Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai kan Hajiya Mammah ba ya ɗauka side bag ɗinsa irin ta maza matasa masu ji da gayu ya saka. Kansa tsaye babban ƙofar sashen ya nufa, dan sai ya fara zuwa yaga Ummiensa kafin ya ƙarasa sashensa. Yasan dai yanzu su Paah duk basa gida suna office........✍️

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 thirty-two


.......Zaune nake cikin dauriya kan Ummie a saman cinyata ina mata kitso tare da raira karatun Alkur'ani a hankali. Duk da dai Alhamdullah yau ina jin jikina da sauƙi ba kamar jiya ba. Tunda na shigo Mama Balki ta sanar min ai Hafizzullah yazo da safe tare da Hayatu amma sun fita har da Maash sai kawai nace bara nai zaman yima Ummie kitsonta da tun jiya naso yi ALLAH bai ƙaddara ba. Muna fara kitson Mama tace bara taje ta duba su Aunty Falila a kitchen dake girkin rana. Da to na amsa mata na cigaba da kitson ina karatun. Fitar tata baifi da mintuna biyar ba aka buɗe ƙofar ɗakin, sai ban damu ba na cigaba da kitsona ina karatuna da tunanin ko itace ta dawo ɗaukar wani abu. Jin shiru bata ƙaraso ba bata kuma yi magana ba ga wani baƙon ƙamshin turare da ban santa da shi ba yasa na ɗago idanuna na kalla ƙofar.

Cak na tsaya da kitson ina bin black beauty matashin saurayin da kallon mamaki kamar yanda shima ya zubamun idanunsa sak irin na Yaya Awwab. Ganin kallon nasa na neman wuce gona da iri fuska a yamutse na ce, “Malam lafiya? Wanene kai? Miya kawoka nan?”.

Gira ya ɗan ɗage cike da salon iya shege sai kuma ya saki wani faffaɗan murmushi. Hannu ya kai ya ɗan shafi dan tsigigin gemunsa na ɗaukar magana ya wani karkace kai gefe tare da furta, “FAHAD EL-MU'AZZ ADAMS. Kefa ƙyaƙyƙyawa?”.

Maganarsa ta ƙarshe ta sani ƙin cemasa komai duk da naji wani daɗin jin sunan daya ambata ɗin . Sai ma ɗauke idanun nawa da nai na maida kan Ummie. Takowa yay shima a hankali zuwa inda muke. Zama yay kusa da Ummie ta ɗayan side ɗin, kamar wani ƙaramin yaro ya kwanto jikinta yana mai rungumeta. Cikin rawar marya ya ce, “I miss you mom. I love you with all my heart. You are my world and everything.” sai ga hawaye sharr, sake ƙanƙameta yay sosai a jikinsa. Sosai wani irin tausayinsa ya shiga ratsa min zuciya. Kaina na kauda daga kallonsu nima hawayen na zubo min. Da sauri na share su tare da ƙoƙarin cire kanta a jikina ya ɗago.

Da sauri ya ce, “Oh oh beauty sai ki tafi kuma? Ki bari na gama da Ummie na zan dawo kanki”.

Harara na zuba masa. Kafin na girgiza kaina da faɗin, “Ka kama kanka fa.”

Da sauri yako damƙe kan nasa. Sai kuma ya saki murmushi cikin komawa serious saboda hararar dana zabga masa. Hannayensa ya haɗe waje guda. Ya ce, “Am sorry. Barka da rana. Sunana Fahad El-Mu'azz Adams. Autan Ummiensa da Paah”.

Na kula akwaisa da shaƙiyanci, dan haka nayi murmushi da ɗan girgiza kaina. Cikin komawa serious nima nace masa sannu da zuwa. Sai dai yanzu ba kaine autan Ummie ba nice.”

Cikin marairaice fuska ya ce, “A'a dan ALLAH kada kimun haka. Na yarda ki zama aunty na kawai. Daga yanzu ma zan na ce dake aunty beauty”.

“Dama Auntyn taka ce ai”.

Muka tsinkayi muryar Mama a bayanmu. Da sauri ya juya, sai kuma ya miƙe cike da farin ciki ya nufeta. Babu kunya ya rungumeta. Dariya Mama ta shiga yi da ɗan bubbuga bayansa tana faɗin, “Oh ni maigado sai yaushe ne Fahad ɗina zai girma. Haba autan Ummie kafa isa aure”.

“Ina ban isa ba Mama. I miss you wlhy”.

“Muma munyi kewarka sosai Fahad. ALLAH yay maka albarka kaji.” ta faɗa tana ɗagosa. Daka gansu kaga waɗanda ke a cikin farin ciki sosai. Cike da girmamawa ya gaisheta, tare da tambayarta jikin Ummie yana mai bin sashen da kallo. Ta amsa masa da kulawa. Kafin ya tambayeta wai wacece ni dan ya matsu ya sani. Ƙaramar dariya Mama tayi, tare da faɗin, “A'a bakaji a bakina ba. Ka bari zaka sani”.

Cikin yanayinsa na mutum mai sauƙin kai a yanda na fahimta ni dai ya ce, “Okay Mama ba damuwa. Bari naje nayi wanka sai na dawo ALLAH yasa Ummie ta tashi ta ganni na ganta da ƙyau. Ina fatan kin min farvorite food ɗina dai?”.

“Sasai ma kuwa autan Ummie. Dan har sai kaci ka ture.”

Sosai farin cikin sa ya sake bayyana. Ya ɗaga min hannu yana maida bag ɗinsa da faɗin, “Bye Aunty beauty ki jirani nazo muyi hira. Dan sai kin faɗa min wacece ke zan barki.”

Sosai ya bani dariya. Hakama Mama Balki dariya take yi. Yana gama ficewa na dubi Mama fuskata da sauran dariyar na ce, “Mama wannan ɗan naki akwai dai rashin ji a jikinsa”. Dariya ta sake yi sosai tana kaiwa zaune. Ta ce, “Humm bar Fahad inda kika gansa ya dai so yin barkwancin ne. Amma shima da kike ganinsa wani lokacin akwai miskilancin. Sai dai bai kai Alhaji Ƙarami bane kawai. Halinsu ma sam ba iri ɗaya bane ba. Dan shi Fahad na surutu sosai, shiko Alhaji ƙarami maganar ma aiki ce. Nan fa ta shiga bani labarin Fahad da halayensa. Wani nayi mamaki wani nayi dariya wani al'ajabi. Surutunmu ya tada Ummie ma. Tana farkawa ta fara kiran “Yunwa Muhammad! Yunwa”. Aikin kenan yanzu, daga taci abinci sai barci. Idan kaga ta farka yunwar ce ta sake tashinta. Shiyyasa jikinta yake wani irin murjewa tana ƙiba kwarjininta na sake fitowa. Kwana biyu dai Alhmdllh bata wannan bige-bigen. Bamu sani ba ko hakan nada nasaba da canja mata magunguna da akayi ne. Dan a ranar da jikinta ya motsa sosai ina asibiti a yanda Mama ke bani labari anzo da wani baƙon likita tun daga ƙasar RUMAN (Dole mu tuna Shahan-shan namu na Iffan😘😀). shine ya dubata tare da canja mata allurai da magunguna. Acewarsa a gwada waɗan nan sabin samfir ne da a shekarar nan aka samar dasu akan masu matsalar ƙwaƙwalwa. Ya bada wata ɗaya zai sake dawowa yaga idan an dace. Amma duk da haka a kullum sai doctors daya bari zasu ke kula da ita zasu dinga aika masa da cigaban da ake samu. Sannan ya dakatar da su Hajiya ƙarama da sauran doctors ɗinta a komai acewarsa shi baya haɗa aiki da waɗanda ba wanda yake tare ba.

Sosai naso ace sanda abin ya faru ina wajen. Dan ina buƙatar fahimtar yanayin kowa a cikin doctors ɗin nata na baya. Dan nasan ko suna da gaskiya hakan bazai musu daɗi ba. Amma ko yanzu na ɗauki ɗamarar yin hakan.....

🌛🌜❣️🌛🌜

Ya ALLAH🙏 Wanda ke da rabon shiriya a masu ɗakkowa, da masu yaɗawa, da masu jiran a ɗakko su karanta a matsayin bati, ya UBANGIJIN al'ashi. Ya mai RAHAMA da jinƙai. Ya mai fidda rayayye a cikin matacce, ya fidda matacce a cikin rayayye. Nayi tawasalli da sunayenka masu tsarki, waɗanda ka kirayi kanka da su ka kuma sanar damu, da wanda ka barwa kanka saninsu ka keɓancesu gareka. Nayi tawasalli da ɗan gatan nan naka, wanda kace idan muka so shi, mukabi abinda yazo mana da shi na shiriya ka gafarta mana. Ina roƙonka ka shiryar dani da su. Ya rabbi kafisu sanin wahalar da nake sha a yayin rubutun nan. Nakan hana kaina barci domin sauke hakkin masu saya a lokacin da su suke barcin, nakan yini da ciwon kai, ina fama da ciwon idanu, ina fama da ciwon yatsu. Ina fama da ciwon baya. Wataran nakan wayi gari banama jin farin ciki ko sha'awar rubutun, wataran na tashi da uzirin baƙi ko fita. Amma duk nakan kuntata kaina domin naga nayi. Idan har ban kasance na cutar dasu da komai ba a rayuwarsu, ya rabbi! ya rabbi! ya rabbi!! ka shiryar dasu su guji taɓa hakkin daba nasu ba. Ka shiryar dasu su guji ɗaukarma kansu nauyin da zasuyi dana sani a ranar da ake fansa da lada da zunubi. Ya rabbi ka gafarta mana kurakuranmu. Ka shiryar damu, ka nisanta mu ƙuntata zuciyar kowa koda kuwa dabbace. ALLAH kasa mu samu sauƙaƙƙen hisabi batare da an jinkirta mana ba saboda hakkin wasunmu da mukaci a duniya. Dan ALLAH, dan ALLAH. Dan girman ALLAH mu saukaƙama kammu kunji bayin ALLAH. Ni kaɗai nasan a yanayin da nake wannan rubutun musamman a ɗan tsakanin nan, kada ki bari UBANGIJI ya kamaki da laifin hakkina nima bazan so haka ba. Dan bana son akai gaɓar da zan iya tashi tsakkiyar dare domin miƙama UBANGIJINA ƙararki ko ƙararka. Dan ALLAH, dan ALLAH, dan ALLAH. In har da gaske ke masoyiyar MANZON ALLAH ce kina fatan tashi a tawagarsa ranar da kowa ke fatan hakan, idan har da gaske kin yarda da mutuwa da ranar hisabi, idan har kin yadda wannan rubutun hakkina ne ALLAH zai iya cirar min hakkina a jikinki, idan har kin yarda ban taɓa cutar dake da komai ba, idan har kina fatan kema ALLAH ya kiyaye hakkinki ko hakkinka, ku daina ɗakkowa a inda na killacesa, ki daina yaɗawa, kema ki daina karantawa. Wannan itace maganata ta farko kuma ta ƙarshe in sha ALLAHU, ALLAH ya yafe mana kurakuran mu baki ɗaya.🙏

🪴🪴⭐🪴🪴

Ran Baba prof a ɓace yake kallon Hajiya Mammah dake gaishesa. Bai amsa ba, sai nuna mata agogon dake falon nasa mai shegen ƙyau da ɗaukar hankali yayi. “Kalla time, sai yanzu ne kike zuwa bayan tun 12 da wasu mintuna nai kiranki Nafisa?”.

“Kayi haƙuri Baba. Wlhy na fito zan taho sai ga Fahad. Bamma ko tsaya ya ganni ba na taho dan kar kaita jirana. Wlhy duk a tsorace nake, kada su sake ƙoƙarin ƙona mu a cikin gida kamar wancan karon. Ban san wace jaraba ce ta dawo da yaron nan ba ana zaune lafiya.”

Ɗan jimmm na wucin gadi ne ya riski Baba prof.. kafin tamkar mai koyon magana ya ce, “Wai wane Fahad ɗin?”.

Cikin rashin damuwa Hajiya Mammah ta ce, “Fahad namu mana Baba. Wlhy gashi can ya dawo abinsa. Abinda ma dai ya ɗan bani mamaki shine ganin a motar fitinannen ɗan uwan nasa aka ɗakkosa. Ko sun shirya ne bamu sani ba. Idan ma hakanne ta kasance ai mu abin farin ciki ne a garemu, dan wlhy tsoron tashin hankalin nan nasu nake suzo wataran su ƙonemu ƙurmus mu da gidan kana dai ganin wancan karon da ƙyar muka sha suka so sakamu a tara. Kai ai nikam wannan jini na Ummu-Hidaya ai ba'a cewa komai. Bala'i kala-kala daga wannan sai wancan”.

Yanda Baba prof yay shiru da alama ba fahimtar zantukan Hajiya Mammah yake ba ma shi. Dan sai da ta ɗan kai hannu ta taɓashi sannan ya dawo firgigit. Murmushi yayi zai yi magana dai-dai nan akai knocking ƙofa. Tsaki Hajiya Mammah tayi tana hararar ƙofar dan tasan bai wuce ma'aikatan gidan ba. Cike da wulaƙanci ta bada izinin a shigo. Ilai kuwa cikin ma'aikatan ne. Kansa a ƙasa da girmamawa ya kai durƙushe yana sanarma Baba prof yana da baƙo.

Agogo Baba prof ya kalla, cikin ɗan ɓacin rai yace, “Bani da apartment da kowa yau, koma su waye a sanar musu suje sa dawo next time”.

Kai hadimin ya jinjina. Har zai miƙe sai kuma ya koma ya durƙusa. Kansa a ƙasa cikin ɗari-ɗari ya furta, “Ranka ya daɗe Commando ne fa, kuma kaine kace ko baka gidan nan yazo nemanka a sanar da kai”.

Cikin masifa Hajiya Mammah ta juya zata fara danna masa zagi Baba prof ya dakatar da ita. “Uhmm Nafisa kinga barshi umarni na ne. Kinga jeki gida kawai idan na gama da shi zan zo na sameki. Komi ke faruwa ki dinga sanar dani ta waya. Sannan kiyi ƙoƙarin Mu'azz da Abdullahi su dawo gida gudun tashin hankali, idan kuma Awwab baya a gidan ki sanarma Mu'azz ya hanashi komawa gani nan zuwa yanzu nima”. Maganar yake yana tafiya, dan haka kafin ma ta bashi amsa har ya shige hanyar da zata sadashi da falon baƙi. Galala tai kawai tana kallonsa, can ƙasan ranta mamakin miya rikitashi haka take yi. Tare da mamakin girman wannan baƙo a wajensa. Amma dai koba komai ita hakan yayi mata. Dan ta kuɓuta daga abinda take gudu dai ke nan. Cikin taɓe baki ta miƙe, tare da saɓar handbag ɗinta ta fice hankalinta kwance. Ai garama taje taga show ɗin can gidan, dan babu wasu su Paah da zata kira sai abubuwa sun kankama..........✍️

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 thirty-three


.....Abincin na fara bama Ummie bayan na wanke mata baki da taimakon Mama Balki. Ci kuwa take sosai kamar ko yaushe a kwanakin nan. Lauma biyu uku sai na bata ruwan addu'a ta sha. Ba ruwan addu'ar da nake mata bane kawai, Baba ma na mata, haka akwai wani da Hayatu ya kawo yace daga Sheikh Muhammad bin Khalipha Al-Hussain yake amsowa, tuni kuma ana kawowa masu kula da ita wai ke bata. Dan haka dana tashi sai nake haɗesu waje guda ina bata, kullum kuma Mama Balki kan shafa mata sau uku a jiki, safe, rana da dare idan zata kwanta. Shi kansa Yaya Awwab daga jiya zuwa yau sune ruwan shansa batare daya sani ba. Dan kaf ruwan dake a cikin freight na kwashe na sanya masa na addu'oin a ciki, duk da ina ɗar-ɗar ɗin karya gane wajen buɗe murfin, dan haka nake ta kaf-kaf ɗin bashi ruwa yanzu da kaina. Dawowar Fahad ɗakin ya katse mana shirun da mukayi. Dan yana yin sallama yay tozali da Ummie dake zaune ina bama abinci ya ƙaraso cikin sassarfa ya wani rungumeta har sai da ta saki ƙaramar ƙara tana turesa. Ɗagowa yay cikin tsananin damuwa idanunsa share-share da hawaye yana kallonta. Itama kallon nashi take yi, sai kuma ta kauda kanta tare da zamewa ta kwanta ta juya mana baya. Ƙoƙarin komawa side ɗin data juya yayi, amma sai Mama Balki ta dakatar da shi ta hanyar riƙesa. Yayinda ni kuma ƙwallar tausayin ɗa da mahaifiyar suka cika min idanu.

Dai-dai nan aka turo ƙofar aka shigo. Tuni ƙamshin turarensa ya wani irin mamaye hancinanmu. Hakan ya samu ɗaga kai mu duka muka kallesa. Shima tsaye yay cak kamar wanda akama umarnin tsayawar. Yayinda Fahad yay wani kalar ɗauke kansa. Mama Balki ce tai ƙarfin halin masa sannu da zuwa. Da ƙyar ya amsa mata yanayinsa na ƙara komawa na ainahin stubborn ɗinsa. A cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara batare da ya karaso ba ya juya ya fita abinsa yana jan sirrin tsaki dake bayyana fushinsa. Harara Fahad ya raka bayansa da shi shima yana jan tsakin mai kauri. Sai kuma a hankali ya furta, “Mugu kawai azzalumi”.

Har cikin tsakkiyar kaina naji shigar zagin nan. Na ɗan kalla Fahad ɗin naga yanda yake wani cika yana batsewa. Maimakon naji haushinsa sai ya bani tausayi, dan hatta da jijiyoyin kansa duk sun fito raɗa-raɗa haka ma idanunsa sun wani bala'in kaɗawa jazur a ƙanƙanin lokacin nan. Kamar wanda aka tsikara shima ya miƙe zaram. Dai-dai nan Hayatu ya shigo ɗakin da sallama. Cak Fahad ɗin ya tsaya daga yunƙurin fitar da yake yi. Sai kuma murmushi ya ɗan kufce masa, da sauri ya nufi Hayatun yana faɗin, “Oyoyo sweet Yayana”.

Tuni shima Hayatu ya ajiye kayan hannunsa ya buɗe masa hannayensa suka rungume juna. Ajiyar zuciya na sauke a hankali, sai kuma na miƙe batare da nacema kowa komai ba na fita....

🩸🩸🩸🩸

Cikin yanayin gajiya ta shigo gidan. Ga damuwar dake a ƙarƙashin zuciyarta a kwanaki biyun nan game da rashin ganin Samraah. Tun a jiya bincikenta ya tabbatar mata da Samraah ce a sashen Awwab dai Hajiya Mammah da bata san an sallamota ba ta gani ba wata ba. Taso sanar ma Yallaɓai amma ta kasa hakan dan tana son ta fara sanin mi bincikensa ya samo masa akan yarinyar. In har wanda zata iya canja ra'ayinsa ne daga kasheta daya ambata sai ta fara shirinta. Idan kuma na wanda bazai iya canja ra'ayin nasa bane nan ma sai ta ɗauki mataki. Dan a wannan gaɓar bazata taɓa bashi goyon baya ba. Tanama Samraah wani irin mahaikacin so mai taɓa zuciya. Ita kaɗai tasan a halin matsanancin kishin da take ciki na Awwab a ƴan kwanakin nan musamman daga jiya zuwa yau.

Babu kowa a falon sai ƙamshi da sanyin ac. Tasan su Arwa sun fita yawonsu, dan Muhseen ne kawai ke zuwa makaranta yanzu a gidan sai Aneesa autar Hajiya Mammah ƙanwar Azizat kenan. Cikin rashin kuzari ta kama ƙarfen upstairs zata fara haura steps ɗin ta tsaya cak. Rawa jikinta ya nema fara yi sakamakon abinda idanunta ke kallo. Cikin wani irin bugawar zuciya da rawar baki ta furta, “Fahad!”.

“Yes Ummy. Surprise”.

Ya faɗa cikin fara'a yana ƙarasowa gareta. Cikin rashin kula da yanayinta ya bata side hug abinsa. Da ƙyar Hajiya ƙarama ta iya jan numfashi da kokarin controlling kanta. Amma ina jikinta karkarwa yake. Dan koda Fahad ya ɗago yana gaisheta sam bama fahimtarsa take ba. Sai da ya ɗan tanƙwaɓeta da zai gittata yana dariya sannan taji abinda yake faɗi na ƙarshe. “Oh Ummy mamakin ganina da alama ya sumar dake. Bari naje dai yanzu zan dawo karki faɗama su Azizat na dawo”. Daga haka yay wucewarsa ya barta a yanayin ƙaulani.

Sosai taji fitsarin dake a mararta na ƙoƙarin zubowa. Tuni ta saki handbag ɗinta a wajen ta juya ta fice a falon ƙafafunta na matuƙar rawa. Tana shiga motarta motar Hajiya Mammah na shigowa gidan. Ko bi takanta batayi ba ta wani irin yin reverse da mahaikacin gudu kamar ba'a cikin gida take ba ta fice har tana kusan takama ɗaya a cikin securitys ɗin ƙofar ƙafa ALLAH dai ya taƙaita yaja baya da sauri. Babu wanda ya kawo komai a ransa sai tunanin kiran gaggawa maybe ta samu daga asibiti. Dan sometimes takan yi irin wannan fitar idan hakan ta faru. Sai in ta dawo ta basu haƙuri da sanar musu abinda ya rikita tan. Shiyyasa kowa a gidan ke mata uziri da mata kallon innocent woman dako hannu ka saka mata a baki bazata ciza ba.

Wani irin mahaikacin gudu tayi ko'a titin. ALLAH dai ya taƙaita titin anguwa ne. Gashi kuma anguwan masu kuɗi ba wani yawan kai-kawon mutane ake samu ba, motocin ma sai jefi-jefi. Yanzu kam dama rana da wahala ka gani kasancewar duk ana wajen aiki. A cikin ƙanƙanin lokaci ta iso gate ɗin gidan yallaɓai. Horn ta dinga dannawa daya rikita maigadi, jikinsa har rawa yake wajen buɗewa. Ruɗanin da take ciki ya sata mantawa gaba ɗaya yau bata saka niƙaff ba. Sannan kuma da motarta ta amfanin ko yaushe ta shigo gidan bata ɓadda kama ba kamar yanda ta saba. Kasancewar a duka kamanni biyun na baɗini dana zahiri tana da power ɗin shigowa gidan yasa babu wanda yay mamakin ganinta sai dai mamakin yanda ta shigo. To amma idan suka auna da kafin zuwanta wadda tazo zasu iya kallon abin a wani abu daban kuma. A dai-dai ƙofar falon gidan tai parking, ko rufe motarta batayi ba ta afka ciki. Babu kowa a falon, sai tv dake magana ƙasa-ƙasa. Hannunta ta kalla da nufin neman waya, wayam babu handbag. Tunanin ta barta a mota ya sata jan tsaki. Juyawa tai da nufin ɗakko wayar dai-dai nan wanda zata fita ɗakowar dominsa ya fito. Baiyi mamakin ganinta ba, dan yasan zata iya zuwa ɗin dama..

Zaune ta kai dan wata irin hajijiya take ji na neman ɗibarta. Da ƙyar ta iya haɗa kalmar, “Fahad ya dawo, yanzu haka yana gida”.

Zaune ya kai shima a hankali batare daya ce mata komai ba. Sai ma file ɗin hannunsa daya ajiye yana mai dafe kansa da duka hannayensa biyu. Jin shiru baice komai ba ta ɗago ta kallesa. Muryarta har rawa take wajen sake faɗin, “Yallaɓai baka ji abinda na faɗa bane?”.

Wani irin murmushi ya saki, mai bayyanar da tsantsar ɓacin rai da tsufarsa. Ya ce, “Na jiki sarai, shima wanda ke bincike akan yarinyar nan ya kawo sakamakon yanzu”.

Bai gama rufe baki ba ta ɗauki file ɗin ta fara dubawa cikin rawar jiki. Abubuwa masu muhimmanci kawai take dubawa. Abu na farko daya fara jan hankalinta shine cikakken sunan yarinyar. Samraah Abdul-wahab Gwarzo. Na biyu aikin mahaifinta da sanadin rasuwarsa har ma da inda ya rasu. Na ƙarshe MATAR AURE. Rawa bakinta ya fara da ƙyar ta iya haɗa kalmar, “Ba...ban fahimci komai ba yallaɓai”.

Murmushi ya sake saki, sai kuma ya kalleta da idanunsa dake jazur kamar tsohon maciji. Musamman yanda tsufarsa ta sake fitowa fili sai taga har baƙinsa ma ya sake bayyana fiye dana baya mai tsananin shining ɗin hutu. Shima ɗin kallonta yake cikin ido, batare daya janye ba ya furta, “Ita ɗin ɗiya ce ga Abdul-wahab Gwarzo (jirgin mota)”.

Kaɗan ya rage zuciyar Hajiya ƙarama ta ɓaro. Ta wani irin miƙe zambar jikinta na karkarwa tace, “What! Jirgin mota? Drivern mahaifin Ummu-Hidaya da kenan?”.

Kansa kawai ya ɗauke daga kallonta alamar tabbatarwa. Cikin kaushin murya ya cigaba da faɗin, “Tabbas nayi kuskuren ƙin bibiyar bayan Abdul-wahab kamar yanda nake biye dana Ibrahim Alonso. Idan baki manta ba nayi hira da yarinya shekara ɗaya data gabata a Kano sakamakon turamin program ɗin bikin buɗe Company da Awwab yayi. Zargin akwai dalilin da yasa ya amsa mata zaiyi hira da ita alhalin bai taɓa yi da ko manyan channels ba yasa na baro India nazo danna tabbatar da ko akwai alaƙa a tsakaninsu. Tako ina bincikena babu ta inda wata alaƙa ta alaƙanta su, dan haka ban maida hankalina ga cikakken sunan yarinyar ba....”

“Wai kana nufin itace yallaɓai?”.

Hajiya ƙarama da gaba ɗaya take a gigice ta jeho masa tambaya cikin katsesa. Iska ya furzar mai kauri tare da miƙewa tsaye. Taku ya fara hannayensa duka biyu a goye ya ce, “Of course itace yarinyar”.

“Tashin hankali. To amma tayaya tazo Lagos bayan ma'aikaciya ce? Ta yaya kuma Lagos ɗin ma take zaune a Maash Mansion? A ƙarshen zance shine tayi aure bayan fasa aurenta da saurayinta da suka jima a tare. Abin tambayar anan waye ya auretan? Waye kuma yay kidnapping ɗinta kafin auren har sau biyu? Tabbas akwai abinda ya kawota Maash Mansion, minene shi?. Yallaɓai wlhy zan haukace, wane irin ruɗani da tashin hankali ne haka yazo mana a rana ɗaya? Gashi mun gagara magance batun likitocin nan abu sai ƙara nisa yake, duk da dai ba wannan bane kaɗai hope ɗinmu wancan ma zasu iya mana illa tunda ko ganinta bamayi a yanzu balle sanin halin da take ciki”.

Amaimakon amsa mata dukkan tambayoyinta da maganganunta a mugun fusace yay wurgi da ɗan abin deco.. ɗin dake a saman Centre table ɗin gabansu........✍️

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 thirty-four


......Mugun tsorata Hajiya ƙarama tayi har sai da ta rumtse idanunta da toshe kunnenta jikinta na rawa. Shima nashi

Please Login or Register in order to submit comment