Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya fita daga motar ya Bud'e masa back seat Afeef ya k'arasa ya shiga Yana ansawa ma'aikatansa Dake mafan Yi Mai sauka lafiya dama....


Tafiyar mintun 30 ce ta kawo su airport d'in ya fito da sauri John kuma ya zaga boots ya fito masa da boxes d'insa har kayan da yaywa su HUYAAM siyayya suna ciki duk john ya fito dasu kafin ya bi bayansa.... Afeef na zaune a VIP dake cikin jirgin ya duba rantsatstsan agogon Dake tsintsiyar hannunsa yaga k'arfe biyu da mintuna 10 jirginsu ya fara tashi a hankali harya tashi zuwa sararin samaniya maida kansa yay ya lumshe ido Yana Jin yadda jirgin ke ratsa gajimarai....



Tun bayan tafiyar su Huyaam islamiya Ammie da baba magajiya da wasu masu aikinta su biyu suka had'u a k'aton kitchen d'in part d'in suna taya Ammie Dake had'awa Afeef Abinda zasu tarb'eshi dashi.. girki sukeyi kusan kala 6 ake masa duk Wanda za'a tarb'eshi dashi ne Kuma ko wanne kalarsa daban har Yanzu Daya kasance k'arfe biyar saura Basu gama ba Amma Saura kad'an su k'arasa.gabad'aya k'amshin girkin nan ya cika b'angaren Ammie.D'azu dai lokacin da su Afeef suka tashi ya k'ira Ammie ya fad'a mata sun taso Da yay sa'a Kuma jirgin direct kano zai sauka.....



Hajiya Lubabatu ce Zaune a d'akin da suka saba k'ulla duk Wani abubuwan su ita da Fulani Salamatu Suna zaune kan kujerun Dake d'akin.Hajiya Lubabatu tai k'asa da da tana kallan fulani Salamatu wacce tai sak'are tana kallanta Jin abinda ta fad'a. tace.


"Wallahi fulani kar kice wasa motocine gasu can na barsu a compound sabbi dal dasu Irin Wad'anda suke k'erawa d'in nan ne Wanda aka kawosu kwanaki ko ta tab'a bawansu ba'a tab'a yiba tunda aka kawosu gidannan kusan guda biyar anfito dasu an wanke za'a je d'auko magajin gidan dasu sai kace shine sarkin Danko sarki ne zai Yi tafiya iya comboi d'in da za'a masa kenan".ta fad'a tana Wani mele Baki... fulani Salamatu da idonta ya kad'a yay ja Jin abinda Hajiya Lubabatu ta fad'a mat ta sauke numfashi tace.


"Wato kullum Abin nan nasu K'ara cigaba yakeyi Lubabatu, ni kenan ba'a tani tunda 'ya'ya mata gareni shikenan ba'a tab'a sakani a lissafi 'ya'yan Maryam sune 'ya'ya a gidan nan.wato dawowar ma da Afeef d'in zaiyi har Wani comboi za'a masa aje d'auko shi ?..."Fulani Salamatu tace.


"Uhmm!! gashi dai can ana shiri ban sani bama ko harda Mai martaban Za'aje d'auko shin oho?.."da sauri fulani Salamatu tace .

"Banda shi baya nan tun d'azu ya fita shine ma yake cemin yau Afeef d'in zai dawo". Hajiya Lubabatu ta kad'a kai tace.

"Uhmm Ai dama nace Baki sani ba shiyasa nace bari nazo na fad'a miki. Ai maryam malaminta ya iya aiki karki Wani damu kinsan Allah asiri ne bayin kan Mai martaba bane ba, saida ta riga da tasan kan mai marataba tass sannan taje aka mallake mata shi ". fulani Salamatu ta sauke numfashi tace.

"Aikuwa Wallahi Bata Isa ba Dan saina k'ask'antar da ita agidan nan Dani take zancen yadda ta dasa min rauni a zuciyata wallahi ni kuma raunin zanji mata". Hajiya Lubabatu tace .


"Ai Bari kawai k'awata bari malam ya dawo wallahi bazamu zauna ba".sai Kuma ta d'aga kai ta Kalli time tana mik'ewa tace.

"Uhmm! Bari naje fulani yaran nan sun kusan dawowa daga islamiya karsu su zo su Tarar Dani". Tana fad'ar haka ta nufi k'ofa.fulani Salamatu tace.


"To idan sun tarar Dake sai mene?..."Hajiya Lubabatu ta juyo tace.


"A'a fulani Kar muje su shigo bamu sani ba muna wannan maganar suji abinda muke fad'a kar suyi mana wani kallo". Fulani Salamatu tabita da kallo batace komai ba Daga nan zaunan da take ta ansa mata sallamar da Hajiya Lubabatu take mata. tsabar abinda Hajiya Lubabatu ta fad'a mata ya bugeta ko iya tashi daga inda take zaune Batai ba kallan Hajiya Lubabatu kawai take har ta fita daga d'akin.....


K'arfe biyar da mintuna 10 motacin da aka wanke tun d'azu wanda za'a d'auko Afeef dasu suna jere a harabar gidan. drivers d'in da zasu ja motocin duk suna ciki sun ta-da su D'aya bayan D'aya suka fara fita daga cikin gidan bayan an wangale musu gate d'in. Sannu a hankali suke fita daga gidan Dan zuwa d'auko Afeef a air port kamar yadda Mai martaba ya Bada umarni tareda rakiyar wasu daga cikin fadawan gidan har motocin suka gama fita daga gate d'in gidan gabad'aya reras su biyar abin sha'awa.d'aya bayan d'aya suka hau kan titin motacin nan sai wani d'aukar ido suke saboda sabi ne dall aka fito dasu yau d'in nan aka fara hawansu direct Airport suka nufa Dan d'auko Afeef Wanda jirgin nasu baima sauka ba sai nan da k'arfe biyar da Rabi kafin lokacin Kuma sunje.......




#<Ø9ß HUYAAM
#<Ø9ßAZIZ CHIROMA
#<Ø9ß LAMID'O
#<Ø9ß AFEEF




07066508376________
'þFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD



*<Ø9ßHUYAAM<Ø9ß*



*NA*



*__NAJA'ATU UMAR FAROOQ __*



*__(MRS SARAKIES =Ø‹Ü)__*




*PAGE 1þã 8þã *



*Bismillahirrahmanirrahim*



__________¡&


K'arfe biyar da Rabi dai dai jirginsu Afeef ya sauka a airport d'in Aminu kano international airport.matafiya ne ke saukowa daga cikin jira wad'anda suka dawo daga zuwa k'asar Ingiland zuwa Nigeria.d'aya bayan D'aya passengers d'in suke saukowa daga matattakalar jirgin kowa Daya sauko zai wuce zuwa wajen d'aukar kayansa .can na hango Afeef sanye cikin k'ananun kaya riga da Wando Wanda da sukai masa bala'in kyau furkarsa rufe da face mask ya D'ora facing cap a kansa.sannu a hankali shima yake ta saukowar harya k'arasa saukowa gabad'aya.tun kafin ya k'arasa fitowa daga wajen ya hango dogarayen da suka zo d'aukar sa gabad'aya sun fito daga cikin motocin suna jiki suna zaman jiransa ko ba'a fad'a masa yasan daga gidansu suke . hangoshin da sukai yasa suma wasu daga cikin dogarayen suka taho cikin sauri Dan su tarb'eshi. Yana kallansu har suka k'araso wajen sa cikin girmamawa suka karb'i box d'in hannunsa guda d'aya wasu Kuma suka k'arasa suka d'auko sauran boxes d'in nasa . tun kafin ya k'araso wajen motar akai saurin Bud'e masa back seat tareda zabga masa kirari ta ko Ina .da ka kawai Afeef ya iya ansa musu har ya shiga motar suka rufe a hankali. Boxes d'in da suka d'auko suka gama Sakawa a cikin boot d'in motar Saida suka gama saka su du, sannan suka rufe boots d'in kafin su bar wajen cikin sauri kowa ya shige cikin motocin da suka zo a cikinsu...Alaye cikin nutsuwa motocin suka fara fita daga cikin air port d'in har suka gama fita gabad'aya,duk inda suka wuce acikin kano kallan motacin kawai ake saboda d'aukar idon da sukeyi da Kinga motocin ma kinsan babu k'arya sun Had'u iya had'uwa Dan acikin kano ma ba kowa zaki samu Yana da Irin motocin ba sai wanda kud'i suka zaunawa zai iya mallakarsu. cikin nutsuwa motocin suke tafiya akan lafiyay yan titin,shiko Afeef Yana zaune a bayan motar ya jinginar da kansa da kujerar motar idonsa a lumshe......



K'arfe biyar da mintuna Arba'in motar da ake d'auko su Huyaam daga islamiya ta shigo cikin palace d'in, k'arasawa tai tai parking a inda akeyi.bayan motar ta tsaya dogarin Dake gaban motar ne yay saurin Bud'e inda yake Zaune ya fito ya k'araso ya Bud'e musu murfin motar.D'aya bayan D'aya su Huda suka shiga saukowa daga cikin motar har suka gama fitowa gabad'aya daga nan Kuma kowa ya nufi b'angaren su .tun kafin su Huyaam su k'arasa shiga cikin falon k'amshin girkin da Ammie Sukayi ya cika hancinsu,Dan tunda suka shigo b'angaren k'amshine kawai ke tashi.da sallama suka k'arasa shiga har cikin falon, babu kowa aciki Dan haka kowa ya shige D'aki Dan sauya kayan jikinsa.A Dining din sama suka tarar da Ammie Dake tsaye a dining d'in tana K'arasa setting table d'in.nan ma sallamar sukai ganin Ammie falon.tsayawa tai daga abinda take tana ansa musu sallamar su muneefa ta tafi da sauri ta rumgume Ammie tana cewa.

"Ammie mun dawo".ta fad'a tana murmushi. Ammie ta rik'e ta tace.

"Sannunku da zuwa".dukkansu suka had'a Baki wajen gaida Ammie.nan ma Ammie ansa musu tai tana murmushi . Huyaam na cire hijab d'in jikinta anan falon tace .


"Ammie yayan ya dawo ne?.ta fad'a tana kallan Ammie..Ammie ta girgiza kai tana kallonta tace. "D'azu aka tafi d'auko shi,Amma nasan yanzu haka ma suna hanyar dawowa in Sha Allah".Huyaam ta sauke numfashi . muneefa tana kallan Huda tace.

"Ya Huda addu'a ta ta karb'u Yaya Bai rigamu dawowa ba".ta fad'a tana murmushi.huda ta gyad'a mata tace.

"Eh fa. tom Allah ya kawo su lafiya". Ammie da Huyaam suka ansa da Ameen. Ammie na kallansu tace.

"to Maza kuje ku shirya kafin su iso". Huyaam da Huda suka ansawa Ammie kowa ya shige d'akinsa ita dama ya Zarah tun tuni ta bar wajen tun bayan data gaida Ammie..Ammie Kuma ta kama hannun muneefa suka shige d'akinta Dan ta shirya ta itama ......


Horn d'in motar farko ce datai a bakin gate d'in yasa D'aya daga cikin fadawan Dake zaune a bakin gate d'in yay saurin mik'ewa Daga inda suke zaune,ya taso da sauri ya k'arasa har gaban gate d'in ya danna Wani D'an Abu take Gate d'in ya Wangale motocin suka fara danno kai cikin gidan D'aya bayan D'aya.gabad'aya dogarayen Dake Bakin gate d'in saida suka mik'e ganin shigowar yarima Afeef cikin masarautar. motacin na k'arasowa dai dai inda suke tsaye take suka zube a k'asa kawunansu na kasa da babbar murya suka Shiga jero masa Barka da zuwa had'i da kirari. bayan motocin sun gama wucewa Kuma suka mik'e gabad'aya wasu sukabi bayan motocin da sauri kowa Yana k'ok'arin yaga shiya Bud'ewa yarima Afeef motar da yake ciki duk da Basu San a wacce yake ciki ba Sauran kuma suka tsaya suna Tsaron gate d'in.gabad'aya suka zube a k'asa bayan sun k'arasa inda motocin sukai parking suka jeru gaban motar kaf ma'aikatan gidan sarki saida suka fito dan yiwa yarima Afeef barka da zuwa.motar Dake tsakiyar duka motoci hud'un na hango Wani dogari wanda dashi akaje d'auko Afeef a air port ya fito da Sauri Yana gyara zaman babbar rigar jikinsa Irin ta dogarai yasa hannu ya bud'ewa Afeef bayan motar da yake ciki ya ja baya da Sauri Yana kirari da cewa.

"Eh!! fitowarka Lafiya takawarka yariman kano magaji magajin masarautar kano idan Allah yaso ya yarda. gaisheka saraki madara Mai kama da nono d'a Mai kamar uba.ire Iren wannan kirarin suka dinga jero masa.yana jinsu Bai iya yace musu komai ba.illa K'afarsa D'aya daya fara zirowa sannan ya ziro da d'ayar ma kafin ya gama saukowa daga cikin motar gabad'aya .kamar had'in Baki haka dogarayen nan da suka zube tun k'arasorsu wajen suka shiga yiwa Afeef barka da zuwa kansu a k'asa Cikin girmamawa.matsawa daga jikin motar Afeef yay yana ansa musu lokaci D'aya Yana k'arewa gidan nasu kallo kamar Wanda ya sauya masa .ya haidar ne ya yazo wajen fuskarsa da murmushi Shima dawowar sa gidan kenan ya k'arasa har wajen yayan nasa ya bashi hannu tareda Yi masa side huge Afeef ya sake shi Yana ansa masa sannu da zuwan da yake masa kafin ya bar wajen ya haidar ya bishi suka jera zuwa b'angaren Ammie gabad'aya. tuni dogarayen suka Bud'e boots d'in suka kai kayan nasa bangaren Ammie.


Tun shigowar motacin da muryoyin fadawa da suke ta jerowa Afeef kirari Had'i da barka da zuwa su Huyaam suka San yayan nasu ne ya iso,ko Wacce tayi wanka ta shirya cikin shiga Mai kyau Huyaam da Huda kaya iri D'aya suka sa, doguwar rigar atamfa ce D'inkin beat work Mai bala'in kyau ga stone sai Wani walwali sukeyi.Huda ce ta shigo d'akin HUYAAM tana kallanta tace cikin farin ciki.

"Yanzu yaya suka iso ki taso muje falon k'asa muga shigowarsa".ta fad'a tana kallan Huyaam..Huyaam Dake gaban mirror tana kokarin Parking gabanta da ribbons tace ."jeki Gani nan Dan sai nayi sallah ma zanzo lokacin ya huta Dan yafi ganina da kyau".ta fad'a tana kallan Huda ta cikin mirror d'in . Huda ta tab'e Baki tace.

"To saikin fito bari nidai naje Dan naji kamar muryarsu ya Zarah ma a falon k'asa". Tana fad'ar haka juya tabar d'akin.huyaam ta juya ta k'arasa parking gashin.


A falon k'asa kuwa gabad'aya su Ammie da ya Zarah suna tsaye suna zaman jiran shigowar Afeef Huyaam ce kawai Bata nan.ya haidar ne ya fara shigowa falon sai Afeef Dake biye dashi a Baya Hannunsa cikin na muneeb suka shigo bakinsu d'auke da sallama.har suka k'arasa shigowa falon. da gudu muneefa taje ta rumgume shi tana murmushi cikin murna tace .

"Well come back Yaya".ta fad'a tana k'ank'ame shi .hannu yasa ya d'agota yana sakin fuskarsa yace.


"Thank you so much muneefa" gabad'ayansu suna tsaye suna kallansa fuskarsu da murmushi kafin kowa ya shiga yi masa Barka da zuwa kallansu yayi D'aya bayan D'aya Yana ansa musu.Ammie na murmushi tace.

"Sannu da zuwa Afeef".ya k'arasa gaban Ammie da murmushi a fuskarsa ya cire face mask d'in fuskarsa ya zare hular kansa sannan ya D'an duk'ar da kansa kad'an agaban Ammie.hakan da yay Ammie ta Gane Mai yake nufi,Ta K'ara fad'ad'a murmushinta . kafin ya furta .

"Lafiya lau Alhamdulillah Ammie nasameku lafiya". Ammie na murmushi tana kai hannunta ta shafa kansa tace. "lafiya lau Alhamdulillah! sannu da zuwa ka k'arasa ciki ka huta". ya dago da kansa yana kallanta yace cikin deep voice d'insa.

"Alwala Zanyi naji ana K'iran sallahn magrib ne". Ammie ta Jin jina kai tace.

"Eh hakane ka k'arasa cikin to saika fito". ya Jin jina mata kai Daga haka Afeef ya haura sama zuwa b'angarensa . Bayan tafiyarsa Ammie ta sauke numfashi tana kallansu Huda tace.

"A'a! ina huyaam ya bangan taba?..." Ta fad'a tana waige waige a falon ko zata ga inda ta mak'ale.Huda tace.

"tana d'aki Bata gama bane". Ammie tace.

"Ok shikenan to ku wuce kuma kuje kuyi alwalan sai kuyi sallahn".Babu musu duk suka juya suka haura sama Dan zuwa suyi sallahn ya haidar kuma da muneeb suka fita daga falon suka tafi masallacin palace d'in.....



____________¡&


Tunda Afeef ya Fita sallahn magrib Bai dawo ba Har Sai da akai har sai da akai sallahn isha'i sannan suka dawo b'angaren nasu shida ya haidar sai muneeb .da sallama suka shigo babu kowa a falon sai k'arar AC data fan da suke tashi.bayan sun k'arasa shigowa falon ganin Babu kowa suma su Ammien Basu Sau ko ba yasa ya Afeef ya Haura sama zuwa d'akinsa Dan ya watsa ruwa,shi Kuma ya haidar ya samu waje anan falon ya zauna kan D'aya daga cikin kujerun falon. muneeb kuma ya wuce ya haura sama zuwa d'akin Ammie...Da shigar Afeef falonsa Wani daddad'an k'amshi ne ya Doki hancinsa ya lumshe ido at the same time Yana bud'ewa Dan d'azu Daya shigo da yake ko zama Bai yiba yasa Bai k'arewa falon d'akin kallo ba.karasawa k'ofar bedroom d'insa yayi ya Murd'a k'ofar a Hankali ya tura ya shiga ciki .nan ma Wani daddad'an k'amshin ne ya sake ziyartar hancinsa tsayawa yayi ya Shiga k'arewa d'akin kallo yayi neat kamar Wanda ba tafiya yay ya Barshi a haka ba, sai dai wannan an gyara shi an can za zanin gadon da kayan Dake kan mirror Wanda duk yawancinsu ma kayan shafa shafa ne kamar su lotion sai turaruka na maza kala kala d'akin dai yayi masa sosai yadda yake buk'atar ganin sa Dan sai kace dakin wata amarya yasan Kuma wannan ba aikin kowa bane saina Ammie.sauke numfashi yayi ya k'arasawa gaban makekem gadonsa ya fara rage kayan jikinsa Yana gamawa ya shige toilet d'in nanma dai Wani k'amshin ya tadda a toilet d'in, shima kansa banda k'amshi Babu abinda ke tashi acikinsa babu Bat'a lokaci ya cire towel d'in jikinsa sannan ya had'a ruwan wanka ya shiga bath tube d'in....


A falo kuwa su Huyaam suna yin sallahn isha'i kowa ya fito Suka zazzau na a nan falon saman kujeru ,Huyaam da Huda na zaune waje D'aya suna hira k'asa k'asa ya Zarah kuwa wayarta ta d'auka ta kunna data,Ammie ce k'arshen fitowa bayan ta zauna kan kujera tana kallan ya haidar tace .

"Ina Afeef d'in yake?.." ya haidar ya d'ago da kansa daga kan wayar sa Yana kallan Ammie yace.

"Bai fitoba Yana d'akinsa".Ammie ta Jin jina kai tana kallansu Huyaam tace.

"Ku taso ayi dinner kafin ya fito ko?..Babu musu suka mik'e suka k'arasa dining d'in....fitowarsa daga wanka kenan duk jikinsa Yana d'igar ruwa ya k'arasa tsakiyar d'akin ya yatsa hannunsa rik'e da k'aramin towel ya fara goge ruwan jikinsa dashi tun daga kansa har gadon Bayansa bayan ya gama ya k'arasa gaban mirror ya fara shafa lotion d'insa bayan ya gama ya K'arasa wardrobe ya d'auki k'ana nun kaya zai sa yasa ya ya d'au tarare ya feshe duka jikinsa dasu sannan yasa hannunsa ya d'auki comp ya fara gyara gashin kansa bayan ya gama ya k'arasa kan gadon ya d'auki wayoyinsa sannan ya fito daga d'akin bayan ya kullo k'ofar.tun kafin ya gama saukowa downstairs k'amshin turaransa ya fara isar musu da zuwansa,take duk suka zubawa stairs d'in ido har ya k'arasa sauko gabad'aya Yana rik'e da wayoyinsa ahannunsa.yana d'ago da kansa idanuwansa akan Huyaam suka fara sauka wacce itama ta zuba masa nata Idon tana kallansa,kafin ta D'an Bud'e ido kad'an alamar Mamakin ganinsa da tai tana kallansa tare D'an murmushi sai Kuma ta rufe Bakinta har lokacin murmushi take Wanda ya kasance na murnar one and only yayan nasu tasowa tai daga dining d'in ta k'araso cikin falon har inda taga yaja ya tsaya ya rungume hannunsa Yana kallanta ganin ta nufoshi d'aukar sa yanzun ma rungume shi zatai ya hanata. Aikuwa dai sai yaga rungume shin zatai take yay mata Wani kallo jiki a Sanyaye Huyaam taja ta Tsaya a inda take ganin Irin kallon da yake Mata ta sunkuyar da kanta k'asa kafin ta d'ago tai masa murmushi kan kyakkyawar fuskarta da k'yar ta iya cewa.

"Well come back Yaya".ta fad'a tana langwab'ar da kanta tana kallonsa. janye idonsa yayi Daga nata Yana wuceta yace.

"Thank you". HUYAAM ta juya tana kallonsa ganin yadda ya ansa mata ta sai Kuma tura Baki gaba tana k'unk'uni tabi bayan sa sudai su Huda kallansu kawai suke suna Murmushi ganin har yanzu dai yayan nasu Yana nan da tsare gidan da yake musu bai sauyaba..da A falo zai zauna Hakan yasa Ammie tace .

"A'a k'araso ka zauna abinci zaka anan ci anan ko su tashi ne?..." Ta fad'a tana kallansa.girgiza mata kai yay Batare da yace komai ba harya k'araso dining d'in Huda tai saurin tashi ta ja masa kujera kallanta yay sai kuma ya zauna.yana furta thanks a saman lab'b'ansa.huda tai murmushi ta koma itama ta zauna ido suka had'a da Huyaam Hakan yasa ta sauke nata ta k'araso dining d'in itama dama a kujerar Dake kusa da Huda take zaune Dan haka tana zuwa taja ta zauna har lokacin bata daina tura Bakin gaba da take Yi ba shiko Afeef Bai K'ara kallantaba har ta zauna kan kujerar sai ya zamto sunyi passing juna ita da Afeef .ya Zarah ce tai serving kowa Ammie kuma tai serving ya Afeef tai selecting Irin abincin da tasan yake so Kuma yay missing ta ajiye anan gabansa. yana kallan Ammie da murmushi yace.


"Thank you mother". Ammie tai murmushi ta zauna nan suka fara cin abincin.tunda ya fara cin abincin nan Bai d'ago da kansa ba Huyaam dai tana ci tana Satan kallansa magana take son Yi Amma Kuma tana tsoro haka nan dai ta maida hankali kan Abincinta itama..shine ya fara mik'ewa bayan ya yasha ruwa ya d'auki tissue ya goge bakinsa dashi ya fita daga dining d'in ya koma falor ya zauna duk suka bishi da kallo Amma babu Wanda yay magana har Ammien ma... D'aya bayan D'aya suma suka dinga tashi bayan kowa ya k'oshi duk suka koma falon suka zauna .Huyaam ta mik'e bayan ta gama ta koma falon ta zauna kan kujerar da ya Afeef yake kai Dama akan two seater yake tana kallan sa tana murmushi.Afeef ya juyo Yana kallanta tai k'asa da murya tace.


"Good evening Yaya". ta fad'a tana Wani narke masa .ya Motsa bakinsa kad'an yace.

"Evening HUYAAM ya kike".ya fad'a Yana kallanta tana murmushi tace.

"Lafiya lau Yaya,ya hanya ya gajiya".yana d'auke kansa daga kallanta yace.

"Alhamdulillah". Ammie ce ta sauko k'asa tana kallan Afeef tace.

"Mai martaba ya shigo Yana falonsa ta k'ofar Bata yabi". Afeef yace.

"Ok".mik'ewa yayi ya haye stairs Dan zuwa falon Mai martaba huyaam ta d'aga murya tace .

"we are waiting for you Yaya saika dawo". ta fad'a cikin D'aga murya,Bai juyo ba harya gama hayewa stairs d'in.sai kuma ta mik'e da sauri ta koma kusa da Huda suka zauna tana mata magana k'asa k'asa gefe D'aya Kuma suna zaman jiransa...



#<Ø9ß HUYAAM
#<Ø9ß AZIZ CHIROMA
#<Ø9ß LAMID'O
#<Ø9ß AFEEF



07066508376________
'þFollow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD




*<Ø9ßHUYAAM<Ø9ß*



*NA*


*__NAJA'ATU UMAR FAROOQ__*



*__(MRS SARAKIES =Ø‹Ü)__*



*Bismillahirrahmanirrahim*



PAGE 1þã 9þã


___________¡&


Da sallama a bakin Afeef ya k'arasa shiga falon Mai martaba.ya sameshi zaune ya kishin gid'a jikin tuntun sarautan dake babban falon nasa,Mai martaba ya d'ago Jin sallama Yana kallan Afeef harya k'araso ya Zauna a k'asan carpet d'in idonsa na kan Afeef.duk'ar da kansa Afeef yayi cikin girmamawa yace .


"Barka da dare rankai Dad'e na sameku lafiya".ya fad'a har lokacin kansa Yana k'asa Bai d'ago ba.mai martaba ya gyara zamansa Yana kallan Afeef da kyau yace da kulawa.

"Lafiya lau Alhamdulillah Muhammad ya ingiland d'in fatan kadawo lafiya?...". Afeef yace cikin girmamawa.


"Alhamdulillah rankai Dad'e"Mai martaba ya Jin Jina kai yace.

"Masha Allah! ya company Kuma? kodan ina kallan komai ma ta system kuna k'ok'ari sosai..."sai a sannan Afeef ya d'ago Yana kallan Mai martaba da kyawawan idanuwansa Wanda suka kasance kamar ruwa saboda yadda suke garai dasu yace cikin nutsuwarsa a Koda yaushe.


"Lafiya lau Alhamdulillah Abba".Mai martaba ya Jin Jina kai yace. "Masha Allah!, sai Kuma ya cigaba Yace. "Kun gaisa da Babanka turaki kuwa? wambai dai nasan baya nan?..."Afeef yace. "Eh! mungaisa d'azu a masallaci rankai Dad'e".Mai martaba ya Jin Jina kai yace. "Masha Allah Hakan yayi kyau Allah yay muku albarka". Afeef ya ansa da Ameen,sai Kuma yace.

"Allah ya tai makeka ka duba budget d'inmu na new year Dana tura Maka ta email kuwa?Ina so ne tunda na dawo muyi komai a gida kawai...."Mai martaba yace. "na gani komai yayi Muhammad amma tunda yanzu kana gida zamu sake zama in Sha Allah in yaso sai a sake wasu tsare tsaren, sannan company kullum samun cigaba yake Allah yayi albarka yasa afi haka". Afeef ya ansa masa da Ameen.basu Dad'e ba Sosai suna magana ba Mai martaba yace yaje ya huta shida ya dawo daga tafiya yana buk'atar ya huta, Babu musu Afeef yaywa Mai martaba sallama sannan ya fito daga falon gabad'aya.su huyaam suna Zauna har lokacin Basu bar falon ba Ido Huyaam ta zuba masa har ya k'arasa saukowa downstairs d'in gabad'aya Batare da ya Kallesu ba tun kallan farko da Yay musu .ganin zai nufi b'angaren sa Bai musu magana ba yasa Huyaam tai saurin cewa.

"Yaya ka dawo kuma shine zaka tafi?ta fad'a cikin shagwab'a..." Kamar bazai tanka tab'a sai Kuma ya juyo yana kallonta yace cikin yanayin muryarsa. "Eh". atak'aice .Huyaam tai saurin cewa "To Yaya Ina tsarabarmu take?...."yace. "Saida safe".tai murmushi tace.

"Tom Allah ya kaimu".nan ko Batasan tun dawowarsa aka shige da kayan d'akin Ammie ba, Bai ansa ba ya juya Yana kallan Ammie da take masa magana tace.


"Ya kamata kaje kan ka huta Afeef tafiya daga ingiland zuwa Nigeria ba nan bace..." Ya Mutsa bakinsa kad'an yace.

"In Sha Allah! good night". Ammie tace.

"Okay good night,Allah ya tashe mu lafiya".ya ansa da Ameen su Huyaam duk sukai masa saida safe sannan ya juya ya haye stairs d'in b'angaren su Yana ansa musu,dama tuni ya haidar ya bar wajen tun lokacin da sukai dinner, su muneefa ma tun bayan da Afeef ya shiga b'angaren Mai martaba sukai shige D'aki sukai bacci.. bayan tafiyar Afeef Ammie na kallan su Huyaam ganin k'arfe shad'aya ta wuce yasa tace musu .

"To Kuma tashi Haka nan kuje ku kwanta ko?...". gabad'ayansu suka mik'e sukai mata sallama kowa ya

Please Login or Register in order to submit comment