Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Dai-dai nan aka fara fito da mutane daga kowanne sashe na gidan ana maidasu sashen masu aiki mazansu da matansu. Ashe tuni ma yaransa sun gama zagayemu da sunan masu decorretion batare da an farga ba. Sai dai ashe nice mai tunanin ba'a fargan ba. Shi gogan yana sane da duk motsin su tunda suka fara aikin. Sai dai ya barsu a ƙarƙashin nasa shirin shima. Ganin ya nufi ƙofar falon shima a fusace muka take masa baya ni da Hayatu da Fahad. Zaune muka sameshi yay zaman ƙasaita, yayinda ƴan iskansa suka zagaye Maash. Muma muna shiga suka zagayemun. Su Azizat dake falon duk sun rikice suna kallon kakan nasu a firguce.
Fito da duk wanda ke sashen yasa ayi. Kusan su Ummie sune ƙarshen fiddowa. Sai Hajiya ƙarama da tai sumar tsaye. Dan ta fahimci shirin wannan makirin tsohon ya danne nata kenan. Sai dai koba komai ta ribantu itama ai, sannan tanada tata nasarar. Ƙananun kukan da su Arwa keyi a wajen yasa ƴan iskan daka tsawa tare da yin harbi. Sake rikicewa falon yayi sai da ƙyar suka lafa. Ta gefen ido na kalla Maash da aka fi zagayewa da bindugun amma babu ko ɗar a tattare da shi. Sai ma tsaiwar ƙasaita ta yay bayansa jingine da bangon falon ya harɗe ƙafafunsa waje guda hannayensa duka biyu cikin aljihun wandonsa. Gefensa Fahad ne shima dai an zagayesan kamar yanda akaima yayansa. Sai Hayatu da ni ma da akaima ƙawanya tun a farkon shigiwarmu. Daga can ma Ummie sun zagayeta haka ma Hajiya ƙarama. Hajiya Mammah da itace ƙarshen fiddowa kasancewar tana ɗaki kwance tana jiyyar hannunta suna isowa wajen ihu ta fasa da faɗin, “Mun shiga uku Baba!”.
Gilashin idanunsa ya cire yana mai binta da kallo. Bakin baya iya shiru cikin rawar laɓɓa ta sake faɗin, “Baba wai mike faruwa ne haka? Wane kalar bala'i ne wannan kuma ni Nafisatu Adams ƴan fashi da ranar ALLAH. Ni wlhy duk na ma rikice ko kidnapping ɗinmu akayi....”
“Ko kuma yay kidnapping kansa ba”. Muryar Ummie ta ratsa kunnen kowa a wajen a bazata. Duk kallonta akayi dan dariyarta take hankali kwance idonta akan Baba prof.. da mamaki Hajiya Mammah ta ce, “Ummu-Hidaya! Ban gane ba. Baba ne fa taya zai yi kidnapping kansa kuma? Kina ganin mutane sun zagayemu da bindigu kamar babu hukuma a ƙasar”.
Haɗe fuska Ummie tayi da watsa ma Hajiya Mammah ɗin wani kallo. “Kamar yanda kika gani mana Nafisa. Ai uban naku lusari ne ba jarumi bane. Sannan mata maza ne ba namijin gaske bane. Dan namijin gaske a filin daga baya riƙe garkuwa. Amma shi harda ƴan baranda ya zo. Adamu kenan, a tunaninka zuwa da waɗan nan wawayen dake hura hanci da bindigu a hannu zaisa ka amsa sunan NAMIJI a gabana? Ai kazo kai kaɗanka ne zan maka kallon ɗan rakkiyar mazan ma. Ka manta na faɗa maka, na faɗa maka in dai ni jinin Ibrahim ce da izinin UBANGIJI sai ka ƙare rayuwarka a ƙarƙashin ƙafafuna kamar yanda tun farko kake a ƙarƙashin ƙafafun mahaifina. Ai na faɗa maka dama bazaka taɓa tsira ba, kuma kafin ka mutu mutuwar wulaƙanci sai ka biya bashin CIN AMANAR da kayi ma mahaifina.....”
“Ƙarya kike ƙaramar ƴar iska ni ba MACI AMANA bane. UBANKI shine ya fara CIN AMANATA. dan haka shine MACI AMANA, BUTULU, MARA ADALCI, mai son kansa kawai. Shekaru ashirin da shida na ɗauka ina masa bauta da durƙusawa ƙarƙashinsa, alhalin dukiyar da yake taƙama da fankama da ita dani aka tarata. NI!! NI!! nan Adams. Yazo ƙasarmu a matsayin matsiyacinsa faƙirin da baida banbanci da mabaratan kan titi kafiri mai bautar gunki. Mune muka tallafesa ya zama mutum, muka buɗe masa idanunsa ya fahimci a inda yake, musamman ma NI! NI ɗin nan. Uwata ta zama sanadin shigarsa musulinci. Babu irin wahalar daban masa ba, duk da shekarun daya bani ba wasu masu tazara bane haka nake kiransa YAYANA ko YALLAƁAI, idan ya buƙaci aikena jikina har rawa yake domin son ganin na cika masa fiye da yanda ya buƙata. Ko kallon banza wani ya masa zafi nakeji a cikin zuciyata har na ɗauki mataki. Nasha yin faɗa da abokan aikina idan suna gulmarsa. Idan yana ciwo nine tsaye a kansa har ya samu lafiya. Hatta da wankin kayansa da gyaran ɗakin barcinsa kullum nine keyi batare da jin komai ba a raina. Kafin ya furta yunwa na sayo abinci na ajiye masa, haka nake girmamashi a duk wani motsinsa tamkar yayana uwa ɗaya uba ɗaya. A duk lokacin da naga wani abun cigaba da zai ɗaga darajar Company bana baƙin cikin kawo masa shi. Kuma haka za'a gwada a samu nasara. Amma duk da wannan hidimta masan dana ƙare ƙuruciyata inayi a matsayi ɗaya yake kallona har a randa zai bar duniya. Wato YARONSA. Yaronsa da darajarsa kawai yayi aiki a biyashi sai idan wani ya taso a sake nemansa yayi ya biyashi da ƴan kuɗaɗe.
Butulci na farko da tabbatar min shiɗin BAƘON HAURE ne mai rama ALKAIRI da SHARRI shine haɗa baki da budurwata ya turani karatu ƙasarsa bayan tafiyata sukayi aure saboda shi ɗin TSINANNE NE kafirin banza. Na danne zuciyata na ƙyalesa saboda dalilai biyu. Na farko ina masa kallon Yaya ne da zan iya sadaukar da komai a garesa kamar yanda nake tunanin shima zai iya sadaukar min. Na biyu yaci darajar mahaifiyata daya riƙe hannu biyu take masa kallon ɗa jininta. Sai dai nayima kaina alƙawarin komai tsahon lokaci sai na hukunta Rabi'ah da kaina da shi kansa. Dan a lokacin ita nafi kallo a mai laifi, idan shi bai san ina sonta ba ai ita tasan ina sonta. Idan kuma shi bai san ana barin halak dan kunya ba ita ai ta sani. Amma abin duniya ya rinjayeta. Koda yake banyi mamaki ba kasancewar ta ƴar KARUWA mai TUWO-TUWO kuma KARUWAR.
Wasu irin hawaye ne masu zafi suka silaloma Ummie. Yayinda jikin Maash ya fara rawa na tsantsar fusata. Yana motsawa ƴan iskan nan suka sake attacking ɗin sa da bindugun. Amma duk da yasan zafa su iya harbin nasa ya mutu har lahira tuni ya watsar da su ta hanyar hankaɗe bindugun ya nufi mahaifiyarsa. Dan a duniya bai haɗa al'amarinta da kowa ba. Da sauri suka ɗana kunamin bindugun su da wanda ke zagaye da ita amma sai Baba prof ɗin ya ɗaga musu hannu yana murmushi. Kamo Ummie Maash yay jikinsa, maganar da babu wanda ke ji yake mata ƙasa-ƙasa cike da kulawa da tattali. Dariya Baba prof ya kwashe da ita kamar ba tsoho mai shekarun girma irinsa ba. Jinai zuciyata na ƙuna. Bamma san lokacin da nima na furta, “Wawa jahili”. ba
Ai gaba ɗaya waɗanda ke zagaye da ni, da wanda ke zagaye da Maash ɗin sukayo kaina...
“Duk wanda ya taɓa min MATA a cikinku wlhy! Why UWARSA ma sai tayi dana sanin HAIHUWARSA!!!”.
Razananniyar muryar Maash ta ratsa kunnen kowa dake a wajen sai da muka firgita. Dan hatta da kamaninsa sai da suka sauya. Cikin nuna Baba prof da yatsa ya furta, “Kai kuma kafi JAHILAI JAHILCI tunda har kake iya maida FARI ya koma BAƘI. WULAƘANTACCE kawai da bai san girma da kimar HALLACI ba, mai faɗa da ƙaddara ɗan son banza. Kai har kana da bakin zaman yima mutane wannan surutan banzar naka soki burutsu. Duk abinda kake lissafin ka masan ai badan ALLAH kayi masa ba, kayine daman dan ka shiga jikinsa ka cimma wata manufarka baƙin annamimi. Idan kace duk ya maka wannan, inganta rayuwarka data ƴaƴanka da yayi fa. Bai kuma ji ƙyashin ɗaukar ƴarsa ɗaya tilo ya aurama ɗanka da ke a gurɓace ba. Sannan ya kama UWARKA ya riƙe da hannu biyu fiye da yanda ma kai kake riƙon nata. Sai ka gaya min UBAN mi kake so ya maka bayan duk wannan?”.
“Ni kake zagi Awwab?”.
“An zagekan, zan maka ma mafiyin wannan ɗin ne. Dan ni wlhy tuni na daina maka kallon MAHAIFIN UBANA. Na tsaneka”
“Kamar yanda nima ban taɓa maka kallon ƊAN ƊANA ba tun ranar haihuwarka naji bana sonka”.
“Alhamdullahi hakan yamun daɗi ai, dan ka taimaki kanka wajen gane abinda yafi ƙarfinka har abadan yafi ƙarfin naka. Kai ko kunya bakaji ba a duk wannan surutan naka ka faɗi ta inada Abie ya cutar da kai...”
“Oh so kake kasan ta inda ya cutar dani mara kunya. To zakaji yanzun nan kuwa. Dan zan ko gaya maka idan ita uwarka ta gagara sanar maka. Ko aure da kake faɗin ya ɗauka uwarka ya bama Mu'azz ni na sakashi yin hakan ta ƙarfin tsiya ba hallacinsa bane ba........”✍️


Hummmmmmmmmm🏃



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕𝒚-𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_


*_Wai ni Balki ina duk masoyan Bilyn Abdull ɗin nan dake a manhajar Instagram da TikTok ne?🤔? Kai jama'a gaskiya da kunya ace account na Bilyn Abdull a Instagram da TikTok iya kar fallowers ɗin kenan🥲😣. Ina masoyan facebook ɗin nan dana WhatsApp, Please a fito mana ai fallowing ɗina. Accounts ne na Bussines ko bazaki/zaka saya ba zakaga abinda ya burgeka ko kalarka ka nema a inda kake. Maza ku garzayo BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING kodan kashe kwarkwatar idanunku ku more kallo iya kallonku da kaya ƴan yayi cikin farashi mai sauƙi da rahusa. Muna bada sari, muna adashen gata, muna sai da ɗai-ɗai. Ka gani su burgeka, ka saka ka birge mai kallonka sai Bilyn Abdull online shopping. Bari muga akwai ƙaunar kodai-kodai....😉🫣. Ga link nan naga accounts ɗin nan biyu kamar zasu fashe da fallowers 😘😘😘😍😍👍🏻👇🏻_*.

*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

_Ina masu son zuwa ganin likita ko yawon buɗe ido ƙasar Egypt?. To ku garzayo munada hanya mai sauƙi ta sama muku sauƙin tafiya cikin ƙa'ida da bin dokar ƙasa. Katafi anan cikin aminci, ka dawo kuma cikin aminci. Wajen kwananka a can zamu tanada, asibitin da zakaga likita duk zamu tsaya maka da tsayawar UBANGIJI. Hakama yawon hutawa zamu zame maka jagora. Kai ko hanyar zuwa domin sayo kaya duk muna da ita. Kai dai kawai kazo garemu kaga aiki da cikawa da iznin ALLAH. 09032345899. A nememu tanan ga masu buƙata, dan ALLAH serious bama son latsi ko wasa dan ba wasan muka fito ba 😂😍👍🏻._


......Dukkan ƙuruciyata a wajen hidimtawa rayuwarsa na ƙarar da ita, amma da yake shi kansa kawai ya sani haka ya tattare dukkan dukiyar da aka tara da gumina a ciki ya rubuce sunan ƴarsa akai da naka, kai ɗin nan ɗan mitsitsinka dama baka san kanka ba balle waninka. Niko ya haɗani da wani tsohon companyn da ya gama mutuwa ya manna min ƴan kuɗaɗe wai ya sallaman naje na gyara. Tun daga lokacin na fara tunanin ta yanda zan mallake dukkan abinda ya handame ɗin nima tunda naga kowa kansa ya sani kawai. Haka na shiga na fita na kwaɗaita masa haɗa aure tsakanin Mu'azz da uwarka. Tsabar mutumin nan shi butulune nunawa ma yay kamar bai da wannan ra'ayin. Baya son wannan haɗin saboda Mu'azz baya jin magana. Rashin jinsa yayi yawa. Bazai iya riƙe masa Ummu-Hidaya ba miye-miye. Kai ko ga ƴar gwal an haifi a Nigeria. Komai bance masa ba a randa ya kawo min wannan zantukan banzar nashi. Na koma kawai gefe na shiga na fita shege a dawowa ta biyu baima san sanda ya amince ba jikinsa na rawa. Suma duk da akwai shaƙuwa a tsakaninsu na sake ƙulle zukatansu a waje guda suka nuna suna son junansu. A zatona wannan haɗin auren zai sa ya dunƙule dukiyar ya bama Mu'azz matsayinsa na mijin ƴar tasa tilo da yake taƙama. Kokuma ya tattara duka aikin ya bama Mu'azz ɗin. Ya cigaba da jagorantar companyn. Amma shegen mutumin nan sai ya ɗauki ƴarsa ya ɗorata akan komai. Tana wata ƙasar tare da ɗana da aka maida hoto amma tana juya kan dukiyar duk da ƙananun shekarunta.
Wannan abu ya ƙara ƙona min zuciya matuƙa. Wato ni na ɓata ƙuruciyata a banza wajen hidimta masa ɗana ma zai koma ɗan amshin shata mijin Hajiya. Haba never. Tuni na je na kunno musu wutar da Mu'azz ya fara cin ubanta. Dan a lokacin data samu cikin farko ya jajibemu domin dubata da shirina naje. Na banka masa maganin da Malamina ya bani bamu baro ƙasar ba sai da ya zubar mata da cikin da ake ɗogafi da shi. Da matuƙar farin ciki na dawo a lokacin har kashi biyu kuwa. Na zubar da cikin da Mu'azz yay mata da ƙararshi data kawo min wai bata son ubanta ya sani ai masa faɗa akan neman matan da yake da dukanta da yake yi. A zahiri na amsa mata da to kawai, amma ko uhun bance masa ba. Yo neman mata sai na hanashi ya more ƙuruciyarsa ya ƙare kanta iya kaɗai kenan ma, ko kuwa tana matarsa bazai jibgi shegiya ba yanda yake so a kuma sanda yake so. A dawowar tamu ma dukkanin baya nai ina samu akan zaman nasu. Ubanta yake ci gwargwadon iko shine ma dalilin da yasa tana kammala karatun ta saka suka dawo Nigeria da zama. Duk da dai tana dojewa wai ta dawo ne tai aiki a kamfanin babanta. Ƙaryar banza kenan. Koda ta dawo ɗin nasan Mu'azz na aikata duk abinda yake acan bai fasa ba. Ban kuma tsawatar masa ba. Babban abinda ya fara saka min tsanar shegiyar yarinyar nan bayan wadda nake ma ubanta ta shafeta shine ɓoye zancen cikinka da tayi tare da wannan munafukar annamimiyar da mijinta. (Ya nuna Mama Balki) Ban tashi sanin tana da ciki ba sai da ya shiga watan haihuwa, shiyyasa ashe ubanta ya tura Mu'azz wata ƙasa aikin watanni har shida. Ni kaɗai nasan a halin dana tsinta kaina a wannan lokacin, dan haka na nutsu domin nemo mafita akan yanda ko ta haihu za'a maida abinda ta haifa lahira dan ubansa. Ƙawarta da naga tana yawan zirga-zirga a gidan ce tazo min rai. Dan haka na nemeta amma sai taƙi bani haɗin kai a lokacin da yake Lawisa shegiyar makira ce. Tata yawo da hankalina duk da barazanar da nake mata da kurari, sai da ta latsani da ƙyau har bayan an haifeka sannan ta yarda mukai magana. Wannan shine mafarin alaƙata da Lawisa duk da bata da wani ƙarfi sai idan dalili ya taso. Jawota jikina yasa na fahimci itama shegiyar tana kwana da tashi da baƙin cikin Ummu-Hidaya ɗin. Amma tana dannewa kullum tana jikinta. Kamar dai yanda nake ma ubanta wahala, itama tanata yima ƴar wahala. Duk da mun haɗe kai da Lawisa tako ina mun gagara samun nasara akan kauda kai a duniya. Dan koyaushe idon baƙar matar nan da mijinta na kanka. Ya nuna Mama Balki cikin tsana.
Tako ina sun rufe komai sun katantane. Daga baya ma sai na fahimci shi Abdul-wahab kamar ya sakama motsina ido. Dan bawai ga Ummu-Hidaya ba hatta da uban gidan nasa wanni kaffa-kaffa yake da shi idan har ina waje. Rana ta farko dana zuba ma Ibrahim wasu ƙwayoyin da Lawisa ta samo mana ta kuma tabbatar min da in har Ibrahim ya shasu bugun zuciyarsa zai ƙara ƙarfi da ga ƙarshe ta buga ace heart attack ne ya kashesa bayan na gama wahalar zuba maganin a cikin shayinsa kawai matsiyacin yazo da wani salo ya ɓarar da shi as mistake. Ya kuma katantane shi da kansa ya haɗo masa wani ya bashi a gabana. Wannan abu yamun ciwo na fara ninka tsanar da nake masa a raina tare da saka masa alamar tambaya. A karo na biyu ma dana haɗa wutar lantarki a office ɗinsa kawai bamma san ta yanda akai ba kawai shi yaje ya kama wayar ya hana Ibrahim kamawa. Satinsa guda a asibiti yana jiyya a maimakon Ibrahim. Wannan ma ta wuce bance da shi komai ba na sake kafa wani tarkon a cikin gidansa da fetur nan ma Abdul-wahab ya wargaza min. Haka ya dinga bina kafa da kafa yana wargaza min ayyukana akan Ibrahim. Daga ƙarshe na fito ƙuru-ƙuru na masa gargaɗi da barazana. Amma da yake shi taurin kai ya masa yawa sai ma ya maida abun rainin hankali, har yana wani sanar min cikin gadara wai in ma ina wani tunani a kansa ne na canja dan TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE shi ɗin ba kanwar lasa bane. Idan kuma zan shekara dubu ina ƙulla makircin kashe Ibrahim zai kasance a bashi kariya da izinin UBANGIJI. Kar kuma na ɗauka zai faɗa masa ne ya ɗauki matakin hukuma shi da kansa zai cigaba da bashi tsaro da tsarewar ALLAH batare da ya taɓa sanar da shi wanene ni ba har sai idan shine ya gano da kansa. Alwashi na ɗauka masa kan nima mu zuba ɗin, ni da shi ɗan halak ka fasa. Muka ko zuba ɗin ba tare da sanin Ibrahim ba. Tabbas Abdul-wahab ya nema zamenim bala'i a rayuwata. Dan haka na shirya shirin ƙarshe da shi a ciki dan ya cancanci irin hukuncin Ibrahim shima.
“Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un, Baba yanzu har wannan ya kai ka kashe Abie da ya inganta rayuwarmu. Shine fa sanadin barowarmu ƙauye”. Hajiya Mammah ce ke maganar cikin matsanancin kuka. Hakama Hajiya Mama da Paah kansu kawai suka duƙar suna hawaye.
Cikin kaushin murya da zafin rai Baba prof ya daka mata tsawa da faɗin, “Oh dan yayi sanadin barowarku ƙauye bada wahalar ubanku bace Nafisatu. Ko a banza yasa na kawo kun badan ya cigaba da amfanuwa da ƙuruciyar mahaifinku bane. Kar wanda ya sake katseni ki bari nakai ƙarshen zancena mana kafin kiyi alƙalanci!!!”. Ya ƙare maganar a tsawace yana wani irin huci kamar bajimin sa. Kafin ya cigaba da magana a zafafen nasa.
“Sai da na gama shirya komai sannan na tunkari Ibrahim da sigar neman alfarmar aron kuɗi da zan inganta bussines ɗina. Amma shi da yake butulu ne, kansa kawai ya sani sai shegiyar ƴar nan tasa da kai dake matsayin jikan da ni nama fisa matsayi da ƙarfi a wajenka domin ubanka na haifa. Haka ya nuna min baida waɗan nan kuɗin. Sannan ko yana da su ma bazai bani ba dan sunyi yawa. Naje na cigaba da juya na hannuna wai fara kasuwanci da kaɗan yafi albarka. Kuji min shegen makiri, shi bada manyan ya fara ba. Na zafafu ranar da ƙyar nai controlling kaina. Ban sake masa magana ba sai bayan wasu kwanaki na sake zuwa masa dai da wannan buƙatar amma na rabin abinda na nema a farko nan ma ya nuna min sam shifa bazai bani ba tunda ya sallameni. Idan ma dukiyar da nake kallo a hannunsa ce shima ba tashi bace mallakin ƴarsa ce da jikokinmu. Kam babbar bala'i kenan. Wai abinda aka tara da gumina ake min gadara da shi hahaha yaro bai san wuta ba kenan sai ya taka. Daga haka ban sake masa batun ba sai bayan kusan wata ɗaya naje masa da tayin sayen Shere a companyn nawa dan nayi amfani da kuɗin na tada companyn da ke neman durƙushewa. Abin mamaki wai azzalumin nan a wannan ɓangaren babu musu ya amince. Ya sayama ƴarsa kaso ɗaya bisa uku na Shere ɗin company na. Ya kuma biya akai duk abinda ya dace ya amshi takardu a gabana ya damƙa mata. Daga wannan ranar nai alƙawarin sai na ɗanɗanama Ummu-Hidaya azaba da wutar dalma a tafin hannunta. Matakin farko kuma shine kashe ubanta. Anyi haka da ƴan kwanaki kawai a bazata akace min wai tana naƙuda. Imagen matar ɗana nada ciki ban sani ba a karo na biyu. Hakan na nufin akwai abinda take shiryawa kenan itama ko ubanta ya kitsa mata a kaina, domin idan babu rami miya kawo rami? Ta ɓoye na farko na biyu ma haka........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕𝒚-𝒇𝒐𝒖𝒓_


*_Wai ni Balki ina duk masoyan Bilyn Abdull ɗin nan dake a manhajar Instagram da TikTok ne?🤔? Kai jama'a gaskiya da kunya ace account na Bilyn Abdull a Instagram da TikTok iya kar fallowers ɗin kenan🥲😣. Ina masoyan facebook ɗin nan dana WhatsApp, Please a fito mana ai fallowing ɗina. Accounts ne na Bussines ko bazaki/zaka saya ba zakaga abinda ya burgeka ko kalarka ka nema a inda kake. Maza ku garzayo BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING kodan kashe kwarkwatar idanunku ku more kallo iya kallonku da kaya ƴan yayi cikin farashi mai sauƙi da rahusa. Muna bada sari, muna adashen gata, muna sai da ɗai-ɗai. Ka gani su burgeka, ka saka ka birge mai kallonka sai Bilyn Abdull online shopping. Bari muga akwai ƙaunar kodai-kodai....😉🫣. Ga link nan naga accounts ɗin nan biyu kamar zasu fashe da fallowers 😘😘😘😍😍👍🏻👇🏻_*.

*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

_Ina masu son zuwa ganin likita ko yawon buɗe ido ƙasar Egypt?. To ku garzayo munada hanya mai sauƙi ta sama muku sauƙin tafiya cikin ƙa'ida da bin dokar ƙasa. Katafi anan cikin aminci, ka dawo kuma cikin aminci. Wajen kwananka a can zamu tanada, asibitin da zakaga likita duk zamu tsaya maka da tsayawar UBANGIJI. Hakama yawon hutawa zamu zame maka jagora. Kai ko hanyar zuwa domin sayo kaya duk muna da ita. Kai dai kawai kazo garemu kaga aiki da cikawa da iznin ALLAH. 09032345899. A nememu tanan ga masu buƙata, dan ALLAH serious bama son latsi ko wasa dan ba wasan muka fito ba 😂😍👍🏻._



.......Banyi magana ba dai sai shi Mu'azz ɗin na samu na ci masa ƙaniya sai da ya koma yana rantsuwar shima wai bai san da cikin ba sai da ya kai watanni kusan huɗu. Ta kuma roƙesa kada kowa ya sani idan kuma ba hakaba zata gudu tabar gida har sai ta haihu ta dawo saboda ta fahimci baya son haihuwa shine ya zubar mata da cikin farko. Na Awwab ma shiyyasa ta saka mahaifinta ya turashi wani aiki na watannin rainon cikin

Please Login or Register in order to submit comment