Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

naku”.
“Tabbas Ummie. Dan komai ya fara buɗewa ne daga ranar bikin buɗe Company. Sai dai komawarki a halin ciwo a lokacin ya sake tayar min da hankali. Sai dai koba komai na fara fahimtar daga ina ainahin komai yake, duk da anyi yunƙurin daƙileni da sihiri fiye dana farkon daya raba tsakanina da ke. Aka kuma sake ta'azzara ƙiyayyata da Fahad. Sai kuma ALLAH ya shigo da Samrh rayuwata a lokacin...” tiryan-tiryan ya kwashe komai ya bata labari hatta aurensa da Samraah. Har zuwa wannan rikicin da ya faru na kwana biyun nan. Kuka sosai takeyi kamar yanda Fahad dake laɓe yana saurarensu yake yi shima. Hakama Samraah da ko Fahad bai gani ba kuka take yi. Dama tazo gaida Ummie ne, saɗaf-saɗaf ta koma da baya tunda ALLAH yasa kowa bai ganta ba.
Daga ƙarshe dai shima Fahad ya faɗa ɗakin. Rungume Maash yayi da Ummie yana mai basu haƙuri. Murmushi Maash da gaba ɗaya yanayinsa ya canja yayi yana mai shafa kansa.
“Kai zan bama haƙuri Fahad, dan na maka abubuwa da yawa marasa daɗi, na kasa riƙe amanar Ummie. Na kasa kula da tarbiyyarka. Ban san cinka ba bansan shanka ba balle muhallin da kake rayuwa. Duk da ina son yin hakan a ƙasan raina amma bazan iya ba. Akwai lokacin danai yunƙurin neman inda kake amma hakan ya gagara, sai da nayi jiyyar sati biyu. A randa nai maka mugun dukan daka bar gidan nan sai da nayi kuka naji sanyi a raina. Ka yafe min kaji Kiddo, dan wlhy ni kaina ban san duk taya nayi waɗan nan abubuwan ba sai da Abbah ya fargar da ni shi da Baba (Sheikh Muhammad ibn Khalipha Al-Hussain da Baban Hayatu). Amma duk da haka na gagara basu haɗin kan shan maganin da suka tabbatar min in sha ALLAHU suna fatan ya zama waraka a garemu”.
Kuka sosai Fahad ya sake fashewa da shi shi da Ummie. Sosai ya rungume Maash fiye da farko. “Ni Yaya bakamin komai ba. In ma kamin na yafe maka. Dan koda baka yimun da hannunka ba Yaya Hayat na mun komai. Kuma koda zanji haushi yana sanar min da kuɗinka yamun. Wlhy bazan taɓa yafema mutanen nan ba. Kuma ni dan ALLAH ku gaya min waye-da-waye ALLAH sai na musu yankan kifi”.
Dariya Ummie ta sanya, yayinda Maash yay murmushi da dungure masa kai. “Kai bakinka baya gajiya da ambaton yanka mutane?”.
Cike da shagwaɓa Fahad ya ce, “To yaya ai kaima dai jiya kace zaka yanka min”.
Yanzu kam dole sai da Maash ya ɗan dara da faɗin, “ALLAH ya shirya min kai. Ni tadani naje na duba Matata kaji”.
Cike da shaƙiyanci Fahad ya ce, “Uhhm su Yaya fa an zurma da yawa. Ummie ki ƙara godema Aunty Samraah ita babbar ƴar su ce tunda ta kamo babban kifin nan naki a kogi cikin ƙanƙanin lokaci”.
Mi Ummie zatai banda dariya. Maash ya kama kunnen Fahad ya murɗa har sai da yay ƙara sannan ya sakar masa ya fice yana murmushi kawai...

Rungume Ummie Fahad yayi cike da farin ciki ya ce, “Wlhy Ummie da gaske yana bala'in sonta. Kigafa yanzu murmushi baya masa wahala.”
“Kaima saika dage ka samo min wadda zata maka irin wannan kamun kaji Autana”.
“Kwantar da hankalinki ke dai Ummie ai ni biyu ma zanyi rana ɗaya”.
“Biyu fa Auta?”.
“Yes Ummie na, ba gara na more da ƙyau ba”.
“ALLAH ya shiryeka”.
Ta faɗa tana dungure masa kai. Dariya yayi, sai kuma ya marairaice mata wai ta bashi labarin abinda ya faru a bayan dan shi bai taɓa tunanin ciwonta nada alaƙa da wani abu ba. Saboda babu wanda ya taɓa zama ya nuna masa.......✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒚_


......Ƙarfe biyu da rabi na rana bayan jami'an tsaro sun gama bincike-bincikensu suka saki labarin kama Commondo da Madam Jannifer. Tare da samo Paah da aka tabbatar da Commondo ɗin ne yay kidnapping ɗinsa ya kuma kashe drivern sa. Ita kuma Jannifer suna kan bincike domin sanin dalilinta na yunƙurin sake zuwa domin ɗaukar Paah ɗin a daren jiya.
Sakin wannan labari dai-dai da isowar tawagar motocin Maash har bakwai asibitin. Dan gaba ɗayansu suka taho hatta da Falaq mai jego ba'a bari ba. Samraah ma ce yaso hana ta biyosu. Aiko ta saka masu kukan taɓara. Sam baya son ganin damuwa a tattare da ita, dole ya barta ta biyosun amma ya saka TJ yin tuƙi a hankali. A waje wajen motocin suka bar wasu guards ɗin nasa. Wasu kuma suka take masu baya har ciki. Ummie da Mama Balki ne a gaba su Sha'aibu na jagorantarsu. Sai Falaq da Samraah biye da su, Samraah na ɗauke da Baby Awwab. Maash da Hayatu sai Fahad da Hafizzullah na take musu baya. A ƙarshe sauran guards ɗin. Tako ina suka ratsa daga ƴan dubiya har ma'aikata da patients kallonsu sukeyi. Ɗakin da aka kwantar da Baba prof suka shiga. Yana kwance sharkaf, a kallo ɗaya zaka fahimci ya jigata da cizon kunamar nan. Ga wani uban ƙullutu a goshi da alamu suka nuna ya buga kanne a bango maybe waje neman ceton kai. Ƙafafunsa a wawware suke an yafa masa duvet kamar dai babu wando ne ta maganar Lado(🥱🤭😝).

Ummie ce ta fara gaisheshi da masa yaya jiki. Idanu kawai ya zuba mata batare daya iya amsawa ba. Ba kuma dan baya magana ba sai dan bakin nasa ya gaza koda motsi ne, sai kallon tsana da gargaɗi yake mata kamar zai cinyeta da idanun. Murmushi ta sakar masa tamkar bata fahimcesa ba ta ce, “ALLAH ya kiyaye na gaba”.
Sai su Mama da su Samraah suka gaidashi a jimlace. Fahad kam ko kallon inda yake baiyi ba. Maash ma dai da farko bai tanka ba, sai da ya mula dan kansa ya wani taka cike da ƙasaita da izza hannayensa duka a aljihu ya matsa gaban gadon. Zama yay a kujerar gabansa yay crossing ƙafafunsa tare da folding hannayensa a ƙirji ya wani zuba masa cat eyes ɗin nan nashi masu kaifi da kwar jini. Ji kawai baba prof yay wani abu na tsarga masa. Dan gaba ɗaya kamanin Awwab ɗin rikiɗa masa sukai tamkar Ibrahim Alonso.
A daƙilen nan nashi cike da manners ya furta, “Ya kake?”.
(Ya kake?) Baba prof ya maimaita a zuciyarsa, zuciyarsa tasa na masa zogi. Da ƙyar ya iya buɗe bakinsa ya bashi amsa da, “Awwab kasan a gaban wa kake kuwa?”.
Murmushi rainin wayo Maash ɗin ya wani saki. Sai kuma ya kalla haɗaɗɗen agogon hannunsa mai shegen tsada yana ɗan wani laɓe small pinkish lips ɗinsa. Hannun ya sauke yana ɗan juya idanunsa ya maidasu ga Baba prof ɗin. Kansa tsaye ya furta, “Mahaifin Paah ɗina”.
“Mahaifin Paah ɗin ka?”.
Baba prof ɗin ya sake maimaitawa a fili yana wani tsare Maash ɗin da idanunsa. Ta cikin wando kuwa saboda harbi da wajen ya sha baya iya riƙe fitsari sosai yanzu ma sai da ya tsillo. Dan wani banzan kallo Maash ya sake masa yana faɗin,
“Bayan hakan ko akwai wata alaƙar? Oh sorry ashe yaron Grandpa ɗina ne kuma, sorry Mr Adams K/Mashi”.
Tsuuuu!!
Fitsari ya ɗan sake kufcewa Baba prof again. Jikinsa ko har ɗan rawa yake duvet ɗin da aka lulluɓa masa ne kawai ya rufa asiri. Ashe tsugunne bata ƙare ba. Dan Maash na rufe baki Fahad da idanunsa ke kan television ɗin ɗakin ya ce, “What!! Uncle Abdullahi!!”.
Yanda ya ambaci sunan da ɗan zabura yasa hankalin kowa komawa can banda Maash da bai ko motsa ba. Uncle Abdullahi ɗinne kuwa ke bayani matsayin babban ɗan sandan sirri da yaransa suka samu nasarar cafke Commondo da Madam Jannifer a daren jiya. Ta re da tabbatar da sun amso Alhaji El-Mu'azz k/mashi. Babu wanda baiyi mutuwar tsaye ba a ɗakin, wasu ma har murza idanu suke domin son ƙara tabbatarwa. Kasa haƙuri Fahad yay jikinsa na tsuma ya tako gaban Maash da ke zaune baida alamar nuna yasan mike faruwa. Amma kuma kunnesa na jin dukkan bayanin Uncle Abdullahi ɗin. Riƙo hannunsa Fahad yayi murya na karkarwa ya ce, “Kaga fa Uncle Abdullahi wai ɗan sandan sirri. Imagine”.
Karo na farko Maash ɗin ya ɗago. Idanu ya zubama Fahad ɗin, sai kuma ya janye a hankali ya maida ga television ɗin. Fuskar Uncle Abdullahin kawai ya zubama idanu, sai kuma ya saki murmushi tare da lumshe idanunsa ya sake buɗewa akan Fahad. A taƙaice ya furta, “Na gani”.
Ba Fahad ba hatta Ummie sai da ta waro idanunta waje. Mama Balki kam ai baya tai ɗan mamaki sai da Hafizzullah ya ɗan riƙota. Babu zato suka ji an faɗo ƙasa timm. A tare duk suka juya, mi zasu gani Baba prof ya sulmiyo ƙasa dan kiɗima. ALLAH ma ya taimaka jikinsa cikuykuye yake da duvet da anyi abin kunya. Rawa jikinsa yake sosai yana nuna television da yatsansa. Magana yake son furtawa amma ko harafi guda ya gagara fita a bakin nasa. Sai kawai ya zube gaba ɗaya raƙwam alamar suma.
Hayatu ne yay ƙarfin halin kiran doctor, akai kama-kama aka maida Baba prof saman gado. Dole kowa ya fito aka barsa da doctor. Daga nan suka shiga inda aka haɗa su Hajiya Mammah su duka. Sukam da sauƙi dan tunda akai musu alluran kashe dafi ta sauka. Barcin da aka sakasu yine ya jasu har zuwa yanzu. Sai Hajiya ƙarama ce dai ansha wahala. Sun samu suma duk sun ɗimauce da labaran da ake nunawa a television. Ba labaran ne yaja hankalinsu ba ganin Uncle Abdullahi a matsayin ɗan sanda. Sun samu itama dai Hajiya Ƙarama na mazarin jiki. Dan abu biyu ne ya ɗimautata zuwa uku. Ganin an kama Commondo da Madam Jannifer, sai Uncle Abdullahi matsayin ɗan sanda babba kuma na sirri. Ƙarin tashin hankalin ma wai shine ya kama su commondo. Itama dai sai da aka nemo likita kanta. Daga nan ɗakin da aka kwantar da Paah muka fara shiga. Ɗakine na musamman dake zagaye da tsaro na musamman. Barci yake shi kam hankalinsa kwance. Duk da ya rame alamar yasha wahala. Rawa jikin Ummie ya fara. Ta ƙarasa gaban gadon da sassarfa. Tuni ta manta da wanda ke tare da ita batama san ta kai dirƙushe ƙasa ta kamo hannun Paah ɗin ba hawaye masu zafi na rige-rigen sauka mata a kumatu. Karyayyar muryarta na rawa ta furta, “Azz! kaine haka? Ya Arrahaman”. Sai kawai ta saki kuka tana mai rungumesa.
Da baya-baya na koma na fice a ɗakin, dan haka kawai naji tausayin Ummie ya masifar shigata. Karo naci da mutum, dan haka na ɗaga kai da sauri na kalleta ina mai ambaton ban haƙuri gareta. Itama dai-dai ta ɗago zata bani haƙurin. Ban iya na ƙarasa ba ni, sai idanu dana zuba mata zuciyata na wani irin sauka a hankali. Raɓani tai zata wuce na damƙo hannunta, sai ta juyo a girgice zatai magana nai azamar girgiza mata kaina da zipping ɗin bakina alamar tai shiru. Cikin rawar jiki ta haɗiye maganar da take son yi kuwa. Ni kuma naja hannunta muka bar ta wajen duka. Sai da muka bar ƙofar ɗakin na tabbatar ba idon kowa ata inda muke sannan na ce, “Miye sunanki?”.
Sosai fuskarta ya nuna alamar mamakin tambayar da nai mata. Amma ganin na haɗe fuska babu alamar wasa a tattare da ni, ga shi na tabbatar tasan wacece ni dan yanda muka shigo suna kallonmu ko ita bata gammu ba nasan za'a bata labari, ga kuma tranding da hotunana dana Maash sukai a kwanakin nan koma nace suke kanyi. Amma duk da haka sai da na ƙara mata da faɗin, “Sunana Samraah Abdul-wahab Gwarzo, Mrs Awwab El-Mu'azz Maash. Nasan kin sani. Minene sunanki?”.
Kanta ta shiga jinjina min tana ƴan waige-waige, mutyarta na karkarwa ta ce, “Murjanatu Usman”.
“Masha ALLAH Murjanatu kwantar da hankalinki ba wani abu bane ba, magana nake son nayi da ke amma bazai yiwu anan ba. Ko zaki iya bani number naki?”.
Yawu masu kauri ta haɗiye da ƙyar. Cikin ƙara daburcewa ta ce, “Dan ALLAH Maa kiyi haƙuri idan akan turekin nan da nayi ne. Wlhy ban san kin tahoba sam shiyyasa”.
Murmushi na mata dan naga ta firgice. Cikin son dai-daita yanayi na na ce, “No kwantar da hankalinki ba wannan bane ba. Tambaya zan miki akan wani abu daya shafi mace mai ciki, amma bana son yi anan shiyyasa”.
Da masifar ƙarfi ta sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta sake sauke numfashi da faɗin, “Wlhy ranki ya daɗe harna tsorata. Kin san abunne akwai tsoro balle ku manyan nan. Na zata ko na miki wani laifine. Ba damuwa ko gida kike son nazo zanzo na same ki ai. Sai dai matsalar baza'a barni na shiga ba”.
“No karki damu zansa azo har nan ɗin a ɗaukeki. Ko zaki iya bani number ɗinki?”.
Cike da zumuɗi ta amsa min tana amsar wayar hannuna. Ni saima taso bani dariya. Dan hannunta har rawa yake wajen loda number ɗin. Amsa nayi nai saving. Da murmushi na ce mata, “Zaki iya ji kirana akoda yaushe in sha ALLAHU. Amma fa maganar nan ta tsaya iya ni da ke kawai. Dan na fahimci kina da hankali da nutsuwa tun wancan kwanciya asibitin da nayi shiyyasa”.
Sosai ta sake washe baki cike da farin ciki tana Murmushi. Da ga haka muka baro wajen. Sai da naji shock da hango Maash tsaye da alama ta inda zan fito yake son gani. Amma sai na dake abina a nutsena na ƙarasa inda yake. Batare da nayi magana ba na zare wayar da yake dannawa daga cikin hannunsa. Sai da yana wani sakanni kafin ya ɗan ɗago cat eyes ɗinsa ya kallan. Ido ɗaya na kashe masa cike da salon basar da shi na ce, “Tsaiwa anan kamar wani dogari”.
Maimakon tanka min sai ya wani cigaba da kallona, kusan minti ɗaya sannan ya motsa lips a hankali ya furta, “Let's go”. Yana kama hannuna. Banda zaɓin daya wuce bin nasa. A haka muka dinga keta mutane ana kallonmu. A karan farko naji banji kunyar hakan ba. Sai dai a raina ina jin wasu fa zasu iya ɗaukar hotonmu musamman a wannan gaɓar da dama ake neman labari a kammu. Kamar ko ina gani har hanji, dan bamu ƙarasa gida ba sai ga hotunanmu sun fara yawo a media. Sosai na tsarkake sunan UBANGIJI da jinjina halin gulamar mutane da ƙaikayin hannayensu nason yaɗa abinda sam bai shafesu ba. Dan su birge ne ko dan ace a bakinsu aka fara ji oho musu........✍️


Zazzabi ya tasani gaba posting yanzu sai a slow. Ayi hakuri dai in sha ALLAHU muna gab da tsargewa kowa ya huta🥲.


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒚-𝒐𝒏𝒆_


.......Washe gari tunda Baba prof da Hajiya ƙarama suka dawo hayyacinsu duk sai suka matsa a sallamesu a safiyar. Iya ƙoƙari doctors ɗin sunyi dan ganin sun fahimcesu musamman ma Baba prof da tai masa illa a inda ya kamata ya samu kulawa amma sam hakan yaƙi yiwuwa. Dole suka haƙura suka sallamesun. Dama shi Paah tun a daren Maash yasa aka sallamesa saboda Ummie ta tada hankalinta akan zataje asibitin zaman jiyyarsa. Shiko bai amince da hakan ba. Shiyyasa ya yarda da a dawo da Paah ɗin gida likitan ya cigaba da zuwa dubashi anan.
Kai tsaye sashen Maash ɗin aka kaisa ɗakin da Ummie take. Sai ganinsu kawai tayi. Sosai ta nuna farin cikinta taita sanya musu albarka. Su dai basu ce komai ba musamman ma Maash da ke matuƙar jin zafin Paah har yanzun. Isma'il ne yay kiran Maash ya sanar masa ai an sallamo Baba prof gashi a gida. Baiyi mamakin hakan ba, dan haka baice komai ba sai murmushi. Lokacin da kuma yake fitowa ya shiga ya duba Paah ya fito zasuyi break fast su Fahad ke sanar da itama Hajiya ƙarama ta dawo gida yanzun nan. Dama su su Hajiya Mammah tun jiya aka sallamosu. Uffan shi dai Maash baice ba, sun kuma san bazai ce ɗin ba daman....

✨✨✨✨

Iya faɗin yanayin da Baba prof ke ciki kawai sai dai kintace, dan a matuƙar harmutse yake. Duk da yanda yake jin rashin ƙarfi a jikinsa suna isowa gida wanka yay tare da yin shiri cikin manyan kaya. Sai da ya fito sannan ya tuna babu drivernsa fa a gidan yanzu. Gashi bai san ina Commondo ya kaisa ba. Zaune ya kai cikin kujerar falon kawai yay shiru. Sai da yaja tsahon lokaci a haka kafin ya ɗauka waya yay kira. Ana ɗagawa da ga can batare da ko sallamar da akai masa ya amsa ba cikin bada umarni ya furta, “Ka sameni a gida yanzun nan”. Ƙitt ya yanke kiran.
Sake zabga tagumi yayi na wani lokaci, sai kuma ya miƙe ya fara safa da marwa a falon cikin rashin ƙarfin jiki. Tsahon awa ɗaya ciff sannan Uncle Abdullahi ya iso gidan. Ya nuna mamakin ganin mahaifin nasa a gida, kasancewar duk sun san bai isa a sallamesa ba haka da wuri dan jikin nasa da saura. Ga Doctors ɗin ma sun tabbatar da yana buƙatar hutu..
“Baba ina kwana? Yaya ƙarfin jikin?”.
Ya faɗa cikin ƙoƙarin danne komai dake a ransa. Shiru Baba prof bai amsa ba, sai da yaja lokaci mai tsaho sannan ya juyo a wani irin yanayin mai wahalar fassara yake kallon sa. Kasa jurewa Uncle Abdullahi yay ya duƙar da kansa ƙasa, ya san minene laifinsa, ya kuma shirya amsa komai da za'a tuhumesa da shi. Kamar ko yanda yay zato a zafafe Baba prof ya furta,
“Abdullahi!! Wanene ni a wajenka?”.
Sosai tambayar ta bama Uncle Abdullahi mamaki, amma ya daure kansa a ƙasa ya amsa da, “Baba mahaifina ne kai, wanda yay sanadin kawoni duniya, ya tarbiyyace ni ya tufatar da ni da ciyar dani a lokacin ƙuruciya da kula da ilimina duk bisa amincewar UBANGIJI”.
“Ban yarda da hakan ba Abdullahi. Ƙarya kake yi!. Da ace ni ɗin mahaifinka ne da baka zaɓi wata rayuwa bayan idanuna ba. Da ace ka yarda ni Adamu ni na ciyar da kai, na tufatar da kai, na biya maka kuɗin makarantar da har kayi kaurin wuyan aikata abinda ka aikata to lallai fa da baka kasance wani abu a bayan ganina ba. Abdullahi idan ban manta ba ni da kaina na hana ɗan uwanka aikin interpol a sanda ya ƙwallafa ransa. Amma shine kai ka zagaye ka zama jami'in sirri bada sani na ba. Hakan na nufin akwai wani abu a ranka ke nan ko kake shiryawa”.
Hankali tashe Uncle Abdullahi ya ke girgiza ma Baba kai. “Wlhy Baba sam ba abinda kake zargi bane ba. Kuma a lokacin daka hana Yaya Mu'azz zama jami'in interpol na ɗauka wannan aikinne kawai baka ra'ayin muyi. Zama wannan jami'in kuwa wasu dalilai ne suka kaini ga zama hakan. Ban kuma ɓoye ba domin wata manufa tawa sai dan yanayin aikina kenan. A jiyan ma dole ce ta tilasta ni fitowa har duniya ta sanni da wannan matsayin. Amma idan har na ɓata maka rai ka gafarceni dan ALLAH”.
Shiru Baba prof kamar bazai tanka masa ba. Sai da ya mula dan kansa kafin cikin bada umarni ya furta, “Bazan taɓa aminta da kai ba Abdullahi a yanzu sai na tabbatar. Sai dai a matsayina na mahaifi ina baka umarnin ka saki wannan yaron Commondo....”
A bala'in firgice Uncle Abdullahi ya ɗago yana kallonsa. Har bai san sanda ya furta, “Baba saboda mi? Akan mi kuma zanyi hakan bayan shi ɗin mai laifi ne. Dukkan bincikenmu ya tabbatar mana da cewar da hannunsa a yin kidnapping ɗin Yaya Mu'azz. To wai kai minene ma haɗinka da shi da har kake so a sakesa Baba?”.
“Babu ruwanka da alaƙar dake tsakanina da shi. Kidnapping Mu'azz kuwa ni da kaina zan hukunta shi na kuma ji ba'asinsa nayin hakan”.
Wani murmushin ɓacin Rai Uncle Abdullahi yay da faɗin, “Baba to ai kai ba jami'in tsaro bane. Dan mi zan barka kayi hakan? Sannan babu ta inda dokar ƙasata ko aikina suka bani damar sakin Commondo a halin yanzu. Saboda yanzu haka ana kan binciken mugayen ayyukansa ne ma. Shawarar dazan baka ma shine Baba kai gaggawar barranta kanka da shi idan ma wata alaƙa ta taɓa alaƙantaku. Dan wannan mutumin mugayen ayyukansa zasu iya kaisa ƙasa dama duk wanda yake tare da shi. Ka gafarceni Baba na barka lafiya”. Ya ƙare maganar yana miƙewa ya fice. Dan gaba ɗaya kansa juya masa yake. Idan bai bar gaban Mahaifin nasa ba zai iya rasa control ɗinsa ne gaba ɗaya...

Ko sau ɗaya Baba prof ya kasa motsi. Sai kalaman Uncle Abdullahi ne ke masa wani irin amsa kuwwa acikin kunne har bai ma san ya fita a falon ba. Cigaba da jin sautin muryar Uncle Abdullahi na masa ihu cikin kunne ya sakashi fassa wani ihu shima yana wancakalar da Centre table ɗin gabansa. A guje wasu a cikin ma'aikatan

Please Login or Register in order to submit comment