Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da kike kallonta yanzu. Jarumi kennan ba irin wannan lusarin mijin naki ba da ko ciki ya kasa baki kusan 18years. Kima shirya aikin nan na zama done no more mata a cikin rayuwar mu”.
“Kai dai ka sani”.
Ta faɗa cikin taɓe baki.
“Kema zaki sani ai. Ina my sweet daughter? Ina fata baki takura min yarinya ko? Dan duk duniya a yanzu banda kowa sai Arwa. Itace farin cikina itace nishaɗi na a itace mafarkina. Dan a yanzu duk wahalar da nake wajen ganin na tara dan ita ne. Ina son duk randa zata kalleni a matsayin mahaifi tasan cewa eh na cancanta.....”
“Hummm kaga ba wannan ya kawoni ba. Akwai matsala fa. Wawan tsohon nan nason raina mana hankali. Tana neman ƙwaɓewa amma ya zauna fushin banza da wofi a maimakon mafitar da zata ɓulle”.
Yanzu kam serious commando ya koma.........✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒗𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_


.........A cije ya ce, “Miya faru kuma?”.
“Humm! Miye ma bai faru ba”.
Tsaff Hajiya ƙarama ta kwashe labarin komai ta bashi. Har korar da Baba prof ya mata yanzun nan. Ta ɗora da faɗin, “Nifa na fara tunanin tafiya plan b. Kawai mu kauda tsohon nan dan na gaji da harkar nan wlhy. Ina buƙatar zuwa na huta. Tuni da mun gama aikinmu amma tsohon nan sai raina mana hankali yake yana jammu a ƙasa, shi banda ma kansa a toshe yake a shekarun nan nasa an gama barbaɗa masa gishirin mutuwa uwar mi zaiyi da kuɗin nan? Amma yabi duk ya maidamu yaransa, garama kai dama yaronsa ne, amma Ni dan uwar ubansa ba aiki mukeyi kai da kai ba, nafa fara gajiya da raina min hankalin da yake dan yana ganina mace, wlhy na fisa bushewar zuciya”.
“Bake kaɗai bace kika gaji da aiki da wannan mutumin, ni kaina na fara gajiya. Dan na fahimci kansa kawai ya sani. Sannan kuma tunaninsa sam baya tafiya yanda ya kamata. Yanzu ko akan zancen yarinyar nan da ake tayi da kuma Maash na bashi ƙafa ne naga ko zaiyi tunani irin na masu hankali. Sai dai da alama giya ta cinye brain ɗinsa. Sam baya tunani irin na masu hankali. Maash fa ba shashasha bane ba, dan shi yana aiki ne da ƙwaƙwalwa da zuciya a lokaci ɗaya. Idan da bai san wanene shi ba tabbas da alama yanzu ya fara farga, dan idan har zamuyi lissafi irin na masu hankali a bayanin da kikamin yanzu akwai lauje cikin naɗi. In babu rami to miya kawo rami. Ya ɗauke mahaifiyarsa ya maida sashensa duk da azababben asirin da oga ya musu. Ƙaninsa ya dawo, a gaba ɗaya yanda yaron ya dawo kuma an tsarata ne. Mi hakan ke nufi”.
“Abinda naso ya fahimta kenan ai amma shi jaki ya wani kironi. Nifa yanzu wannan duk matsalarsa ne. Kawai mu tafi plan b. Dan bazamu cigaba da zama yana juyamu ba. Idan bai sani ba shine a tafin hannunmu ba mune a tafin hannunsa ba. Sannan muke juyashi, ba shike juya mu ba. Duk randa kuma yasan su waye mu wlhy sai zuciyarsa ta buga”.
Dariya sosai Commondo ya kece da ita, sai da yayi mai isarsa kafin ya kalleta yana wani rausayar da kai irin na manyan ƙwari. “Barsa wasa yake da wuta, amma bai san itace zata ƙona shi ba. Na yarda dake kaiwa mu tafi plan b”.
Idanu ta kashe masa tare da bashi hannu suka tafa. Sai kuma ta ce, “Kai tsaya! tsaya! Kayi maganar akwai alaƙa tsakanin yarinyar nan da Awwab. Kana nufin akwai abinda kake ɓoyema yallaɓai akan binciken daya sakaka akan ta ne? Danni fa na gama yarda da gasken gaske yarinyar nan Awwab ya aureta”.
Wani shegen murmushi Commando ya saki, a zuciyarsa yace (Shegiya tsuntsuwar kanari mai wayo. Ai kema bazaki sani ba dan da wannan makamin zan yaƙeki. Yanda zamu haɗu mu kauda yallaɓai haka nima zan kaudaki, kudai gama yimin wahalar, ɗiyata kuwa sai ta dawo hannuna) a fili kuwa sake faɗaɗa murmushin yayi har haƙoransa na bayyana ya ce, “Karki damu zaki sani idan ma akwai in babu sai nan gaba. Yanzu dai ina da uziri. Amma mu haɗu zuwa gobe kamar zai fi.”
(Matsiyaci tabbas akwai abinda kake ɓoyewa. Amma zanyi maganinka. Mudai gama da Yallaɓan kaine next. Dan ku dukanku sai na goge muku hadda. Badai Arwa ce mai gadonka ba, ka gama amsar kason ka kaima na kaudaka dan har abada ƴata bazata san kaine mahaifinta ba. Kamar yanda na sanarma iyayena ka jima da mutuwa da itama kanta har abada a haka zamu cigaba da tafiya) Hajiya ƙarama ce ke wannan zantuka a zuciyarsa. A zahiri kuwa sai ta saki murmushi da faɗin, “Yanda kace ai haka za'ayi Abban Arwa. Kadai tabbatar ka kirani da wuri dan muyi mu gama kasanshi baya tsayawa waje ɗaya. Dan yana ganin yanzu tana neman ƙwaɓewa wata hanyar zai nemo balle ga Awwab ɗin yayi tafiya”.
“Baki da matsala kema kin sanni ai. Na barki lafiya”. Ya ƙare maganar yana buɗe ƙofar ya fice abinsa. Yana gama fita ta dallama bayansa harara tare da taɓe baki. Mamaki ma take yanda akai ta auri guy ɗin nan. Babu yanda Ummu-Hidaya bata bata shawara ba amma a lokacin ta dage akan itafa taga miji. Haka tayi zaman shekaru kusan biyu da shi suka haifi Arwa. Arwa nada shekara ɗaya aka kamashi akan laifin kisan kai. Prison aka kaisa ɗaurin rai da rai. Hakan yasa kawai ta yanke hukunci da tsarama iyayenta da duk danginta cewar yayi haɗarin mota ya mutu dan ba'anan Lagos aka kama shi ba a arewa ne. Kowa ya yarda da ita dan yanda ta tsara komai dole ne ma a yardan, balle ita ba cikakkiyar bahausa bace tana da yare. Anyi zaman makoki da komai da akema mamaci tayi basajar yin takaba. Bayan nan da shekara ɗaya da wasu wattani sannan Arwa nada kusan shekara uku ta auri Alhaji El-Mu'azz, kusan shekara huɗu da aurensu kwatsam sai ga Commondo ya dawo, ba kuma kowane ya fiddosa ba sai Baba prof.. fitowar commondo taso zame mata matsala, dan ya ta mata barazana akan indai bata bar Paah ba sai ya tona mata asiri ya kuma halaka ta. Barazanar nan yasa ya dinga cin kuɗi a hannunta na hauka, har sai da taga abin ya tasarma gurguntata sannan ta zauna ta sanar masa planning ɗinta na auren El-Mu'azz. Tun daga lokacin suka shirya sabon plan akan yallaɓai kasancewar shi commondo yaron yallaɓai ne na ammana kusan ma yana ɗaya a cikin waɗanda suka ƙara kangarar da shi a sanda ya fara rashin ji. Dan haka ɗan amana ne na Baba prof matuƙa shiyyasa suke ganin zasu kadashi cikin sauƙi. A mafi yawan lokuta idan ya ƙulla sukan warware masa batare daya sani ba. Hakama Hajiya ƙarama idan ta ƙulla commondo na warware mata batare data sani ba. Shima kuma commondo ɗin Hajiya ƙaramar kan warware masa. Haka dai suke wannan rayuwa tacin amanar juna amma a zahiri su amintattun juna ne....

🌿🌿🌿🌿🌿

Ranta a ɓace yake har ƙololuwar zuciya. Ta kuma gama yankema kanta koyama Fahad da yarinyar nan dama Awwab ɗin hankali. Hatta da ɗan uwanta bazata ƙyale ba. Waya ta ɗauka tai kiran Auta. Kamar itace ta mata laifin cikin masifa ta zayyane mata komai. Mashi'a sam bata da son fitina. Sai kawai ta shiga bata haƙuri da tabbatar mata cewar tana nan tafe in sha ALLAHU. A satin nan zata shigo Nigeria dan sutukarta ma babu lafiya. Jin hakan ya ɗan sakama Hajiya Mammah nutsuwa. Amma duk da hakan sai da tai kiran Rubayya da rabon da suyi waya harta manta. Da farko Rubayya masifa ta balbaleta da shi. Sai da itama Hajiya Mammah ɗin ta hayayyaƙo mata sannan suka koma dai-dai. Amma duk da hakan ita Rubayya tace bazata zo Maash Mansion ba sai dai ita taje gida ta sameta. Da yake itace ke so kuma a ƙage take ko gardama batai mata ba tace tana jirata gata nan zuwa.
Hakan kuwa akai, ta tashi tai shiri cikin shiga ta alfarma da fariyya data saba ta fita drivern ta ya jata suka wuce gidan aminiyar tata....

To ALLAH yasa a ƙulla alkairi ƙawar o'e🥱😵.

🩸💦🩸💦🩸

Na jima a kwance ina ƙullawa da kwancewa akan rayuwa da kwamacalar gidan nan, tare da abinda na gani game da Ummie. Sai kewar mijina data addaban, dan kona faɗa kona ɓoye haka dai al'amarin yake ina jin kewarsa matuƙa. Hirarsa ta jiya da mutumin nan a office ce ta sake dawo min. Tuna abinda ya bashi flash da file yasa na miƙe na fito. Ɗakinsa na shiga, komai tsaff kamar yanda na gyarashi a ɗazun. Bincike na fara a closet ɗinsa dan tabbas ina son sanin mike a cikin flash ɗin nan. Duk inda nai hasashen zai iya ɓoyesa ban ganshi ba, sai a ƙarshe a banza na samosa ata inda ma mutum bazai taɓa tunanin an ajiye ba. Ganin harda file ɗin yasa na yarda shine. Iya flash ɗin kawai na ɗauka, dan nafi damuwa da son ganin abinda ke'a cikinsa. Sai dai yanzu damuwar a ina zan samu waya ko laptop na kallonsa? Badan babu wayoyi a gidan ba, sai don komai na son sirri ai a rayuwa. Musamman ma wannan shima bazai so ace na saka a wayar wani na kalla ɗin ba. Ban samu makamar kamawa ba. Dan haka na maidashi na ajiye a wajen na fito akan sai na samu mafita. Ƙasa na sauka domin nema mana abincin lunch, amma sai da na leƙa Ummie. Na samu Mama na kwance mata kai sai kawai na fito nima na shiga kitchen ɗin. Ban jima da farawa ba sai ga Fahad da Hafiz. Nan fa sukai zaman tayani munayi muna hira. Ni harma mamakin shaƙuwar Hafiz ɗin da Fahad nakeyi. Sai ka rantse sun san juna tuntuni. Muna kammala abincin salla muka nema, daga nan kowa yayo wanka muka fito.........✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚-𝒕𝒘𝒐_


......Bayan mun kammala lunch su Fahad suka tafi ɗakko Aunty Falaq. Basu wani jimaba kuwa sai gasu. Matuƙar farin ciki duk muka tsinta kammu. Yanda naga Falaq ta rungume Ummie tana kuka da yanda Ummien keta faman shafa kanta da cikinta yasa na sake shiga ƙaulani. Tabbas akwai shaƙuwa a tsakaninsu daka gani, amma duk mai hankali zai iya sakama yanayin Ummien alamar tambaya. Daga baya kuma da taga kamar zamu farga sai ta canja yanayi tama kwanta. Dole muka dawo falo aka buɗe babin sabon hira, salla kawai ke tada mu. Kamar wasa da dare sai ga TJ da saƙo wai inji boss. Ina buɗewa sai ga waya, harda sim card a ciki da cajinta da komai. Nayi farin ciki sosai kowa kuma ya tayani har Mama.
Samun wayar nan ya matuƙar sakani a farin ciki. Dan ji nai kamar na taka rawa. A falon na barsu nacema aunty Falaq zanje nayo shirin barci nazo a ɗakinta zan kwana. Kai tsaye ɗakinsa na wuce na ɗakko flash ɗin nan. Ɗakina na koma jikina har rawa yake. Kamar mai tsoron a kamata sai da na kulle har windows bayan ƙofa sannan na haye gado na saka flash ɗin jikin wayar.....

🌟🌟🌟🌟

Karan farko a rayuwarsa da tun cuɗewar abubuwa ya zauna yin nazari. Sosai abubuwan dake faruwa a gidan ke dawo masa dalla-dalla. Tabbas lokaci yayi da zai gyara mu'amalarsa da ƴaƴansa. Ya kuma tsaya tsayin daka wajen ganin lafiyar matarsa rufin asirinsa. Baya ganin laifin Awwab da Fahad, dan suna da hujjojin da zasu juya masa baya a rayuwa. Suna son mahaifiyarsu, babu kuma wani ɗa na kwarai da za'a wofantarwa da mahaifiya ya iya kawaici koda kuwa mahaifinsa ne. Tun suna masa alkunya da tunatar da shi muhimmanci mahaifiyarsu a garesa har sun daina sun wofantar da shi kawai. Dan gara-gara ma Muhammad na ɗan rangwanta masa sai idan ta ƙurane yake magana. Amma Fahad ko kallo bai siheshi ba. Yanzu haka tunda ya dawo ko hangosa yay sai ya canja hanya. Jiya ne ma data ƙure suka haɗu babu yanda zai yi ya ce masa ina yini. Bai ko jira ya amsa ba yayi wucewarsa...
Shigowar kira ya katse masa tunaninsa. Kamar zai share sai kuma dai ya kalla wayar. Ganin Baba ya sashi sauke ajiyar zuciya. Ɗagawa yay cike da girmamawa ya gaishesa duk da kuwa bai jima da barin gidan ba. Baba prof kam dako amsawa baiyi ba kai tsaye yace yazo ya samesa a gida yanzu nan. Ya amsa masa nan ma da girmamawa. Bai kuma ɓata lokaci ba ya shirya ya fita amsa kiran mahaifin nashi...

Kusan a tare suka shigo gidan, har shi Paah ɗin ma yayi mamaki dan da'alama tunda Baban yabar Maash Mansion sai yanzu ne yake dawowa gidan. Sai da ya dakata Baban ya fara shiga ciki sannan shi yabi bayansa. A falo ya samesa, duk da basu jima da rabuwa ba ya sake gaishesa yana mamakin ganin yanda duk fuskar mahaifin nasu ta birkice. Daga ƙarshe ma kasa haƙurin yayi sai da ya tambaya.
“Baba kana lafiya kuwa?”.
Murmushin yaƙe Baba prof ya ɗan yi, sai kuma ya jinjina ma Paah ɗin kai cikin furzar da numfashi ya ce, “Idan nace da kai babu komai Mu'azz na maka ƙarya.”
Cikin tashin hankali paah ya ce, “To baba miya faru?”.
“Ba daga ni bane Mu'azz daga kune. Al'amarinku ya fara tayar min da hankali musamman kai da ƴar uwarka. Sai kuma Awwab. Yanzu kuna ganin a matsayina na mahaifin ku da mahaifiyarku ta tafi ta barni da ku kun min adalci kenan ku dinga cima kan ku mutunci?. Yanzu har kun kai girman da zaku dinga gorantama kanku akan ƴaƴanku. In ce kamata yay ni da ku mu nutsu mu fuskanci abinda Awwab ke ɓoye mana dangane da yarinyar nan. Ko kuna ganin zancen fyaɗen nan ba komai bane....”
“Baba kayi haƙuri bana katseka bane. Amma bana tunanin Muhammad zai aikata wannan mummunan aikin da gangan. Mu zauna mu auna maganganun Addah da abinda ya faɗa mata ranar. Dole akwai abinda ya kamata musani.”
“Humm banƙi ta taka ba, amma dai ni da kai duk munsan wacece Nafisa ko. Tunda mun san ita fitina bata mata wahala mizai hana mu mata uziri. Ƙaramin abu kaɗan daga aikinta ta maida shi babba.”
“To amma Baba su kuma sai a dinga musu adalci ai. Bai kamata ace muna ƙara musu zafi ba a rayuwarsu. Sun rasa mahaifiyarsu tun suna ƙanana. Duk da bawai ta bar duniya bane amma banbancin kaɗan ne. Ni kuma a matsayina na mahaifi son zuciya ya hanani fuskantar su, na kasa rungumarsu na zame musu madadin uwa na kuma amsa sunan uba. Birinƙyaɗuwata kawai nake yi kuma a matsayinku na iyayena da ita dake matsayin yaya a gareni kun kasa nuna min kuskurena. Badan ALLAH ya kiyaye yaran nan ba wlhy tuni sun iya faɗawa criminals rayuwa. Dan kaine ma mai ɗan jan Muhammad a jiki da, sannan ya samu tattalin Abie kafin yabar duniya. Amma Fahad sam bai samu gatan nan ba. Baba mufa duba al'amarin nan da mahangar adalci.”
Kai kawai Baba prof ke jinjinawa kamar tsohon ƙadangare. Sai da Paah yay shiru kafin yaja gwauron numfashi da faɗin, “Shike nan na yarda duk munyi wannan kuskuren. Sai muyi fatan haɗuwa mu gyara mu duka a yanzu. Amma ita wannan yarinyar da Fahad yace ɗiyar Sarkin mota ce ita da ɗan uwanta kai dama kasan da hakan?”.
“Wlhy sam ban sani ba sai yanzu nima daya faɗa ɗin na sani. Amma nakega ai hakan ba komai bane ba. Dan Abdul-wahab ya cancanci kowane irin ƙyautatawar mu. Ka kuma san shaƙuwar dake tsakanin Abdul-wahab da Muhammad zai iya yin komai domin ganin ya binciko sauran zuri'arsa. Tunda mu bamuyi hakan ba. Da kuma Ummu-Hidaya na lafiya na tabbatar da tuni tayi hakan. Shiyyasa ni sam ban wani yi mamakin hakan ba sai ma daɗi da naji dan sun tabbatar da su ƴaƴan halak ne da basa manta alkairi”.
“Hakane”.
Baba Prof ya faɗa cikin ɗacin rai. Kafin ya nisa da cigaba da faɗin, “Hakan da Awwab yayi na jawo yaran jiki abin a jinina masa ne kam. To amma batun maganar fyaɗen da ake zargin ya mata kuma fa?”.
“Wannan batun Baba yana buƙatar bincike. Kuma shine maƙasudin zargina akan akwai abinda ita Adda ta sani akan al'amarin. Ya kamata kuma ka binciketa, tanan ne kawai zamu iya kamo bakin zaren.”
Nanma kai Baba prof ɗin ya jinjina. Yana dai ta danne zuciyarsa. Sai can yace, “Amma baka tunanin aurenta Awwab yayi?”.
“Aure fa Baba? Yayi aure shi Muhammad ɗin batare da mun sani ba? To waye zai masa walicci? Minene kuma dalilin da zai sa ya aikata hakan? Tunda yasan mu dukanmmu burinmu shine yayi auren?”.
“Nima irin waɗan nan tambayoyin naka sune a raina Mu'azz. Amma tabbas mu zauna muyi tunani irin na masu hankali. Idan har mun tabbatar Awwab zai iya nemo zuri'ar Sarkin mota dan ƙyautatawa taya zai haikema yarinya batare da dalili ba. Gashi nan yin hakan ya zame masa matsala, ya kuma zame mana muma ahalinsa. Duba nan ka gani, na tabbatar zuwa gobe wannan labarin shine zai zama latest”.
Jikin paah har rawa yake wajen amsar magazine ɗin da Baba prof ɗin ke bashi. A shafin farko yaci karo da abinda ya nema rikito masa zuciya waje. A take rawar jikinsa ta ƙara ƙarfi. Idanunsa suka kaɗa jazur. Muryarsa na rawa da yatsarsa dake nuna abinda Mujallar ta rubuta da kuma hoton Maash da yarinyar (Samraah) ya ce, “Bab....ba ya akai wannan maganar ta fita?”.
“Taya zan sani Mu'azz, ni kaina wannan tashin hankalin yasa ka ganni haka. Ina fitowa da Mansion na samu kira. Wani ma'aikacin Mujallar ne ya min gulmar tare da turo min ita. Ya kuma tabbatar min nayi gaggawa kafin su saketa yau ɗin nan. Sai dai ashe na makaro, dan ya turo saƙon ne tin daren jiya ban lura ba sai a yau. Koda na isa gidan Magazine ɗin aikin gama har ya gama.”
“Aiko wlhy Baba sun takalo rigimar da bazasu iya maganinta ba. Dan yau ɗin nan ba gobe ba sai na saka an kama duk wani shege dake aiki a gidan wannan mujallar” ya miƙe a matuƙar fusace ya fice batare da ko sallama ya sake ma Baba prof ɗin ba. Wani shegen murmushi baba prof ɗin ya saki har haƙoransa na bayyana. Sai kuma ya jawo waya ya hau danne-danne tare da kaiwa kunnensa. Ana ɗagawa cike da bada umarni ya furta, “Duk su saki labarin. Ina son daga yanzu zuwa safiya kaf Nigeria dama duniya su san da wannan labarin”. Ƙitt ya yanke kiran, tare da kwashewa da dariya tamkar ba baba prof ɗin nan ba da tsufa ya gama cinyema rayuwa gaba ɗaya sai abinda ya sara kuma. Kai duniya ɗan adam abin tsoro. Idan har jininmu basu tsira daga zaluncinmu ba, to waye kuma zai tsira daga garemu. ALLAH ka gafarta mana kurarenmu, ka hanemu son zuciya da zalunci ga waninmu koda dabba ce😭🙏......✍️

_Masha ALLAH kowa na buƙatar samun lokacin kwalliya a gobe idan ALLAH ya kaimu, jibi kuma suyar mama😋, (to kar dai a manta da ni gaskiya ɗan hanji-hanjin nan na gobe ina jira). ALLAH ka karɓi ibadunmu da wanda sukaje hajji, ALLAH ya dawo mana da su gida lafiya. ALLAH kuma ya maimaita mana da rai da lafiya. ALLAH ya rufama kowa asiri ya hana kowa cin bashi. Mata ƴan uwana dan ALLAH kada a takurama maza yin abinda basu da shi. Duk abinda suka kawo mu amsa kuyi haƙuri mu sanya albarka, ALLAH sai ya bamu ladan haƙuri._



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚-𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_


........Wani irin suya ta bala'i zuciyar Paah keyi. Kai tsaye ya bama driver ɗinsa umarnin wucewa da shi DSS office. Sai dai me suna ɗaukar hanyar a tafiyar da bata fi ta mintuna biyar ba kawai wata mota tasha gabansu, ga titin baida yawan mutane haka sosai sai jefi-jefi. Rai ɓace Paah ya fito ganin drivern sa na ma mai motar magana amma bashi ma da niyyar gyara musu balle fitowa ya basu haƙurin ɓarnar da yay musu dan ya gogi musu mota sosai. Saitin drivern yaje yay knocking glass ɗin wajen. Ana buɗewa kawai aka huro masa abu a fuska. Babu shiri ya haɗiye abinda yake son faɗa ɗin yay baya yana kai hannu a fuskarsa ya share abinda aka huro masan, yana ɗagowa kawai luuuu ya tafi zai faɗi. Ihu drivern sa ya ƙwala yana yo kansa da kiran, “Alhaji! Alhaji!!” kawai suka harbesa har sau biyu. Kafin wani lokaci mai tsayi sun saka Paah a mota sun bar layin driver kwance cikin jini yana magowar mutuwa dan sun samesa ne a ƙirji da cikinsa......

🤔Waye da wannan aiki kuma??.

❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥❤️‍🔥

Gaba ɗaya ji nake tsigar jikina na tashi sosai. Dan har ga ALLAH zuciyata ta ƙara girgiza da ganin Baba prof

Please Login or Register in order to submit comment