Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gani da ido in sha ALLAHU. Ka gani su birgeka, ka saya ka birge masu kallonka sai a *BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING*👇_


https://chat.whatsapp.com/LkRMFFQZakP55c7xK0QaMG



https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5

_____________

........“Ya zamu bar masa ke. Sai dai ya ɗauki rabi ya bar mana rabi. Ke dai ki kwantar da hankalinki kinji. In sha ALLAHU ni da Musaddiq muna nan tafe har inda kike. Dama a tunaninmu idan kinji sauƙi zai dawo mana dake gida ne shiyyasa. To amma uzirin daya kawo akan zaman naku anan yanzu dole a haƙura har sanda ya kawoki da kansa ɗin. Ni dai kawai roƙona ki kwantar mana da hankalinki, ki mance da Mansoor kamar yanda mahaifiyarsa ta buƙata, ALLAH shine shaidar mu ba laifinmu bane sune sukaƙimu. Dan a ranar ɗaurin aurenku mahaifiyarsa da kanta tazo tace sun fasa ɗanta bazai aureki ba saboda ba'a san mi aka aikata miki ba da akai kidnapping ɗinki. Babu yanda su Kawu Musa basu lallasheta ba har gwaji sukace aje ai miki amma fir matar nan taƙi sai ma cin mutunci da gori data shiga musu. Suko sun san mutuncin kansu ai, dan haka suka janye suka bama wannan bawan ALLAHn ke dan su mutuntaki da mu kammu. Dan inba hakaba wannan mugun baƙin fentin da sukai miki zaita bibiyar rayuwarki ne harma mijin ya gagara gareki a gaba”.
Sosai maganganun aunty Zakiyya suka ratsa min jiki. Mamaki da al'ajabin mahaifiyar Mansoor ya tsaya min a zuciyata. Harna kasa daurewa na ce, “Amma Aunty shi yaya akai yasanni yazo neman aurena? Ko su kawun sun sanshi ne su?”.
“To ni dai bazance ba gaskiya. Amma dai kamar naji ance shine yazo yace yana son aurenkin da kansa. Ki dai tambayi Gwaggo tasan komai kuma nasan zata sanar miki. Ko kuma shi mijin naki ki tambayesa ai bazai ƙi sanar miki ba”.
Shiru nai tsahon lokaci na kasa cewa komai. Sai kuma can na ce, “Okay Aunty in sha ALLAHU zan tambayesa”.
Nasiha suma suka min cikin lallashi ita da Yaya Musaddiq. Bayan munyi sallama na jima zaune a garden ɗin ina tunani kafin na miƙe na koma sashenmu bayan na kashe wayar na sakata a jikina. Ina shiga Aunty Sadiy ta shigo wai naje Hajiya Mammah na kirana. Idanu na ɗan waro dan harga ALLAH nama manta da batunta...

A ɗarare na tafi amsa kiran nata, sai dai cikin sa'a ina zuwa na samu wai tana da baƙuwa sun ma fita yanzun nan. Ajiyar zuciya na sauke na juya na koma ina godema ALLAH. Dan dana sameta ban san mi zance ba wajen kare kaina.

✨★✨★✨

Da ƙyar aka samu Mom ta farfaɗo. Tana kuwa farfaɗowar wasan ya koma sabo. Dan tuni Ummanta da su Baby da basa gidan sun dawo harma da wasu ƴan uwanta. Faɗa ne mai ƙarfin gaske ya ɓarke tsakanin dangin Mom da ita kanta da dangin Abba. Dan dangin amarya su dai ƴan kallo suka zama. Sai dai kuma ransu ko ɗar balle gezau akan ƴarsu bazata iya zama ba. Sai ma murna suke da rahamar da UBANGIJI yay mata na samun wannan danƙareren gida a matsayin gidan aurenta. Itama ɗin dai Halimen ko'a kwalar rigarta. Yo ita wane kalar masifa da bala'i ne bata gani a wajen Innarta ba. Sannan faɗan kishi babu irin wanda ba'ayi a gidansu. Dan kaf matan kawunanta ba su ɗaɗɗaya bane Innace ma kawai ita kaɗai a wajen Baba. Amma sauran daga mai mata uku sai mai biyu harma da mai huɗu. Kuma haka ake shan cakwakiya a gidansu gashi gidan yawa. Ita dariya ma abinda ke faruwa ke bata. Sai da Hajiya Asabe ta ƙwaɓeta daga yanda take kwasar dariya tana leƙe ta window sannan ta nutsu.

Shi dai Abba ma tuni ya fita ya bar musu gidan bisa umarnin Gwaggo Gudidi. Haka aka ci uwar sabada mata anguwa nata shigowa. Masu yima Mom dariya da ALLAH ya ƙara sunfi yawa. Dan har a cikin ƙawayen nata wasu abin ya musu daɗi. Ummanta ce data fahimci al'amarin fa shiryayye ne dan dangin Abba sun kafa sun tsare yasa ta janye Mom ɗin suka shige ɗaki. Ba'a sake ganinta ba har kusan goma na dare sai ga likita wai yazo zai dubata hawan jininta ya tashi. Babu wanda yabi takan batun kowa ya cigaba da sabgarsa. Sai ita da ƴaƴanta da Ummanta ke ƙulle-ƙullensu can a sashenta su kaɗai.

Har washe gari daga ɓangaren Mom dai babu daɗi, gashi Abba yaƙi shiga inda take tun dubatan da yaje yay na farko bai sake zuwa ba, dan yana shiga ta sake birkicewa harda shaƙeshi tana kuka da faɗin sai ta kasheshi sai dai duk su rasa. Har ita zai tozarta yama kishiya, to wlhy ya sani ya ɗakko bala'i da masifar da bazata taɓa ƙarewa ba har sai cikin abu uku ɗaya ya faru. Kodai ta kashesa, ko kuma ya saki yarinyar a yau danginta su koma inda suka fito da ita, ko kuma idan ita ta mutu. Kuma koda ta mutu yace zai sake aure sai ta dinga masa fatalwa. Abin nata kamar wasa ya nema zama babba, dan da ƙyar aka fiddo Abba a ɗakin tana neman murɗe masa jikinsa ALLAH dai ya taƙaita masa wahala akwai babbar riga tare da shi.
Su dai ƴan uwansa da dangin amarya sabgar gabansu suke hankali kwance dan basu san mike faruwa a cikin ba sai da su Gwaggo Gudidi suka fito da Abba ne suke jin komai. Aiko fa kowa ya shiga ALLAH wadarai da wannan baƙin hali na Mom, daga nan kowa ya sake ɗaura ɗammara a kanta. Dan a ranar dangin amarya sukai walima tare da rabon kayan gararsu cikin bajinta da aka san katsinawa da ita a wajen rabo. Al'amarin ya ƙayatar da kowa a dangin Abban, sun kuma yaba da ƙoƙarin mutanen. Ana yin sallar azhar motocin da zasu maidasu gida suka kwashesu aka bar amarya Halime na kwasar kuka. Sai da su Aunty Zakiyya suka jata ɗaki suna lallashi. Daga ƙarshe ma dai su suka cigaba da zama da ita suna ɗebe mata kewa har washe gari da suma kowa yay haramar kama gabansa bayan sun kimtsa gidan. Har kuma sannan babu wanda yaga idon Mom. Sai dai duk sun fahimci akwai abinda suke ƙullawa ita da uwarta dan sai shigi da fici Ummar tata keyi a kwana biyun nan, saboda rashin sanin ciwon kai a gidan take kwana itama har a yau da bikin ya tashi. Ƴan Gwarzo ma sun rigata wucewa. Ganin bata ma da niyyar tafiya ne yasa Gwaggo Gudidi itama ta fasa tafiya a yau duk da dai dama wasu a dangin sun kawo shawarar Gwaggon ta ɗan zauna har gidan ya dai-daita gudun kar'a cutar da yarinyar mutane. Kowa kuma ya gamsu da shawarar dan haka Gwaggon tai zamanta. Sai hakan kuma yayima Abban daɗi shima. Dan dama yana tunanin ta yanda zai fita yabar Halime daga ita sai Mom ɗin a gidan har sai ya gama saita gidan...

💦💥💦💥💦

Kwanaki biyar kenan da faruwar dukan da naci a sashen Hajiya Babba. Alhamdullah jikina yayi sauki, dan hatta ciwon da taji min ma ya warke sarai sai tabo. Tun wannan ranar ban sake gigin komawa ba duk da hankalina na'a kanta. Haka shima uban gayyar ban sake ganinsa a gidan ba. Sai ma a bakin Mama Balki nake jin wai yayi tafiya ai tun a washe garin faruwar al'amarin da dare. Ranar da Hajiya Mammah ta aikani sashensa kai masa coffee kenan harna taho masa da waya. Bakina kawai na taɓe na cigaba da harkar gabana, dan damuwar data daman daban, duk da kuwa tana da alaƙa da shi. Sosai ina buƙatar zama dashi a wannan gaɓar, dan ina son jin yanda akai har ya je gidanmu ya nema aurena. Ai abin da mamaki, dan Mansoor mahaifiyarsa ta hanashi aurena shi kuma ace yaje ya auran bayan babu wata alaƙa data alaƙanta tsakanina da shi bayan ta kidnapping ɗina da yayi da hira da nai da shi a station ɗinmu...
Zuwa yanzu aikina ya koma sashen Hajiya Mammah, nice kullum mai mata gyaran sashenta safe da yamma. Da farko dai abinda na fara fahimta ga halayyar matar shine nuna isa da mulki. Na biyu shegen kallon raini na ƙurillar tsiya kamar zata cinyeka da idanu. Sai masifa komai kayi sai ta maka jaraba kamar itace ta halicceka. Shiyyasa idan na tashi kafin ma ta tashi a barci na gama gyara ko'ina nabar sashen, sai kamar 11 sai na koma na gyara mata bedroom lokacin ta fito. Yau ma kamar kullum da wuri na kammala aikin nawa, sai dai ina ƙoƙarin sauka dawn stairs na jiyo kamar sautin kuka na fitowa ta sashen Hajiya Babba. Tsamm nayi da raina kusan mintuna uku, jin dai da gaske tanan ɗin ne bamma san lokacin dana juya cikin sauri da sassarfa ba. Idanuna a rufe na faɗa sashen batare dana tuna da wahalar dana sha a hannunta kwana biyar da suka wuce ba. Ganin key a ƙofar ya sani murɗawa na afka ido rufe, jikina har rawa yake jin sautin kukanta da yanda take ambaton kiran sunan “Muhammad” dan zuwa yanzu na fahimci Maash kadai suke kira Muhammad a gidan ita da Paah. Zubewa nai a inda take zaune can karƙashin ƙafar bene ta cure jikinta waje guda fuskarta cikin ƙafafunta.
“Ummi miya sameki? Baki da lafiya?”. Na faɗa cikin rawar murya ina kamo hannayenta dake ɗauke da sayin ɗauri har yanzu amma duk ciwukan sun warke. A mamakina sai naga ta ɗago a hankali. Yanda idanunta suka kumbura sukai jaa sosai ya sake tayar min da hankali. Ga hawaye face-face da fuskar tata. Sai kawai nima na fashe da kuka tare da faɗawa a jikinta. Tsamm ta rungumeni itama tana ƙara fashewa da kukan da cigaba da magana cikin sambatu. “Muhammad ciwo, kaina ciwo zai fashe Muhammad. Ga jikina ƙaiƙayi yake min. Muhammad ina jin yunwa”.
Kuka na sake fashewa da shi ina mai ɗagowa a jikin nata. Amma sai ta hanani tashi ta sake matseni sosai. Duk da zafin da nake ji ban sake yinƙurin tashin ba. Tsahon mintuna biyar muna a haka har na fara numfashi da ƙyar. Sai kuma ta sakeni ta dafe kanta da riƙe cikinta. Zumbur na miƙe jikina na rawa, ga hawaye sun kasa tsaya min, “Kiyi haƙuri Ummie ki daina kuka dan ALLAH, yunwa kike ji ko?, Zakici abinci na kawo miki?”.
A mamakina kai ta ɗaga min tare da kamo hannuna ta ɗaura a saman cikinta hawaye na sharara ta shiga jujjuya min kanta. Ta ce, “Yunwa Muhammad yunwa”.......✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_


.......Da sauri na jinjina mata kai ina ƙoƙarin miƙewa. “To Ummie in sha ALLAHU yanzu zan kawo miki abinci bani ɗan lokaci ƙalilan.” ban jira amsawarta ba na tashi na fita a guje dan nasan bama amsawar zatai ba. A falonta na farko naci karo da wasu mata guda uku sabbin fuska daban sani ba a gidan. Nayi mamaki dan ɗazun ban gansu ba, ko kuma ban lura dasu bane oho. Takan kowa banbi ba a cikinsu nafice zuwa downstairs na afka kitchen, ganin an gama komai har an gyara kitchen ɗin ma fito dining, komai an shirya na breakfast, sai dai babu kowa a kai dan sai sun gama barcin safensu suke fitowa karyawar. Hajiya Ƙarama ce kawai bata a gidan ta wuce wajen aiki. Komai sai da na ɗiba tare da haɗa shayi mai ƙauri na ɗauka ruwa. Da gudu na koma saman, inda na barta nan na sameta, sai dai yanzu tana kwance ta naɗe a waje guda sai nishi take alamar yunwar tacita ta cinye matan nan na tsaitsaye a kanta kamar a tsorace. Ina shigowa duk suka zabura kanta. Tsawa na daka musu tare da nuna musu ƙofa alamar su fita. Har rige-rigen fitar kuwa sukeyi. Basket ɗin hannuna na ajiye, sannan na durƙusa gabanta na ɗagota. A jikina na sanyata ina kuka da bata haƙuri, shayin dana haɗa dai-dai zafi na ɗauka na kai bakinta, jikinta har rawa yake wajen damƙe kofin, tsam ta dafesa tare da hannayena kamar mai lafiya, kwal-kwal ta shiga kwankwaɗar shayin tamkar ta samu ruwa. Kafin wani dogon lokaci ta shanyesa gaba ɗaya, sai ga zufa na karyo mata tako ina ta fara sauke ajiyar zuciya jikinta na saki. Jinai hawaye sun ƙara ziraro min, na kwantar da kanta sosai a saman cinyata ina shafa cuɗaɗɗen gashinta daya danƙare saboda datti. Tabbas ɗiya mace daban ce, da ace baiwar ALLAHr nan nada ƴa mace a cikin ƴaƴanta duk tsanani bazata dinga barinta a cikin wannan dattin ba. Amma kalla yanda aka saketa kamar mara gata. Dukiyar tatace, gidan ma nata ne, ɗan da suke taƙamar da shi a yanzu haka nata ne. Amma ita bata san daɗin ko ɗaya a ciki ba, sai wasu banzaye da sukazo suka cika gidan badan su amfana mata da komai ba. In sha ALLAHU na ɗauki alƙawarin daga yau koda baiwar ALLAHr nan zata halakani sai na ƙwato mata ƴancin rayuwarta a gidan nan, tun daga kula da ita har zuwa sanin tushen wannan ciwo nata da nake ji a raina ba banza ba. Kai harma ɗan nata da alama ba haka suka barsa ba shima. Sai da na tabbatar shayin da tasha ya faɗa mata sosai sannan na jawo abinci, ban tasheta a jikin nawa ba, a haka na dinga bata da kaina kuma tana amsa. Sai kallona take dan har ta kauda kanta alamar ta ƙoshi idonta a kaina ƙyam. Lemo na ɗakko zan bata ta kauda kai, sai na ajiye na ɗauki ruwa. Ina saka mata a baki kuwa ta hau sha. Sosai tasha tana sauke numfashi, sai kuma ta gyara kwanciya a jikina, mintuna bai fi biyu ba barci mai nauyi ya dauketa. Ganin barcin nata yay nisa na fara kwance mata kitson kanta da yay bala'in danƙarewa, da naga ta motsa sai na ɗan dakata, sai ta koma barcin sai na cigaba. A haka na kwance gashin tana barci a jikina. Sosai take da gashi, da alama shima a wajenta ya gaji wannan gashin nashin da yakema mutane iyayi da shi. Ganin barcin nata yayi nisa na lallaɓa na kwantar da ita, gyaran sashen na fara, harda wancan ɗakin da naci duka a ciki wancan karon. Da yake na saka aikin a raina kuma an rage dattin da yay wancan karon sosai koma nace an gyara komai ƙal sai dai ban san wanda ya gyara ba kafin wani dogon lokaci na kammala tsaff, amma ina zargin matan nan dana gani sabbin ma'aikata ne aka kawo mata, maybe kuma sune sukai aikin. Ko'ina sai ƙamshi yake kamar ba shi ba, ruwa na haɗa inata tunanin ta yanda zatai wanka, dan harga ALLAH jikinta na buƙatar wanka, saboda alamu sun nuna an ɗan rage dattin jikinta ba kamar a ranar farko dana sameta na, harma kayan bana waccan ranar bane ba, sai dai kamar kuma ba'a sake mata ba tun waccan ranar ɗin. Ni kuma bamma san ta yanda zan iya cewa zan mata ba dan ina jin kunya. Dabara ce ta faɗo min, na fita zuwa kitchen dan nasan yanzu sun dawo aikin rana. Babu kowa a falon kuwa, cikin sa'a kuma na samu Mama Balki a dining tsaye tana waya. Tana ganina ta yanke kiran. Sai da ta wawwaiga ta tabbatar babu kowa a wajen sannan ta kama hannuna. Can ƙarƙashin stairs muka je, fuskarta cike da damuwa ta ce, “Ina kika shiga Kandala? Tun ɗazun ake nemanki a gidan nan amma babu ke”.
Kaina tsaye nace mata, “Mama ina sashen Hajiya Babba fa. Yanzu ma kiranki nazo yi ki taimakeni”.
Sosai fuskarta ta nuna mamaki, ta ce, “Sashen Hajiya Babba fa?”.
“Eh wlhy Mama. Dan ALLAH kizo ma muje kiga taimakon da zaki min kafin wani ya gammu anan a hanamu. Bata musa ba muka hau upstairs. Ni kaina tsaye nake tafiya, yayinda ita kuma take ta faman waige-waige da gani duk a tsarge take. Ita kanta sai da tayi mamakin yanda na ƙara gyara sashen, Hajiya Babba dake kwance na nuna mata. “Mama ki taimakeni jikinta na buƙatar wanka ne. Idan akai mata zataji sanyi. Ga kanta na buƙatar wanki ma, sannan matan can dake zaune a falon farko wai su wanene?”.
Ɗan jimm tai alamar tunani, sai kuma ta amsa min da, “To yanzu yaya za'ayi kenan? Kin san fa dole aka saka mata ruwa a jiki dole ta farka. Kuma hakan akwai matsala shiyyasa ma Alhaji ƙarami ya hana a jika mata kai ranar. Waɗan can matan kuma sune sabbin masu aiki da Baba ya kawo tun ranar da abin can ya faru tsakaninku”.
“Mama in sha ALLAHU baza'a samu matsala ba. Dan yanzu da kanta taci abinci. Kota farka kuma da izinin UBANGIJI babu abinda zai faru mama. Su kuma ki gargaɗesu dan ALLAH ko kuma suje waje idan anjima sa dawo”.
Badan ta gamsu ba ta yarda da magana ta, da taimakona muka kamata zuwa bathroom. Sannan ta fita ban san yaya tayi da matan ba ta dawo. Sake ɗaukar ta mukayi zuwa toilet. Ganin ta buɗe idanunta alamar ta farka cikin ruwan dana haɗa a bathtub muka sakata. Da farko taso zabura, sai da na dafe mata hannu da sauri cikin lallashi da roƙo ga hawaye a fuskata ina tofa mata addu'a sannan ta haƙura ta koma ta zauna. Kanta muka fara ƙoƙarin wankewa, sai faman sauke ajiyar zuciya take a jajjere. Yanda wata muguwar dauɗa ke fita ban san lokacin dana ƙara ƙarfin kukana ba dan tausayi. Kai da kaga wannan baiwa kasan kafin lalurar na anyi manyan hamshaƙan mata. Amma jiba yanda ƙaddara ta maidata, ɗan adam kenan ba'a bakin komai yake ba. Bamu bar kan ba sai da ya koma fidda farar kumfa sol da ruwa mai ƙyau, baiwar ALLAH sai sauke ajiyar zuciya take, barci ma ɗibarta yake. Fitowa nayi nabar Mama Balki tai mata wanka, duk da na fahimci ita tana komai a tsorace ne. Sai dai Alhamdullah ta daure ta mata wanka na gaske duk da ni na fito duba kaya kozan samu. Anan dai ɗakin da muke babu, sai da na duba ɗayan kusa da ita dake a kulle sai nayi sa'an samu, ashe ɗakin duk kayan sawarta ne da duk wani abun buƙata na gyaran jiki. Da alama tana ɓatawa ne shiyyasa ake rufesa abar key ɗin a jiki, sai dai kuma babu tabbacin ana mata amfani da su, dan da jikinta baiyi wannan masifar dattin ba ai. Komai da za'a iya buƙata na ɗauka harda towel sannan na koma inda suke. Har lokacin basu fito ba, dan haka na miƙama Mama Balki towel guda biyu, na ajiye duk abinda zasu buƙata na fita dan ta samu damar shiryata. Ina daga falo zaune kusan mintinan talatin sai ga Mama Balki ta fito tana sharar hawaye ga murmushi akan fuskarta. Zumbur na miƙe ina tambayarta ko lafiya. Maimakon amsa saita jawoni jikinta ta rungume tana mai fashewa da kuka mai ƙarfi da sanya min albarka. Ban iya kwace jikina ba har sai da tayi mai isarta ta ɗagoni dan kanta. Hawayen nima na share kafin na sake tambayarta abinda ke faruwa.
“Babu abinda ya faru Kandala. Ke dai ALLAH yay miki albarka. Kin kwatanta abinda wani bai taɓaba a gidan nan. Ashe baiwar ALLAHr nan ba kowane lokaci bane take a yanayin da ake gudunta. Dama ƙyaƙyƙyawar mace ce mai ƙyawun siffa da cikar haiba amma ƙaddara ta maidata haka. Zo ki ganta Kandala zo kiga cikar zati da asalin kwarjinin manyan mata dan ALLAH”.
Jiki na rawa nabi Mama Balki. Muna shiga ciki sai da na kusa faɗuwa dan mamakin abinda naci karo da shi. Lallai anan Awwab ya gado cikakken ƙyawu da asalin kwarjini. Hatta da idanun magen nan nasa irin nata ne. Bamma san lokacin dana ƙarasa gareta cikin sassarfa ba na durƙushe, hannayenta duka na kamo a cikin nawa na runtse, tamkar wadda ke cikin hankalinta sai ta sakar min wani guntun murmushi tare da lumshe idanunta a lokaci guda ta buɗe sai kuma ta sake maidasu ta lumshe. Bamma san lokacin da ƙaunar matar ya ƙara mamaye jini da ɓargona ba. Nai zaman dirshan a gabanta na cigaba da kallonta tamkar na samu television. Tsahon lokaci ina a haka har sai da mama Balki ta fargar dani muyi mu fita kafin mutanen gidan su farga da zamanmu a ashen. Gashi su kansu wadancan matan bamu san a ƙarƙashin ikon wa suke ba. Kaina tsaye nace “To mama minene dan sun san muna anan? Dama ba so suke su sami mai kulawa da ita ba? Nifa waɗan nan matan bazasu cigaba da zama da ita ba sai dai su koma inda suka fito”.
“Hummm” kawai Mama Balki tace dani batare da fashin baƙi ba. Daga haka ta fita tana mai tabbatar min nayi sauri na kammala tunda tayi barci na fito ita zata koma akan bakin aikinta. Da to kawai na amsa mata badan zanyi yanda tace ɗin ba, dan tana fitar ma kayan gyaran gashi na jawo tare da gyara zama na hau gyara gashin Ummie. Gashine mai uban yawa ga tsayi shiyyasa nasha wahala sosai. Ban bar mata shi a haka ba nai zaman kitsa mata shi. Nan ɗin ma dai ansha cakwakiya kafin a kammala, dan takan farka ta dafe hannuna tana yamutsa fuska. Har sai na tsaya ta huta ina tofa mata addu'a sannan nake cigaba. Sanda muka gama barcinta yayi nisa sosai, dan haka na miƙe na tattare kayan dana kawo mata abinci ɗazun da wanda nai gyaran gashinta na maida inda suke na fita da sauran samo mata wani abincin. Kusan cin karo mukai da yarinyar da Bahijja tace min agola ce a gidan, tana ƙoƙarin hawowa upstairs ina ƙoƙarin sauka ni kuma. A ɗan yamutse da kallon raini tace min nazo ana nemana........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒘𝒐_


.......Uffan bance da ita ba na cigaba da sauka ƙasan. Tunkan na ƙarasa nake jiyo hargowa da ihun Hajiya Mammah. Nadai dake na cigaba da sauka ina kallon Mama Balki dake durƙushe gabanta kamar ma kuka take yi, sai matan nan guda uku

Please Login or Register in order to submit comment