Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

isasshen barci a ƙalla na awa goma sha ɗaya kowace rana. Bayan munyi wanka da brush mun fito ya ciro kayan barci a wardrobe ya saka min, sannan shima ya fita. Babu wani jimawa ya dawo cikin nasa kayan barcin harna kwanta ma ni. Fitilar ɗakin ya rage shima ya hawo saman gadon yana mai kwantar da kansa a saman filon da nawa yake. Tare da rungumoni jikinsa sosai. Ajiyar zuciya na sauke a hankali, dai-dai lokacin da yake kai hancinsa saman wuyana yana busa min numfashinsa da shinshinar wajen. Da sauri na ƙanƙame hannunsa dake saman cikina.
“Kin fara barci ne?”.
Kaina na girgiza masa.
“Bayan an kawo amarya ɗakinta, angonta ya bata kazan al'ada. Sunyi sallan godiya ga UBANGIJI miya rage kuma?”.
Jinai gaba ɗaya na daburce musamman yanda yake maganar a cikin kunnena da shinshinar sa yana kuma busa min numfashi duk a lokaci ɗaya. Muryata na rawa na ce, “Ba komai sai suyi barci su huta gajiyar biki”.
“Faɗi gaskiya dai?”.
A shagwaɓe na ce, “Da gaske”.
“Bashin kazan shi fa?”.
Ya sake faɗa cikin salon ruɗa min jiki. Da ƙyar na iya furta, “Ai ba bashi bane ƙyauta ne na tarba”.
“Ni dai nawa bashi ne a biyani”.
Ya bani amsa yana birkitoni jikinsa gaba ɗaya. Bamma san na shige ba kawai na ƙanƙamesa ina masa kukan shagwaɓa da faɗin wannan ai wayone kawai....

💙🩸💙🩸💙

Tari ne ya hanata sukuni cikin dare, ga barci ta kasa saboda abubuwa sunma zuciyarta yawa matuƙa gaya. Gashi yau Ummanta ta wuce gida, tayi zaton Abba zai shigo ya kwana anan sai dai har yanzu babu shi babu alamarsa. Tashi tai ta shiga bayi, kawai sai tarin ya sake sarƙeta. Sai da tayi sosai hannunta a saman bakinta. Tana samu ya tsagaita ta janye hannun mi zata gani. Jini a cikin hannun nata. Wani irin tsargawa zuciyarta tayi. Tai tsai tana kallon jinin al'amarin kamar a mafarki. Jini fa? Mike nan? Mi hakan ke nufi?. Jitai gaba ɗaya tana neman susucewa ma. Tuni ta zame jaɓar ta zauna a ƙasan bayin wani zufa na keto ma illahirin jikinta dake tsumar rawa. Ta jima zaune a wajen batare data san makama ba. Kafin tai ƙarfin halin tashi ta wanke hannunta da bakinta da fuskarta ta fito. So take ko kuka tayi kam yanzu amma hakan yaƙi yiwuwa. Haka ta ɗauki waya batare da duba ƙarfe nawa ba tai kiran Ummanta. Cikin alamun mai barci ta ɗaga daga can, sai kawai ta sakar mata kuka. Hankali tashe Umma ke tambayarta lafiya. Da ƙyar ta iya mata bayanin abinda ya farun. Ita kanta Umman daga can duk ta gigice. Sai maimaita kalmar, “Jini! Jini fa da Jalilah. Miya kawo jini kuma daga tari. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un na shiga uku ni Larai. Kinga yanzu dai ki kwantar da hankalinki dare ya riga yayi, kuma ko mijinki kada ki faɗawa da sassafe zanzo muje asibiti kinji ko”.
Mom na sharar hawaye ta ce, “To Umma sai kinzo”.
Koda ta yanke wayar sai ta faɗa saman gado kawai ta saki kuka, dan bata da abinda ya rage mata kuma sai dai kukan kawai. Al'amarin yaran nan su Samraah da Haihuwar nan ta Halime yayi masifar tsaya mata a zuciya fiye da komai. Dan shi kansa Musaddiq yaron gaba ɗaya ya sauya ya canja tamkar bashi ba. Sai ka ɗauka ama can ƙasar wajen yake rayuwa ba watanni kawai yay da tafiya ba. Hafizzullah ƙaraminsu na baya-baya da bama ta damu da shi ba shi kansa yaron baka gajiya da binsa da kallo yanzu. Balle kuma babbar giwa. Yarinya ƙarama jiba yanda take gara kan babban mutum irin Maash da manyan ƙasa ma ganinsa garesu aiki ne babba. Ai dolene ma a wannan al'amarin akwai aikin asiri. Bata yarda da tsohuwar nan ba Gwaggo Gudidi. Akwai abinda suka nemawa yarinyar nan ta mamaye Maash da danginsa. Kuma wlhy sai ta tona mata asiri dan sai inda ƙarfinta ya ƙare auren nan sai ya tarwatse. Bari dai tasan inda Baby take tukunna”. Sai kuma hawaye sharrrrr.....

Hummm Mom! Mom!! Mom!!!!!!🤨


❣️❣️❣️❣️

Barci na sha sosai da safe dan tun bayan sallar asuba dana koma ban tashi farkawa ba sai sha ɗaya. Nayi mamakin ganinsa gefena shima yana barcin. Sai duk ya bani tausayi. Babu wanda baya buƙatar hutu a rayuwarsa. Sai dai kawai dan babu yanda za'ayi dole a haƙura. A gefe mutane sha'awarsa suke ya tara, a rayuwarsa kam cike take da ƙalubale da buƙatu kamar kowa. Na tabbatar inda zai samu dama zai kwanta a gida ya huta koda na tsawon sati ɗaya ne. Amma sam bashi da wannan damar. Koda ya gwada yin hakan bashi yiwuwa garesa, ni kaina matar tasa lokacinsa ƙayyadajjene a gareni. Numfashi na sauke a hankali, tare da kai lips ɗina saman small nashi na sumbata. Sai kuma na shige jikinsa kawai na rungumesa sosai. Saukar hannunsa a saman kaina, da yanda ya tura yatsun cikin gashin yasa na sauke ajiyar zuciya mai nauyi. Muryarsa a raunane cikin yanayin wanda ya tashi a barci ya furta, “Kin tashi?”.
Kaina na jinjina masa tare da sake shigewa jikin nasa na ce, “Amma kai bana son ka tashi yanzu”.
“Why?”.
“Saboda ina son ka huta Please. My Hot wlhy jikinka na buƙatar hutu sosai. Ka duba hanlin daka shiga wata huɗu da suka wuce saboda stress. Shike nan kullum kai ina zaka neman kuɗi, ina ka dawo neman kuɗi. Daga jirgi sai zaman mota. Ko lokacinka bana wani samu. Please kuna hutawa mana, duka rayuwan nawama yake wai. Mu gama nema da tara dukiyar mutuwa ta zo ta tsamemu a cikinta mu tafi kamar ba'a taɓa yinmu ba. Sai ma mun dace da haihuwar ƴaƴa na ƙwarai ne zamu tafi mubarsu da dukiyar su mana addu'a, wasu bishashar gabansu kawai itace damuwarsu. Please mu kasance tare kawai ni basai kaje ko ina ba”.
Na faɗa ina sake shigewa cikin jikinsa sosai. Shima sake ƙanƙameni yay yana sauke wasu irin ajiyar zuciya a jajjere. Kamar yanda nai tsammani baice komai akan batun ba. Sai taimaka min da yay mukayi wanka. Bayan mun gama kimtsawa falo muka dawo, banyi mamakin ganin an kawo mana abinci ba sai dai naji kunya dan daga gani daga gida ne. Haka na zauna muka karya koma nace ni na karya dan shi kam bana ɗaukar cin abincinsa cin abinci. Yanda bai nuna zamu bar gidan ba nima sai nake jin daɗin zama a cikinsa. Salla kawai ke fitar da shi. Ina ganin kiran su Aunty Falaq naƙi na ɗaga dan nasan tana can ta haɗa kai da Fahad iya shege zasu min. Hafizzullah dai gida muka barsa yaga Yaya Musaddiq ya nane masa.
Ba ƙaramin farin ciki na tsinta kaina a ciki ba da zaman gidan nan na yau. Sai la'asar muka fita, nazata ma gida zamu koma sai naga mun nufi wani waje daban. Ashe gidan Sheikh Muhammad ibn Khalipha Al-Hussain muka nufa. Acan muka samu su Ummie. Aiko sai naji duk na daburce. Ga Aunty Falaq ta sakani gaba da tsokana. Ummie dai da Mama murmushi kawai suke. ALLAH ya taimakeni Fahad ya shigo tare da Bahijja sai tsokanar ya koma kansa. Har dare muna a gidan Malam, koda muka baro can gidan dai muka koma ni da shi su Ummie kuma suka wuce can. Yau kam a ɗakinsa muka kwana, katifa ce kawai a cikinsa ƙatuwa. Nan ɗin ma mun kasance cikin farin ciki sosai. Washe gari babu barcin safe mukai shirin tafiya Gwarzo. A gidan Abba muka haɗu da su Ummie, nayi mamakin ganin harda Mom, sai dai daga gani bada son ranta bane ba. Dan ina ganin Abba na mata masifa, ga Ummanta tsaye galala tana bin Abban da kallo.
Mota duk muka shiga, dama shi Maash tunda ya fito ya gaida Abba ya koma ciki abinsa. Su Ummie kam bama su fito ba. Wajensu Gwaggo ta shiga. Aunty Falaq da mijinta sai Yaya Musaddiq. Hafizzullah da Fahad motarsu daban. Ni da uban tafiya sai TJ dake jan mu. Abba shi da Mom da su Bibaa sai Kawu Jafaru da muka ɗauka a hanya. Gaba da bayanmu motar guards ce. Ɗan kwanciya nayi a jikinsa dan shi yanata aikinsa ne a laptop. Tun ina kallonsa ina cin chocolate ɗin hannuna harna fara barci. Sai da ya ɗan motsani zai gyara min kwanciya na ɗan buɗe ido. Lumshe mun nasa yayi ya sake buɗewa da faɗin, “Sleep” akan lips ɗin sa. Maida idanun mai kawai na rufe dan barcin nake ji sosai.......✍️




_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑯𝒖𝒏𝒅𝒓𝒆𝒅 & 𝒐𝒏𝒆_


*_Wai ni Balki ina duk masoyan Bilyn Abdull ɗin nan dake a manhajar Instagram da TikTok ne?🤔? Kai jama'a gaskiya da kunya ace account na Bilyn Abdull a Instagram da TikTok iya kar fallowers ɗin kenan🥲😣. Ina masoyan facebook ɗin nan dana WhatsApp, Please a fito mana ai fallowing ɗina. Accounts ne na Bussines ko bazaki/zaka saya ba zakaga abinda ya burgeka ko kalarka ka nema a inda kake. Maza ku garzayo BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING kodan kashe kwarkwatar idanunku ku more kallo iya kallonku da kaya ƴan yayi cikin farashi mai sauƙi da rahusa. Muna bada sari, muna adashen gata, muna sai da ɗai-ɗai. Ka gani su burgeka, ka saka ka birge mai kallonka sai Bilyn Abdull online shopping. Bari muga akwai ƙaunar kodai-kodai....😉🫣. Ga link nan naga accounts ɗin nan biyu kamar zasu fashe da fallowers 😘😘😘😍😍👍🏻👇🏻_*.

*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

_Ina masu son zuwa ganin likita ko yawon buɗe ido ƙasar Egypt?. To ku garzayo munada hanya mai sauƙi ta sama muku sauƙin tafiya cikin ƙa'ida da bin dokar ƙasa. Katafi anan cikin aminci, ka dawo kuma cikin aminci. Wajen kwananka a can zamu tanada, asibitin da zakaga likita duk zamu tsaya maka da tsayawar UBANGIJI. Hakama yawon hutawa zamu zame maka jagora. Kai ko hanyar zuwa domin sayo kaya duk muna da ita. Kai dai kawai kazo garemu kaga aiki da cikawa da iznin ALLAH. 09032345899. A nememu tanan ga masu buƙata, dan ALLAH serious bama son latsi ko wasa dan ba wasan muka fito ba 😂😍👍🏻._


......Mun iso tushe asali abin alfahari. Tarbar da muka samu ya sake tabbatar min da ansan da zuwanmu. Dan mun sami gidan Kawu Musa cike da dangi ƴaƴa da iyaye kamar ba safiya ba. Bayan gaishe-gaishe da ƴan koke-koken tuna mahaifinmu suka sake neman gafarar Mama Balki da Falaq. Kai tsaye sukace su sun yafe komai ya wuce. Suka kuma nuna farin cikin kasancewa a cikin ƴan uwa da yanda aka musu tarba ta mutuntawa da nuna ƙauna. Falaq nata kuka dan ita kaɗai tasan a kalar farin cikin da take a ciki yau ɗin nan. Abinda ta gama fidda rai da samunsa yau gata tsundum a cikinsu wato dangin mahaifinta, kuma kowa na nuna mata soyayya da ƙauna kamar za'a cinyeta dan kulawa, hakama little Awwab kowa nata ma yaron addu'a.
Su Kawu sun damƙa mata gadonta a hannu, yayinda Ummie ta damƙa mana alƙawarin mahaifinta. Sai zuciyar Abba ta sake karaya yau ma harda kukansa yana bamu haƙuri akan kuskuren da yay na salwantar mana da namu hakkin dake a hannunsa na mahaifinmu dana mahaifiyarmu. Dan gona ɗaya ta rage itama dan tana a hannun Kawu Sabi'u ne yana nomata shiyyasa Abban bai sayar ba, Mom kuma bata san da ita ba. A gaban kowa ya faɗi Mom ce duk ta dinga saka shi yin hakan, shi kuma a lokacin wlhy baya gane komai sai bin umarninta da sabon faranta ma zuciyarta. Kuka ta sanya masa wai ya kawota cikin danginsa dan ya tozartata ashe su sake ɗaukarta a wulaƙance. Babu wanda yabi takanta dama tunda muka zo duk ta kasa sakewa saboda da can ba zuwa take cikinsu ba, ba barin ƴaƴanta take su zo ba. Idan kuma su sunje ta wulaƙantasu da nuna musu ƙyama.
Dangin su Mamanmu ma da mukaje kasa sakewa tayi. Can ma mun samu tarba ta mutuntawa da girmamawa. Haka muka kasance cikin farin ciki a tsakkiyar danginmu. Sai naji kamar a barmu muɗan kwana amma nasan uban gayyar ba yarda zaiyi ba. Dan koda naima Ummie magana sai tace nayi haƙuri idan na haihu ita da kanta zata tsaya har sai nazo nayi sati da ga ni har Falaq. Na ɗan ji sanyi da jin hakan, falaq ma nata murna dan tana son zuwa ta kwana ɗin ko dan sanin kowa yanda ya kamata.
Yini guda muna a can, dan sai bayan sallar la'asar muka barosu suna kewarmu muna kewarsu. Ga uban alkairi naban mamaki da Maash yay musu. Ni kaina sai da naji hawaye sun cika min ido da alkairin nasa. Gashi an tsaida magana gobe idan ALLAH ya kaimu su Kawu zasu zo akai komai na Yaya Musaddiq dan Abba yaje yayi magana da iyayen Ruƙayya sunce su babu wata damuwa suzo kawai tunda dama sun san da maganar Musaddiq ɗin. Sai da muka raka su Abba har gida sannan muka wuce muma. Yau dai kam wajen su Ummie muka wuce. Gajiyar da kowa ya kwaso yasa ba'a zauna falo ba duk muka shige ciki. Ni wankan ma sai da tainakonsa nayi, dan barci kamar zan zube ƙasa nake ji..

WASHE GARI muka samu baƙuncin abokan aikina su Ruƙayya. Abin mamaki harda MD da kansa. Hayatu ne ya saukesu a falon baƙi. Aka kai musu kayan tarba kafin na kimtsa na fita tare da boss. Naji daɗin hakan da yay min, gashi maƙale da hannuna har muka shiga falon ko kunyarsu bai ji ba. Har su Ruƙayya sun miƙe da nufin zuwa su rungumeni suna ganinmu tare sukai surrender. Murmushi na musu cike da nuna jin daɗin ganinsu. Mutuniyata dai sai sinne kai take nasan kunya ce ta isheta. Niko sai na basar na haɗa su duka na nuna jin daɗin ganinsu. Cike da girmamawa MD da su Usman suka gaida Maash, nima muka gaisa harda cemun wai ranki ya daɗe. Ɗan harararsu kawai nayi bance komai ba. Kada na tanka cibi ya zama ƙari dan kafin mu fito harda gargaɗi a kan na kula yanzu ba da bace kada naje ina musu murmushi tunda harda maza. Ni dariya ma ya bani, amma dai na amsa dan a zauna lafiya. Mun ɗan taɓa hira da duk dai mai alaƙa da aiki ce. Shi dai baya saka mana baki sai idan yaso dan kansa. A hirar ne suke sanar min ashe MD yanzu baya wajen, an ɗan samu rikice ne ya ajiye aikinsa. Station ɗin ma yanzu neman durƙushewa take saboda sabon MD ɗinsu bashi da aiki sai wulaƙanta mutane. Ga son yaɗa labaran sirrin mutane, yanzu haka muma wai akan video da yake yawo a media na sayen agwalima da Yaya Awwab yayi yana nan yana shirya abu a kansa. Shiyyasa ma sukai azamar zuwa su gammu tun kwana biyu da suka wuce amma basu samu damar hakan ba sai yau.
Maimakon Maash ya tanka akan batun sai ya shiga yima MD tambayoyi akan ainahin masu companyn. Cike da girmamawa ya dinga bashi amsa. A mamakin mu da zasu wuce sai kawai yace MD ya fara shirin komawa aiki on Monday. Ba su ba hatta ni sai da na kallesa. Amma sai ya basar. Bayan wucewarsu naso muyi maganar sai bata yiwu ba saboda zuwan Yaya Musaddiq. Shi kuma suka fita shi da Hayatu. Bayan la'asar koda suka dawo ya shigo ɗaki na biyosa da ruwa sai na samu ya shiga wanka. File ɗin daya ajiye a side drawer na ɗauka ina dubawa dan haka kawai yaja hankalina ganin tambarin gidan TV ɗin mu. Ba ƙaramin razana nayi da ganin sunana ba matsayin mamallakiyar gidan tvn. Zufa naji tana keto min, da ƙyar na iya controlling kaina na maida na ajiye yanda ya ajiye abinsa. Koda ya fito ban nuna masa na gani ɗin ba sai taimaka masa da nayi ya kimtsa muka fito falo dan yace zai ci abinci. Koda ya kammala cin abincin kuma hira da su Ummie dake falon ya ɗauke hankalinsa. Sai kuma ga kiran Uncle Abdullahi yana sanar musu ai ALLAH yay ma Arwa rasuwa yanzu babu jimawa. Ashe yarinyar jiyya take sosai zuciyarta ta kumbura. Sunƙi sanar mana ne saboda kunya da nauyin abinda mahaifinsu ya aikata mana da nata iyayen. Shi kuma Maash ko shigowa yay ƙasar baya zuwa asibitin ta yanda zasu gansa. A ɓoye yake zuwa ya duba Paah kawai ko shi Paah ɗin ma bai san da haka ba. Harga ALLAH bai taɓa maida hankalinsa kan yarinyar ba dan shi yama manta da ita sam. Iyayenta kuwa dama bai yaɓa sha'awar dubasu ba da Kakansa. Paah ɗin ma dan ya zame masa dolene yana kuma fatan sauke hakkinsa dake kansu matsayin mahaifi. Shiyya dukkan ɗawainiyar asibitin shike ɗaukar nasa batare da shi kansa Uncle Abdullahi ya sani ba. Dan bai hana a amshi kuɗinsu ba, amma yace su ajiye duk randa aka sallami Paah ɗin su basu abinsu.
Wannan rasuwa ta shigemu. Dan haka a ranar muka fara shirin wucewa dan Ummie ta roƙo Uncle Abdullahi da a jinkirta jana'izar har zuwa safiya ayi a Mansion. Ita yarinya bata da laifi, bata san komai ba akan abinda ya faru itama tsintar kanta tayi a tsakanin hakan. Idan ma za'azo dubi ta wani fannin ita aka cutar Haka kuwa akayi bayan sallar isha'i jirginmu ya wuce Lagos badan mun shirya hakan ba. Dan sati guda muka zo da niyar yi a Kano. Sai dai kana naka ne ALLAH yana nashi. Daga airport dai duk gida muka wuce, kowa kuma makwanci ya nema domin hutama rayuwarsa. Sai washe gari bayan sallar asuba aka kawo gawar Arwa gidan. Dangin iyayenta guda biyu sun iso daga ƙauyensu kasancewar tunda wancan zancen ya fasu ashe sunzo dama. Sai dai Uncle Abdallahi ya hanasu zuwa Mansion, da suka dawo kuma a lokacin mu mun wuce Spain. Mama Balki tai mata wanka da kakarta data haifi Hajiya ƙarama. Aka shiryata aka kaita makwancin ta na gaskiya. Duk da Arwa yarinya ce sannan uwarta kawai ta sani a gidan mutuwar ta shigi su Mama Balki sosai. Ita Ummie ba wani shaƙuwa sukai ba amma taji rasuwar. Ni kaina da ban taɓa damuwa da shirgin yarinyar a gidan ba sai da rasuwar ta dakeni. Hakama Maash bai dai ce komai ba face yimata addu'a amma nasan koyaya zai ji, dan yarinyar harga ALLAH tana masa kallon ɗan uwane kamar uba ɗaya. Duk da itama ya jima da fahimtar take-takenta na son shi. Abin mamaki sai ga su Azizat sun zo daga Niger suma a washe gari. Azizat tayi kuka sosai dan kowa yasan a gidan suna shiri matuƙa da Arwa. Duk da shirin nasu baya wuce akan a ƙuntatama Malika ko yanda za'a shawo kan Maash dai. To koma dai yayane ita dai ta tafi ta huta kuma. Sai fatan ALLAH ya gafarta mata kurakuranta da namu dana iyayenmu baki ɗaya...
Rasuwar Arwa tayi matuƙar jijjiga iyayenta. Musamman ma Hajiya ƙarama. Dan a wannan ranar likitoci kwana sukai kanta tanata wani irin kuka da aman jini. Ɗayan ɓarin jikin ya ida mutuwa. Dama ga allurar poison ɗin da Prof yay mata ta fara aiki kaɗan-kaɗan kamar yanda wadda tai masa shi tuni ma ta gama masa illa. Haka dai aka sakata barcin dole har washe gari da aka bizne Arwa bata farko ba. Shima dai Commondo yaci kuka rurus. Dan duk da bai taɓa nuna damuwarsa akan ƴar tasa ba yana matuƙar sonta da ƙaunarta. Yana gani ko wahalar da ya sha a rayuwa zata tafi a banza a ƙalla dai ya bar mai masa addu'a. Dan koda ta masa abinda ya sakashi shiga a wannan halin bai taɓa jin soyayyarta ta ragu masa a zuciya ba. Ashe itace zata fara tafiya ta barsu, inama shine ya tafi ba ita ba. Kaicon wannan mummunar rayuwa tasu mara ƙyaƙyƙyawan tarihi da alƙibalar gani a koya........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑯𝒖𝒏𝒅𝒓𝒆𝒅 & 𝒕𝒘𝒐_


......Har akai sadakar uku jikin kowa dai a sanyaye babu wani ƙarfi. Dangin su ma sukai shirin kama gabansu. Dan sun san anmusu halacci. ALLAH sarki Ummie, bata barsu haka ba sai da ta musu alkairi. Suka tafi suna mai sanya mata albarka da addu'oin fatan alkairi har ma damu kammu. Sun wuce da safe gidan ya sake komawa shiru. Dan su Azizat dama ba'a nan suke kwana ba can wajen mahaifiyarsu gidan Prof da safe su zo su koma can da yamma. Batare da mun sani ba washe gari akace mana sun wuce. Ita dama Hajiya Mammah tun randa akai jana'iza da tazo bata sake zuwa ba saboda kunya ne ko munene dai oho mata. Da yammacin ranar tafiya ta tasowa Yaya Awwab, haka ina fushi da kumbure-kumbure suka wuce shida PA ɗinsa da ƙandarariyar baturiyar nan dana tsana. Yanda take wani kwarkwasa da iyayi agaban Yaya Awwab na ƙona min zuciya. Bandai ce komai ba amma ALLAH idan bata kiyayeni ba sai na mata zanen yarabawa. Bayan wucewarsu gidan sai ya sake koma mana shiru, sai kawai na tattara na koma sashen Ummie dan bazan iya zaman sashen ni kaɗai ba. Ashe can ma Aunty Falaq ta gudo wajen Ummie ɗin. Dariya Ummie taita mana wai mu ragayen mata ne. Daga maza sun tafi sai mu gudo wajen Mamanmu. Shagwaɓa muka dinga mata tana biye mana. Ita dai Mama ido kawai take saka mana.
Muna waya da ƴan Kano, Musamman Yaya Musaddiq da Hafizzullah da Abba. Sai aunty Halima sabuwar ƙawarmu. Dan yanzu mun ɗinke da ita kamar ba matar Abbanmu ba. Bahijja ma na Kano maƙale bata dawo ba. To batun dawowar tatama dai sai da aure a kanta. Dan an gama tsaida magana bikinsu za'ai kawai da Fahad a huta kafin mu koma. Sai yanzu ne ma nake jin batun komawar tamu Spain. Harga ALLAH na ɗauka mun dawo gida kenan. Kasancewar a gari ɗaya Abba ke cemin an saita bikin Yaya Musaddiq da na Fahad ɗin rana ɗaya. Nan kuma

Please Login or Register in order to submit comment