mata zai dawo ,don haka ta shirya abinci wanda Zainab ta saka direba ya siyo duk kayan buata na girki.

Misalin biyu da rabi ya shigo da jakar shi rataye a kafaWar sa,sai dai kamar mahaukaci ya shigo saboda zargin sa da yake na Zainab ta yi tafiya zuwa Dubai saro kaya duk da ya hana ta.
Duk da cewa ta ji shigowar shi sai ba ta fita ba ta yi zaman ta a Waki ta na jan carbi,domin ta sama ma kanta natsuwa.

" Ina Zainab?"

Muryar sa ta ji lokacin da ya banko ofa ya shigo da sauri ta matsa ganin kamar zai kai mata duka lokacin da yake tambayarta.

Ba ta ba shi amsa ba amma yanayin da take kallon sa ya tabbatar masa da Zainab ta tafi duk da gargaWin ta da ya yi,cikin Sacin rai ya lailayo ashar zai yi ko me ya tuna sai ya fasa ya fita cikin Wakin da sauri.

Juwairiya da sauri ta bi bayan sa saboda tashin hankalin da ta ga ya shiga,abincin da ta girka masa ya yi jifa da kwanonin da suke jere a dinning Win,ya zaro wayar sa ya kira ta sai dai har ta gama ringing ba ta Wauka ba.

Jifa ya yi da wayar ta faWi a kan tayas ta fashe ya dunule hannun sa guri Waya ya furta." Zainab ki na son sa min hawan jini sai dai wannan karan ba zan Wauki wannan iskancin ba,ina mijin ki ki tsallake ki tafi wata asa hakan ba zai yiwu ba.

Idanun Juwairiya suka kawo ruwa sai hawaye ganin ita kuma haka Allah ya addara rayuwar ta su dun ga sauke fushin su akan ta.

" Ke!"

Ya daka mata tsawar da ya firgita ta sannan ya ci gaba da magana da ce wa." Wallahi yanzu jikin ki zai gaya miki dukan ki na yi zaki saka min kuka bayan na gaya miki na tsani kuka a rayuwata,maza fice ki ba ni guri sannan ki ara min wani abincin.

Hakan ya ara saka ta sakin wani kukan tuna yadda ta sha wahalar girkin ya zubar kuma yake buatar ta ara yi masa.
Da sauri ta wuce kicin ta bar shi a falon ya kai gwauro ya kai mari da ga arshe wayar sa ya Wauka da nufin ya kira A.k,sai dai kuma ya ga aika-aikar da ya yi tsaki ya yi da nufi Waki don ya Wauko wata.

Bai jima ba ya fito bayan ya yi wanka ya canza kaya ko kallon abincin da ta girka bai yi ba ya fice daga gidan.

A haka suke ta zama na rashin daWi duk da A.m na buatar ya kawo arshen zamanta a gidan amma ya kasa,haka dai yau ya daure da nufin zai yai zuciyar sa don ta bar mishi gidan sa saboda ba ya son ganin ta a ciki.

Da misalin biyar da rabi ya dawo gida Juwairiya na falo ta na kallo da aton hijabin ta,ya na hango ta ya tsaki wawan tsai saboda shi haushin hijaban da take sawa yake yi bayan ta san ko shi wanene a gurin ta.

" Wawiya azamiya a haka yadda kike Soye jikin ki ko uban me take Soyewa shi bai ga abin sha'awa a jikin ta ba."

Ganin sa ya sa ta mie da sauri za ta shige cikin Wakin ta.


"Ke."
Tsayawa ta yi ba tare da ta kalle shi ba don ta san wani wulaancin zai yi mata.
Hararar ta ya yi ya zauna akan kujera tare da Waukar remote ya canza tasha,sannan ya kalle ta ya ce " Gidan uban wa za ki saboda dodo ya dawo ko?Wai haka kika ga matan aure suna rayuwa a gidan mazajen su kullum cikin hijabi ke sam baki da wayewa ne?"

Juwairiya ta yi sororo ta na kallon shi jin wani sabon salon da ya fito da shi,amma ba ta ce masa komai ba sai kallon shi da take tamkar bao a gare ta.

" Maza ki je ki kawo min abinci."

Ya ce ganin ta kafe shi da ido ba ta san shi ma ransa a Sace yake maganar ba saboda tsanar ta da yake ji kuma wai ta na matsayin matar sa.

Juwairiya ta so ta bi umurni n shi ta cire hijabin sai dai ina sam ba za ta iya ba,don tsananin kunyar shi take da ke,don haka ta i cire hijabin ta Wauko abincin ta na ije mishi ta ruga zuwa Waki.
Bayan ya ci abinci ya na zaune a falon har aka kira magariba ya yi sallah bai dawo ba sai da aka kira isha'i,sannan ya dawo gida ya rufe gidan duk da ran sa a Sace yake akan Zainab kuma ya rantse in ta dawo sai ta ga abin da zai yi mata,amma sai ya daure ya Wauki wayar sa ya shiga Wakin.

" Ki biyo ni Wakina kin san ba zan iya kwana a Wakin asantu an aiki ba."

Ya fice kallon sa kawai ta yi amma ba ta ce mishi komai ba har ya fita ta gyara kwanciyar ta tare da karanto addu'ar bacci ta janyo bargo ta kwanta.
" Wataila maganar Baba Sani ta yi tasiri a zuciyar sa ya yadda ba ni da kamun kai ne har yake tunanin na bi shi Wakin sa a she zai bushe da jira na.

Washegari da safe bai ci ko abincin karyawar da ta yi masa ba ya fice daga gidan, don ko da ta gaishe shi harara ya banka mata.
Sai abin ya ba ta dariya kawai ta ruga da sauri ta laSe a ofar falon ta na kallon sa har ya fice saboda wankan da ya yi ya tafi da imanin ta.

Sakin labulen ta yi ta zauna a falo tare da Waukar filo ta rungume a irjinta ta na jin wani irin nishaWi, don ko kaWan ba ta yi tunanin rayuwa tare da shi ba ko da kuwa a matsayin matar sa kuma ar aikin matar sa.
Bai shigo gidan ba sai da daddare tare da A.k suka shigo suna ta hira abin su.
A.k na ta baza ido ya gan ta bai gan ta ba musamman da ya ga Zainab ba ta nan,kallon A.m ya yi da yake ta aika ma cikin sa abinci saboda tun zuwan Juwairiya gidan hankalin sa ya kwanta na rashin samun abinci.

" Kai wai ina maryar ka ne ?Tun na yanzu madam ba ta nan na san ila an samu baby?"

Ya faWa ya na kallon shi ya na dariya tare da kai mishi duka a kafaWan sa.TaSe baki ya yi ya ce.Ina zan sani kai kyale ni da wani amarci Juwairiya muguwar bagidajiya ce kullum cikin hijabi ka san kuma ba haka Zainab take min ba."

Ya Wan kalli A.k da ya daina cin abincin ya na sauraron sa ya ce."Jiya da na kira ta Wakina in zuwa ta yi ban san tunanin ta a kai na ba."

" To kai in ban da abin ka A.m ai kai za ka bi ta kuma kuma mace take Hausa dole ta ji kunya."
A k ya ce da shi ya na kallon sa.A.m ya ara taSe bakin sa ya ce." Ok ka manta abin da anin mahaifinta ya ce a kan ta ni ban ga abin kunya ba."
"A haba A.m ka san halin sa kar ka yadda da maganar sa kuma koma mene ne kai ka amince za ka aure ta sai ka ba da azama mu sami baby.".
Dariya suka yi duka daga bisani A.k ya matsa mishi ya kira ta su gaisa ya na zaune ya wala mata kira ba ta jima ba sai ga shi ta fito,kamar dama laSe take musu ta na jin maganar da suke yi.

A.m tashi ya yi ya nufi Wakin sa zai Wauko tsaon da A.k ya biyo shi ya karSa ba tare da ya kalle ta ba.

Da ladabi ta gaishe shi ya amsa ya na ta tsokanar ta dai murmushi take masa.
" Na so mu haWu kafin ayi auren ki da shi sai dai kuma Allah bai nufa ba ko Juwairiya?"

Ya faWa tare da mai da maganar ta tsigar tambaya.aga masa kan ta ta yi ta na kallon shi " Ok ba komai da ma na so na Wan miki wata magana ne Juwairiya don Allah duk yadda zuciyar ki za tai ki karki yadda ki saka son A.m a ran ki kawai ki sama ran ki zaki ci arziki ki tafi ne.Ki Wauke ni a matsayin Yayan ki duk lokacin da wata matsala ta haWa ku ki sanar da ni."

Ya yi maza ya arashe maganar jin takun A.m daga matakalar bene.Kallon sa ta yi sai kuma ta ji ya burge ta sosai yadda bai Wauki rayuwar sa da zafi ba.
aga masa kanta ta yi alamun ta ji amma kuma a cikin zuciyarta sai ta ce.
" Ka makaro A.k da ce wa ka yi na yai zuciyata da take son sa ila da na karSi shawarar ,amma na riga na daWe da shiga cikin kogin son sa."

Sai da A.m ya yi masa rakiya sannan ya dawo ya tsaya ya na kallon Juwairiya da ta kasa tashi ta na ta tunani a ranta." Me hawayen banza maza ki tashi ki gyara min Wakina saboda yau haushina da kike ji sai kika huce akan Wakin,sam gyaran bai yi kuma ki ara wanke bayi."
Ya faWa tare da zama a falon kamar ya na son ta gama sai ya shigo.
Wucewa cikin Wakin ta yi ba tare da ta ce masa komai ba amma ya faWi son ransa ne kawai duba ga yadda take ba da dukkan lokacin ta in ta je Wakin sa gyara.

A.m ya na ganin ta shige ya bi ta tare da tura ofar a hankali ganin ya shigo ta tsaya dama tun da ta shigo ta rasa mai za ta gyara saboda Wakin ya na tsaftace da kyan sa.

" Ki zo mu kwanta a gadon da baki taSa hawa ba amma albarkacin aurena zai saka ki din ga moresa in matar so ba ta nan."

Hawaye suka wanke mata fuska ba ta ce mishi komai ba kuma ba ta motsa ba bare ya saka ran za ta hawo,asalima gaban ta ne ya faWi ras!

Hannunta ya jawo ya na faWin." Na lura kuka shi ne farin cikin ki to ki sani ba zan taSa buWe bakina rarrashe ki ba,ko na Wauki hannuna na share miki hawaye da su.

Yanayin da suka shiga a ranar yanayi ne mara fasaltuwa da bayyanuwa a gare su musamman Juwairiya da ta sha kuka har ta gode ma Allah,domin kwana ta yi ta na kuka ko kaWan ba ta bar shi ya rintsa ba,wanda in ta tuna dalilin kukan na ta biyu ne sai ta ara sakin wani kuka.

A.m da bacci ya fara Waukar sa a hankali bayan wata sabuwar duniya da ya shiga kuma ya kasa fahimtar wace duniya yake ciki,kukan da take yi ya na Waga masa hankali ya yi maganar duniya tai yin shiru,har ya gaji ya yaleta ya rintse idanun sa da arfi ya na son bacci ya Wauke sa.
Ganin tai dai na kukan ya janye bargon da ya udundune kan sa da shi ya kunna fitilar Wakin."

Ke wai ke."

Sai kuma ya yi shiru daga ninyar faWar da yake ya yi mata ya Wan sausauta murya ganin dare ne ya ce." Ko fa wace mace da kika gan ta a gidan mijinta da haka ta fara.Kuma idan bakya son haka ba sai ki gaya min ki gode ma Allah auren kwangila muka yi so ba daWe wa za ki yi da ni ba."

Hakan sai ya saka Juwairiya ta ara fashewa da kuka ganin ta ba ma mutumim da ya tsane ta rayuwarta,ga shi bai san mahimmancin ta ba bayan wahalar da ta sha yake gaya mata waWannan kalamai.

Bakinta ta murguWa a ranta ta ce." Mugu kawai azzalimi."sai kuma ta ci gaba da kukanta wanda A.m ya lura harda shagwaSa don shi ya gama fahimtar ta shegen shagwaSa ne da ita shi ya sa da an yi magana sai kuka.

Wani irin waliya a ka saki lokaci guda aka fara tsawa nan ne A.m ya fahimci garin hadari ne ya taso,da sauri ya sauka don ya duba ko windina a kulle ne kawai sai ya tsinci kan shi da jin daWin ya na yin garin har ya buWe labule ya na shaar iskar gurin.

Iskar ya ara ma Juwairiya zazzaSin da ta ji ya saukar mata ganin haka sai ya rufe windon ya na addu'ar Allah ya sa ta yi shiru kenan,jin ta sassauta sautin kukan da take yi sai ya koma ya zauna.

Wayar sa ta fara ruri da sauri ya Wauka don gabansa ya faWi ya na tunanin waye da daddare zai kira shi,ganin numbar masoyiyar sa ya sa shi miewa da sauri take Sacin rai ya bayyana a fuskar sa.

A wannan lokacin da yake duba wayar sa aka tsuge da ruwa sosai kamar da bakin warya.
Zubbur ya mie ganin numbar Zainab ce ya yi kamar ba zai Wauka ba,saboda tun da ya gaya mata zai dawo ta de na Waukar wayar sa ashe mara mutuncin tafiya ta yi tabar asar.Sai kuma ya kanga wayara a kunnin cikin tsanani Sacin rai a ransa ya na tunanin Allah kawai zai raba ta da shi.

" Hello zauji don Allah gani a airport ka zo ka Wauke ni kuma na samu ar matsala da kayana har mutumim ya na min barazana.Ga kuma ruwa da ake yi kazo ka ji zauji."

Wani irin tashin hankali ya ziyarce shi ya kalli Juwairiya da take cikin wani hali don shi kan sa ya san ya wuce gona da iri,kuma ba tare da sanin haka ba ya kuma kalli kansa da har yanzu ya kasa tantance duniyar da yake ci.


Tunani ya fara yi ko Zainab ta hauka ce ne da za ta dawo da tsakar dare sai ya Wauki wayarsa da nufin ya duba lokaci, ai wallahi ba zai fita yanzu ba sai dai koma mene ne ya faru musamman da ta Sata masa rai ta yi tafiya ba tare da izinin sa ba.

Tsananin mamaki ya kama sa da agogon wayar sa ya nuna mishi arfe biyar da mintuna,ya na cikin kokwanton ko wayar sa ce saitin ta ya goce sai ya ji ladani ya kwaWa kiran sallah.

Da sauri ya yaye labulen Wakin don ya ara tabbatar ma kansa take kuwa ya ga har hasken alfijir ya keto gari ya fara wayewa..
Sai hankalin shi ya ara tashi musamamn da Zainab ta turo masa tsaon ba sai ya zo ba,don sun daidaita da mutumim yanzu haka ma suna hanyar gida,saboda mijin Anti Fati ya turo direba ya Wauke su kuma duka za suzo gidan.


TO FA JUWAIRIYA GASKIYA NA TAUSAYA MIKI DA RANAR KI TA KASANCE A HAKA KOMAI DAI MENENE ALLAH YA BAKI HAURI DA JURIYA.KUCI GABA DA BIBIYAR LINTAFIN SAKACINA KO HALIN MAZA

NAI YIN TYPING DA YAWA SABODA GASKIYA FANS BA KWA RUWAN COMMENT SAI DAI KU YI TA BIYO NI TA PC KUNA FAIN ALLAH YA ARA FASAHA INA GODIYA AMMA NI NA FI SON NA GA RUWAN COMMENT YA NA TASHI DON GAKA IN KUNA SON NAADIN GA TYPING DA TSAWO KU DIN GA COMMENT.







TAKU

JAMILA LAWAL ZANGO


UBBIN GAISUWA GARE KU SABODA COMMENT IN KU YA NA SAKA NI NISHAI.

MAMAN SUDAIS
AISHATU MINNA
FATIMA ZARA JOS
SAHURA NURA RABIN RAINA
NABILA MAMAN SAFWAN
HAMDIYA UMMU ABDULHAKIM








Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haWu a shafi noma sha shidda.Ga masu buatar shiga cikin group Wina na whatsapp ga numba 08144072423_.


Kuma ofa a buWe take na orafi gyara ko arin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce.
Kar dai ku manta da wannan lintafin sadaukar wa ne ga zaauran marubuciya,kuma awata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani.






COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE.








*SAKACINA KO HALIN MAZA?*



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*

*SADAUKARWA GA:-*

*SUMMY M NA'IGE*
_(Aminiya)_


*FIRST CLASS WRITER'S ASSO....*

*Page 19*

BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM


A.m ya shiga cikin tsananin tashin hankali ya juya ya kalli Juwairiya da take jin duk abin da yake faruwa,ga jikinta sai kyarma take yi har ta fara haWa haori kar-kar!

Sai tashin hankalin sa ya nunku ya kuma rasa tunanin da zai yi.Hannunsa ya sa ya tallafe kan sa can kuma ya shiga shafa sumar kan sa ya na tunanin mafita,don shi babban tashin hankalin shi da Zainab ba ita kaWan za ta dawo ba ya san ce wa ta ce su zo ne su rarrashe shi.

Wayarsa ya zaro ya yi kiranta ringing Waya ta Wauka ta na kashe murya ta ce." Hello Habibina ai mun kusa arasowa gidan..."

Wata uwar tsawa ya daka mata da ya firgita ta ya ce." Ni ko Zainab wallahi in kika shigo gidana na da waWannan dabbobin sai na yi miki mugun rashin mutunci,don haka ki ce musu ko wace banziya ta kama gabanta tunna su mahaukata ne.Kuma zaki dawo zaki ga abin da zai faru! Allah ya sa su yi gangancin shigowa gidan."

Da fushi yake magana tamkar ta na gaban shi don iya abin da zai yi kenan ya hana su shigowa cikin gidan.

Zainab ta yi shiru da waya sororo a hannunta, ta rasa ya za ta yi ga shi ta gama koWa kanta ta isa da shi,don sun nuna in zuwa saboda sun san halinsa ba kamar mazajen su yake ba.
" Kai direba tsaya wallahi Zauji yau rashin mutunci yake ji kun ji abin da ya ce."
Ta faWa a kunya ce ta na kallon su.
"Mai ya ce Wan rashin mutuncin?"
Anty Fati ta tamabaya don ta san za'a rina sanin hali."Gaskiya ko wace mace ta tafi gidan ta ku sauke ni anan kawai ina ga an iskan an uwansa sun zuga shi ne,amma da amincewar sa na tafi Dubai yanzu ya na faWa min kar ku zo mishi gida ."

Ta faWa a kunyace don ya ba ta kunya ga shi ta gama zuga musu arya." Kar ki yadda Zey ya haWa ki fita kin ga dai irin ribar da muka samu,ki nuna mishi turjewar ki."
Anty Fati ta faWi cikin maganar zuga ta na son ta ara zuga ta don ta shirya duk abin da yake ji.
" Ke ma kin san halina kawai ba na son ya wulaanta ku ne ku je kawai ni wallahi akan sana'ta zan iya haura da aikin gwannati bare kuma ya ce zai kawo min cikas."

Anty Maryam da ba ta ce komai ba ita ma ta na tunanin abin da za ta tarar,in ta koma sai yanzu ta yi magana ta ce." To ki rabu da shi mana yadda kike da kyan nan ai kin san ki na fita za'a wawushe."
Wani mugun kallo ta yi mata tamkar za ta kai mata duka ta ce." Ka ji Anty Maryam da maganar banza ni da Hubbi ai mutu ka raba takalmin kaza! So kike na kashe aurena na je na auri mai mata ko wanda zai yi min kishiya nan gaba,hakan ma ba zai yiwu ba don ni da kishiya ko a lahira ba na fata kuma zan iya yin komai a kanta ni da ita yai ne tsakaninmu."
"To ki tafi mana ga shi har yanzu ana yayyafi kuma kin buWe mota kin tsaya ki na zuba,don kawai an miki maganar kishiya duk da family Win mu ba'a mana kishiya, amma Zey ki rage kishin ki to ke da mijinki ba ya haihuwa wace mace za ta zauna da shi ai sai ke ar wahala."

Dariya ta yi ta na Waga musu hannu ta ce da arfi ta yadda za su ji ta don motar su ta fara tafiya." A huta gajiya a haka nake son abina kuma sai mutuwa za ta raba mu.Kayana zan shigo na karSa."

Sannan ta juya da nufin ta shiga gida yayin da gabanta yake dukan tara!Tara!! Don ta san ba za su kwase da saui ba.

A.m ya juya da nufin ya yi ma Juwairiya magana amma sai ya ga ba ta a cikin Wakin har ya fara taku zai bita sai kuma ya dawo,jikinsa na rawa da shi kan sa ya kasa gane kansa ya na jin wani canji a jikinsa.

Sai kawai ya nufi cikin bayi don ya tsarkake kan shi ya yi salla amma sa ya fasa jin ana buWe gida da alamun Zainab ce ta shigo,da sauri ya arasa gurin windo ya buWe ilai kuwa ita ce ta shigo da gudu saboda ruwa da yake dukanta.

Girgiza kan shi ya wuce cikin bayi da sauri don ya san in Zainab ta same shi a haka za ta fahimci wani abu,kuma rashin mutunci yake son ya yi mata sai dai yanayin da yake ciki na rashin arfi ba zai ba shi damar yin hakan ba.

Ya jima a cikin bayi duk da kiran da Zainab take kwaWa masa bayan ta shigo ganin ba ta gan shi ba,amma hakan bai sa ya ko Waga kan sa ba ya na ta tunanin da shi kansa in aka tsare shi ba zai ce ga dalilin tunanin ba.

Ikon Allah dama Baba Sani arya yake yi wa Juwairiya mace ce mai nagarta da kamun kai?Haka kawai sai ya ji tsanar mutumim ya kama shi har ya na jin zai iya komai don ya taimaki rayuwarta.

Ko da ya fito faga Wakin bai ga Zainab ba wacce ya tabbata ta ga ji da zaman jiran shi ila ita ma ta na bayi ta yi wanka.
Sallah ya yi da sauri don yau ne karon farko da ya rasa jam'i shi lokacin ne ya wuce gani yake yau gari ya yi saurin wayewa.
" Hubbyna oyoyo zuciya ta yi kewar ka da gangar jiki."

Ta faWa lokacin da ta buWe ofa duk da cikin tsoro take amma sai ta daure ta kauda tsoronta ta furta hakan,don ita a shirye take koma mai zai faru ya faru in dai akan fita ne saboda ta ji daWin fitan sosai.

Wani irin

Please Login or Register in order to submit comment