Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta shiga mimmiƙewa tuna yanda Ummien ke amsa a yanayin buƙata. Kalamanta ne suka shiga sake dawo masa. Da ƙarfi ya kai hannunsa ya harbar da kayan saman mirrorn tare da faɗin, “I hate myself Ummie! I hate myself!!”.
Yanda yay maganar cikin ƙaraji jikinsa har rawa yake yi. Tunda yake ba'a taɓa faɗa masa kalaman da suka tada masa hankali irin na yau ba. Cikin ƙanƙanin lokaci jijiyoyin kansa da gashin jikinsa duk suka miƙe. Tuni idanunsa sun jirkice sun koma golden maimakon blue. Sake dunƙule hannunsa yay ya kaima mirror ɗin naushi. A take ya shiga tsagewa. Sake kai masa naushin yayi. Sai ga jini ta gaba ɗaya bayan yatsun alamar yaji ciwo. Bai damu ba, sai ma hannuwan da ya kai gaba ɗaya saman kansa dake wani kalar mahaukacin sara masa ya dafesa gaba ɗaya, jiyay gaba ɗaya ɗakin na juya masa. (Wannan ba sabon abu bane a garesa. Aduk sanda zai zurfafa tunani ko damuwa da al'amarin mahaifiyarsa ko san ɗaukar mataki akan wani abu da bai masa ba game da ita tofa sai ciwon kai. Sai kuma hankalinsa ya gushe gaba ɗaya. Idan kuma ya farko shike nan ya manta komai bazai sake tunawa ba ko magana ko maida hankali akan wani abinda ya shafeta).
Yanzun ma dai zubewa yay a kan gadon, tare da cure jikinsa waje guda wani kalar masifaffen sanyi na ratsa illahirin ƙasusuwansa, sai zazzaɓi mai masifar zafi da nuƙurƙusar ɓargon jiki....


💥💥💥💥💥

Nutsuwar data samu game da shawarar Hajiya Rubayya ya sata ajiye batun hukunta Samraah. Sai ma zuciyarta data gama tsara mata fara shirinta a yanzu. Zuciyarta fes ta fito falon. Arwa da Muhsin kawai ta samu a falon suna kallo. Sai masu aiki dake ɗan kai kawo na tsaftace sa duk da babu wani datti. Komawa tayi da baya zuwa ɗakin Azizat. Kwance ta sameta da waya a hannu tana charting, sai Bahijja dake cikin closet ɗinta tana maida kayan data watso ƙasa. Batare data kalla uwar tata ba ta ce, “Mammah any problems?”.
Maimakon taji haushin yanda Azizat ɗin tai magana a tsaitsaye sai ma tai murmushi. Cike da kulawa takai zaune a kusa da ita tana shafa kanta. “Babu komai Baby na. Aikenki dai zanyi sashen Yayanku”.
Da sauri Azizat ta ɗago fuskarta da murmushi. Sai kuma ta tura baki tana mai haɗiyewa. “Mammah bayan Yayan ya sake fita shi da tawagarsa. Ina kuma ƙyautata zaton wata tafiyar ma ya sake yi”.
Da mamaki Hajiya Mammah ke kallonta ta ce, “Tafiya kuma? Bayan yau ya dawo?”. Sai kuma ta dauki wayarta ta shiga daddanawa batare data jira amsa ba. Kunnenta ta kai. Batare da yin ko sallama ba ta ce, “Kuna ina?”.
Cikin girmamawa da ga can aka bata amsa da, “Gamu a airport zamu wuce Chaina”.
“What! Shine ba labari?”.
“I'am sorry Maa. Da alama tafiyar gaggawace ta tasoma Boss ne.”
Ƙwafa tayi, tare da yanke kiran. Batare da tace komai ba kuma ta miƙe tai ficewarta. Da kallo Azizat ta bita sai kuma ta taɓe baki itama ta cigaba da charting ɗin ta.....

✨✨✨✨

A ɓangaren Paah shima hankalinsa ba'a kwance yake ba. Dan tun randa abin nan ya faru bai sake saka samun ko kallon arziƙi daga ɗan nasa ba. Ko jiyyar kwanaki uku da yay a gidan idan ya shiga dubasa sai ya ƙirƙiri barcin ƙarya. Yana samun sauƙi kuma ya tattara ya bar musu gidan. Sai yau ne matarsa ke sanar masa Awwab ɗin ya dawo gida. Shine dalilin barowarsa inda yake a gaggauce yazo gidan. Kai tsaye sashen Awwab ɗin ya nufa, amma tun kafin ma ya shiga Hayatu daya samu a compaund ke sanar masa Awwab ɗin na sashen Hajiya Babba.
Sashen Hajiya Babban yaso nufa shima. Sai dai hakan ya gagara saboda shakkar haɗuwar tasu. Dan yasan a rayuwa Awwab bai haɗa al'amarinsa dana mahaifiyarsa da komai ba. Taɓashin da Hajiya ƙarama tayi ne ya sashi dawowa a hayyacinsa firgigit. Cike da mamaki ta ce, “Lafiya kuwa Abban Awwab?”.
Numfashi ya sauke mai ƙarfi, sai kuma cikin damuwa ya amsa mata da, “Ba komai” yana miƙewa. Da sauri ta riƙo hannunsa. “Ya zakace babu komai bayan ga damuwa ƙarara a fuskarka? Nasan dai bazai wuce akan fushin da Awwab yake ba. Ni a ganina mizai hana kaje ka samesa. Sai ka lallashesa dan yaron nan ya fimu gaskiya, shiyyasa kullum nake nusar da kai illar biyema Addah a gidan nan. Dan koba komai Hajiya Babba uwar ƴaƴanka ce”.
Wani mugun kallo ya watsa mata. Sai kuma ya fisge hannunsa batare da ya tanka mata ba yaja tsaki. Fuuu ya fice abinsa batare da ko waiwayenta ba. Da kallo kawai ta bisa itama. Sai kuma ta girgiza kanta ranta duk a dagule....


💕💕💕💕


*_INDIA_*

Kai kawo take kawai tana kuka ita kaɗai a ɗakin, a kallo ɗaya zaka fahimci tana a cikin matsanancin tashin hankali da bai da misali. Kanta ta shiga girgizawa cike da sakin zantukan da suka zame mata sirrinta cikin sambatu. “Kai ina bazai yiwu ba. Bazan halaka yarona da hannuna ba wlhy. Saimah bazai yiwu ba. Na tafka kuskuren farko bazan bari na sake aikata na biyu ba”. Ta ƙare maganar tana rarumar wayarta. Number ƙanwarta Saimah dake Dubai ta shiga lalubowa. Cikin sa'a kuwa ta sameta a sama-sama dan ko a jiya sunyi waya. Kira ta danna mata, sai dai harta fidda rai da za'a ɗauka tana gab da tsinkewa aka ɗaga.
Mamy da zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri tamkar zata fito ko sallama bata tsaya yi ba ta ambaci sunan yar uwar tata kai tsaye.
“Saimah!”.
Cike da mamaki da shiga tashin hankali ta amsa mata daga can. Sai kuma ta ɗora da faɗin, “Lafiya kuwa Aunty najiki cikin tashin hankali? Kar dai kice min mun rasa Mansoor ne?”.
Wani irin suka ƙarshen zancen Saimah yayiwa Mamy a zuciya. Dan haka a fusace ta bata amsa da, “Oh haka kuke zaman jiran ji kenan shiyyasa kika saka ƴarki ta kirasa a waya ta tada masa da hankali da yake bata da isashiyar tarbiyya. To bai mutu ba, ba kuma zai mutu a sanadin auren shashashar ɗiyarki ba in sha ALLAHU....”
A fusace Saimah ta ce, “Wace irin magana ce wannan kuma daga tambaya Sadiyya?”.
“Kin fini sani Saimah. Nace kin fini sani. Duk wata masifa kece ummul ana isin sakamu cikinta. Kai haba nagaji bazan iya jurewaba gaskiya. Maganar auren Mansoor da Husnah babu shi tunda baya so”.
Wata shegiyar dariya Saimah ta sanya daga can. Sai da tayi mai isarta sannan ta ɗora da faɗin, “Wannan shine kuskure mafi muni da zakiyi a rayuwarki kuwa Sadiya. Dan in har Mansoor zai ce bazai zauna da Husnah ba to kemafa ki shirya tsaff dan auren shekara talatin da takwas zai guntule shima. Zan sanarma mijinki da ɗanki abinda kika aikata game da auren Mansoor na farko. Na kuma sanarma duniya komai. Ya rage naki yanke hukunci. Kin san kuma shima Maash ɗin ba kanwar lasa bane dan ya tabbatar miki da hakan”. Ɗit-ɗit ta yanke wayarta.
A matuƙar fusace Mamy tai wani irin masifar yin cilli da wayarta. Sai kuma ta zube a saman gadon ɗakin hotel ɗin tana fashewa da kuka mai masifar ƙarfi...

“Mi kike ɓoyewa Halimatu?”.
Firgigit ta juyo tana kallonsa. Sai kuma ta mike zumbur tana goge hawayenta jikinta na karkarwa. Cikin rawar murya da kaƙaro murmushi take girgiza masa kanta. “Abban Attahir yaushe ka shigo? Dama kana ɗakin nan? Ai ban san kana nan ba wlhy....”
Hannu ya ɗaga mata. Dole tai shiru. Cikin ɓacin rai ya sake maimaita mata tambayar farko. Sake daburcewa tayi. Harshenta na sarƙewa ta ce, “Ba komai. ALLAH ba komai. Ko kaji wani abu ne?”.
Maimakon amsa mata idanunsa kawai ya dasa mata. Sai kuma ya jinjina kansa batare daya sake tanka mata ba ya juya ya fice abinsa. Gaba ɗaya ji Mamy tai ɗakin na juya mata tsabar tashin hankali. Birkicewa ta sake yi tamkar sabon kamun hauka. Itako idan har Abban Attahiru yaji wayar nan tata ta shiga uku. Wannan wace kalar rayuwa ce ta jefa kanta da ɗanta a ciki saboda kwaɗayin abin duniya. Wane irin son zuciya ne? Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un...

Da ƙyar likitoci suka iya controlling sabon yanayin da Mansoor ya shiga. Dan a baya baya aman jini sam. Gashi yanzu iyayensa sun sake jangwaɓo abinda yafi na farko. Bayan dawowa a hayyacinsa hana kowa akai shiga ganinsa har na tsawon kwanaki uku. Sai da suka tabbatar komai ya dawo normal sannan suka barsu ganinsa bayan anja musu dogon gargaɗi.
Sunji farin cikin samun lafiyar tasa. Sai dai bai kula kowa a cikinsu ba har suka gaji da zama suka fito saboda adadin lokacin da aka basu ya cika. Suna fitowa Dad yay wucewarsa, dan har yanzu babu jituwa tsakaninsa da Mamy. Ya tattarata ya watsar da al'amarin ta. Bai kuma sake mata magana akan komai ba. Itako duk wanda ya kalleta yasan bata a cikin hayyacinta a kwanakin nan. Dan komai ya gama ƙwace mata. Ta rasa ina zata kama danta mafi soyuwa a ranta da mijinta na neman kuɓuce mata a dalilin son zuciyarta........✍️


_Humm Mamy wai mi kika aikata ne haka? Miya kuma alakantaki da Maash??🤔_


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_


......A kunyace ta fito daga banɗakin bayan kammala canja kayan da Abba ya bata na barci. Tana fitowa suka haɗa ido da Abba dake zaune a bakin gado saitin ƙofar toilet ɗin. Ƙara cikuykuye Hijjab ɗin nata tayi da saurin duƙar da kanta ta koma jikin bango ta lafe. Murmushi ya saki tare da miƙa mata hannu alamar tazo. Sai dai ta gagara yin hakan sai ma idanunta ne da sukai ƙwalƙwal kamar zata fasa kuka. Murmushi Abban ya sake yi da sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ya miƙe ya nufeta. Hannunta ya kamo ya jawota jikinsa ya rungume. Kafin a hankali cikin dabara ya zane Hijjab ɗin nata ya cilla saman kujera ƙwara ɗaya dake ɗakin. Ƙoƙarin raba jikinsa da nata yayi amma taƙi yarda da hakan. Sai ma sake ƙanƙamesa da tai tana jujjuya kan nata alamar dai bata son ya ganta a kayan barcin.
A hankali ya ranƙwafa saitin kunnenta ya raɗa mata, “Mu kwana a haka kenan bazaki gaji ba?”.
Kafaɗa ta noƙe masa alamar a'a. Sai kuma cikin rawar murya ta ce, “Dan ALLAH zan saka hijjab ɗin dai”.
“Kin taɓa ganin amarya da hijjabi a gaban angonta?”. Ya sake raɗa mata cikin kasala. Kasa iya cemasa komai tayi, sai ma cusa kanta da ta sake yi cikin jikinsa. Shima sai bai sake magana ba ya ɗagata cak sai tsintar kanta tayi a gado. Yanda tai wani mugun duƙunƙunewa waje guda kamar ƴar mage ya bashi dariya. Gadon ya hau shima tare da rage wutar ɗakin ya sake jawota jikinsa ya rungume....

★“Umma ki buɗe min, na rantse da ALLAH Imamu bai isa ya kwana ɗakin tsinanniyar yarinyar can ba.”
“Jalilah bazan buɗe ba. Wai miyasa ke baƙya jin nasiha ne a rayuwarki. Wannan shirmen naki wai kina tunanin zai haifar mana da ɗa mai ido ne? A gabana a gaban ƴaƴanki fa ya rantse ya maya akan in har kika cigaba da ɗaga masa hankali sai ya sake ki babu ko shakka balle kunyata. Amma har kike kasa maida hankalinki jikinki ki nutsu mubi hanyar mai ɓullewa. Imamun yanzu fa ba irin na da bane ba. Ko so kike ya sake kin ki tafi ki bar mata gidan ne shike nan taci nasara a kanki?”.
Kuka mai ƙarfi Mom ta saki. Batare data amsawa Umman tata ba ta zube a wajen tana kara ƙarfin kukanta har numfashinta na seizing tamkar zai rabu da gangar jikinta. Duƙawa Umma dake cikin matsanancin damuwa tayi itama tana cigaba da lallashinta...

★Zumbur Halime ta miƙe tana zare idanu jin hannun Abba akan jikinta. Shima Abba sai ya miƙe cikin mamakinta ya kunna fitilar ɗakin. “Lafiya kuwa Halimatu?”.
Kai ta girgiza masa tan ƙoƙarin sauka a gadon, riƙota ya sake yi, sai kawai ta fisge hannun ta sauka gaba ɗaya har tana haɗawa da kamar gudu. Zuba mata ido kawai Abba yay mamaki na neman kasheshi. Itako tana lafe jikin bango sai zare idanu takeyi. Murmushi Abba yayi da girgiza kansa. Sai kuma cikin ɗan rage murya ya furta, “Kina son wani abu ne?”.
Kanta ta girgiza masa. Shima sai ya sake jinjina kan. “Okay miya faru to?”.
“Zan je falo na kwanta?”.
“Saboda me?”.
“Naga zaka kwana anan ne”.
“Ai nan ne ya dace dana kwanta Halimatussa'adiyya”.
Da sauri ta ce, “Hu'imm tabb”.
(Badaƙala) Abba ya faɗa a zuciyarsa yana cizon lips ɗinsa. Sai kuma yay ƙoƙarin sakkowa a gadon. Tana ganin zai nufota ta kwasa a guje zatai falo. Ai baima san lokacin daya buga tsalle ya cafkota ba. Kuka ta fashe masa da shi. “Dan ALLAH kayi haƙuri Alhaji. Ni wlhy babu ruwana bana so. Kai fa babba ne”.
Hankalin Abba tashi ya nema yi, a zuciyarsa ya ayyana (Haba Halimatu taya zan iya haƙuri da wannan baiwar taki) a fili kuwa sai ya jawota ya matse a jikinsa. Duk yanda take mutsu-mutsu yaƙi ya saketa. Dan ya tabbatar tana samun sa'a wlhy sai dai yaji a salansa. Shiko yanda ya samu ya killafa Mom ai gara dai ya angwance dan ganin Halime matsayin amarya zuwa gobe sabon show ne yasan zai tashi. Gara ya mora yasan ya mora duk ma wadda za'ayi sai ayi kawai ko.
Cak ya ɗaga Halime zuwa saman gadon. Aiko ta ƙwalla ƙara tana ƙoƙarin turesa. Duk da su Abba an girma ai ƙarfin ba ɗaya ba. Ganin ma tana neman tona mas asiri gida cike da ƴaƴa ga suruka ga Gwaggo sai kawai yay maganin bakin ta hanyar rufesa da nashi. Daga haka ya shiga tabbatar ma Halime shima ɗin da duk da shekaru sun ja da sauransa....

Wani masifaffen ihu da Halime ta fasa tuni ya gama karaɗe gidan. Sai ko a kunnen kowa musamman Mom data gagara rintsawa ita da Ummanta. Dan Gwaggo Gudidi tuni tayi barcinta hankali kwance. Wani irin masifar yankawa zuciyar Mom tayi. Sai ko gata ta ɓaro daga saman gado jikinta na masifar rawa da karkarwa. Ƙofa ta nufa cikin rufewar ido tana dannama Abba zagi da tsinuwa. Tana buɗe ƙofar tayo baya da sauri tare da saka duka hannayenta biyu ta toshe kunnuwanta tana mai fashewa da kuka.. Cikin sauri Ummanta ta miƙe. Kanta tayo da sassarfa. Sai dai me, itama tana zuwa jikin ƙofar ta jiyo kukan Halime da roƙon da takema Abba. Tare da surutan Abba cikin sakin layi...
“A'uzubillahi minnashshaiɗanirrajim. La'ilaha illalahu Muhammadurrasulillahi Sallallahu alaihi Wasallam. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un Imamu ka gama tambaɗewa. Imamu kayi asara kayi girman kwabo. Wlhy ka gama watsewa Imamu gagararre mara mutunci” ta danna ƙofar da ƙarfi cikin sambatu da ruɗewa. Tuni tsohuwa ta rikice taji abinda yafi ƙarfin rashin kunyarta🥱. Yayinda Mom ta sake gigicewa dalilin salatin Ummanta. Sai kawai ta dinga numfashi da ƙyar kamar zata shiɗe.....

😒Mom ƙyale Abba kinji, ai zai dawo ne zaici mutanen garinsu gwarzo 🥱🤥.


💢💢💢💢

*_INDIA_*

A India kam sama da ƙasa an nema Mansoor an rasa. Dan a daren jiya ya gudu daga asibiti. Matuƙar ƙololuwar tashin hankali iyayensa da ƴan uwansa sun gama shiga. A take suka shiga bincike. Sai gashi an gano cewar yabi jirgin zuwa Abu-dabi a daren jiya. A yanzu hakama awanni biyu kenan da saukar jirgin.
Hankalin Mamy ne yafi na kowa tashi a wannan karon. Dan haka ta azalzalesu akan su bishi. Da farko Dad yaƙi bata goyon baya, sai da Attahir yayta roƙonsa dan shi baisan mike faruwa ba sannan ya amince bisa shawarar da tashi zuciyar ta bashi shima na bari suje ɗin yaga ƙarshen abinda Mamyn ke shiryawa. A ranar basu sami jirgin wucewa Dubai ɗin ba. Sai kuma hakan ma ya zame musu alkairi dan Mamy a daren ta samu labarin zuwan ƙanwar tata Nigeria, dan haka ta sauya akalar tafiyar tasu suma zuwa Nigeria. Dan ta tabbatar in har Mansoor yaje Dubai bai samu Sakinar ba shima Nigeria ɗin zai nufa.
Hakan kuwa ce ta faru, sai dai a washe garin ma basu sami jirgin Nigeria kai tsaye ba sai na Dubai ɗin. Hukuncin UBANGIJI a Dubai ɗin kuma sai jirgi ya haɗasu da Mansoor da shima zai wuce Nigeria ɗin. Nunawa yay ma kamar bai gansu ba, sai da Attahir yaje har inda yake ya masa magana cikin tsokana da lallashi sannan ya kulashi. Suma su Dad ya gaidasu a ciccinkushe. Shi dai Dad ɗin bai kulashi ba. Sai Mamy ce keta nan nan da shi.

Koda suka iso Nigeria tun a airport suka sake nema Mansoor suka rasa. Tashi hankalin Mamy ya sake yi, bata ko saurari Dad ba ta shiga taxi tace ya kaita anguwar su Sakina. Dan suna da gida anan Kano da in sunzo suke sauka. Attahir ne cikin damuwa yay ƙoƙarin tsaidata, amma sai bata ko sauraresa ba dan haka yay zuguy yana kallon motar. Sai kuma ya juyo yana kallon Dad da shima yake tsaye cikin matsanancin ɓacin rai bai ce komai ba. Rasa abin cewa Attahir ɗin yayi, sai kawai ya duƙar da kansa yay shiru zuciyarsa duk a dagule dan shi kam ya rasa mike faruwa haka kuma a tsakanin iyayen nasu cikin kwanakin nan.....

💞⭐💞⭐💞

MAASH

Har dare bai san inda hankalinsa yake ba. Sai gabannin asubahi zazzaɓin ya sakesa. Ajiyar zuciya ya ringa saukewa a jajjere. Kafin ya miƙe zaune cikin dauriya saboda kiraye-kirayen sallar asubahi da ake tayi tako ina. Cikin nauyin jiki da rashin ƙwari ya nufi bathroom yana haɗa hanya. Ruwa mai zafi ya samu ya shiga. Sai da ya tabbatar ya ratsashi tare da watsakke masa jiki sannan yay wankan da alwala ya fito. Dukkanin sallolin daya rasa jiya saboda yanayin da yake ya fara ramawa. Bayan ya idar da sallar asubahi har zai kwanta sai kuma zuciyarsa ta gargaɗesa akan hakan. Alkur'ani ya ɗauka ya fara karatu, tun yanayi da ƙyar har jikinsa ya fara sakewa nutsuwa ta fara riskarsa. A jajjere ya dinga sauke ajiyar zuciya nan ma. Sai da ya kai har inda yake buƙata kafin ya miƙe ya hau gadon ya kwanta. Shi ba ma'abocin yawan kwanciya barci bane musamman ma na safe saboda yawan uziri. Amma rashin samun na dare yana kwanciya barci mai nauyin gaske yay awon gaba da shi...

A lokacin da Maash ke a sashensa yana fama da ciwo a ɓangaren Samraah tsaye take ƙyam akan ƙafafunta tana miƙama UBANGIJI kukanta. Kaso biyu bisa ukun daren ta rayashine da ƙiyamullail. Kafin ta ɗora da karatun Alqur'ani har asubahi. Tana idarwa duk da barcin dake a cikin idanunta haka ta ɗora shi ta cigaba dayi. Tanayi tana tofama a ruwan data ajiye botiki guda. Da yake tasa himma kafin goma tayi taci kusan izifi ashirin da wani abu. Motse-motsen da Ummie keyi ya fargar da ita, (yunwa) ta ayyana a ranta tana ƙoƙarin miƙewa. Ilai kuwa sai gashi tana farkawa da kiran sunan “Muhammad yunwa. Yunwa Muhammad” ta fara cin karo. Zumut ta miƙa ta nufeta har tana tuntuɓe da katifa............✍️


_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒘𝒐_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_


........Sosai mamaki ya kama Paah jin wai Maash ya sake barin gidan. A take ya ɗaga waya yay kiran Hayatu dan yasan ko kiran Maash ɗin yay a yanzu ba lallai ya ɗaga ba. Dan a ganinsa har yanzu fushi yake akan abinda ya faru. Amsar da Hayatun ya bashi na tabbacin sun wuce ya sake tsaya masa a rai. Sai kawai yaji duk yana ƙara zargin kansa da kansa. Da sauri ya miƙe ya nufi sashen Hajiya Babba. Sai dai me ya samu sashen a kulle. Kai tsaye zargin Maash ne ya kulle yazo masa. Jiki a sanyaye ya sakko yana jin lallai dole shima ya nufi Chaina a yau ko gobe su haɗu da Maash ɗin.


🌟🌟🌟


Cikin barci ya farka da matsanancin ciwon kai. Duk da yanda yaso samun nutsuwa hakan ya gagara. Har magani yasha duk da tsanar da yay masa amma ina. Ya jima yana tsintar kansa a irin wannan halin a mabanbanta lokuta. Sai dai na yau ya tsananta sosai. Dan duk yanda yaso sake komawa ya duba Ummie ya gagara hakan. Har dare yana cikin mawuyacin hali. Salla kawai ke tada shi. Ai kusan ƙarfe ɗaya babu shiri dole yabar gidan. Dan ji ya dinga yi tamkar ana masa yayyafi da garwashin wuta. Ya tsani gidan da komai na cikinsa matuƙa. Kasancewar cikin dare sosai ya fita a gidan babu wanda ya sani da ga ALLAH sai shi sai mijin Mama Balki da ya kira ta waya. Hatta da securitys ɗin gate sanin matsayin Malam Baba agidan yasa koda zai fita da baƙo babu wanda ya iya cewa komai. Azatonsu ma ko mai magani ne tunda yau ciwon Hajiya Babba ya tashi sosai tun safe aketa fama..
Can wani gidansa ƙarami dake a wata anguwa daban dole Malam Baba ya kaisa, anan yay jiyyar kwanaki uku ya dawo ragal, sai sannan yake ji a bakin Malam Baba ai jikin Ummie ya motsa sosai amma itama dai da sauƙi. Dan baƙuwar yarinyar nan na tsaye akan al'amarin dan ma taji mata ciwo. Kasa cewa komai Maash ɗin yayi, sai guri ɗaya daya zubama idanu kawai

Please Login or Register in order to submit comment