Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nan ya kamata muyi tunani a kansu. Dan nayi tuya na manta da albasa kasancewar ban san makirin can ne ya karɓi waliccin auren ba. Bana son maganar nan ta lafa da ga nan har zuwa randa zan saka a buɗe Awwab. Dan ina son lokacin da zai fito kansa yay matuƙar ɗaukar zafi ya rasa ina zai fara kamawa, ta hakanne kawai zan iya cimma burina a kansa. Sai maganar Ummu-Hidaya, bana son akai safiya bamu san inda suke ba. Hakama Mu'azz”.
“Ka ɗauka wannan matsalar na maganceta ma. Dana fita daga nan zan fara samar da masu binciken ne ta ɓangarori biyun”.
Kai kawai Baba prof ya jinjina masa. Sallama commondo ya masa, shi kuma ya samu giyarsa ya kwankwaɗa sannan ya tashi ya shige ciki....

Commondo na barin gidan Baba prof gidansa ya wuce. Bai yi mamakin samun Hajiya ƙarama ba, gaba ɗaya ta hargitse masa falo da hayaƙin shisha. Ƴar dariya yayi tare da kaiwa zaune. Dan yasan dai bata shan komai yau kuma gata da shisha. Lallai ran manyan mata ya ɓaci kenan. Yanda take bulbula hayaƙin sai kawai yaji yana buƙatar kasancewa da ita. Miƙewa yay ya shige ɗakinsa. Babu jimawa ya fito da allura. A kusa da ita ya zauna tare da kama hannunta kawai ya fara mata. Kan shisha ɗin ta wurgar tare da juyowa a fusace. “Oh har ya baka allurar guban da zaka mun ɗin na mutu ne?”.
Murmushi yayi tare da rungumota jikinsa yana magana ƙasa-ƙasa kamar ba commondo ba. “Haba kema kin san bashi da wannan matsayin, ya sani na kashe uwar ƴata da hannuna. Never for ever sai dai shi ya wuce. Cool down na miki allurar nan ne dan ki samu nutsuwa musan miya kamata muyi. Dan na jiyo mana komai akan plan ɗin nasa”.
Jikinta ta janye tana mai sauke ajiyar zuciya. Daga haka barci ya fara rinjayar idonta. Wata shegiyar dariya yayi da ɗaukarta gaba ɗayanta duk da tana da jiki badai can sosai ba yay cikin ɗakinsa da ita. Duk tana jinsa, sai dai bata da ƙarfin hanashi. Daga ƙarshe ma allurar na fara mata aiki a jiki da kanta ta fara kai masa kanta. Haka ya shiga yin yadda yaso da ita. Ya kuma tabbatar daga nan har zuwa gobe allurar zata iya kaiwa jikinta, dan haka daren yau na party ne gaba ɗayansa kawai...

💢🌿💢🌿💢

Matsanancin ciwon cikin dana farka da shi ya sakani fara fisge-fisge. Tuni na fincike ruwan da aka saka min. A dai-dai nan naji wata muryar da nake da tabbacin nasan mai ita tana ma ƴan sandan dake bakin cell ɗin da aka sakanin tsawa. Har rige-rigen buɗe ƙofa suke su shigo. Ciwo yaci ƙarfina bamma tantance maza bane ko mata suka ɗaukan, sai da aka shiga da ni mota na iya kallon mutum ɗaya a cikinsu wadda mace ce. Da ga haka na maida idanuna na lumshe gaba ɗaya.
Sama-sama nake jin kai-kawon komai har isarmu asibiti da taimakon da likitoci suka shiga bani. A ɗan maganarsu nake jin wai ina zubar da jini. Daga haka ban sake fahimtar komai ba sai farkawa nayi na ganni kwance a gadon asibiti police mace a gefen gadon da nake zaune. Sannu tayi min, tare da kiran likita. Ya ɗan dudduba ni ya tabbatar ma da ƴar sandar yana buƙatar ganin mijina ko wani a cikin ahalina. Kai tsaye ta bashi amsa da ina a ƙarƙashin kulawar su ne. Za'a iya sanar musu minene matsalata.
Ɗan jimm likitar tayi kamar mai tunani sai kuma ta ce, “Mijin nawa dai tafi buƙatar gani. In har za'a iya yi mata wannan alfarmar zata so hakan”.
Cikin rashin damuwa jami'ar tace zata duba. Daga haka likitar ta sake fita ni kuma barci ya sake rinjayata. Ban sake farkawa ba sai cikin dare sosai. Na tashi da wata masifaffiyar yunwa. Tun ina juye-juye har na fara kuka da roƙon a bani abinci. Tsaki ƴar sandar tayi cikin masifa take faɗin itafa na takura mata na hanata barci, a ina zata samo min abinci yanzu cikin daren nan. Ban iya amsata ba na cigaba da murƙususu na kawai. Sai kawai ta tashi ta fita rai ɓace. Tun ina saka ran zata dawo harna fidda rai, ga cikina yay wata irin masifar ƙullewar yunwa na cure waje guda ina hawaye. A hankali wani irin daddaɗan ƙamshi ya dinga ratsa min cikin hanci, tun yana a nesa da inda nake har na fara jinsa a gab-gab da ni. Ƙoƙarin buɗe idanuna dake alumshe nayi jin saukar hannun mutum akan jikina. Bana iya ganin ko waye da ƙyau, sai dai a tsaye yana da tsayi, akwai kuma facemask a fuskarsa, gashi ya ɗaura hular rigar jikin nasa a saman kai ta yanda har ba'a iya gane ainahinsa, dan hatta idanunsa akwai glass........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚-𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_


........Kamani yay gaba ɗaya ya tada zaune, shima ya kai zaunen tare da sakani a jikin nasa ya rungume. Wani kalar nutsuwa ce ta fara ratsani, irin wadda nake ji a tare da mutum ɗaya kacal a duk sanda ya rungume ni irin hakan. (Tabbas bana tantama wannan Maash ne, Awwab ɗina ne). Na faɗa a zuciyata hawaye masu zafin gaske na gangaro min suka sauka a kan ƙirjinsa, sake ƙanƙameni yayi sosai. Munfi mintuna biyu a haka kafin ya ɗagoni ya gyara min zama da ƙyau, wani ɗan mitsitsin flaks ya ciro a jikinsa mai ƙyau sosai ya buɗe. Sai da ya ɗan kalla abinda ke ciki kafin ya kawosa saman lips ɗina, ganin na tsaya kallonsa ya jinjina min kai alamar na sha.. kamar wadda ake bama umarni a hankali na ɗaura nawa hannun akan nashi dake da handglove na gyara zaman flaks ɗin a bakina da ƙyau, ai ko tunda na kafa kai ban janye bakina ba sai da na shanye shayin dake a ciki mai matuƙar daɗi da kauri duka. A take wata irin zufa ta shiga karyo min tako ina a jikina. Sake kwantar da kaina nai a jikin nasa ina sauke numfashi, na jima a hakan kafin na ɗan ɗago ina kallonsa. Hannu na kai a hankali saman fuskarsa zan cire facemask ɗin fuskar tasa ya hana hakan ta hanyar riƙe min hannun yana ɗan jujjuya kansa gefe.
Cikin dasashjiyar muryata na ce, “Why?”.
Maimakon bani amsa kafaɗuna ya kama da hannu biyu ya kwantar dani a gadon tare da jamin bargo ya rufa min. Sai kuma ya min nuni dana rufe ido batare da yayi magana ba har yanzu. Babu musu nayi hakan, kamar abin tsafi sai wani irin barci ya sake yin awon gaba da ni da alama dama yunwar ce ta tada ni....

*_WASHE GARI_*

Yana tsaka da aiki a kitchen kusan shidda na safe kira ya shigo wayarsa. Ringing ɗin da yaji wayar nayi ya nema birkita masa lissafi. Dan ya tabbar ringing ne daya saka shi domin mutum ɗaya. Sai ogansa ma nasa daban. Sai dai kuma mai wannan kiran a daren jiya ya gama jin cewar baya ma ƙasar, shima kuma ya shaida hakan. Da ƙyar ya iya ƙundunbalar ɗaukar wayar ya duba. Tabbas shine kuma da no ɗin Nigeria. To mi hakan ke nufi kuma? Rashin samun amsa ya sashi ɗagawa kafin ta tsinke. Yana kaiwa kunne tare da yin sallama aka katsesa da faɗin, “GGC GARDEN yanzu” daga haka aka yanke wayar ƙittt. Shiru yayi yana mai nazari tare da mamaki. Shi jami'in tsaro ne mai matuƙar fiƙra na sirri. Yasan kaɗan da ga aikin mutanen banza tsara komai. To amma kuma tabbas wannan muryar mai number ɗin ce. Kenan mi hakan ke nufi? Wani ne ya kwaikwayi muryar? Bayan ya samu nasarar samun wayar. Ko kuwa dai su Baba prof sunyi BONONO ne rufe ɗaki da ɓarawo kamar yanda yay zato. Sun shuka ne an tone. Kai shi kam dama dai yayi mamaki ace Maash aka rutsa a Dubai. Duk da hakan zata iya faruwa kasancewar shiri ne babba amma kuma idan za'a haɗa 1+1 ai amsa ɗaya zata bada. Dan shima Maash ɗin shegen kansa ne akwai hatsabibanci... Wayar ya sake ɗagowa ya ƙura ma number ɗin ido, da ga ƙarshe dai ya yanke shawarar fara neman ogan nasa ya sanar masa. Yana ko ɗagawa ya zayyane masa komai. Shi kansa ogan nasa yayi mamaki ƙwarai da gaske da jin wai Maash a Nigeria. Amma sai yace ya dakata bari suyi bincike. Yana nan zaune cikin shirin kira da tafiya ba'a cika mintuna biyu ba kuwa ciff ogan nasa yay kiransa yace yaje Maash ɗin ne dai. Rasama abin faɗa Isma'il Kuku yayi. A ransa kam faɗi yace, (anya Maash ɗin nan kuwa ba aljani bane, anya).....
(😂Nima dai Isma'il na fara tsoron Yayan nan namu gaskiya😝😝).

Koda ya isa GGC GARDEN ƙoƙarin sake kiran Maash ɗin yayi, sai dai harta tsinke ba'a ɗaga ba. Sai ma knocking window ɗin side ɗin da yake akai masa. Sauke gilashin yayi, batare da wanda yay knocking glass ɗin yayi magana ba yay masa nunin ya sakko. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa. Fitowa yay ya kulle motar yabi bayansa. Duk da akwai ƴar tazara a tsakaninsu bazaka taɓa ma tunanin tare suke tafiya ba. Sai dai a ransa yana mamakin a maimakon su bada umarni matsayinsu na jami'ai sune ake bamawa, lallai ƙarfin dukiya na nuna iko a wannan tafiyar. Can cikin vip na garden ɗin ya kaisa, bai kumayi magana ba anan ma ya juya ya fita. Wajen yayi ƙyau sosai, ga haske tako ina kamar rana. Idanu ya ɗan zubama bayan wanda ke tsaye ya juya ma ƙofar shigowar baya. Baƙaƙen kaya ne a jikinsa hatta da hannunsa dake zube a cikin aljihun wando da alamun handglove a tare da su. Hakama kansa yaja hular rigar. Sallama ya sake yi a karo na biyu, zuciyarsa na masa ɗari-ɗarin Maash ɗin ne ko kuwa ba shi ɗin bane. Shiru har fin minti ɗaya kafin ya juyo. A hakan ma fuskar a rufe take da facemask ga gilashi ga hular ta taimaka wajen hana ganin fuskarsa da ƙyau, batare da yayi magana ba ya nuna masa wajen zama shima yana kaiwa zaune. Hannayensa ya harɗe a ƙirji ya zubama Isma'il ɗin ido na tsawon sakanni. Kafin a hankali cikin silent voice ɗin san nan ya furta, “Gaba ɗaya wasan ya canja a gaɓar da banyi zaton fara yaƙin ƙarshen ba.”
A karo na farko Isma'il ya saki murmushi, dan tabbas yanzu ya sake yarda da Maash yake magana. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, tare da faɗin, “Ranka ya daɗe wlhy gaba ɗaya zuciyata a ɗari-ɗari take, na kasa gaskata kai ɗin ne ko waninka.”
Hannayensa ya warware da ga ƙirjinsa, tare da kai yatsu biyu saman fuskarsa ya zame mask ɗin zuwa ƙasan haɓarsa. A daƙilallen yanayi ya furta, “Ina Ummie na da Mama da ƙanwata?”.
Mamaki ne ya ɗan kama Isma'il amma sai yay niyyar latsashi. Cikin ɗan nuna firgita ya ce, “Ranka ya daɗe ban gane ba?”.
Shiru yay kamar bazaice komai ba kansa a duƙe, kusan mintuna biyu sannan ya ɗago yana kallonsa. Duk da idanun sakaye suke a cikin gilashi sai da Isma'il ɗin ya dinga jin kaifinsu, dan haka shi ya ɗan rissinar da nashi. Da wani irin taurin zuciya ya furta, “Isma'il ni ba jami'in tsaro bane. Amma brain ɗina da zuciyata na aiki fiye da ta wasu jami'an tsaron dake a cikinku. Ba kuma dan na kasance na daban ba. Sai dai na rayu ne a matsayar ƙin yarda da kowa hatta kaina.”
Kai Isma'il ya jinjina yana mai sake rissinar da kansa. Cike da girmamawa ya ce, “Suna gidana. Ƙanwarka kuma ta haihu namiji. Ina mai farin cikin kasancewa wanda zai fara maka albishir guda biyu. Na haihuwa dana alamomin samuwar lafiyar Ummie. Dan da taimakonta suka fito a gidan kamar yanda Mama ta sanar min.”
Wani shegen murmushi daya saka Isma'il tsayawa kallonsa ya saki, batare da yace komai ba. Sai da ya ɗan bubbuga table ɗin gabansu da yatsa sannan Isma'il ɗin ya kawo numfashi, sai kuma yaji kunya. Ɗauke kai Maash ɗin yayi da faɗin, “Bayan nan fa?”.
Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi. “Abunuwa da yawa sun faru a cikin gidan, nasan kuma ƙarin bayani kawai kake son ji, dan in har baka sani ba a yanzu kana da hanyar saninsu ko anan gaba. Sun ɗauke Alhaji, amma abinda na fahimta ba Prof.. bane ba.....”
“Nasan inda yake”.
Ya faɗa a daƙile. Sai Isma'il kawai ya saki baki yana kallonsa. Sannan cikin in ina ya ƙarasa faɗin, “Anyi uwar watsi tsakanin Hajiya Lawisa da Prof...”
Sake sakin murmushi Maash ɗin yayi a karo na biyu, kafin a wani kalar soft voice ya ce, “Miya haɗasu?”.
Tsaff Isma'il ya kwashe komai ya sanar masa. Kafin ya ɗora da faɗin, “Amma ranka ya daɗe naji yana sanarma yaronsa Commondo cewar kana Dubai ya maka tarko, yasa an yanke wutar gidan da kake ciki, da network, da ruwa. Sai kuma gaka a Nigeria. Wlhy ni gaba ɗaya ma sai na raina kaina. Anya yallaɓai baka cancanci zama jami'in sirri ba”.
Maimakon ya amsa masa sai ya miƙe yana mai maida mask ɗinsa. “Zaka iya tafiya, da ga yanzu zuwa asuba zan tura a ɗauka su Ummie”...
Da kallo kawai Isma'il ya bisa, sai da ya ga ya ɓacema ganinsa ya sauke wani nannauyan numfashi yana miƙewa. Kamar ɗazun yanzu ma rakashi akai har mota, yana barin wajen office ya wuce. Dan bazai iya haɗiyewa ba sai ya gana da ogansa....

A ɓangaren Maash ma Isma'il yana gama ficewa ya ɗaga waya yay kira. Cikin bada umarnin ya furta, “Ina son scorpions dake rayuwa a cikin yashi mai zafi kamar guda ashirin nau'i daban-daban daga nan zuwa gobe in ALLAH ya kaimu”. Da ga haka ya maida wayar cikin aljihu batare da ya kashe ba ya shige ƴar bukkar dake a wajen da aka yi ta domin hutawa kawai. Abu ya ɗakko ya fito suka bar Garden ɗin........✍️


Munga idi. Yayanmu kunamai kuma😳? Mi zakayi da shi🤦? To gaskiya kowa yay ta kansa ni dai ba ruwa na🏃🏃🏃🏃🏃🏃🏃🏃🏃.



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚-𝒏𝒊𝒏𝒆_


......Duk wanda yace yayi barci mai daɗi a daren jiya tako wane ɓangare yayi ƙarya. Dan kowa da abinda ya damesa. Daga masu shiryawar har waɗan da aka shirya mawa ɗin. A Maash Mansion dai an samu cigaban isowar Aunty Mama (Aunta Mashi'a) da duk labari ya sameta ta kuma ga komai. Abinda ya tada mata hankali shine rashin sanin inda Ummie take da Paah. Sannan ance Hajiya ƙarama da Baba prof sun bi bayansu suma har yanzu basu dawo ba. Da yake hankalin su Hajiya Mammah ɗin a tashe yake ita da Maman Malika basuyi tunanin bincika gidan Baba prof ɗin ba sai Aunty Mama ɗin ce tai tunanin hakan. Sun ji daɗin jin ya koma gida, itama Hajiya Ƙaramar sai sukai tunanin ko tana asibiti damuwa ta hanata dawowa gidan. Abu na biyu da aunty Mama ɗin tayi shine haɗuwa ita da Uncle Abdullahi da abin duniya yama yawa dan shima dai sai dare ya shigo gidan yanayinsa yasa Maman Malika bashi maganin barci aka samu ya runtsa. Police station sukaje suka fito da duk ma'aikatan gidan da aka rufe. Anan ne suke jin Samraah babu lafiya tana ma asibiti ita. Kasa magana ma Aunty Mama tayi dan ɓacin rai, sai Uncle Abdullahi ne ya balbalesu da masifa. Itama dai sunje asibitin sun ganta. A lokacin tana barci suka gana da likitar dake kula da ita.
Bata basu a ɓoye ba ta sanar musu Samraah nada ƙaramin ciki ne, sai dai akwai ɗan matsala dan yaso fita sai dai ALLAH ya taimaka tana fara bleading ɗin aka kawota asibitin. Sunyi nasarar tsaida shi amma tana buƙatar bed rest gaskiya. Sannan duk wani abu da zai tayar mata da hankali ba'a sonshi. Akwai Ummie da take yawan kira ya kamata tazo asibitin ko hakan zai bata nutsuwa. Sai mijinta shima da suke buƙatar gani.
Sosai Aunty Mama ta nuna farin cikinta da har ya bama Uncle Abdullahi mamaki. Dan shi dai yasan cakwakiyar da akeyi akan batun yarinyar nan a gidan. Amma yaga autar tasu ita ko'a jikinta ma. Bai daiyi magana ba sai da suka fito daga asibitin. Gefen titi ya samu ya faka motar yana kallonta. “Auta wai halan baki san mike faruwa bane? Duk fa wannan tashin hankalin akan batun yarinyar nan ne”.
Murmushin itama tayi tana mai fuskantarsa. Ta ce, “Yaya nasan komai. Sai dai hakan bazai hanani murnar samun ƙaruwar da mukayi ba. Dan koba komai cikin dake jikin yarinyar nan jininmu ne.”
“Amma bata hanya mai ƙyau aka samar da shi ba ai kin sani”.
“Kamar ya?”.
“Fyaɗe fa Awwab ya mata”.
Karo na farko dariya ta suɓucema Hajiya Mama. Ta ce, “Humm yaya kenan, wai ku har yanzu kuna akan keken ɓeran da Awwab ya sakaku kenan? Zuwa yanzu ya kamata ace kun gama haddace halayyarsa sai dai ku bama na waje labari kuma. To wannan yarinyar matarsa ce da gaske. Duk abinda kaji Sheikh Muhammad bin Khalipha Al-Hussain ya faɗa shine gaskiyar magana. Abinda keta kai-kawo kuwa shirine kawai na magauta bana raba ɗayan biyu kuma abokan kaduwancisa ne”.
“To ke ya akai kika sani?”.
“Yaya labari ne mai tsaho, amma bari na gajarce maka shi. Tiryan-tiryan ta bashi labarin komai tun bayan ɗaura aure, ciwon Samraah da kawota asibiti Abuja har zuwa guduwar da tayi ta faɗa hannun Madam Jannifer da sakata amsota da Maash yayi, da kawota gidan matsayin ƴar aiki kamar yanda ya buƙata. Rasama abin cewa Uncle Abdullahi yayi, dan harga ALLAH zancen ya girgizashi. Sai tausayin yaron ya sake kamashi. Tabbas matarsa ta faɗi gaskiya da tace basu damuwa da damuwarsa sai ayyukansu kawai. Haka ya tada motar jiki a sanyaye suka koma gida.
Sun samu Hajiya Mammah nata masifa akan dawo da masu aiki da akayi, sai da Hajiya Mama ɗin ta mata bayanin sune suka je suka saka aka sakosu. Cikin masifa Hajiya Mammah ta ce, “Amma banda waccen shegiyar yarinyar ko?”
“Saboda mi Adda?”.
“Saboda bata da gaskiya, ita dake matsayin ƴar jarida a Kano ubanmi ya kawota nan? Dan ko kunsa an fiddota wlhy sai na maidata. Sai ta faɗi inda Mu'azz yake”.
“Addah kina kwantar da hankalinki idan abu ya faru dan ALLAH. Samraah bata da hannu akan kidnapping Yaya sam saboda ita ɗin matar Awwab ce da gaske, kuma shine yasa na kawota nan gidan a wancan lokacin” tsaff ta kwashe labarin komai ta basu kamar yanda ta bama Uncle Abdullahi. Gaba ɗaya falon yay wani irin tsitt tamkar ruwa ya cinye kowa. Hatta da Baba prof dake ƙoƙarin shigowa ƙamewa yay a ƙofar duk da ya jima da yarda da hakan, ya kuma ji bayanin Sheikh Muhammad ɗin, amma jin komai a bakin autar tasa da yanda Maash ya shigo da yarinyar gidan sai yafi jin labarin kamar shine ainahin na gaskiya. Daɓar Hajiya Mammah ta kai a kujera, yayinda Malika da Azizat suka fasa ihu a tare. Da ga ƙarshe ma Azizat zubewa tai a wajen wai ta suma.....

💥💥💥💥

Wani irin kallo take ma jikinta da Commondo dake a gefenta kwance. Bama tasan lokacin data fasa ihun masifa ba a kanshi. Firgigit ya tashi fuska a yatsine. Kafin cikin jin haushi ya ce, “Haba Lawy baby, miyyasa kike abu kamar wata ƙaramar yarinya. Ina barci na mai daɗi da nishaɗi kin wani tadani”.
“Nayi ɗin, amma baka da hankali ko? Mika mun?”.
Dariya ya kwashe da ita harda ƙyaƙyƙyewa. “Ka jimun ƴar iska. Mi kika kawo kanki na miki dai. Naga keda kanki kika dinga jawoni kina roƙon nayi. Shegiya kinji mazan ƙwarai ko. To miye ma in nayin, naga dai har yanzu matata kike. Kona sake ki ne? Karki manta da aurena kika je kikai aure. Dan haka inada hakki a kanki. Yanzu ba gashi kin tashi fresh ba, basar kawai hajjaju kije kiyi wanka muzo mu tattauna abinda ya dace kafin shegen tsohon nan yasan ina mahaukaciyar matar can take. Dan mune yafi cancanta mu samota mu haɗa da Mu'azz dan uban Maash tsoffinsa duka na hannunmu ai dole ya bamu abinda muke so.”
Takaicinsa ne ya hanata yin magana. Batare data tanka masa ba ta miƙe ƙawai ta hau saka kaya. Shiko dariya kawai yake kwasa ta wulaƙanci. Fuuu ta fito a ɗakin sai jin tashin motarta yaji. Baki ya taɓe dan ko'a jikinsa, shi dai ya samu abinda ya ke so. Kuma ya jisa fiye da yanda yay fata. Ya kuma san da kanta zata dawo dan yanzu a tafin hannunsa take neman mafita kawai ce hanyar binta....

✨✨✨✨

“Isma'il lafiya na ganka haka kamar wanda aka koro?”.
“Humm oga am sorry, ai badan ma na riƙe kaina ba zaka iya ganina a fiye da hakan. Tabbas Maash yana gari, dan daga wajensa nake yanzu. Anya mutumin nan bashi da aljanu? Shifa aka nuna bashi da lafiya a asibiti sannan da kunne na naji prof.. na zancen yasa a yanke wutar gidan da yake da network da ruwa, aka kuma zagaye gidansa da jami'ai. Kuma yana da tabbacin yana a cikin gidan fa. Kuma mu kammu mun tabbatar ya shiga Dubai a shekaran jiya. Amma gashi yau alamu sun nuna a Nigeria ya kwana. Wlhy ni a karan kaina

Please Login or Register in order to submit comment