Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ƙamshin turarenki yasa naso na farga da ke, amma hankalina ba'a wajen yake ba dan haka na fice kawai. Ansha matuƙar wahala kafin samun rayuwar yaron, sai dai da yake ALLAH ya ƙaddara akwai sauran kwananasa gaba yasa ya warke kamar komai bai faru ba.. Ambatar sunan Grandpa ɗina a wannan ranar da shi Muktar Jaga yayi da ita Lawisa yasa na tabbatar da gaskiyarsa dalilin zuwan sa Kano a bazata har hirar da yay da ke. Tun daga lokacin nai doubling question mark ɗin dana sakama kowa a kansu. Nasa ya zama biyu. Na kuma janyema Lawisa sosai . Wannan video kuma ya tabbatar min da inahin fuskar ita Lawusar dai ce ba wata ba..”
A hankali hawayen da naketa riƙewa suka silalo min. Muryata na rawa na ce, “Hajiya ƙarama?”.
Kansa ya jinjina min alamar eh kawai. Wasu hawayen ne suka sake ɓulɓulo min. Cikin sake ƙanƙamesa na ce, “Yaya Awwab kayi haƙuri, amma wlhy zuciyata na bani sune suka kashe Abie da Babana......”
Da wani irin mugun sauri ya ɗago idanunsa da launinsu ya canja gaba ɗaya ya kalleni. Kaina na jinjina masa nima cikin tabbatarwa na ce, “Tabbas Yaya akwai ƙamshin gaskiya a magana ta. Dan na bibiyi videon ɗin nan da ƙyar tare da tankaɗesa da rairaiye sa. Kuma alamu sun nuna Ummie tasan wani abu shiyyasa ya durƙusar da rayuwarta zuwa wannan yanayin”.
Ai sosai ya tashi zaune gashin jikinsa na wani mimmiƙewa. Muryarsa har rawa take wajen faɗin, “Samrh miyyasa kikayi wannan tunanin?”.
“Yaya hujjoji da yawa. Dan kasan jami'in tsaro, da lauyoyi, da likitoci, da ƴan jarida al'amarinsu na kamanceceniya da juna. Saboda komai nasu yana tafiya ne a bigiren bincike. Shiyyasa zakaga a mafi yawan lokuta indai masu wannan ayyukan sun san abinda suke basu da wahalar fuskantar case irin wannan da saurin kama bakin zaren sa.”
Hannu ya kai saman yay wani kalar shafosa tamkar mai sharce ruwa ya yarfar. Bawai yau ya fara irin wannan tunanin ba shima. Sai dai a kaf bincikensa bai taɓa samun wanda ya ƙarfafa wannan hasashen nashi kamar ita ba a yau. Dan yanda ta fassara abin da confidence abin a duba ne..
Yunƙurawa yay zai tashi na riƙosa da sauri. “Yaya ina zaka je?”......✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don *_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒚-𝒔𝒊𝒙_


.......“Ina son naga Ummie”. Ya faɗa da alamar ran ƴan maza ya ɓaci. Kaina na girgiza masa da sake damƙe hannun nasa na ce, “No Ya Awwab ba yanzu ba. Ummie da bata bukatar kowane irin matsi daga garemu akan son sanin gaskiyar al'amarin kamar yanda doctor ya faɗa al'amarin ta daki-daki yake buƙata. Dole mu cigaba da haƙurin binta mataki-mataki dan akwai abinda itama take shiryawa, kar kuma ka manta ya sanar mana ba komai ya dawo kanta yanda ya kamata ba a yanzu. Sannan tanama naka takun tankaɗa da rairaya ne shiyyasa taƙi fitowa fili ta gaya maka koda abinda ya rage a zuciyarta ne. Dan haka mizai hana muyi wani abu domin gabato da komai a gaggauce”.
Idanu kawai ya zuba min batare daya amsa ba. Ban damu ba na cigaba da faɗin, “Ban san tsare-tsaren ka ba. Amma a nawa tunanin ya kamata kayi wani abu saboda dalilai biyu. Na farko matsayin Baba prof mahaifin Paah. Bafa abune ƙarami ba fiddo da ainahinsa ta ɓangarenka kai tsaye ko ɓangaren Ummie. Hakan zai kawo rabuwar kan family ɗin nan, dan koba komai sunan mahaifi yake amsawa a garesu. A kai kanka ma bar ganin ba komai bane wlhy sai ka jigata matuƙar jigata dan jini ya wuce wasa. Sannan babu alfanu duniya ta raja'a akan rikicinka da Family ɗinka. Hanya zaka bama abokan gaba na bayan fage suci tuwo a kanka tako wane fanni. Kasan dai masu iya magana sunce, DAUƊAR GORA CIKI KA SHATA. Dan haka kamar yanda ka fara yaƙin ta hanyar sunƙuru, tofa mafitar ɗayace a ƙarasashi ta hanyar TURNUƘU FAƊAN IBILISAI. yaro bai gani ba balle ya raba. Ma'ana mu zuba kamar yanda suka ɗauki shekaru suma suna zubawa. A maimakon baƙin fenti ya shafe ka, ruwan sama ne zai wankeka tatas ya kuma wanke Ummie su da bakinsu su faɗi ainahin abinda suka shuka, idan ma tonama kan nasu asiri sukai wa duniya sune suka zaɓi hakan. Ya kaga wasan zai kasance”.
Na ƙare maganar da kashe masa ido ɗaya. A mamakina sai naga kawai ya saki murmushi da cije lips ɗinsa. Hannunsa ya dunƙule tare da miƙo min🤜🤛 Nima kawai sai nayi yanda yay ɗin muka buga. Da sauri na janye nawa ina yarfarwa da faɗin, “Shiiii azaba wanan hannu kamar rodi”.
Ƙaramin murmushi yayi da ɗan ɗallamin lips kaɗan da yatsarsa. Sai kuma kawai ya jawoni jikinsa ya rungume tsammm. Ajiyar zuciya muka dinga saukewa a tare. Na ɗan motsa zanyi magana a hankali ya ce, “Shiiii bana son surutu”. Sai kuma ya ɗaukeni cak yay bedroom da ni. (Ba sai kunji miya faru ba kuma ehe😉 dan naga fans ɗin bily kun cika sa ido😌🥱😝🏃)

Lallai yau Samraah taci tuwo a kammu bari mu ware🏃🏃🏃🏃, danginta kuma har daku shinnnnnn😂😝?.

💢🌿💢🌿💢

Ƙarfe goma na dare Baba prof da Hajiya ƙarama suka kama hanyar station. Dan dama tana asibiti tun bayan sallar magrib. Ta can ma Baba prof ɗin ya ɗauketa kasancewar da kansa yay driving abinda ya jima baiyi ba. Amsar tuƙin hajiya ƙarama tayi. Kasancewar al'amarin hanya ce daga babban jami'in da yafi Uncle Abdullahi faɗa aji yasa tun a gate aka tarbe su. Baba prof ya yankema zuciyarsa sai ya fara jin tabakin commondo da tabbatar da gaskiyar Hajiya ƙarama sannan ya fitar da shi, dan ba fitar da shi ɗin ne mai wahala ba, amma maganganun Hajiya ƙarama suka canja wancan tunanin nasa. Yana son tabbatarwa, idan gaskiya ta faɗa shi da kansa zai saka a ɓatar da Commondo tun a daren yau. Idan kuma ƙarya take zai saka a fiddashi batare da saninta ba. Daga ƙarshe hukuncin da yay niyyar ma Commondo zai sa Commondo ɗin ya maidashi a kanta.
Kamar yanda yake nasa tsarin a zuciya itama yana yin nata ne. Dan tayi waya da Dr Khunal yanzu haka zuwa gobe abinta data biya maƙudan kuɗi ita da Baba prof ɗin domin Maash zai iso a daren yau. Za kuma tayi aiki da shi akan Maash kamar yanda suka tsara tun farko, da shi Baba prof ɗin da Mu'azz. Ummie kuwa nata tanadin na musamman ne. Shiko Commondo ta riga ta gama bada kwangilarsa. Jannifer ma Baba prof zai ƙarasa mata ita shiyyasa ta azashi a keken ɓera.
Tunaninta ya katse lokacin da aka shigo da Commondo da Jannifer hannayensu duk da Handcuffs. Ga raunuka a jikinsu dake tabbatar da Dukansu akai babu jinawar nan. Dan bayan la'asar Uncle Abdullahi ya bada umarnin fara tuhumarsu amma su duka sunƙi cewa komai saboda damar da duk suka ƙudiri aniyar bama iyayen gidan nasu na yau kawai. Idan basu zo ba zuwa gobe zasu fara buɗe aiki. Shiyyasa suka jure da dukan bawai dan basa jin zafi bane ba ko ciwo...

Cikin tsawa jami'in daya kawosu ya nuna musu ƙasa matsayin wajen zama. Sannan ya koma daga ƙofar ɗaki ya tsaya dan yasan basu da wata hanyar guduwa tako ina office ɗin zagaye yake da jami'an tsaro irinsa. Daga Hajiya ƙarama har baba prof kallon Commondo da Madam Jannifer sukeyi kamar yanda suma suke kallonsu kallo irin na ƙurilla...
Kusan mintuna biyu kafin Baba prof ya janye nasa idon cikin gyara zama da kafe Commondo da ido ya ce, “Commondo ya akai aka faɗi a ragaya?”.
Murmushi Commondo yay da jinjina kansa. Sai da ya kalla gefen Hajiya ƙarama ya furta, “A ɓaɗinance talalace! A zahirance kuma ɗaurin goro ne!”.
“Akasin lissafi kenan fa”.
Baba prof ya faɗa cike da waro idanu.
“Na dukkan lissafi ne ma aka samu a wannan gaɓar oga. Dan shi macijin cikin ciyawa idan har yay kala da ciyawar sai yayi illa batare da ma'abocin taka ƙafa ya farga ba. Rafi da kogi zasu iya haɗa tafiyar wucewar ruwan cikinsu a hanya ɗaya. Amma shi kududdufi da gulbi koda suna maƙwaftaka akai rami a tsakaninsu ba lallai ruwan ɗaya ya ɓulla a cikin ɗaya ba. Dan ramin su baya kogo kamar na rijiya”.
Cikin ɓacin rai Hajiya ƙarama ta tare numfashin Baba prof dake ƙoƙarin yin magana. “Amma kun san magana cikin duhu haramunne a wannan tafiyar tamu. Anan duk ɗaya muke. Dan itama Jannifer abokiyar cin mushe ce. Banga dalilin ɗaure zance ba bayan muna neman hanyar gudu tare mu tsira tare ne a wannan gaɓar. Idan kuma har kukace wasan na nuna zalama ne, to karfa ku manta ku duk biyun nan linzamin dokin Lawisa ne. Musamman ma kai ɗin nan”. Ta ƙare maganar da nuna Commondo.
Wani shegen murmushi Commondo ɗin ya saki. Cikin ɗage gira ya furta, “Lawisa! Ke ƙaramar giwace, ragon layya kawai yay dogon miƙi zai iya yaddaki a dokar jeji. Ashe baki shirya wasan ba da ƙyau amma kikayi tunanin tararsa. Shi zuciyarki bata baki tabbacin ko Giwa ta faɗi tafi ƙarfin wawason ƴaƴan damisa ba. Shike nan, tunda kince muje a buɗe, muje ɗin, kin san dai ni bishiyar dabino ne wlhy bani ƴaƴan banza. Dan ko a ɗanyena nake rububin cina akeyi”.
“Kamar yanda kasan nafi ƙarfin damisar takarda. Sannan ni uwar bakirikice ba yarinya ba. Duk wanda ya sanni a cikinta ya ganni ba raino na akai ba. Miyyasa ka shirya cin amanata?”.
“Saboda kema naki shirin kenan?”.
“Amma kasan komi nayi akwai dalilinsa?”.
“Kamar yanda kika san nima bana komai sai da dalili. Miyyasa na ɗaukeki Hadari zaki maidani hazo?”.
“Ohooooooh!! da ƙyau!”.
Baba prof ya faɗa yana wani kwashewa da dariya da tafa hannaye. Gaba ɗayansu juyawa sukai suka kallesa. Duk kuma sai suka sha jinin jikinsu. Cikin daina tafin da musu nuni da hannu ya ce, “Ku cigaba mana, miyyasa zaku bari kuma?”.
“No oga relax. Kada ka ruɗar da kanka kadai san makircin wannan wawuyar”. Cewar Commondo da sauri. Da saurin itama Hajiya ƙarama ta cafe da faɗin, “Sai dai wawaye. Kai ni fa a wannan gaɓar banƙi a mutu ba har liman wlhy. Dan na gaji da tafiya da maciya amana waɗanda kansu kawai suka sani. Na kuma gaji da barin jakai ina dukan tanki.”
“Oh really?! To ai Lawisa ke ce babbar mai cin amana a cikinmu. Dan kece kika nunama kowa tashi ta fisheshi. Oga shine ya jawoki a wannan tafiyar ya kuma maidaki abinda kike a yau amma har kike tunanin watsar da shi...”
“Hahahaha!!! Commondo! Commondo!! Commondo!!. Lallai kai jaki ne na yarda. Wai shin kana yin duk wannan ne saboda tunanin wannan abun zai iya fiddaka a wannan wajen? To lallai kayi kuskure dan anzo gaɓar jifar gaffiyar ɓaidu. Dan anzo gaɓar da shi ɗin ma takansa yake bazai iya maka komai ba. Idan ma lissafin barin nan ɗin kake to ka bari, dan zama daram mai naƙuda ta samu katifa hahahaha!!!”.
Wani irin kallo Commondo yake ma Baba prof. Cikin zafin rai ya ce, “Oga!!”.
“Don't call me Oga again!!”.
Baba prof ya faɗa a matuƙar zafafe. Wani shegen murmushi Commondo ɗin ya saki da jinjina kansa. Tabbas badan handcuffs ɗin hannunsa ba babu abinda zai hanashi raunata mutanen nan guda biyu, har shi zasu haɗema kai. Amma babu komai zai musu abinda sai sun gwammace inama raunin yaji musu. Cikin tsantsan tsana ya kallesu ɗaya bayan ɗaya, “Lallai ku sani ku dukanku zaku tafka babban kuskuren da sai kun dawwama kuna nadamarsa a rayuwarku. Dan ni Commondo tauraro ne mai wutsiya. Sannan cinnaka nake ban san na gida ba. A tafiyata kuwa bana GUDU DA WAIWAYE. Idan har kaga nayi, abu mai matuƙar muhimmanci na dawo ɗauka. Kada ku taɓa tunanin ƙarfin iko ko faɗa ajin da kuke taƙama da shi zai tserar da ku daga tarkon Commondo. Dan *_TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE_*. Kusa a ranku yanzu ne wasan zai faraaaaaa!!!!”.
Daga Hajiya ƙarama har Baba prof sai da suka ja baya saboda yanda Commondo ya ƙarasa magana ta ƙarshe a kausashe kuma da tsawa. Yayinda Jannifer ta kece da dariya. Sai da tayi mai isarta duk suna kallonta sannan ta dubi Hajiya ƙaramar.........✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒚-𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_


......“Hajjaju wannan duk damuwarku ce dan ku kuka san kanku. Ni a wane matsaya nake? Dan bana buƙatar sake kwana a wannan wajen da ga ni har yara na. Kin san fa ni ba irin Commondo bace, da an cigaba da takura min bakina buɗewa yake caaaaaa!!!!! Da magana”.
Fushin Commondo yasa Hajiya ƙarama watsama Jannifer harara. A harzuƙe ta furta, “In bakin naki bai buɗeba baki cika ƴar halak ba Jannifer. Shashasha kawai ana batun masu hankali kina sako ruɓaɓɓen bakinki. K! har kina da bakin ma jefama mutane maganar banza batare da an sakoki ciki ba”.
“Oh yeer! Hajiya Lawisa amma dai kin san ni tururuwace bana jidon banza ko?”.
“Duk jidon naki kiyi dan iyakarki tsintar gero da dawa amma ƙashi ko nama ƙaryarki”.
“Haka kika ce?”.
“Nama ce fiye da haka. Dan ku dukanku anan zan iya da ku”.
“Ai ba abin mamaki bane dan MAGE taci amanar KARE!!”.
Wata murya a bazata ta daki dodon kunnensu. Gaba ɗayansu suka juya ga ƙofa da basu san yaushe aka buɗeta ba har mai maganar ya shigo musu babu notis. Kusan a tare Hajiya ƙarama da Baba prof sukai baya. Yayinda Commondo yay wata irin zabura da ga zaune yana ƙwalalo idanu waje. Jannifer da bata san ko waye ba kuwa ta ce, “Wannan gaskiya ne ɗan uwa”.
Murmushi Jaga ya sakar mata tare da kashe ido ɗaya yay mata alamar jinjina. Sai kuma ya wani ɗan jujjuya kai yana mai gyara tsaiwa cike da gadara ya bisu da kallo ɗaya bayan ɗaya. Kafin ya tsaida idanun kan Commondo. Rawa jikin Commondo ya farayi sosai. Da ƙyar ya iya furta kalmar, “Jaga! Fatalwa?”.
“Yes I'm. Amma ni ba fatalwa bane JAGA!!!! ne”. Ya ƙare maganar da wani irin kashe ido ɗaya cike da salon iskanci. Lokaci ɗaya Hajiya ƙarama da Commondo suka saki ihu. Yayinda zuciyar Baba prof kawai ta tsarga lokaci ɗaya cikinsa yay wani irin kalar bada sauti sai gudawa tsuuuuuu!!! Daga tsaye. Dariya Jaga ya kwashe da ita. Sai kuma ya nuna Baba prof da yatsa, ya nuna Commondo, ya nuna Hajiya ƙarama sannan ya kai hannunsa kan wuyansa yay alamar yankawa. Tuni itama Hajiya ƙarama fitsari ya ɓalle mata ƙafafunta suka fara rawa.
Cike da mamakin abinda ke faruwa da yanda zakunan dake hanƙoro kusan na mintuna talatin babu mai jin wani duk suka gigice Jannifer ta kalla Jaga cike da rashin damuwa ta ce, “Ɗan uwa halan kai ɗin waye dan ALLAH?!”.
“JaGa!!!! Gawa ta ƙi rami kenan. Sun gina naƙi shiga, ɗan Badamasi ke nan ajiyar ALLAH, mutuwarka sai cikar kwanakinka. Namiji ƙi gudu sa maza gudu. Ki basu shawara, yanzu ba lokacin gardama bane ba lokacin GUDUN CETON RAI NE. Domin gab ZAKI na gaskiya yake da fitowa shawagi. Dan haka mun shiga ƙarnin MAI RABON GANIN BAƊI YA GANI. Maƙiyanka fadawanka. A kafta Yaya Maaaaashhhhhhh!!!”.
Ya faɗa yana tafa hannunsa sai ko ɗiffff wuta ta ɗauke duhu ya bayyana. Wani irin masifaffen ihu Hajiya ƙarama ta fasa dan a zatonta fa Maash ɗinne ya shigo, itama sai gudawa zuuuu. Yayinda Baba prof ya yanke jiki ya faɗi kawai. Commondo kansa a gigice yake dan shi fa kamar su duk sun ɗauka fatalwa jaga yay musu, sannan ganin Maash anan ɗin tamkar ƙarshen numfashinsu ne. Ita kanta Jannifer da bata fahimci tushen zancen ba jin sunan Maash ya saka ƙirjinta fara karkarwa ta kawai fashe da kuka. Ga duhu office ɗin......

😂Wai miyyasa mutanen ke tsoron Yayanmu haka🤣. Koda yake shifa mara gaskiya ko a ruwa jiɓi yake🥱

🩸✨🩸✨🩸

Gaba ɗaya ya hanani sake sauka ƙasa. Sai shine yaje massalaci. Bai dawo ba sai da akai isha'i. Da wannan damar nai amfani na sauka na haɗo masa abinci. Ummie na ciki saboda Paah, su Hafizzullah ma da alama suna masallaci tare da shi. Aunty Falaq ma na ɗaki dan haka harna gama abinda zanyi babu kowa a farlon. Ina idar da sallar isha'in na kwanta a wajen dan ɗan sanyi-sanyi nake so. Daga azhar har zuwa gabannin asubahi zaka sameni lafiya Lau kamar banda wata damuwa. Ana ce miki asuba tayi da ƙyar nake yin salla sai zazzaɓi da amaye-amaye har sai rana ta ɗaga kuma. Jin an ɗagani na buɗe idanuna, dan nasan mai mun hakan sai dai shi. Kallonsa nayi tare da ɗan tura baki gaba. Cike da shagwaɓa na ce, “Please My Hot ALLAH can yafi daɗi”.
Bai tanka min ba sai da ya sauke ni saman gadon. Yana ranƙwafe a kaina idanunsa cikin nawa yana bina da wani kasalallen kallo da zuwa yanzu na fara fahimtar fassarar halin da yake ciki a duk sanda yake mun shi. Cikin motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta, “Kina son ki haifar min yara da sanyi?”.
Kai na girgiza masa a marairaice kamar zanyi kuka na ce, “ALLAH yafi min daɗi ne fa”.
Bai ce komai ba ya kwanta ta gefena yana mai rungumeni a jikinsa. A tare muka sauke ajiyar zuciya. Nima sai na sake shige masa da sake ƙanƙame shi. Mun jima a haka kafin ya fara canja salon kwanciyar tamu zuwa wani abu daban. Mamaki ya sani ɗagowa na kallesa. Ɗazun nan fa barowarmu falo ya.... Tunanina ya katse jin saukar mitsitsin lips ɗinsa kan nawa. Yanda ya iya bin hanyoyin mantar da mutum kansa yasa tuni ma na saki ragamar duk da nasan wahala ce dai bazan fasa shanta ba. Dan shi ɗin bana wasan yara bane. Marmarine da ga nesa....

Nako ji a jikina, haka na lafke masa wanka ma sai da taimakonsa. Dan ma yunwar da nake ji ta sa na kasa kwanciya na ce masa abinci zanci. Da kansa ya zubo abincin yazo ya zauna ya dinga bani. Nima sai na amsa ina bashi. Hakan ya ɗan taimaka min na ɗan ci shima yaci. Ina cewa na ƙoshi shima kuwa yace ya ƙoshi. Mamaki yake bani dan ban taɓa gamo da wanda bai damu da zaman cin abinci ba irinsa. Kwance zan kai ya kamani ya zaunar yana girgiza min kai alamar karna kwanta. Cikin shagwaɓa na ɗan tura baki dan kwanciyar nake so. Bai kulani ba sai jinginani da yay da jikinsa kawai ta ɗauki wayarsa yana latsawa. Ajiyar zuciya na sauke kaɗan, idona akan wayar nima nace, “Ya Awwab”.
“Uhhyimm”.
“Yarinyar nan ya kake ganin zamuyi da ita?”.
Shiru kamar bazaice komai ba. Sai kuma ya ajiye wayar yana furzar da numfashi. “Ki bar komai a hannuna dan zuwa yanzu haka ma tana hannu”.
“What! Ya akai hakan?”.
Na faɗa ina tashi zaune da ƙyau. Kallona yay shima sai kuma ya ɗan lumshe ido ya sake buɗewa akaina. Akan lips ya furta, “Bana wasa da DAMA”.
“Ni shaida ce”.
Na faɗa cikin kashe masa ido ɗaya da kai baki a hankali na sumbaci kumatunsa. Murmushi ya saki mai ƙayatarwa ya jawoni jikinsa ya rungume. Kiran wayarsa ne ya katse mu. Ɗauka yay, kasancewar muna a kusa da juna yasa naji duk abinda Hayatun ke faɗa. Yana ajiye wayar ya miƙe nima na miƙe. Kallona yay na ɗaga masa gira da faɗin, “Lokacin da zan taimaki mijina da tawa basirar yayi. Let's go”.
“My baby”.
Ya faɗa da soft murya yana kallon cikina.
Nima ƙasan nayi da muryata ina mai ɗora hannuna saman cikina na furta, “Yana tare da kariyar UBANGIJI”.
Baice komai ba yay gaba. Nima sai na juya na fita zuwa nawa ɗakin. Babu jimawa na fito, sai naci karo da shi a ƙofa yana niyyar shigowa. Batare da yace komai ba ya kama hannuna kawai.....


💥💥💥

Sai da taimakon Isma'il Baba prof ya koma gida. Tsabar ɗimuwar da yake ciki yasa baima fahimci wanda ya maida shin ba. Hakama Hajiya ƙarama ita kanta bata san a yanda ta dawo gidan ba. Kawai dai ta tsinta kanta a bakin gate. Batako saurari mai taxi daya kawota ba ta afka ciki sai securitys ɗin ƙofa ne dake binta da kallo suna toshe hancin qarin kashin da take suka biya shi. Da ga Maash har Hayatu da Samraah da TJ dake jan motar da zasu fita da kallo suka bita suma.
Nannauyan numfashi na sauke da faɗin, “To ita kuma wannan ƙalau take kuwa? Jibafa jikinta kamar wadda tai kashi, gashi sam bata a hayyacinta”.
Hayatu ne cikin ƴar dariya ya karɓe da faɗin, “Babu tantama aikin Jaga ne wannan”.
“Jaga kuma?”.
Na faɗa ina kallon Maash da yay kamar ma bai san abinda ake yi ba. Yanzun

Please Login or Register in order to submit comment