Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yana faɗin, “Kuzo to ku gani wlhy”. Duk binsa sukai cikin sassarfa suma. Wanda ke da ɗan yanayin hausawa a cikinsu ne ya ce, “Kamar suma tayi dai, Ayo ka kira oga Please, kasan dai irin gargaɗi da sharuɗɗan daya gindaya mana. Kar muce zamuyi shiru mu samu matsa”.
“Exertly maganarka gaskiya ne.” ya faɗa yana ƙoƙarin danna waya. Duk cikin harshen nasara suke maganar. Baifi mintuna biyu ba sai gashi ya dawo. Ya sanar musu oga yace duk su fita a ɗakin za'azo da doctor yanzu. Hakan kuwa akai duk suka fita, Ayo ya kulle ɗakin kamar yanda aka umarcesa. Bako a cika minti talatin cif ba sai ga driver ya kawo doctor. Ita kaɗai ta shiga ɗakin bayan Ayo ya buɗe mata. Sai da ta ƙarema fuskar Samraah kallo kafin ta kira Ayo ya taimaka mata suka maidata saman katifar. Duk taimakon daya dace tai ƙoƙarin bata, cikin ko ƙanƙanin lokaci ta farfaɗo. Sai dai tana buɗe ido ta dafe mararta da hannu bibbiyu tana kuka da murƙususu sosai. Da ƙyar ma take iya amsa tambayoyin doctor ɗin. Kasancewar likitar ƙwararriya ba'a wani ja da nisa ba ta fahimci matsalar Samraah. A take tai kiran wanda ya sakata aikin. Ta sanar masa zata turo sunayen magungunan da alluran da take buƙata yanzun nan a sayo a kawo mata. Yace okay ba damuwa ta tura. Rubutawa tai ta tura, sannan ta cigaba da bama Samraah taimakon daya dace kafin a kawo. Ba'a ɗauki lokaci ba Ayo yay knocking, izinin shigowa ta bashi. Ya shigo ɗauke da leda yace an kawone a bata. Amsa tai da godiya, shi kuma ya juya ya fita.
Duk zafin ciwo baya hanani shiga ruɗani a duk sanda za'amin allura. Yanzun ma hakane. Dan tunda na fahimci abinda take shirin mun na birkice mata. Duk yanda taso tankwarani kuwa ta kasa. Dan da gasken gaske na tsani allura harma da magani. Dole tai kiran wani wai yazo ya riƙeni. Nako tubure akan wlhy babu shegen gardin da zai taɓani. Ta ɗauka azabar ciwoce kawai ta sakani faɗin hakan. Sai da mutumin data kira ya shigo yana kawo hannu sukaga na rarumi handbag ɗinta zan kai masa duka sannan. Shiko yay baya da sauri yana yare da ɗaga hannaye sama. Ina kallonta tai murmushi da bashi umarnin fita. Ita kuma ta ɗauki waya, sai da ta daddana sannan takai kunne. Ina jinta sama-sama tana sanarma wanda ta kira cewar ina tsoron allura, na kuma ƙi yarda a riƙeni. Ban san mi aka gaya mata daga can ba na dai jita tana cewa okay. Daga haka ma ciwo yaci ƙarfina har tai allurar bamma sani ba saboda yanda marata kemin azaba har ina shiɗewa. Sai gani nai kawai ta haɗa kayan tafiya. Babu jimawa barci ya ɗaukeni, dama haka allurar kemin duk sanda akayita.
In dai aka min irin allurar nan cikin amincin ALLAH da nayi barci na farka shike nan. Amma abin mamaki yau saɓanin haka. Dan cikin dare na farka amma da sabon ciwon mara da yafi na farko ma. Ciwo sosai harna suma sau kusan biyu. Bamma san yaya akai ba naga doctor ɗin ɗazun a kaina. Tare da wata fuska dana taɓa sani sai dai na mance a ina nasan fuskar dan ciwo ya sakani galabaita dishi-dishi nake ɗan ganinsu, amma tabbas nasan fuskar wannan mutumin, kuma ya kamata na tuna ina ne na sanshi.......✍️


_🥱Ya kamata ki tuno dai kam, koma fita a ruɗani muma Samraatu🚴._



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_



.......Yanzun ma dai barci ne mai nauyi sosai ya sake yin awon gaba dani batare dana gama tantance fuskar mutumin ba. Ban kuma farka ba sai washe gari da rana gatse-gatse. A yanzun ma dai ba farkawar daɗin rai bace ba. Dan still dai ciwon ne ya farkar dani ta yanda har sai da doctor ta sake dawowa. Yanzun kam naga alamun ruɗanin yanayin nawa a fuskarta itama. Dan bayan ta ɗan duddubani fita tayi tana danna waya, da alama magana take son yi da wani...
Bata wani jima sosai ba ta sake dawowa. Allurar dai ta sake fakar idona tamun, sai dai da alama tamafi ta jiya ƙarfi. Dan ko minti biyu cikakku banyi ba na sake komawa barci, daga haka ban san wainar da ake toyawa ba kuma...

A ɓangaren Doctor bayan tama Samraah allurar barci ya ɗauketa babu jimawa wanda tai kira a waya ya iso. Kamar yanda ta shawarcesa da kai Samraah asibiti ya amince. Sai dai da kansa ya nuna zai kaisu asibitin data tabbatar masa akwai dukkan tsaron da suke buƙata. Dan ya sanar mata alaƙarsu da yarinyar ta yanda hankalinta zai ɗauka bawai ainahin gaskiyar sato ta ko kwatota ne ma oho musu ba. Ita kuma jin wanda ya saka aikin yasa bata wani damu ko ɗarsa zargi a ranta ba take bata duk wannan kulawar. Dan tun jiya da tasan yana a garin Abujar nan take jin wani farin ciki, tasan kuma a dalilin aikin yarinyar nan zata iya haɗuwa da shi, duk da dai yanayin ciwon yarinyar yana buƙatar aje da ita asibitin da gasken..
Sun isa asibiti batare da wata matsala ba. An kuma yima Samraah dukkan binciken daya dace. Dan har dare suna a asibitin, sai kusan goma suka gano matsalarta. A take suka haɗo duk abinda zai taimaka mata a matakin farko kafin ai mata abinda ya dace. Gidan suka sake maidota aka saka mata drip kamar yanda ya buƙata, daga haka suka fice aka barta da masu tsaronta.

Tunda suka shigo katafaren ginannen gidan take jin jina kai da sakin kurmushi. Duk da tasan wannan ba komai bane daga mamallakin gidan. Amma dai tayi mamakin yanda yaron nasa ya bata labarin an ginashi cikin ƙanƙanin lokaci tare da wani ma a Kano. Duk da kuwa tasan yana da gidaje sosai a Abujar nan da basu da adadi ma musamman ga ita da ba kowanne ta sani ba, amma tasan wannan ɗin na musamman ne gaskiya. Har kusan ƙofar falon ya kai kafin yay parking, cikin murmushi yay mata nuni da suje ciki. Babu musu ta ɓalle murfin motar ta fita, sai wani taku take cikin yauƙi da yanga. Tun a takun farko na shigowa falon wani sanyi da ƙamshi mai sauke gajiya suka ratsata. Ta wani shaƙi iska da dogon hancinta ta fesar a slowly. Ko makaho yasan falon ya haɗu tamkar mai shi. A hankali ta ɗan kai dubanta ta gefen damarta da take jin ƙamshinsa yafi yawaita a tanan. Shine kuwa zaune cikin kujera 1sitter da laptop a saman ƙafafunsa daya miƙe saman Centre table. Yanda keyboard ɗin laptop ɗin ke bada sautin ƙara zai tabbatar maka da typing abu yake. Da alama kuma mai matuƙar muhimmanci ne. Dan gaba ɗaya hankalinsa na kan screen ɗin, kuma yana dannawa ne da ɗan yanayin sauri na ƙwarewar sabo da hakan. Ƙananun kaya ne a jikinsa kamar ko yaushe. Dan sune suturar da yafi sakawa sai ko suit kamar dangin yahudu. Sai dai kasancewar wandon nasa kaɗan ya zarta gwiwa ya bama ƙafafunsa damar bayyana samɓal. Har suka kai zaune bai kallesu ba balle ya nuna yasan da shigowarsu. Sai da ya ɓata kusan mintuna shida curr sannan yay magana batare da ya kallesun ba yanzu ma.
“Any problems?”.
Ya faɗa a daƙile cikin silent voice ɗinsa. Hayatu ne ya jin jina kai yana mai sake sakama kansa nutsu da gyara tsaiwarsa cikin nuna girmamawa sosai. “Eh to Sir dama dai akan batun yarinyar can ne. Kasan tun jiya na sanar maka abinda ke faruwa na rashin lafiyar da take ciki, har kace Dr Rumaisa tazo ta dubata. To tun dai jiyan tayi duk abinda ya dace amma ba'a dace ba. Ɗazun dai dole tasa mukaje da ita asibiti domin a bincika matsalar ta shine dama muka zo sanar maka dan yan zun ne muke dawo wa...”
Shiru kamar bazai tanka ba, sai da ya mula dan kasa ya furta, “Uhum ina sauraren ku”.
Da sauri Doctor Rumaisa tai tsigil ta ce, “Ranka ya daɗe Good evening”.
Bai amsa mata ba, illa ɗan jinjina kansa da yay kawai alamar amsawar kenan batare da ya kalleta ba kuma. Taji ba daɗi, dan ba haka taso ba. Amma sai ta daure ko za'a dace ta cigaba da faɗin, “Gaskiya yarinyar akwai babbar matsala a tare da ita. Da alama tun kafin yanzu tana fama da pain a duk sanda zatayi prioud, kuma yana mata tsanani. Maybe hakan ne ya jata ta dinga shan maganin hana zuwan prioud ɗin a duk sanda lokacinsa yayi, shine ya haifar da matsalar wannan karon ɗin. Dan sai wahala kawai take sha amma jinin yaƙi ya fita, yanzu dai in sha ALLAHU na mata dukkan abinda ya dace akoda yaushe zai iya fita ɗin, sai kuma ta kiyaye cigaba da shan wancan magungunan inba haka ba zatama kanta illa. Dan a yanzu hakan ma sai an ɗorata akan magunguna masu ƙarfi sosai da zai dai-daita mata komai, sai dai sunada wahalar samu maganin dan sunada tsada gaskiya, ba kowanne pharmacy zaka iya ganinsu anan ba ma”.
A yanzu ɗin ma dai babu alamar zai amsa dan kamar ma bashi takema bayanin ba. Hakan yasa Hayatu bata amsar dan yasan Maash bazai sake magana ba kuma. “Sir zan ƙarasa komai in sha ALLAH. Dama dai na kawota ne kawai ta maka bayani yanda zakafi fahimta.” daga haka yayma Dr Rumaisa nunin ta miƙe shima yana tashi. Sam ba haka taso ba, dan fuskarta ma ta nuna. Ta kafe Maash da kallo tana mai fatan ya sake cewa wani abu koda bazai ɗago ɗin ya kalleta ba, dan dama ita ta matsama Hayatu akan ya kawota ta masa bayani da kanta. Amma sai bai ko kallonsu ba aikinsa ma ya cigaba dayi kamar yanda suka shigo suka samesa. Sai ka ɗauka ma ya manta da su a falon ne tsabar halin yarfin mutumin nan.
Suna fita ta kalli Hayatu rai ɓace. “Amma ba haka mukai da kai ba Hayatu?”.
“To yaya kike so nayi doctor. Kin san dai halin Boss ba sai na sake tisa miki ba. Ba yau ne kika fara masa aiki ba kuma. Shiyyasa naso ma ki bari muyi komai mu gama iya mu kaɗai tunda ba gagara zai yi ba. Tunda kuma shine yasa kizo zai buƙaci ku haɗu kafin mubar garin. Yanzu dai kiyi haƙuri a madadinsa. Kiyi kuma magana da pharmacy ɗin da kikace zasu turo maganungunan nata. Sannan ki bada account number da za'a saka kuɗin.”
Gaba ɗaya fuskarta ta sauya da tsantsar damuwa da ɓacin rai. Duk da dai tasan zata shaƙi kuɗi a aikin nan, dan ko Hayatu hannunsa a buɗe yake tamkar boss ɗin nashi a wajen ƙyautatawa. Kamar zatayi magana sai kuma dai ta shanye da ƙyar, gaba tai idanunta na cika da hawaye ta buɗe motar da suka zo ta shiga. Murmushi Hayatu dake binta da kallo yayi, acan ƙasan ransa kuma yana jin tausayinta. Dan yasan tamkar ta ɗebo ruwan dafa kanta ne dakon soyayyar wanda soyayyar uwa kawai da familynsa ya sani sama data wata ɗiya mace a wannan rayuwar. Shi kansa har mamaki yake anya ogan nasa nada lafiya kuwa, dan shi dai zai iya rantsewa, bayan abokan huɗɗa dana aiki be taɓa ganin wata mace a gefen ogansa ba da sunan yana mata kallon mace mahaɗin rayuwa ko wani ɓangaren jin daɗin duniya. Shi dai kawai neman kuɗi, ina zaka business ina ka fito business. Abinda kawai ke birgesa da shi neman kuɗi bai taɓa shagaltar da shi bautan ALLAH ba. Ga shi dai nan da zubin tsagerun mutane, amma batun ibada babu wasa.. Motar ya shiga shima, yay mata key suka fice a gidan bayan securitys dake gate ɗin sun buɗe masa. Lallashi da daɗaɗan kalamai ya dinga gayama Doctor Rumaisa, acewarsa ta cigaba da addu'a, idan ALLAH ya ƙaddara Maash mijinta ne sai ya aureta. A hankali ta saki murmushi kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta, shi ko ya girgiza kansa dan shima ya san dai gangan yake faɗa, dan ga wata can ma a Lagos data fita wayewa da komai ana tirƙa-tirƙa bayan na bayan fage da iyayensu suke faman masa tallarsu wasu ko sune da kansu suke masa tallar kansun. Shifa yasha ganin ballagazayen wasu matan na kuka akan Maash ko kwanciya yay dasu idana bazai aurensu ba, amma ko kallonsu bayayi ma balle su samu karɓuwa. Gaskiya kuɗi a mafi yawan lokuta fitinarsu tafi alkairinsu yawa. Shi shaida ne. Dan shi kansa ma da bashi ke da dukiyar ba yana cin azaba balle shi Maash ɗin da kansa. Aure ma da ƙyar akai masa a shekarar data wuce, yanzu haka matar nada ciki, amma kullum cikin faɗa suke akan rashin lokacinsa. inaga kuma matar mai gayya mai aiki da ake fatan ta shigo, ai duk wadda zata zauna da shi a matsayin aure kam sai ta jajirce, ko dai ta dinga binsa duk inda zai je itama taji a jikinta dan yawon ma ba hutu bane, ko kuma ta cigaba da hakuri da abinda ta gani kawai.......✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_



......Har gidansu dake anan Abujar Hayatu ya maida doctor. Koda ya dawo a inda suka barsa nan ya sake samunsa. Yanda yaga fuskarsa tai kicin-kicin sosai ya sashi sake nutsuwa, kamar yaron da yayma mamarsa laifi kafin ya tafi makaranta. Sun kai tsahon minti uku a hakan yana satar kallonsa, shiko yana aikinsa kamar bai san da shigowar tasa ba. Sai can a bazata cikin daƙilalliyar muryar nan tasa dake fita silent ya furta, “Bani black tea”.
Da sauri Hayatu ya amsa da, “Okay Sir” yana nufar hanyar kitchen. Bai wani jima sosai ba sai gashi da abinda yace masan. Lokacin da yake amsa ya ɗan kallesa, hakan yasa Hayatu saurin rissinar da idanunsa, dan ko motsi ogan nasa yayi yasan abinda yake nufi. Shayinsa ya kai baki ya ɗan kurɓa sau biyu sannan ya sake kallon Hayatun. “Minace maka akan yarinyar nan?”.
“Sir wlhy ba laifina bane. Kasan tanada shegen naci, nunawa tai ma idan ban kawota inda kake ba a jiya da ciwon yarinyar ya motsa bazata taɓata ba”.
“Sai akace ita kaɗaice likita kuma?”.
“Am sorry Sir. Anyi kuskure amma za'a kiyaye in sha ALLAHU”.
Shiru kamar bazai sake tanka masa ba. Har sai da ya gama shan shayin ya ajiye kofin yana miƙewa sannan ya furta, “A dawo da yarinyar nan gidan”.
Wani mugun waro idanu Hayatu yayi yana binsa da kallo. Sai dai shi bai ko waiwayo ba har ya gama haye stairs ɗin da zai kaika inda bedroom ɗin sa ya ke. Jagwab Hayatu ya zube a kujera tare da faɗin, “Boss rigimarka tafi ta sojojin yaƙin basasa wlhy. Kai komai idan zuciyarka ta raya maka sai kace ayi baka tuna abinda zai iya zuwa ya dawo. Yarinyar da ake nema ruwa a jallo kawota gidan nan ai haɗari ne, mun ɗakkota da ga Kano jiya ALLAH ya somu mun fito lafiya, yau kuma kace a kawota nan. Mu kuma da muka zo jiya zamu iya wucewa akoda yaushe ya za'ai da ita a gidan nan da ko ƴan aiki duk maza ne?” ya zabga tagumi bayan ya gama sambatunsa babu mai bashi amsa. Sai dai yasan ko giyar wake ya sha bai isa ƙin bin umarnin nan ba kuma. Dole ya miƙe ya tattare kayan daya baza falon ya koma tsaf. Shima ficewar yayi domin duba ɗakin daya dace a saka yarinyar idan sun ɗakkota.....


💞💥💞💥💞💥💞

A hankali nake buɗe idanuna da sukai min matuƙar nauyi. Hakama jikina jinsa nake tamkar ba nawa ba dan yayi min jingim. Ga laima ina jina kwance a ciki kamar wadda tai fitsarin kwance. Hannuna na ɗaga da ƙyar nakai inda nake jin laimar na taɓo, da ƙyar na ƙara ɗago hannun domin ganin minene. Duk da dama shi ɗin nai zaton gani sai da gabana ya faɗi, nai wani kalar rumtse ido da ƙarfin gaske ina cije lips ɗina shima da ƙarfi kamar zan huda su. A dai-dai nan naji ana taɓa ƙofar, sake faɗuwa gabana yay, nai ƙoƙarin yunƙurawa dan na tashi zaune amma har an riga an buɗe. Rashin ƙarfin jiki yasa na kasa jawo blanket ɗin dake a gefe, duk da ma wani sashe na zuciyata mamakin ganin kuma a inda nake ya kamani. Dan nan ɗakine mai ɗauke da kayan gado complete, sannan yafi wancan ƙyau fiye da zaton mai zato ma gashi ƙato sosai.
Mutumin nan da sukai min allura tare da doctor a daren jiya ne ya fara shigowa. Sangamemen ƙato biye da shi da da ledoji a hannu. Muna haɗa ido da shi na kauda kaina. Shima nasa kan ya kauda, batare da ya sake kallona ba ya furta, “Waɗan nan naki ne zaki iya amfani da su. Bayan su duk ma abinda zaki iya buƙata akwaisa a ɗakin. Likitarki ta gama aikinta, har magungunanki gasu anan ta kawo”. Daga haka ya juya ya fita. Da kallo na bisa zuciyata na wani irin kai-kawo. Kenan dai da gaske mutanen nan ne sukai kidnapping ɗina. Sune kuma suka saka ake bibiyata? Hakan na nufin sun san na ɗauki wannan video recording ɗin dai kamar yanda nai tunani?. (Ya ALLAH ta yaya hakan ta kasance?) Na faɗa a zuciyata, a zahiri kam ina mai runtse idanuna dake cike da nauyi har yanzu. Na kai tsahon mintuna goma ina faman tunani kafin na yunƙura na tashi da ƙyar, dan dama yanayin da jikina ke ciki yasa bance da shi komai ba da ya shigo. Yanda na jiƙa wajen da jini ya bani tsoro sosai, kamar wadda tai ɓarin ciki jama'a, haka dai na daure na sakko, sai dai ganin an saka min abune a inda na kwanta ɗin ba ainahin gadon na ɓata ba na ɗan saki ajiyar zuciya. Abin mai kama da leda-leda katifa-katifa na tattare na ɗauke. Cikin ɗingisa ƙafata dake ciwo na nufi hanyar da nake ƙyautata zaton toilet ne. Shi ɗinne kuwa, sai dai ya tsaru matuƙa, dan da za'a bani zaɓin wajen kwanciya maybe na kawo katifata nan na shimfiɗa, bawai dan yafi ko ina ƙyau ba, kawai dai ya birgeni ne shima. Duk da rashin ƙarfin da nake ji haka nai ƙarfin halin gyara jikina yanda ya kamata, nai wanka da ruwa mai zafi sosai. Sai a lokacin kuma hankalina ke neman tashi tuna bani da pant balle azo ga batun bad, sai dai tuna abinda yace yasa na fito. Ledojin da suka ajiye na shiga buɗewa, ta farko abinci ne, ta biyu kuwa kayan ciye-ciye ne. Sai ta ƙarshe ce ke ɗauke da kayan sawa, a ciki na samu pants da bad ɗin. Duk da naji wani iri da ganin hakan banda damar ƙorafi, ɗauka nai kawai na koma ciki na kimtsa jikina na dawo ɗakin. Kayan na sake buɗewa na ɗauki doguwar riga na saka batare da na damu da sanin sauran abinda ke ciki ba. Bana jin yunwa, dan in har ina a wannan yanayin ban cika son cin abinci ba, sai masifaffen kwaɗayi kamar sabuwar mayya. Dan hankalina duk yana akan naman can dana gani, ko naso basarwa kuma bazan iya hakan ba, garama naci bai nak yanda zan samu ƙarfin sauke musu abinda ke kaina. Zama nai kuwa nacisa sosai har saida naji na ƙoshi, na fiddo magungunan dana gani na duba duk yanda aka tsara shansu suma nasha.
A yanzu bana buƙatar zaman yin dogon tunani, tunda na fahimci a hannun waɗanda nake saɓanin kwanakin da suka gabata da nake canki canka da rashin tabbas. Yanzu babbar damuwata ahalina. Na tabbata duk inda Yaya Musaddiq da Mansoor suke hankalinsu a matuƙar tashe yake kodan kiran da nai a waya. Amma ina fatan askine yazo gaban goshi, dan nayi alwashin komi mutanen nan zasumin bazan taɓa basu video ɗin nan ba ko faɗa musu a inda zasu samesa, iyaka dai suce nima zasu halaka ni, ban damu ba, dan hakan da zasu yi shine mafi girman kuskure da zai tona asirinsu insha ALLAHU.

Shan maganin ya ƙara saka min jin daɗin jikina. Sai dai damuwa data kasa ɓoyuwa a kan fuskata. Sai gajiyar zama waje ɗaya daban saba ba. Nida nake yini tsaye kan ƙafafuna ina faman bautar aiki, garama idan office naje akan ɗan samu sassauci tunda shi kusan daga zaune ne. Motsin sake buɗe ƙofa da naji ya sakani tashi daga kwancen da nake cikin kujerar ɗakin, ɗan kwalin abayar naja na rufe kaina zuwa ƙirjina da ƙyau. Dai-dai nan aka ƙarasa shigowa. Mutumin ɗazu ɗinne dai, daga bakin ƙofa ya tsaya yayinda ni kuma nake kallonsa a tsiwace. Dan sai yanzu ne komai ke dawo min game da sanin da nai masa. Tabbas shine yaron mutumin nan mai kama da ƴan daudu ko nace ɗan daba ma ko sara suka oho duk ya cancanta, shine kuma ya kira da PA ɗinsa a ranar wancan taron. Nai saurin kauda kaina ina ƙoƙarin dai-daita fuskata da jikina. Tsahon mintuna kusan biyu ɗakin shiru, kafin cikin son nuna jarumta na furta,
“Dama kune kukai kidnapping ɗina?”.
Maimakon bani amsar dana buƙata sai jinai cikin bada umarni ya ce, “Zaku iya shigowa”. Baima ko gama rufe baki ba kuwa garadan samari biyu suka shigo. Ko namiji yaga wannan samudawan dole ya ji tsoro balle ni, amma dai nayi ƙoƙarin dake zuciyata ban bari tsorona ya fito a saman fuska ba. Sai dai faman haɗiyar yawu nake da ƙyar zuciyata na faman kai da kawo a cikin ƙirjina. Umarnin tashi suka bani, bani da ikon yin musu ko dan bindugun dake a hannunsa, ɗaya daga cikinsu ne ya koma ta bayana ya ɗauro ƙyalle a saman idona, zanyi magana ya ce, “Shiii!! Young Lady, inba hakaba harsashi ya rufe miki baki”.
Yawu na sake haɗiyewa mai kauri, daga haka ban sake magana ba har suka bani umarnin

Please Login or Register in order to submit comment