Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Cike da shagwaɓa ta amsa masa tana miƙa masa ƙafarta da tayi fushi. Amsa yay yana danna mata a hankali suna ƴar hirarsu. Hirar data saka Abban kwasar dariya dan Halimen nata zuba masa shirmen turancinta ne data dage tana koyo. Duk da ma dai a tsakanin nan makarantar ta gagareta saboda bata jin daɗi...
Kullum sai Abba yayi waya dasu Samraah yanzu. Ƙoƙarin jawosu jikinsa yake yi domin ya kwaranye abinda ya cusa musu a baya. Su kuma sun saki jiki da shi da alama sun jima suna buƙatar hakan daga garesa amma ya gagara musu. Har dai ranar da su Samraah zasu wuce Spain Mom bata sani ba. Dan Abba ya daina sanar mata komai daya shafesu. Idan ma shawara yake nema Halime ce. Saboda zai iya cewa itace ta dawo dashi kan hanya akan batun su Samraah ɗin. Tunda ta fahimci komai kullum cikin masa nasiha take kamar ba yarinya ƙarama ba. Tun yana fushi da ganin ta shiga hurumin daba nata ba har ya fara fahimtarta. Sannu a hankali ya fahimci kuskuren da take ƙoƙarin nuna masa. Shiyyasa yanzu wani bala'in ƙara son yarinyar yake. Gata dai da ƙarancin shekaru sai hankali da sanin ya kamata. Fatansa dai ALLAH ya sauketa lafiya....

✨🌿✨🌿✨

“Wai yaushe ne batun tafiya Lagos ɗin nan Daddyn Attahiru. Tunda abubuwa sun lafa inaga ya kamata muje muyima bawan ALLAHn nan godiya. Na kuma sake neman gafararsa akan kuskuren dana tafka. Wlhy gaba ɗaya ko'a zuciyata na tuna kunyar kaina da kaina nake ji”.
Murmushi Dad dake zaune idonsa a television yayi, sai kuma ya ɗan kalla Mamyn tare da amsar kofin black tea ɗin da take miƙo masa. Sai da ya kai shayin bakinsa ya ɗan sha sannan ya sauke numfashi. “Karki damu zamuje, sai dai tama ƙara tsayi. Dan yau dana bincika ake sanar min shi da iyalinsa da mahaifiyar tasa duk sun wuce Spain. Dole muyi haƙuri har ALLAH yay musu dawowa.”
“Tofa, ba kwana biyu daya wuce kake cemin kun gama magana da PA ɗin nasa ba zamu je a satin nan ba. Yaya akai hakan to?”.
“Kin san manyan nan barin ƙasa tamkar zuwa bayi ne su fito suka maidashi. Balle shi Maash dake da jiragen kansa ma. Haka dai zamuyi haƙurin har ALLAH ya maidosu lafiya. Yanzu yaya batun shi Mansoor ɗin? Kin tuntuɓesa akan batun yarinyar nan ya amince? Dan so nake a haɗe bikin nan dana ɗan uwansa kawai a wuce wajen kowama ya huta naji da yarana mata suma”.
Murmushi mai ƙayatarwa Mamy tayi, muryarta a sanyaye ta ce, “Ni kasan har yanzu baya wani sakin jiki da ni. Daga gaisuwa dai shike nan. Amma Attahir yace min yaga suna waya sosai da ita. Har yana cemata a weekend ɗin nan zai sake shiga Maidugurin su gaisa. Kaga kuwa idan bai amsheta ba ai bazai ce zai koma gidansu ba bayan zuwan da mukayi muduka ko”.
“Eh gaskiya hakanne kam. ALLAH to ya ƙara daidaitasu. Haka zamu cigaba da masa addu'a ALLAH ya cire masa son ita waccan yarinyar. Dan ta masa nisa sosai sai dai haƙuri kawai. ALLAH kuma ya bamu ikon gyara kurakuranmu baki ɗaya”.
“Amin” Mamy ta amsa muryarta na sake rauni. A haka Attahir da Mansoor suka shigo falon. Da alama daga wani wajen suke a taren. Kowannensu ledar hannunsa ya ajiye. Kafin su gaida iyayen nasu. Da kulawa suka amsa musu, Attahir ya cigaba da faɗin, “ALLAH duk mun gaji. Yanzu ni da ɗan gata ne Mamy sai ki bani shayin nan na Dad mai zafi nasha na more. Amma nasan ba'a sha miki shayin miji”.
Dariya Dad da Mamy sukayi saboda yanda Attahir ɗin ya ƙare maganar abin tausayi. Yayinda Mansoor yay ɗan murmushi kawai dan yanzu ya koya miskilanci. Kofi Mamy ta ɗauka ta saka masa shayin tana faɗin, “A'a babana ai sai na baka. Nasan mika sayo min nima. Ai ba'a hana mai badawa. Man kaima zaka sha ko?”.
Ta maida hankalinta akan Mansoor. Kai kawai ya girgiza mata alamar a'a. Sai ma ya yunƙura zai tashi Attahir ya kamasa ya maida yana harararsa. Badan yaso ba ya koma ya zauna yana sauke ajiyar zuciya. Cikin tsaresa da ido Attahir ya ce, “Yaya mukai da kai ne?”.
Kai Mansoor ya ɗan sosa, sai kuma ya haɗe hannayensa biyu alamar ban haƙuri. Murya a karye ya ce, “In sha ALLAH zan gyara kayi haƙuri”.
Kai kawai Attahir ɗin ya jinjina masa, shi kuma ya maida hankalinsa ga Mamy murya a sanyaye ya ce, “Mamy zan sha”. Murmushi ta sakar masa idanunta na cika da ƙwalla. Haka ta zuba musu kowa ta bashi cike da kulawa. Daga haka suka cigaba da hira. Tun Mansoor na jefa ɗaɗɗaya har dai ya fara sakin jiki. Harma hirar ta koma fannin shirin auren Attahir, daga haka shima Dad ya takalo masa nasa batun da Salimah. Da farko ya ɗan nuna shi ba sonta yake ba, sai da suka dinga masa nasiha da lallashi sannan yace zai ƙara nazari. Abinda ya yanke zai sanarma Attahir. Sun jin daɗin hakan, suka kuma bisu da addu'a su duka........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒏𝒊𝒏𝒆𝒕𝒚-𝒇𝒊𝒗𝒆_



*_Wai ni Balki ina duk masoyan Bilyn Abdull ɗin nan dake a manhajar Instagram da TikTok ne?🤔? Kai jama'a gaskiya da kunya ace account na Bilyn Abdull a Instagram da TikTok iya kar fallowers ɗin kenan🥲😣. Ina masoyan facebook ɗin nan dana WhatsApp, Please a fito mana ai fallowing ɗina. Accounts ne na Bussines ko bazaki/zaka saya ba zakaga abinda ya burgeka ko kalarka ka nema a inda kake. Maza ku garzayo BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING kodan kashe kwarkwatar idanunku ku more kallo iya kallonku da kaya ƴan yayi cikin farashi mai sauƙi da rahusa. Muna bada sari, muna adashen gata, muna sai da ɗai-ɗai. Ka gani su burgeka, ka saka ka birge mai kallonka sai Bilyn Abdull online shopping. Bari muga akwai ƙaunar kodai-kodai....😉🫣. Ga link nan naga accounts ɗin nan biyu kamar zasu fashe da fallowers 😘😘😘😍😍👍🏻👇🏻_*.

*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

_Ina masu son zuwa ganin likita ko yawon buɗe ido ƙasar Egypt?. To ku garzayo munada hanya mai sauƙi ta sama muku sauƙin tafiya cikin ƙa'ida da bin dokar ƙasa. Katafi anan cikin aminci, ka dawo kuma cikin aminci. Wajen kwananka a can zamu tanada, asibitin da zakaga likita duk zamu tsaya maka da tsayawar UBANGIJI. Hakama yawon hutawa zamu zame maka jagora. Kai ko hanyar zuwa domin sayo kaya duk muna da ita. Kai dai kawai kazo garemu kaga aiki da cikawa da iznin ALLAH. 09032345899. A nememu tanan ga masu buƙata, dan ALLAH serious bama son latsi ko wasa dan ba wasan muka fito ba 😂😍👍🏻._



.........Isowar mu ƙasar Spain bata zame mana cikin daɗin rai ba. Dan daga airport ma asibiti aka wuce da Maash. Abu kamar wasa ashe dai ciwo ke cinsa sosai yana dannewa. Sai ɗan jigatar tafiyar nan ta sake ruɓu-ruɓu da shi. Koni mai fama da ciki ban kaisa takwarkwashewa ba. Duk da nima dai sai da suka bani gado ba wasu awwani. Bayan komai ya dai-daita muka wuce gida aka barsa nan dan dokarsu babu mai jiyya. Dan nima ina buƙatar nutsuwar. Gida ne a cikin estate da ya amsa sunansa gida. Gida na farko muka shiga, hakan ya sakani sauke ajiyar zuciya, dan in ba haka ba wannan ai sai ka rikice saboda ginin duk iri ɗaya ne ya tafi reras abin sha'awa. Yay min ƙyau da tsari sosai. Ƙaton falone a farko sai gefen haggu da dama daya zama gidan kamar wani sashe biyu. Sai upstairs. Mun sami masu aiki biyu, mace da namiji, cikin girmamawa suke mana sannu da zuwa. Kafin su mana bayanin tsarin gidan. A take Hayatu yace ni na wuce sama, dan nan ne ɗakin Maash yake. Sai Ummie da dama tana da ɗakinta itama dan sun ɗan taɓa zaman jiyyarta anan ama lokacin ne Maash ɗin ya sai gidan. Itama ya rakata nata a side na hannun dama dake dauke da bedrooms huɗu, sama biyu, ƙasa biyu. Ita zata zauna a saman ne, ɗayan ɗakin kusa da ita tace Falaq ta zauna nan ita da Bahijja, dan tace cikakken wankan jego zata fara mata ta gaji da wannan gantallen jego nata kadama Ya Hayat ya saka ran zata bashi yanzu. Dariya muka saka sosai yayinda Hayat ke faman shafa ƙeya. Ɗakunan ƙasa kuma Mama Balki da Baba suma aka basu. Sai Fahad da Hafizzullah suma a side na haggun aka basu sama. Hayat kuma ɗakunan ƙasa koda dai Ummie ta bashi ƴar matarsa ga inda zai fake nan. Hakan yayi sosai. Dan haka babu wanda yaja zancen kowa ya tafi inda aka bashi.
Sosai saman yay min ƙyau da ƙyatar da ni. Falo ne madaidaici sai bedroom guda ɗaya tal. Babu kuma ta inda muke da alaƙa da side ɗin bedrooms ɗin su Ummie da nasu Fahad. Komai tsaf yake kuma fari tas kamar kaci. Na dai samu nayi wanka na kwanta dan barci ne a idona sosai. Dama kuma likitocin sun ce a barni na huta sosai. Ban samu nutsuwar fahimtar gidan yanda ya kamata ba sai washe gari. Alhamdullah na tashi jikina yay daɗi ba kamar jiya ba. Sai kuma kewar mijina da son zuwa na ganshi amma ina jin kunya. Haka dai na daure a munafunce na tambayi Yaya Hayat. Shine yace na kwantar da hankalina zuwa anjima zai kaimu mu gansa. Naji daɗin hakan. Haka kuwa akai zuwa yamma muka je muka dubashi, yanama barci. Haka muka sakance kullum muna zuwa mu dubashi, wataran yana ido biyu wataran barci. Randa yake ido biyu ya dage nice zan masa komai, babu yanda na iya haka nake yi ina jin kunya har mu taho. Satinsa ɗaya aka sallamesa ya taho gida shima, dan ya matsa likitocin su sallamesa kin san ya tsani zaman asibiti. Murmushi kawai na ɗanyi lokacin da Hayatu ke sanarma Ummie ina mai jin daɗi a raina. Nima nafi son ya dawo gidan na bashi kulawa da kaina ai. Kamar ko yanda Hayatu ya faɗa da yamma sai gasu da shi. Kowa ya nuna farin cikin ganinsa. Bayan sun gaisa da su Ummie muma muka gaisheshi da masa yaya jiki. Da kai kawai yake amsa mana kafin ya tashi ya haura sama. Kasa tashi nayi dan kunyar idon su Ummie sai da Mama Balki tamin wayon maya tace na tashi ga abincinsa can an shirya na kai masa.
A bakin gado na samesa zaune ya zubama ƙofar ido kamar dama ni yake dakon shigowa. Ina shigowar ya wani ɗan lumshe idanunsa da sake buɗesu a kaina. Hannu ya miƙa min alamar nazo garesa. Banyi musu ba kuwa. Saman cinyarsa ya ɗaurani tare da rungumeni muka dinga sakin ajiyar zuciya. Mun jima a haka sannan cikin raɗa nace masa, “Yaya jikin?”.
Maimakon amsa min sai ya ɗagoni yana kallon fuskata. Tare da kai babban yatsarsa saman lips ɗina ya ɗan shafa. Idanuna na lumshe a hankali, dan yanda yake zagaya yatsar tashi sai nake jin tsigar jikina na tashi. Saukar hannunsa saman cikina ya sani buɗe idon. Muryarsa a ɗashe ya furta, “Yaya little Ummu-Hidaya?”.
“Tana lafiya, tare da yima Abbunta addu'ar samun lafiya mai ɗorewa. Ta yi kewarsa kuma matuƙa”.
Wani ɗan langaɓar da kai yayi gefe yana sake ƙanƙance idanu. Jinai sam bazan iya jurar kallon ba na faɗa jikinsa kawai na ƙanƙamesa tare da haɗe lips ɗinmu waje ɗaya....

Rayuwa a Spain wata irin rayuwace da kowa a cikinmu bazai manta da ita ba. Dan mun haɗu ne mun gina wani farin ciki a zukatan junanmu da har abada bazamu manta ba. Idan ka gammu bazaka taɓa ɗauka mu ba jini ɗaya bane. Mama da Ummie sun zama iyaye. Baba ya zama Uba. Maash da Hayat sun zama manyan yayye. Fahad da Hafizzullah sun zama garkuwa. Mukam ƙanne masu matuƙar biyayya gana gaba dasu. A cikin ɗakin mijina kam ni da shi sai sambarka da alhmdllh. Dan dukkan wata soyayya da kulawa ina samu daga garesa harma wadda banyi zato da tsmani ba. Hafizzullah da Bahijja sun koma makaranta. Yayinda Fahad aka fara shiga harkokin Bussines shima. Yaya Musaddiq yazo mana hutun sati ɗaya. Na shiga matuƙar farin ciki da wannan ziyara ni da ƴan uwana da su Ummie duka. A wannan zama ne Ummie ta bamu takardun Company da Abie ya bada a bamu. Munyi kuka munyi godiya sosai. Mun kuma tattauna abubuwa masu yawa da suka jima suna damun kowannenmu. Bayan wucewar Yaya Musaddiq Falaq ta koma ɗakin mijinta dan tayi arba'in. Little Awwab nata wayo Masha ALLAH. Ya Awwab ma jikinsa yayi sauƙi sosai. Kamar yanda Ummie ke sake samun lafiya yanda ya kamata. Dan yanzu haka itama zata fara cigaba da kula da wasu harkokin Bussines ɗin ne anan. Saboda Maash da Hayatu sun koma gantalinsu na ƙasashe. Har Nigeria ashe suna kaɗawa idan ta kama. Sai dai basu taɓa sanar mana ba. Cikina ya fara fitowa ɗan kif da shi, sai dai kunya tasa kullum bana rabo da hijjab in har zan sakko ƙasa wajen su Ummie, ko na saka riga mai burun-burun da ba'a ganewa.
A hankali soyayya da shaƙuwa ta fara shiga tsakanin Fahad da Bahijja. Wannan abu yama kowa daɗi, sai dai ita Bahijja na dojewa saboda kunya. Ni da Aunty Falaq muna sake fanfata kuwa. A haka Jaga shima yazo yay mana hutu na sati biyu ya koma Saudiyya. Bayan wucewarsa bai fi da sati uku ba Abba ya kira yake sanar mana Amaryarsa ta haihu ƴan biyu duk maza. Murna sosai muka dinga yi dan mun san lokacin zuwa Nigeria yayi kamar yanda Yaya Awwab yay mana alƙawari. Gashi a ɗan tsakanin shima Yaya Musaddiq zai je ya musu hutun sati biyu. Sai abin ya sake mana dai-dai. Ganin har ana saura kwana uku suna babu Maash babu alamarsa a Spain jikinmu ya fara sanyi. Idan muna waya ko video call nai masa batun tafiyar kuma baya cewa komai sai ya basar ma. Dana fahimci hakan sai na daina masa batun gaba ɗaya. Mun daiyi ɗan gyare-gyaren muna jiran ikon ALLAH. Sai ana gobe suna da safe suka iso Spain shi da Hayat da Fahad. Munyi farin cikin dawowar tasu, amma harga ALLAH na fidda ran zuwanmu Nigeria a lokacin kam. Amma mi sai kawai yace mu shirya jirginmu zai tashi washe gari zuwa Nigeria. Tsabar farin ciki bamma san na rungumeshi agaban Ummie da Mama Balki ba harda manna masa sumba a lips. Sai da naji Hafizzullah da Fahad na dariyar shaƙiyanci sannan na farga. Ai da gudu na sakesa na bar wajen. Ummie na kirana cikin dariya ban waigo ba.
Har ta gama haye stairs ɗin yana tsaye a inda ta barshi, ta kuma gefen ido yake kallonta. Ba yau ta saba rungumeshin ba. Sai dai koda kwatance bata taɓa yi a gaban Ummie ba. Sai ma idan shi yaso yin hakan ta doje. Jiyay gaba ɗaya ta saukar masa da kasala. Karo na farko sai yaji nauyi da kunyar Ummie da Mama Balki. Amma sai ya dake abinsa yama cema Hafizzullah ya bashi coffee. Tashi Fahad yay yabi Hafizzullah kitchen ɗin, sai da suka gama iya shegensu wai yayan nasu na borin kunya sannan suka kawo masa coffee ɗin. Yana amsa ya miƙe ya haura sama da shi a hannu. Ai ko suka gimtse bakuna suna dariya sai da Mama Balki ta korasu sashensu. Shigowarsa dai-dai da fitowata wanka. Dan ina shigowa bathroom na wuce dama. Alhamdullah yanzu kam laulayi yayi sauƙi sosai, dan tunda na shiga wata na shidan nan kam sai dai kwaɗayi da ciye-ciye nake. Amma ciwo-ciwon nan da jinin da nake gani duk wata kaɗan-kaɗan duk sun bari. Sai kuma ƙulafucin miji abin har kunya yake sakani. Yanda yake bina da kallon ƙurilla yasa na tura masa baki da kauda nawa idon a kansa.
Murmushi ya saki kaɗan da laluba aljihunsa ya fiddo min chocolate ɗaya da indai yana gari ko yay tafiya ne ma zai shigo sai ya shigo min da ita. Bamma san nima nayi murmushin ba da nufosa. Kofin hannunsa ya ajiye yana mai ware min hannayensa duk biyu. Shigewa nai jikin nasa ya ɗagani cak yana juyi dani. Dariya na shiga yi ina ƙanƙamesa da faɗin, “Wayyo My Hot juwa. Juwa my Hot ka bari”.
Saman gadon ya sauke ni tare da rungumeni da ƙyau shima yana murmushi. Nima ina ƙanƙame da shi ina faman sauke ajiyar zuciya. Daga haka lissafin ya canja. Tako wane fanni cikin nan baya hanani bashi dukkan kulawar data dace a zahirin rayuwa da shimfiɗarsa. Hakan ke ƙara saka shaƙuwa ta musamman a tsakaninmu da soyayya mai ƙarfi duk da har yanzu daga ni har shi babu wanda ya taɓa furtama ɗan uwansa kalmar (I love you) sai dai a aikace. Hakan kuma ya gamsar da mu ya kuma wadatar. Dan soyayya a baki ba'itace soyayya ba. Soyayya ta gaskiya ma ta wuce batun faɗi da bakin ai sai dai lokaci da yanayi su tabbatar....

WASHE GARI kamar yanda ya faɗa jirginmu ya wulla zuwa ƙasarmu ta haihuwa bayan barinta kusan watanni huɗu kenan. Mun sauka a Lagos inda motocinsa da guards ɗin sa na amana suka zo ɗibarmu airport. Da taimakonsu muka shige motocin dan ƴan jarida da bamu san ta yanda akai suka san zamu shigo ƙasar ba tuni sun kewaye mu. Ga jama'ar gari da muka zame musu ƴan kallo. Ni da shi mota ɗaya muje, dan tunda muka fito a jirgin yana maƙale da hannuna cikin nashi kamar za'a ƙwaceni. Sanye yake cikin ƙananun kaya da suka masa ƙyau sosai. Ni ko abayace a jikina baƙa data mun ɗas, tare da ɗan ɓoye cikina ɗan watanni kusan shida. Ni kaina nasan na ƙara ƙyau da cikar kamala ga ƙibar da ciki ya sani fatata sai ɗaukar ido take mai birgewa. Mun sha matuƙar mamaki da ganin yanda akai ma Maash Mansion gyara. An canja fentinsa da komai na cikinsa. Su Mama Balki an maidosu ainahin sashen da Ummie ta fara mallaka musu sanda take ginin gidan. Haka itama an gyara mata ainahin sashen da tayi da sunan nata. Sai Fahad shima da Hafizzullah, a kwai kuma ainahin sashen da in yayi aure zai zauna da matarsa. Sai Hayat da Falaq Ummie tace nan zasu dawo suma tafi son ganinmu a tare waje guda. Sai kuma mai gayya mai aiki muna dai anan nasa sashen na fil azal. Sai dai yanzu daga ni sai shi ne. An kawo sabbin masu aiki maza da mata. Kowa ya yaba Ummie harda hawayen farin ciki, dan Maash Mansion ya koma ainahin wanda ta tsara a rayuwarta. Bamu wani hutaba sosai a washe gari da safe jirginmu ya sake ɗagawa zuwa Kano ta dabo tumbin giwa.......✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒏𝒊𝒏𝒆𝒕𝒚-𝒔𝒊𝒙_


......Motocin da suka ɗakkomu daga airport na shigowa gidan da suka kawomu na ganesa. Kallonsa nayi kawai, ganin ni yake kallo shima yasa na ɗan hararesa kaɗan. Sai ya saki mun ƙaramin murmushi. Murya can ƙasa ya ce, “Kin gane gidan ne?”.
“Hummm taya zan mance sa. Gidan da akayi kidnapping ɗina”.
“Harda sharri abun”.
Kwantar da kaina nayi a jikin hannunsa ina murmushi. Na ce, “Babu wani sharri sai gaskiya. Ai kaida Yaya Hayat ko humm”.
“Miza'a mana?”
Ɗan far nayi da idanu na, cike da shagwaɓa na ce, “Sai na bama yaranku labarin rashin jin da kukayi”.
Murmushi yayi kam yanzu sosai har haƙoransa na bayyana. Yayinda na shagala da kallonsa dan in yay irin murmushin nan ba ƙaramin ƙyau yake masa ba. Kaɗan na kaima kumatunsa sumbata. Kafin yace wani abu na buɗe motar na fice abuna. Ashe ma kowa ya fito mune kawai a mota. Duk sai naji kunya ta kamani. Haka dai na dake. Shima fitowa yay fuskar nan a haɗe kamar ba shi ya gama murmushi ba yanzu yana ƙoƙarin gyara rigar suit ɗinsa. Ido muka haɗa nai saurin ɗauke nawa na maida ga little Awwab dake hannun Hafizzullah.
Duk da gidan ba wani ƙatoto bane ba dan ko kashi ɗaya bisa takwas ɗin Maash Mansion bai kaiba shima dai yayi ƙyau. Kuma yana da nasa girma gwagwado da zai ɗaukemu mu dukanmu. Duk a falo muka zube kowa na maida numfashin gajiyar tafiya duk da ba wani nisa bane. Amma kasancewar ta jiya bata gama sakinmu ba sai duk gamu nan dai. Shi dai uban gayyar bai zauna ba ya shige bedroom ɗinsa. Sai TJ da Hayatu ne keta ɗawainuya da mu. Bamu wuce mintina goma ba aka kawo mana abinci daga gidan su Bahijja. Hameed ne da wannan aikin. Ya zauna an gaisa aka ɗan taɓa hira yace zai wuce. Aiko Bahijja ta maƙale masa dan tana kewar gida. Ba'a hanata binsa ba dan tayi ƙoƙari ma.
Muma dai abincin kawai mukaci na marairaicewa Ummie kan zamu fara gaba ni da Falaq da Hafizzullah kafin su taho anjima. Dan har yanzu tara ma batayi ba. Hanyar bedroom ɗin da Maash ya shiga Ummie ta nuna min. Ta ce, “Maza jeki mijinki ne da wannan ikon. Idan ya amince ni nawa addu'a ne daughter. Kema tashi ki gayama naki”. Tai nuni da Falaq. A kunyace duk muka tashi, yayinda Fahad da Hafizzullah ke faman mana dariyar shaƙiyanci. Samarin nan sun ishi kowa. Bare mu da suka sama ido ALLAH ya aurar da su mu huta dai. Idan kuma da mai so a fans ɗinki bily yazo na sayar masa😂.
Banyi mamakin samunsa yana barci ba hankali kwance. Dama nayi zargin hakan tunda naga ya shiga bai fito ba kusan awa ɗaya da rabi. Ashe shi barcinsa yake sha hankali kwance. Kayan daya cire ya zube a kujera yana cikin

Please Login or Register in order to submit comment