Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin tafiyar nan tasa tamkar baya so ya fice. Da kallo Mama Balki ta bisa, sai kuma ta saki murmushin da har haƙoranta suka bayyana. A hankali ta furta, “Humm Alhaji Ƙarami”. Sai kuma ta juya ta zubama Samraah da har ta fara sauke munshari idanun nata. Shigowar Hayatu ne ya katseta. Sallama yay mata dan yasan ba lallai yau ya samu damar sake shigowa asibitin ba tunda suna tare da boss. Gashi ma acan office jiransu ake sakamakon meeting da yasa Juliet ta tara na gaba ɗaya exco ɗin companynsa na cikin Lagos dama wajen Lagos masu alaƙa da abinda ya faru. Ya kuma tabbatar dole meeting ɗin zai jasu lokaci mai tsayi....

🌺🌺🌺🌺🌺

“Magana ta gaskiya sai kun kula Attahir. Kun fa san Hajiya nada hawan jini. Yanzu badan ALLAH ya taƙaita ba a wannan faɗuwar da tayi fa komai zai iya faruwa. Dan ɗayan biyu ne. Paralysis ko heart attack. Saboda a kwanakin nan bincikenmu ya nuna zuciyarta na samun matsi sosai da yawan damuwa. Dan haka dan ALLAH ku kula. Zamu riƙeta anan zuwa 2days, ga wannan sai kaje konan pharmacy na asibiti ka samo dan data farka za'a buƙacesu”.
Numfashi mai nauyi Attahir ya sauke tare da jinjina kansa. Kafin a hankali ya ɗaura da yima doctor ɗin godiya sannan ya miƙe. Tafiya kawai yake amma shi baima san a inda yake jefa ƙafa ba. Dan shi a karan kansa yana buƙatar gadon ne a wannan gaɓar. Da ƙyar ya iya kai kansa pharmacy ɗin cikin asibitin ya miƙa musu takardar da doctor ɗin ya bashi kawai. Koda pharmacist ɗin ya duba ya sanar masa kuɗin baima bi takansa ba ya zaro ATM ɗin sa a wallet kawai ya miƙa masa. Hakama da aka saka adadin kuɗin bai wani dubaba ya amsa ya saka pin ɗinsa. Ledar ya amsa ya koma ɗakin da aka kwantar da Mamy.

Har dare yay nisa babu Dad babu Mansoor. Babu kuma wanda ya kirashi koda sau ɗaya yaji yaya Mamyn take. Haka ya kwana cikin asibitin shi kaɗai, sai a washe gari bayan sallar asuba yana fitowa a massalaci fita yay a asibitin dan likita ya tabbatar masa Mamy zata iya kai sha ɗaya ma bata farka ba. Kai tsaye gidan ƙaninsa na ɓangaren Ummie ya nufa. Kakarsu mace ta rasu, sai tsoho mai ran ƙarfe da ya ragema Ummie kawai. Bai tsaya kwana-kwana ba ya zayyane masa komai dake faruwa. Sosai hankalin kakan nasa ya tashi, Attahiru na gabansa ya shiga bugama sauran ƴaƴansa waya duk yace suzo yana buƙatar ganinsu. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa duk sai gasu, ALLAH ya taimaka ma abin ya haɗa da weekend. Sake saka Attahir yay ya maimaita duk abinda ya faɗa masa. Suma ransu yay matuƙar ɓaci da wannan hali na ƴar uwarsu. Tun tana budurwa sunyi matuƙar yaƙi na ganin ta ajiye waɗan nan banzan halayen amma a banza. Kullum shari'arta da miji bata wuce akan wannan halin na son kuɗi da ƙarya. Gashi nan dai sai da takai ta watsa farin cikin gidanta da kai wa matsayar da suka dinga guje mata sannan hankalinta ya kwanta. Itama autar tasu Sakeena zama da gurɓataccen miji ashe ya canja musu ita ta koma irinta. Ɗunguma sukai su duka harda tsoho zuwa asibiti suka dubata. Sunko samu ta farka, haka duk suka jajanta mata sama-sama. Gaba ɗaya kunya ta hanata iya kallon kowa a cikinsu musamman ma Attahiru. Nauyin yaron take ji, dan yanada matuƙar haƙuri da kawaici. Duk irin banbancin da take nunawa tsakaninsa da ɗan uwansa bai taɓa ɗauka ya sakama ransa balle har taga ɓacin ran hakan akan koda fuskarsa ce. Yau ga wanda take matuƙar nunama soyayyar ya tsallaketa ya wuce akan mace. Duk da dai tasan ita duk ta jawo komai, sosai take jin dana sani da nadamar ƙwaɗayayyar rayuwarta a yau.

Kwananta biyu a asibiti babu ko ƙyallin Dad. Tana son ta tambayi Attahir tana jin tsoron jin abinda bashi zuciyarta take son ji ɗin ba. Dan tana matuƙar so da ƙaunar mijinta. Hasalima kamanninsa da Mansoor ya ɗebo yasa take fifita soyayyarsa akan sauran yaranta. A ranar aka basu sallama. Tun da suka baro asibiti taga an ɗauki hanyar gidan babanta gabanta ke faman faɗuwa. Sai dai tsoro ya hanata tambaya har suka iso. Isowarsu babu jimawa suma su Amal suka iso. Dama suna Abuja gidan kawunsu ne. Sanda zasu wuce India su aka turasu can sai yau suke dawowa.
Anan ɗin ma babu wanda yace mata komai har tsawon kwan biyu, abu ya dameta amma itama tsoron jin abinda bashi take son ji ba ya hanata iya tambaya. Zuwan Sakina biyu gidan babu mai tankama wani ita da ita. Su duka sun ɗauki zafi da juna tamkar ba ƴan uwa ba jini ɗaya. Hasalima a baya sun fi shiri da juna matuƙa, dan rayuwar ƴammatanci gaba ɗaya Sakeenar a gidanta tayita ma..
Attahir dai yakan zo da safe kullum kafin ya wuce aiki ya gaisheta. Hakama idan ya tashi sai yazo nan ya gaisheta sannan yake wuce gida. Kamar wasa a haka kwanaki suka dinga tafiya tana a gidansu. Ga baba ma sama-sama yake amsa mata gaisuwa. Baya shiga sabgarta baya kuma bata damar shiga tashi har gata da watanni biyu cif a gida. Su Amal ma tuni suka tattara kayansu suka gudu gida. Dan sunce bazasu iya zama gidan Baba ba saboda gidansu komai najin daɗin rayuwa suna da shi. Nan ko duk da ƴaƴan baban maza sun tsaya akan al'amuransa shima kasancewar matarsa ba itace kakarsu ba abubuwa da yawa sai a hankali kawai. Ta kankane komai daga ita sai nata jikokin Mamy ma sai tayi da gaske wataran take samun abinci a gidan. Dan ma Attahir baya gajiya da kawo mata kayan shayi da ƴan kayan maƙulashe. Amma itama da tuni yunwa ta kai rayuwarta ƙasa kam.........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_


........Tun fitarsu a ɗakin jiyyar yarinyar har barinsu asibitin akan idanunta ne. Numfashi ta sauke mai nauyi tare da ture ɗan kwalin kanta baya. Dauriya kawai take da danne abinda ke matuƙar cimata zuciya. Wayarta ta ɗauka a ɗan zafafe, tai ƴan danne-danne tare da kaiwa kunnenta. Ana ɗagawa daga can ta ɗan sauke ajiyar zuciya. Sai kuma cikin ɗan farin ciki mai gauraye da sauran damuwa ta furta, “Sabon labari”.
Cike da zumuɗi daga can akace mata “Name fa Hajjaju masu Lagos da kayan cikinta.”
“Hummm Jannifer bar batun wasa Please. Yarinyar nan ce fa suka maido asibitin nan yanzu”.
“What! Kina nufin Samraah?”.
“Yess. Yanzu haka tana nan tare damu. Ban san miya faru ba suka maidota nan ɗin. Naga dai mutuniyarki a zafafe cikin matuƙar damuwa kuma. Yanzu kam na fara zargin akwai abinda take ƙullawa. Na kuma yi alkawarin sai na bincikosa a koma ina taje ta bizne shi”.
“Karki wani damu Hajjaju wannan duk mai sauƙi ne. Ko ni nan na isheta. Har mi akai akayi Alaja Nafee kuma. Matar da bata iya komai ba sai da shawaran banzan Madan Rubayya ɗin nan. Ni dai kawai yanzu shawaran da zan baki kawai kiyi ƙoƙarin ki kula da yarinyar nan da ƙyau, tunda dama tun farko kayanki ce. Kin zauna sakaci ne Alaja Nafee ta nema ƙwacewa. Banzama irinta da ta ƙare a ƙarƙashin guzumomi irin su Rubayya. Dan bana raba ɗayan biyu shakkar Rubayya ɗinne ya hanata taya yarinyar kafin ke, tunda itama ai mayyar ce. Saboda haka kiyi amfani da wannan damar akan ita yarinyar kiyita banka mata maganin da zai fidda mata sha'awar namiji gaba ɗaya a ranta, ina tabbatar miki da kanta zata kawo miki kanta tana kukan ki mora albarkacin jikinta. Haba Alaja Lawusa kamar baku bane Lagos ɗin. Ni fatana ma idan zakije honeymoon da ita aje dani koda a ƴar riƙon handbag ce”.
Dariya mai ƙayatarwa Hajiya ƙarama ta saki, tare da sake lume kanta a cikin kujera idanunta a lumshe tana siffanta cikakkiyar surar Samraah data jima tana birkita mata lissafinta. Dan tun randa Jannifer tayi kiranta ta sanar mata da zuwan yarinyar gidan matsayin gift da Mashi'a tai shirin kawoma Hajiya Babba dan ta kula da ita ta gama jin ƙaguwa da son ganin yarinyar. Saboda haka ta azalzali Paah suka dawo Nigeria washe gari badan ma sun kammala abinda ya kaisu ba. Koda suka iso tai ido biyu da Samraah sai da numfashina ya nema shiɗewa. Dan yarinyar irinsu ne ake kira da full option. Komai yaji yanda ya kamata. Sai dai kash abubuwa da dama sukai mata katanga da hakan, tayi ƙoƙarin riƙe kanta har zuwa sanda ta gama shiryawa sai kuma ga wannan abin ya faru da yay matuƙar ƙona mata rai, dan a yanzu haka ita kaɗai tasan irin kalar zafin yaron nan Awwab da take ji a rayuwarta. Wani irin kishi take ji tamkar ta kashe banza a wuce wajen dan son Samraah take na gaske. Har ma ta gama yankema kanta shawarar auran yarinyar zatayi ta ɗauketa daga Nigeria zuwa duk ƙasar da take so sai ta dinga kai mata ziyara....
“Alaja!”.
Jannifer ta katse mata tunani. Firgigit ta dawo hayyacinta tana mai sauke nannauyan numfashi. Cike da basarwa taja ɗan sirrin tsaki da faɗin, “Sorry Jannifer na tafi wata sabgar ne kuma.”
Dariya Jannifer ta ƙyalƙyale da shi daga can, cike da shaƙiyanci ta ce ko dai kin tafi tunanin kayan alatu ba”.
Murmushi Hajiya Ƙarama tayi tana mai cije lips ɗinta. Kafin a hankali ta ce, “Ke dai Jannifer sheɗaniya ce wlhy. Lallai da ace bakiyi ridda daga musulimci zuwa kiristanci ba da ba ƙaramar sheɗaniyar matar hausawa musulma akayi ba. Amma yanzu mun bar musu, dan inba ma wanda ya sani ba taya zai taɓa yarda kin haɗa iri da fulani. Humm ALLAH dai ya jiƙan General. Ya tafi yabar baya da ƙura. Maybe da za'a shawarcesa a dawo da shi duniya yaga Munirra ɗinsa yanda ta koma kamar bata taɓa haɗa jini da yan arewa da musulunci ba da dakansa zai kashe kansa ma wlhy”.
“Hummm Hajjaju kenan masu Lagos da jama'ar cikinsa. Ai duk nawa wasan yara ne. Idan kuna guri mu kuma wake ta tamu ƙananun ƙwari. Mufa a riddar kawai muka tsaya sai ɗan cinikin goron nan da muke kafawa a faifai da ɗan hutawar nan muna more ƙuruciya. Ku kuwa fa, idan akace ai tone-tone ai kema musulman sai sun gwammace riddar kikayi wlhy”.
“Uhhm to ya isa. Dan ke baki gajiya da zakuɗe-zakuɗe. Yanzu dai sai anjima idan na tashi zan zo gida na sameki mu ƙarasa. Dan zan ɗan shiga theater”.
“Hummm” kawai Jannifer tace daga can tare da yanke wayar tana dariya. Itama sai Hajiya ƙaramar tai dariyar kawai tana ƙoƙarin ajiye wayar, a dai-dai nan wani kiran ya sake shigo mata. Ido ta zubama number na tsawon lokaci, YALLAƁAI ɓaro-ɓaro ya fito. Mamaki ya sake kamata dan rabon da mai number yay kiranta ta jima sosai, dukan tara-tara ƙirjinta ya shiga hi har sai da wayar ta kusa yankewa ta dawo a hayyacinta. Da sauri ta ɗauka tana miƙewa ta nufi ƙofar office ɗin ta murza key cike da rashin gaskiya....

_🤔Hummm wai ina matan nan suka dosa ne? Sannan waye yay kiran Hajiya Ƙarama kuma? Idan na fahimta dai Hajiya Ƙarama na waya da Madam ne a farko, matar data ɗakko Samraah daga Abuja zuwa Lagos. Tab ɗin babbar magana. Ashe ita ɗin musulma ce shine tai ridda. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Anya wannan duniya kuwa. ALLAH mun tuba badan halinmu ba😭🙏._

__________________

*_THREE DAYS LATER_*

Kwanaki uku kenan da faruwar komai. Sam Maash yaƙi yarda ya zauna da family ɗin nasa akan batun Samraah. Dan haka ran kowa a matuƙar ɓace yake. Amma shi ko'a jikinsa sai manna musu hauka kawai yake. Dan gaba ɗaya ma ya maida hankalinsa ne akan binciken yanda akai containers ɗin companyn sa suka ɗiba yara da wiwi saɓanin lodin kayan abinci. Dan suna shirin tunkarar Mr Paul ne da ƙarfinsu a court saboda sun shigar da ƙara ne kafin shi bisa shawarar lawyers ɗinsu.
Ta gefe kuma ga jikin Ummie da ya rikice. Ga kuma Samraah dake asibiti har yanzu ba'a sallamota ba itama, sai dai wata irin kulawa take samu ta musamman da tattali a wajen Hajiya ƙarama har Mama Balki ta fara shan jinin jikinta. Sai dai abinda Mama Balki bata sani ba ita kanta Samraah nazartar Hajiya ƙarama take sannu a hankali. Gefe kuma tana kaima ALLAH kukanta. Koda labari Mama Balki bata sanar mata da ciwon Ummie ba sai yau da Falak tai kiran wayar Mama Balkin, a lokacin ita kuma ta ɗan fita dan haka Samraah ta ɗaga. Har yanzu basu taɓa haɗuwa da Falak ba sai dai tana cin abincin gidanta kullum. Bata da lafiya ne tana fama da tsohon ciki shiyyasa bata zo tama dubata ba, sai dai sun gaisa ta waya har kusan sau uku. Yanzun ma sun gaisa cike da kulawa ma juna tamkar dama can sun san junan nasu, kafin Samraah ta sanar mata Mama ta ɗan fita ne, amma idan ta dawo zata faɗa mata sai ta ƙara kira.
Daga can Falak tai murmushi da faɗin, “Okay ba damuwa ALLAH ya ƙara lafiya, dama zanji ko yaya jikin Ummie ne dan na kira Yaya Hayat ashe garin sauri yama bar phone ɗin a gida, gashi yanda ya fita a hargitse duk na kasa nutsuwa”.
Ɗan jimmm nayi zuciyata na bugawa da sauri-sauri jin ta ambaci Ummie, da ƙyar na iya tambayarta “Ummien Maash Mansion? Wani abu ne ya sameta?”.
Batare data fahimci kan tambayar ba cikin damuwa muryarta na rawa ta ce, “Eh ita, kin san kwana biyun nan jikin nata duk babu daɗi, to yau dai da alama ya tsananta ne dan shima Yaya Hayat a rikice ya fita TJ ya kirashi. Wlhy ina tausayawa Ummie, da ace inada wata babbar dama akan baiwar ALLAHr nan abinda zan farayi shine tsayawa akan samun lafiyarta, amma muna gani an hanamu taimakonta. Wanda keda ƙarfin yin hakan kuma an kulle masa tunani gaba ɗaya, dan wlhy da ace Yaya Awwab basu shiga tsakaninsa da lafiyar baiwar ALLAHr nan ba da kowama yaci ubansa, ai sun san shi ɗin ba kanwar lasa bane har Baba prof ɗin da Paah ba iya tankwarashi suke ba. Amma ba komai ALLAH yana nan, watarana sai labari”.
Tuni ma ni ba fahimtar zantukanta nake da ƙyau ba, rawa sosai jikina ke mun, ga hawaye suna bala'in gudu a saman fuskata. Ashe shiyyasa duk jiya bai zo asibitin ba, yau ma haka. Ko Hayatu mai ƙoƙarin zuwa sama da sau uku yana kawo musu abubuwa jiya sai dare ya shigo ya duba ta. Abinci ma TJ ne ke kawowa. Amma Maash tun daren shekaran jiya da zai tafi take cemasa ya dinga duba mata Ummie da bata abinci bai sake zuwa ba, harta ƙullacesa ma ita da, da tunanin ya gama cin moriyat ganga zai yada kwautrnta, ashe abinda ke faruwa kenan...
“Ya subahanallah Samraah! Wani abu ke miki ciwo ne? Ko tashi kikayi da ƙarfi kika fama ciwon?”.
Mama Balki ce mai maganar nan a rikice. Ɗagowa nayi ina kuka mai tsanani dan shashshekar da nake tasa har fisga numfashina keyi. Lallashina Mama Balki ta shiga yi tare da bani ruwa tace nasha. Da ƙyar na amsa nai maƙwarwa uku, jikinta ta jawoni ta rungume, hakan sai ya taimaka min wajen samun nutsuwa na fara sassauta kukan. Kaina na a saman cinyarta tana shafa gashina ta ce, “Samraah”.
Cikin dasashjiyar muryata na amsa mata da, “Na'am Mama”.
“Mike faruwa?”.
Da ƙyar na iya danne kukan dake taho min na ce, “Mama Ummie. Ashe bata da lafiya amma shine babu wanda ya sanar min”.
Iska ta ɗan furzar cikin damuwa. Kafin ta ce, “Waye ta faɗa miki?”.
“Falak”.
Na bata amsa ina sharce hawaye.......✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_


*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv


*_WhatsApp_*
https://chat.whatsapp.com/LkRMFFQZakP55c7xK0QaMG


https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5

___________

......Kanta ta girgiza da faɗin, “Ni ban san sai yaushe bakin Falak zai iya dinga koyon shiru ba. Kiyi haƙuri an ɓoye miki ne saboda kema ga yanayin da kike ciki. Shekaran jiya ne Alhaji ƙarami ya shiga yana ƙoƙarin bata abinci shine fa kawai jikin ya rikice. Ta jimasa ciwo sosai a hannu da ƙyar aka iya fiddoshi a ɗakin, daga nan duk wanda ya shiga da duka take korosa, to yau kuma sai ta yanke jiki ta faɗi saboda kwana biyun nan bata ci bata sha rashin abinci jikinta yayi week. Amma ki kwantar da hankalinki zuwa yanzu sun ce Alhamdullah komai ya dai-daita. Dan Hayatu ma ya tabbatar min tana barci saboda drip ɗin da aketa ƙara mata.”
Duk da na ɗan ji nutsuwa sai da na sake sharce hawaye, ɗan shiru mukayi kafin a hankali nace, “Mama”.
Da kulawa ta amsa min da, “Na'am Samraah”.
“Mama a yanzu sai nake ganin kamar shi yafi dacewa ma abinda ke tare da shi ya rabu da shi kafin a samu nutsuwar yima Ummie magani. Duk da dai wani abu ya jima yana damuna. Yanzu duk kuɗinsa ace gidan nan babu cctv camaras tako ina?”.
“Tabbas gaskiya kika faɗa Samraah. Sai dai mun kwatanta hakan muma bai yiwu ba, a dalilin tsanar magani da Alhaji ƙarami yayi tun yana ƙaraminsa. Ko yaya ruwa ya surka wlhy bazai sha miki shi ba koda da kala ne. Shiyyasa yin maganinsa keda matuƙar wahala. Gashi kuma shi ba'a zaune yake ba waje ɗaya, duk yanda muka so fara bashi koda ruwan addu'a ne sai kiga abin ya zama shiririta. Ina da tabbacin kuma wanda ke wannan aikin kullum cikin sabuntashi suke bawai sun koma sun kwanta bane suma. Maganar camara kuwa ai Alhaji ƙarami yasha sakawa amma sai a wayi gari duk an ciresu. Har ɓoyayyar camara an saka a gidan nan amma kamar abin maita wlhy sai da aka cireta. Hakan na nufin koma su waye a biye suke, shiyyasa ma kikaga ina sake jin tsoron al'amarin gidan nan da mutanensa. Dan idan bana jikinka ba banga wanda zai dinga maka wannan bita da ƙullin ba a nesa da kai”.
Baki na buɗe zanyi magana sai naji kamar amalar motsin tsayawar mutum a ƙofa. Shiru nayi bance komai ba, sai kuma kamar ance na ɗaga ido na hango inuwa ta jikin window. Magana Mama zatayi na wayance ina mai zame kaina da ga cinyarta na ce, “Mama barci nake ji. Dan ALLAH idan Nurse ɗin nan tazo kice bana son allurar nan ni nama warke karki bari tamun”.
Kallon mamaki da naga Mama namun yasa nai mata nuni da window da ido. Tuni ta ɗauki haske kasancewar dama a ankare take. Itama sai ta wayance ta shiga ƴar dariya da faɗin, “Ja'ira ai allurar nan sai an kaita har ƙarshe, bari ma Hajiya tazo zance ta sake ƙara miki kwana biyu kiyi digir dake yanda zamu koma gida da ƙarfinki”.
Shagwaɓa na shiga mata da faɗin ni bana so. Itako tana dariya. Daga haka mukayi shiru. Kwanciya nayi zuciyata na faman kai-kawo. Tabbas lokaci yayi fa dazan dawo hankalina. Dan na fahimci in har shi bai fita a halin da suke sanyashi ba baiwar ALLAHr nan bazata taɓa samun ingantaccen lafiya ba. Domin sauƙi yana samuwa a gareta, sai dai yanayin kwan-gaba kwan-baya da ake fuskanta yasa al'amarin ke taɓarɓarewa. Idan kuwa har za'a iya hana cctv camaras zama lafiya to lallai waɗan nan mutanen ba ƙaramin shiri sukai ba. Suma kuma suna buƙatar a shirya musu yanda ya kamata. Dan dole wayo al'amarin yake buƙata da hikima kamar yanda suma suke komai ta cikin basira”. Wannan tunane-tunanen da hawayen da suka kasa barin idanuna ne suka haifar min da zazzaɓi mai zafi, gashi naƙi gayama Mama har bayan sallar isha'i. Dan da ƙyar ma nayi alwala saboda sanyin da nake ji. Ina idarwa na haye gado na kwanta tare da duƙunƙunewa cikin bargo. Sosai na gaji da zaman asibitin nan, fatana kawai ALLAH yasa yazo dan shine kawai zaisa a sallameni. Yan gidansu dai dama babu wanda ya sake zuwa sai Hajiya ƙarama da nake gani, ita kam kullum ne sai ma tazo sama da sau uku, sai daga baya na fahimci ai dan asibitinta ne shiyyasa itama muke yawan ganintan.....

🩸🌟🩸

Sosai damuwar halin da Ummie ke ciki a kwana biyun nan yasa bai sake waiwayen asibitin ba. Duk da kuwa wani sashe na hankalinsa na'a can ɗin. Sai dai rashin isashen lafiya shima dana lokaci ta sashi baiyi wani yinƙuri ba. Yau kuma zafi da ƙuncin da gidan ya masa matuƙa ya sashi ɗan kimtsawa bayan ya dawo sallar isha'i. Tun la'asar ya kora Hayatu gida dan haka shi kaɗaine a sashen sai Laalah da TJ dake leƙowa akai-akai duba shi shi da Shu'aibu amintaccen guard ɗinsa. Tsaff ya fito yana zuba mayataccen ƙamshin nan nasa tamkar ba dare ba. Tj da Shu'aibu na ganinsa suka miƙe da sauri, hakama sauran ma'aikatan gidan sai gaisuwa suke miƙawa. Hannu kawai yake ɗaga musu dan kwana biyun nan miskilawan ne a kusa. Da ga shi sai TJ da Shu'aibu sukai fitar dan hana sauran guards ɗin binsu yayi. Tj ke driving Shu'aibu a gefensa. Shi kuma yana baya zaune idanunsa akan wayarsa yana daƙila. Kicin-kicin fuskar nan take babu alamar ya taɓa sanin minene ma dariya.
Cike da girmamawa TJ ya ce, “Boss ina muka nufa?”.
Shiru bashi da

Please Login or Register in order to submit comment