Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tafi, sun kuma barku da gwagwarmaya mai wahala gaskiya. Wahalar da haƙurin nan ne kawai zai iya ɗorar da ku matsayin ahali. ALLAH ya farta mana, ya kuma shiryemu baki ɗaya. Yasa hakan ya zama izna a garemu dama na bayanmu masu tasowa.”
A tare duk muka amsa da Amin. Yayinda Paah ya miƙe zuwa kusa da Ummie ya zauna. Kansa a ƙasa hawaye na sauka masa ya ce, “Tabbas Ummu-Hidaya ni mai kuskurene a gareki mai girma. Nayi abinda ban cancanci duniya ma ta yafe min ba balle ke dana zalunta ko yaƴanmu. Ke ɗin jarumar mace ce da samunki a wannan duniyar sai an sha matuƙar wahala. Kin shanye, kin kurɓe daga zaluncina. Dan nasan tun daga sati ɗaya na aurenki baki sake jin daɗi daga gareni ba. Kuma hatta da mahaifinki baki taɓa faɗa masa wanene ni ba, sai da ya gano da kansa. Saboda dattako da mutunci na wannan bawa ya sameni batare da saninki ko mahaifana ba yamun nasiha da nuna min illar abinda nake aikatawar. Bai tozartani ba, bai ce na sakar masa ƴarsa saboda ni ɗan iska bane ba. Bai kuma samu mahaifina da zancen ba. Bai kuma gaza wajen cigaba da jawoni jikinsa yana nasiha ba. Badan bashi da ƙarfin ɗaukar mataki a kaina ba. Badan bashi da ƙarfin cewa na sakar masa ke ba. Sai dan kawai shi ɗin jarumin mahaifine mai ƙyaƙyƙyawar zuciya. Wlhy ina ji inama ace Abie shine mahaifina tun a wancan lokacin, inama ace naji nasiharsa naji tsoron ALLAH, kai inama ace mutuwa nai tun ina ƙanƙanina.....” kuka ya sarƙesa. Itama Ummie kanta a ƙasa tana nata kukan. Muma kukan mukeyi, shugaban taurin zuciya ne kawai babu ɗogon hawaye a nasa idanun sai dai sun juye gaba ɗaya alamar dai ana na zuci. Da ƙyar Paah ya ciga da faɗin, “Ummu-Hidaya bamma san ta ina zan fara baki haƙuri ko neman gafararku ke da ƴaƴana ba. Sai dai wlhy ku sani duk duniya ban taɓa son wani abu ba sama da ku ɗin nan ba. Ina muku so da baida iyaka. A yawan lokuta nakan aikata abu gareku batare da ni kaina nasan ta yaya akayi ba, sai daga baya nazo na shiga tashin hankali amma bana iya neman afuwarku. Wlhy ban san irin yanda zan kwatanta miki tashin hankali da ruɗanin dana shiga a waccan ranar ba sakamakon abinda ya faru. Kuma wlhy abinda kike tunanin ya faru bai faru ba, kina faɗuwa kika suma hankalina ya tashi, sai dai tsoro yasa na kasa tsayawa a gidan nima na gudu. Ummu-Hidaya dan girman ALLAH basai anyi tone-tone ba ki yafe min, na roƙeki ko bazaki cigaba da zama dani ba kamar yanda ƴaƴanmu suka buƙata ki yafe min. Dan ALLAH ki yafe min na roƙeki. Muhammad da Fahad kuma ku yafe min dan ALLAH, ku tayani roƙon mahaifiyarku ta yafe min. Bilkisu dan ALLAH ku tayani roƙon ƴar uwarki ta yafe mun. Ƴaƴana Falaq da Samraah da Bahijja ku tayani roƙon mamanku ta yafe min. Na tuba nayi nadama wlhy”. Kuka ya sake sarƙeshi. Itama Ummien kuka take mai ban tausayi da taɓa zuciya. Yayinda illahirin mu muke tayasu. Su duka dole ne su baka tausayi, matuƙar tausayi. Tashi Ummie tayi ta haye sama. Da sauri Paah shima ya tashi ya bita yana kiran sunanta. Suna shiga ɗakin ya zube a gabanta gwiyawu a ƙasa, tare da riƙe ƙafafunta yana kuka sosai. Kukan take itama kanta a gefe har numfashinta na shiɗewa. Haka ya cigaba da mata magiya kusan fin ta minti talati. ALLAH sarki Ummie, zuciyar babu duhu, ita ɗin mai tausayi ce, ta gada daga ƙyawawan halaye na mahaifi. Sai kawai itama ta durƙushe ƙasan ta shiga marin Paah ɗin hannaye bibbiyu suna kallon juna su duka suna hawayen. Tayi masa yafi goma dan harda ƙirjinsa take kaima dukan amma daga marin har dukan ba masu zafi bane ba. Kafin ta faɗa jikinsa tana sake fashewa da kuka. Shima amsarta yay hannu biyu ya rungume yana nashi kukan da sake bata haƙuri....

Acan falo ma su Uncle Abdullahi da Hajiya Mammah da Aunty Mama haƙuri suke bama Maash da Fahad. Tare da neman afuwarsu. Musamman ma Hajiya Mammah da tasan tayi abubuwa a gidan. Ba kuma ta ɓoye ba komai da tayi ta sanar musu. Hatta abinda ta saka a abinci ta bama Samraah takai masa yaci da ga ƙarshe abinda ya faru ya faru, ta sanar musu da manufarta tayin hakan. Ashe hatta su kansu su Uncle Abdullahi ba ƙyalesu tai ba. Tayi musu na mallaka ta yanda duk abinda zatai a gidan zasu kasance cikin shakkarta. Sosai al'amarin nata ya sake bama kowa mamaki, amma tunda dai komai ya wuce batun neman gafara ake yi sai suka yafe mata, tare da fatan ALLAH ya yafe musu baki ɗaya. Daga ƙarshe suka bata shawarar ajiye ɗabi'arta ta je ta roƙa mijinta yafiya shima ta koma wajen ƴaƴanta. Ko kuma ta samu miji tai aure dan shine babban mutuncinta da kimarta. Ta kuma dukufa neman gafarar ALLAH tayi tuba na gaskiya da alkawarin bazata sake aikata abinda ya aikata a baya ba. Daga nan malam ya mana nasiha tare da shawarwari akan muma tamu rayuwar da namu mazajen. Suma mazajen namu ya musu a kammu. Har dai aka rufe taro da addu'a Ummie da Paah basu fito ba. Babu wanda yace komai a kan hakan. Amma fa Yaya Awwab ficewarsa yay a gidan bayan wucewar su Malam...

★Har dare bai dawo ba. Tun ina ɗaukar al'amarin da sauƙi har na fara shiga tashin hankali. Gashi na kirashi yaƙi ya ɗauka. Sai na nema Yaya Hayatu. Kwantar min da hankali yayi, ya tabbatar min na shirya dan yanzu dama ya kira shi yace ya kaini inda yake. Banyi mamakin hakan ba, dan na fahimci Yaya Awwab akwai taurin kai. Sai dai ta wani ɓangaren bana ganin laifinsa. Yana ƙaunar mahaifiyarsa ne sosai. Sannan duk wani ɗa na ƙwarai irin abinda zai yi kenan, ko nice ma abinda zanyin kenan magana ta gaskiya. Shiryawar nayi dan ina matuƙar buƙatar ganinsa nima. Abinda zan iya buƙata kawai na ɗauka, koda na fito sai na kasa tafiya sai na nufi sashen su domin sanar ma Ummien. Nayi mamakin samunta a falo ita da mama Balki. Ganin yanda nake sim-sim ta miƙomin hannu cike da kulawa tana faɗin, “My darling miya faru? Zonan naji”.
Hummm yanda Ummien ke treating namu mukanji kammu like babys ne, ƴan shagwaɓa a gaban iyayenmu, musamman ma ni da ban tashi da uwa ba. Ban samu irin wannan gatan ba. A hankali naje gabanta zan durƙusa, amma sai ta jawoni kusa da ita ta zaunar. Sake tambayar tawa tayi, a ɗarare na sanar mata. Murmushi tayi da sake shafa kaina, sai ka rantse bata da wata damuwa. Amma ko makaho ya kalleta yasan tana cikin ta, dan idanunta sun yi bala'in kumbura saboda kuka. Har ina jin sake karyewar zuciya da kallonta a yanayin. Cike da dakiya ta ce, “Karki damu kinji Baby na. Kije wajen mijinki, ki lallashesa ki tausa masa zuciyarsa. Nasan yayi hakane domin samun daidaituwar kansa. Dan Muhammad bai iya fushi ba, idan yana cikin fushi baya iya controlling harshensa ma. Shiyyasa na koyar da shi yin hakan tunƙuruciya, dan idan yabar inda akai masa kuskuren sai kiga ya huce. ALLAH yay muku albarka, ya kuma saukeki lafiya kema dan na ƙagu naga wannan miji na Bilkisu ko Kishiya ne ma dai to”.
Dariya Mama Balki tayi, nima na ɗan murmusa kaɗan. Haka nai musu sallama na wuce batare dana iya kallonsu ba........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒉𝒖𝒏𝒅𝒓𝒆𝒅 & 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒆𝒆𝒏_


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DsaV9faJPfULbIJBU7TS72

https://chat.whatsapp.com/JJkSofA4Hto57YwEu2Z8Xq


*_Wai ni Balki ina duk masoyan Bilyn Abdull ɗin nan dake a manhajar Instagram da TikTok ne?🤔? Kai jama'a gaskiya da kunya ace account na Bilyn Abdull a Instagram da TikTok iya kar fallowers ɗin kenan🥲😣. Ina masoyan facebook ɗin nan dana WhatsApp, Please a fito mana ai fallowing ɗina. Accounts ne na Bussines ko bazaki/zaka saya ba zakaga abinda ya burgeka ko kalarka ka nema a inda kake. Maza ku garzayo BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING kodan kashe kwarkwatar idanunku ku more kallo iya kallonku da kaya ƴan yayi cikin farashi mai sauƙi da rahusa. Muna bada sari, muna adashen gata, muna sai da ɗai-ɗai. Ka gani su burgeka, ka saka ka birge mai kallonka sai Bilyn Abdull online shopping. Bari muga akwai ƙaunar kodai-kodai....😉🫣. Ga link nan naga accounts ɗin nan biyu kamar zasu fashe da fallowers 😘😘😘😍😍👍🏻👇🏻_*.

*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

_Ina masu son zuwa ganin likita ko yawon buɗe ido ƙasar Egypt?. To ku garzayo munada hanya mai sauƙi ta sama muku sauƙin tafiya cikin ƙa'ida da bin dokar ƙasa. Katafi anan cikin aminci, ka dawo kuma cikin aminci. Wajen kwananka a can zamu tanada, asibitin da zakaga likita duk zamu tsaya maka da tsayawar UBANGIJI. Hakama yawon hutawa zamu zame maka jagora. Kai ko hanyar zuwa domin sayo kaya duk muna da ita. Kai dai kawai kazo garemu kaga aiki da cikawa da iznin ALLAH. 09032345899. A nememu tanan ga masu buƙata, dan ALLAH serious bama son latsi ko wasa dan ba wasan muka fito ba 😂😍👍🏻._

_

......Ina a baya kaina jingine da kujera na lumshe idanu, yaya hayatu na daga gaba yana driving dan shine zai kaini. Muryarsa a sanyaye ya ce, “Auntynmu dan ALLAH ki lallaɓa Yayanmu ya yi haƙuri komai ya wuce Ummie da Paah su cigaba da kasancewa tare. UBANGIJI ma muna aikata masa laifuka da sukafi wannan girma, ko mushiriki ka kasance ka dawo ka tuba garesa tuba na gaskiya yana yafe maka duk da ƙin shirka da yake balle mu mutane masu fatan gafara daga UBANGIJIN. Paah yayi laifi, amma yayi nadama, al'amarin sa kuma ya ta'azzara ne bisa jagorancin zaluncin shaiɗanin tsohon can. Amma wlhy Ummie na son shi, shima kuma yana sonta sosai. Koyaya Ummie na buƙatar abokin rayuwa a wannan gaɓar, tana buƙatar mai ɗebe mata kewa da tausasa damuwarta ta tsahon shekaru. Sannan batai tsufan da zata gagara wani auren ba. Ba kuma zasu bari ta auri wani mijin ba saboda dole kishin mahaifinsu na nan a tare da su. Kinga ita ai an tauyeta, sannan ko doctor ya bada shawarar mijinta ya kasance da ita yanda ya kamata hakan zai cigaba da daidaita matsalarta komai ya koma dai-dai game da abubuwan da suka dinga bata, in ba hakaba ta cigaba da shiga damuwa wataran brain ɗin nata zata sake birkicewa ne. Nasan duk son da Ummie kema Paah in har Yaya Awwab bai yarda su koma tare ba itama bazata amince da shi ba. Haka ma Fahad, amincewar Yaya Awwab ce kawai zata rissinar da shi ya haƙuran. Ke kuma rissinar Yaya Awwab a yanzu kamar tana a hannunki ne. Kinada tasiri matuƙa da rawar da zaki taka a wannan gaɓar komai ya koma normal. Mu dawo full family har ƴaƴanmu su taso suma su mora haƙuri da juriyar mu”.
Hawayen dake zuba min na share. Cikin jinjina kai na ce, “In sha ALLAHU zanyi ƙoƙarin hakan Yaya Hayatu, amma kaima sai ka tayani da su Mama kuma. Dan wlhy ina tsoron fushinsa matuƙa. Yaya Awwab nada murɗaɗen hali mai ban tsoro. Amma yanzu dan ALLAH ina Paah ɗin?”.
“Paah ya koma can gidan wajen su Uncle Abdullahi. Amma ki kwantar da hankalinki in sha ALLAHU muma zamuyi ta ɓangaren mu.”
“To ALLAH ya taimake mu Yaya. Amma mizai hana ka fara kaini naga Paah ɗin”.
“A'a kiyi haƙuri kada kije yanzu. Zan dai iya saka miki number sa ki kirashi a waya. Amma batun ku haɗu a wannan halin Yaya Awwab bai gama sakkowa ba akwai matsala.”
“Shike nan na fahimta, hakan ma yayi ka tura min number ɗin tashi.”

Koda muka iso gidan a falo muka sameshi zaune yana karatun Alkur'ani. Yaya hayatu baima shigo ba ya juya. Nima sai na samu waje na zauna ina sauraren muryarsa dake raira karatun cikin nutsuwa. Har ma barci ya fara rinjaye idanuna na zame na kwanta. Sai da naji ƙamshinsa gab da hancina sosai sannan na buɗe idon. Kallonsa nake kamar yanda take kallona. Baiyi magana ba ya ɗaukeni camak zuwa bedroom ya kwantar. Shima kwanciyar yayi ya sakani a jikinsa. Mu duka ajiyar zuciya kawai muke saukewa a jajjere har barci ya ɗauke ni, ashe shima barcin yayi sai da na farka na gansa....

Kwanaki biyu kenan muna tare da ga ni sai shi a gidan. Babu dai yawan magana dan ya koma min Maash ɗin dana sani a baya. Sai dai dukkan kulawa yana bani dan sai nima na kasance duk bana jin daɗin jikina abinka da mai ciki. Abinci safe, rana, dare Mama Balki na ƙoƙarin aiko mana da shi. Yaya Hayat ne mai kawowa. Abinda yake burgeni da shi ya matuƙar maida al'amarin sa ga UBANGIJI. dan a zaman nan ibada ce kawai sai kuma kasancewa da ni. Duk wasu harkokin Bussines ya ajiyesu gefe guda kawai. Hatta phones ɗin duk ya kashe. Tsahon kwana huɗu sannan mukayi shirin komawa gida. Bayan sallar magrib ya shigo yana min maganar na shirya muje sai ga Hayatu yay kiransa, ban san miya ce masa ba naji kawai ya kama faɗa. Sai kuma ya yanke wayar. A fusace ya nufi ƙofa zai fita. Nai saurin tafiya na rungumesa ta baya nima. Kaina kwance a faffaɗan bayansa, na zagayo hannayena ta saman shafaffen cikinsa. A hankali na ce, “Miya faru Zaki na? Ban sanka da faɗa cikin hayaniya haka ba, Please cool down”.
Shiru yay sai ajiyar zuciya da yake faman saukewa a jajjere. Cikin sake tausasa harshe na ce, “Please ka faɗa min miya faru? Maybe na iya baka shawara”.
Nan ma shirun yayi a binsa, sai da ya mula dan kansa ya furta, “Miyasa zai kawoshi nan. Nace na haƙura, mi kuma ya rage”.
“Wanene?”.
“Mijin Ummie”.
Ni dariya ma maganar tasa ta bani, wai mijin Ummie. Yau Paah ɗin ma baza'a kirashi ba kenan. Amma sai na danne tare da sake tausasa harshe na zagayo ta gabansa. Hannayena duk biyu na ɗora akan kafaɗunsa duk da ya mun tsaho ina kallon cikin shakkiyar idanunsa da gaba ɗaya sun jirkice. Na ce, “Haba my Hot, kenan baka hakura ba? Ba kaji nasihar Malam ba. Yanzu kana son kayi min wani kuskure wataran abinda ke cikina ya dinga maka yanda kakema Paah a yanzu. Kai ma fa yanzu uba ne, sannan bamu san mi yau da gobe zatazo mana da shi ba. Kasan kuwa matuƙar wahalar da mukasha a rayuwa saboda rashin iyaye? Amma ku kuna son raba naku dake a tare. Yaya a mafi yawan lokuta nike girka abincin da za'aci a gidanmu, amma ni bazan cisa ba. Wani daga cikin ƴan uwana bazai cisa ba. Badan bama so ba fa ko babu wadatar abincin. Ka gaya min da Baba na darai ko Ummyn mu zasu barmu da yunwa ne? Government school mukayi, amma yaran gidanmu private masu tsada. Ana musu ɗinki sau biyar mu ba'a mana sau ɗaya ba. Shin da ace iyayenmu na raye ko guda ɗaya ne zamuga wannan rayuwar ne. Duk inda zasu faɗi su tashi zasuyi domin mu. Ku godema ALLAH naku duk suna raye, har gamu muma muna jingine jikinsu suna mana gatan da muka rasa a baya. Paah yayi kuskure, ya kuma yarda yayi kuskure, muma kuma bamu wuce kuskuren ba. Shi da Ummie suna son junansu, kada ku ƙi basu haɗin kan cigaba da zama a ƙarƙashin inuwa ɗaya. Ku tausaya mata kodan bayanin likita, yanzu kunfi son ta rabu da Paah ta auri wani banza can da maybe ma dan dukiyarta zai aureta ne kawai? Kai ne babba, idan har kayi mubaya'a Fahad shima zaiyi wlhy. Please ka saki ranka komai ya wuce”. Na ƙare maganar cikin sanyin murya da marairaicewa kamar zanyi kuka. Ganin ya zuba min idanu kawai na sake faɗin, “Please mana”. Naja kumatunsa. Hararata yayi, niko na sanya dariya da sake ja masa hanci. Sai ya dungure min kai shima yana ɗan lumshe idanunsa a slowly.
Cikin farin ciki naja hannunsa muka fito. Ganin Paah a falo zaune nai saurin sakin hannun nasa na koma bayansa na laɓe. Ƙaramar dariya Paah ɗin yayi mai ɗan sauti da faɗin, “Oh oh my daughter please fito mana.”
Fitowar nai kaina a ƙasa ina wasa da yatsun hannuna. Sum-sum nazo gabansa na durƙusa cikin girmamawa na gaishesa. Ya amsa min da kulawa tare da sanya albarka. Cikin jin daɗin addu'ar da yay ma iyayena na miƙe zuwa kitchen. Ruwa na ɗakko masa da yogurt, sai snacks dan bamu da wani abinci. Yanzu kam zaune na sami Yaya Awwab ɗin kansa a ƙasa. A gaban Paah na ajiye tray ɗin zan bar wajen ya ce dani “Daughter dawo”. Dole dawowar nayi, ya nuna min gefen Yaya Awwab ɗin ya ce, “Zauna kusa da mijinki”. Ban musa ba na zauna kaina a ƙasa. Sai da ya ɗauka ruwan dana kawo masa ya sha tare da sanya min albarka sannan yay gyaran murya da gyara zama.
“Muhammad! Kayi haƙuri ka sake yin hakuri kaji. Ni dai koda bazaka yarda na cigaba da zama da mahaifiyar ku ba, ka yafe min. Namaka alƙawarin zanyin nesa da ku na har abada dan nafi so da fatan kuyi farin ciki a rayuwarku, hakan shine ƙaddarar mu...”
Shiru babu alamar zai ce komai. Ganin haka yasa ni na magantu. Murya a sanyaye na ce, “A'a Dady duk ma ba'aje can ba. Babu inda zaka tafi in sha ALLAHU kana tare damu har abadan. Na tabbata shima kansa yana jin nauyin abinda ya farune shiyayasa kaga haka”. Na ƙare maganar ina mintsinin yaya Awwab ɗin dan so nake yace wani abu. Ganin na damesa ya nisa. Muryarsa acan ƙasa ya furta, “ALLAH ya yafe mana baki ɗaya. Kamar yanda ta faɗa kuma ni banga amfanin tafiyar ba. Tunda kun daidaita kanku mu miye kuma namu face mu muku fatan alheri. Kawai dai magana ta gaskiya ya kamata kaje asibiti a tabbatar mata da lafiyark.....”
Da sauri na zaro idanu waje, tare da kai hannuna saman bakinsa na rufe. Cikin rawar baki data murya na ce, “Yaya Please kada kai magana haka”.
Katseni Paah ɗin yay cikin murmushi ya furta, “Daughter gaskiya mijinki ya faɗa, kuma hakan shawarace me ƙyau shine kuma abinda ya dace nayi. Naji daɗi kuma da amincewarsu akan cigaba da zama da mahaifiyarsu, ALLAH yay muku albarka Muhammad”.
Murya a sanyaye na amsa da Amin. Yayinda shi kuma ya amsa a saman lips kawai........✍️




_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒉𝒖𝒏𝒅𝒓𝒆𝒅 & 𝒇𝒐𝒖𝒓𝒕𝒆𝒆𝒏_


Follow this link to join my WhatsApp group:

https://chat.whatsapp.com/JJkSofA4Hto57YwEu2Z8Xq


*_Wai ni Balki ina duk masoyan Bilyn Abdull ɗin nan dake a manhajar Instagram da TikTok ne?🤔? Kai jama'a gaskiya da kunya ace account na Bilyn Abdull a Instagram da TikTok iya kar fallowers ɗin kenan🥲😣. Ina masoyan facebook ɗin nan dana WhatsApp, Please a fito mana ai fallowing ɗina. Accounts ne na Bussines ko bazaki/zaka saya ba zakaga abinda ya burgeka ko kalarka ka nema a inda kake. Maza ku garzayo BILYN ABDULL ONLINE SHOPPING kodan kashe kwarkwatar idanunku ku more kallo iya kallonku da kaya ƴan yayi cikin farashi mai sauƙi da rahusa. Muna bada sari, muna adashen gata, muna sai da ɗai-ɗai. Ka gani su burgeka, ka saka ka birge mai kallonka sai Bilyn Abdull online shopping. Bari muga akwai ƙaunar kodai-kodai....😉🫣. Ga link nan naga accounts ɗin nan biyu kamar zasu fashe da fallowers 😘😘😘😍😍👍🏻👇🏻_*.

*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

_Ina masu son zuwa ganin likita ko yawon buɗe ido ƙasar Egypt?. To ku garzayo munada hanya mai sauƙi ta sama muku sauƙin tafiya cikin ƙa'ida da bin dokar ƙasa. Katafi anan cikin aminci, ka dawo kuma cikin aminci. Wajen kwananka a can zamu tanada, asibitin da zakaga likita duk zamu tsaya maka da tsayawar UBANGIJI. Hakama yawon hutawa zamu zame maka jagora. Kai ko hanyar zuwa domin sayo kaya duk muna da ita. Kai dai kawai kazo garemu kaga aiki da cikawa da iznin ALLAH. 09032345899. A nememu tanan ga masu buƙata, dan ALLAH serious bama son latsi ko wasa dan ba wasan muka fito ba 😂😍👍🏻._


.......Daga ƙarshe dai tare da shi muka fito bayan mun kashe komai. Da kansa ya buɗe mun mota ya taimaka min na shiga, Paah na kallonmu da murmushi. Sai da ya maida ya rufe sannan ya buɗema Paah ɗin shima. Ya shiga ya zagaya mazaunin driver. Yanda Paah ɗin ke janmu da hira yana ɗan amsa masa yasa naji sanyi a raina. Nima yana sakani a hirar cike da kulawa. Murmushi kawai nake iyayi da bashi amsa a kunyace. Dawowarmu gidan tare da Paah ya saka kowa farin ciki, musamman Ummie data kamani ta rungume tana sanya min albarka. Shima Yaya Awwab ta rungumesa. Fahad na tura baki zai wuce Paah ya jawosa ya rungume shi shima yana murmushi. Alhamdullah ita rayuwa komai akai haƙuri sai ya zama mai sauƙi cikin rahamar UBANGIJI. Ranar kowa zaka samesa cikin cikakkiyar walwala da rabonmu da ita tun a hidimar bikin nan. Duk da haka Paah bai kwana a gidan ba. Ya koma can gidan ya kwana. Sai dai ya sanarma Ummie duk yanda mukayi. Ya kuma mata alƙawarin zaije ya binciki lafiyarsa. Idan har akwai matsala zai sawwaƙe mata. Idan kuma babu shike nan. Amma dan ALLAH kada ta sanar ma su Awwab.
ALLAH sarki Ummie haka kuwa tai gum fa bakinta duk da tana a cikin fargaba da damuwa. Haka shima Paah ɗin yana cikin tashin hankali. Washe gari suka haɗu a asibiti, Yaya Hayat tasa ya kaita. A gabanta akaima Paah komai aka basu kwanaki uku zuwa amsar result. Daga nan ne suka dawo gida. Suun samu baƙi daga Kano, Attahir yayan Mansoor da Mansoor ɗin, sai Mahaifinsu ne suka kawo

Please Login or Register in order to submit comment