Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya fito ya rama salloli sannan ya zura jallabiya ya fito falo.
Tamkar fitowar tasa kuku ke jira, dan tuni ya fito ya jere masa kayan abinci a gabansa kasancewar yasan da dare baya hawa dining cin abinci. Duk yanda yake jin matsananciyar yunwa bai iya cin abincin ba ma, sai black tea ɗin nashi na fama ya buƙaci a kawo masa. Shine ya ɗan samu ya sha. Fitilar falon ya rage batare da kunna tv ba ya zauna shiru yana nazartar abubuwa yanda ya kamata. Dan ɗazun gaba ɗaya a birkice yake, shiyyasa hatta bayanin Commando bakwai komai ya gane ba. Dawowar nan ta Fahad ta matuƙar dagula lissafinsa. Sai batun yarinyar da bai taɓa sake maida hankali kanta a lissafinsa ba tun randa ta gitta tamkar walƙiya a tsakkiyar hadarin daya kankama zai zubda ruwa.
File ɗin da commondo ya kawo masa ya sake ɗauka, ya shiga binsa daki-daki dan ɗazun kamar sama-sama ya duba shi. Sai da ya duba tsaff sannan ya fara lissafi. Tayi aure, an kaita gidan miji, har gidan da aka kaita commando yaje amma babu kowa sai maigadi. Ya binciki maigadi, amma bai samo komai ba, dan babu abinda ya sani face ogansa da yake kira da oga. Abinda ya kawo masa ruɗani a wannan gaɓar shine kwanan amaryar ogansa ɗaya a gidan ta gudu da safe, har tai yunƙurin fasa kansa idan bai buɗe mata ƙofa ba. A binciken Commando bata koma gidansu ba, amma tayi jiyya a wani pravet hospital. Ya bibiyi asibitin amma bai samu komai ba sai sunan likitar data kula da yarinyar tama kawota asibitin, a yanzu kuma bata asibitin wai, bincike iya bincike na commando kuma bai ganota ba ko inda take har yanzu balle ita yarinyar sai iya kawai an mata transfer zuwa Abuja. Abuja wane asibiti? Basu gano ba shima.. Kansa yay wani irin dafewa yana mai furzar da huci. Sai kuma ya jawo waya yay kiran Commondo. Bai tsaya amsa ko gaisuwarsa ba yace ya samesa gida. Kawai ya yanke kiran.
Bako a cika mintuna talatin ciff ba sai ga amintaccensa yazo ya sanar masa Commando yazo yana falon baƙi. Hannu kawai ya ɗaga masa alamar yaje. Bayan ya wuce shima ya miƙe yabi hanyar da zata sadashi da falon baƙin tanan cikin falonsa. Da sauri commando dake zaune a kujera ya miƙe tsaye kansa a ƙasa domin girmamawa. Ba zamu kirashi yaro ba gaskiya. Dan shekaru kam zasu iya tasamma hamsin da wani abu. Sai dai yanayinsa ya nuna lallai a lokacin ƙuruciya anyi rashin ji sosai, a yanzun ma bai zama lallai an bari ba. Nuni Baba prof ya masa kan ya zauna. Babu musu ya kai zaune sannan ya sake gaidashi. Nan ma kansa kawai ya ɗaga masa sai kuma sukai shiru. Kusan minti ɗaya kafin baba prof ɗin ya ɗago yana sauke ajiyar numfashi.
“Commando aikinka yayi ƙyau sosai, bance komai bane saboda rana a ɓace yake a ɗazun”.
“Na sani boss, babu wani damuwa kayi komai ba komai girmanka ne”.
Murmushi Baba prof yayi da gyara zamansa. Sai kuma ya ɗan furzar da numfashi. “Ya akai bincike bai ƙarasa inda nafi buƙata ba. Dan ina son sanin wanene mijin nata fiye da komai”.
“Na sani boss, nima naso nakai har can ɗin amma komai ya datse kansa. Sai dai duk da haka bawai na dakata bane. Na kawo maka wannan ɗin ne saboda naga ka matsu. Amma akwai ƴan uwanta Maza guda biyu zan maida akalar aikina kansu, ai dole dai su san wanene ta aura? Sai shi wanda ya riƙeta shima yana cikin tsarina. Kar har walliyin auren da wahala ya tsira”.
Murmushi mai faɗi Baba prof yayi, dan yanda yaron nasa ke wani magana a ciccije yana birgesa. Kansa ya jinjina da gyara zamansa. “Shiyyasa kake birgeni sosai, dan nasan in har zan damƙa aikina a hannunka banda wata matsala a kai. Yanzu ma inada wani aiki a ƙasa, yana da alaƙa kuma da wannan ɗin da kake yi”.
“A to oga lafiya lau ne. Watso umarninka kawai a shirye nake na cafesa da hannu biyu”.
“Ina godiya. Zan ɗan baka aikin kaɗan a buɗe yanda zakafi fahimtarsa. Ita yarinyar da kake wannan binciken a kanta yanzu haka tana a Maash Mansion ne”.
Wani irin dalalo ido Commando yayi waje. Tare da dafe bakinsa ya ce, “Kan ubancan kai. Amma ta barni naketa walankeɗuwa kamar wani shaho. A to lallai tana buƙatar ɓalli-ɓalli a kan fuskarta kenan”.
Murmushi Baba prof yayi kawai, tare da cigaba da faɗin, “Ai bamu zo nan ba Commando. Abinda nake son kamun a kanta biyu ne zuwa uku. Na farko ina son sanin mi tazo yi Maash Mansion. Na biyu ka tabbatar min da tanada alaƙa da Awwab ne tako wane irin fanni ko bata da? Na uku a cikin gidan tanada alaƙa da wani ne? Misalai, masu aiki, ko cikin masu gidan, ko masu huɗɗa da gidan ta waje. Na ƙarshe wanene ya shigo da ita Lagos dan a matsayin mai aiki take a Maash Mansion”
“Oga duka aikinka masu sauƙine a garan kaima ka sani, sai dai magana ta ALLAH tsaurin a waje guda yake. Nifa kasan in dai sabga da Zakin gidan nan naka a ciki tsoronta nake gaskiyar magana. Ka sani na sani aljani ma nan ya ga Maash ya barsa. Dan duk iskancina na tsawon shekaru yaron nan yakan goge min hadda tsaff. Kaga dai Jaga, duk yanda na gatanta yaron nan daga turashi aiki jikinsa sai da yaron nan ya saɓemin ya koma bayansa. Badan munyi wuff mun ƙaddamar mas ba da yanzu ya buɗe mana aiki fa. Boss kasan da haka ta faru fa babu tantama China Maash zai kaimu a markaɗe namominmu da ranmu a ɗurisa a gwangwanaye a dawo dashi Nigeria a dinga sayarwa matsayin naman tsakkiyar shawarma. Kai kanka yanda nake ganin idanunsa zai iya sawa a masa bandarka...”
“Commando!!”.
Baba prof ya faɗa a fusace cikin daka masa matsanancinyar tsawa.........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚-𝒏𝒊𝒏𝒆_


*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku bari ayi babu ku😘😘😘._

*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1

*_Instagram_*

I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv


*_WhatsApp_*
https://chat.whatsapp.com/LkRMFFQZakP55c7xK0QaMG


https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5


......“Kaiyya oga sa'a dai sa'a dai. Kafa san ni a ɓangaren gaskiya ba ruwana feɗewa nake filla-filla. Amma dai tunda baka son ji bari nayi kurumm. Zanje na fara aiki amma dai ka ƙara tunani akan Maash, Nima zanyi tunani muga. Matsalar shi ba mata yake bi ba, baya hawa network kuma, amma da komai yazo da sauƙi ai”.
Gaba ɗaya Baba prof ya gamsu da bayanin Commando. Shi kansa shiyyasa yake a cikin ruɗani akan batun yarinyar nan da kuma abinda ya faru tsakanin Awwab ɗin da ita. Maash baya neman mata, shi shaida ne akan hakan. Sannan akwai wani dalilin da yasa baima kawo cewar shine ya aureta a ransa ba, dan yayi imani da shirinsa a kansa matuƙa. Shiyyasa ko fyaɗen nan har yanzu zuciyarsa bata gama yarda shine ya aikata ba. To amma abinda ya faru a asibiti fa? A gabansu fa yaron nan yay kissing yarinyar (Randa Maash ya samesu a asibiti, su a tunaninsu ma lokacin kissing ɗinta yayi🤣). Dan ɗauka bai wani ɗauketa da muhimmanci ba, hakama kulawa a asibitin, komai zai iya yi dan yana da tausayi. Kai gaba ɗaya shi yama rasa ina zai kama gaskiya..
Waya ya ɗauka har zai dannama Hajiya ƙarama kira sai kuma ya fasa. Saƙo ya tura mata ya kashe wayar tare da miƙewa ya fita. Amintaccensa ya kira suka fita a gidan duk da kuwa dare ne dan har ƙarfe ɗaya ma ta gota....

🤍🌿🤍🌿🤍

Tunda na janyo ra'ayin Fahad muka nufi sashen Ummie ban sake bi takan ahalin gidan ba. Dan ko Hayatu da Hafiz anan suka samemu. Da yake muna a falon farko ne na shiga sashen sai muka baje munata hira abinmu harda Mama Balki. Kamar wasa abota ta ƙullu tsakanin Hafiz da Fahad duk da kuwa Fahad ya girmi Hafiz sosai. Dan koni ma ya girma balle shi. Da alama hakan ya faranta ran Hayatu, dan daga ƙarshe cayay su tashi suje yawo tunda yau boss na hutu. Har zasu fice na ma Hayatu magana. Duk da dai yanzu kunyar abinda na dinga masa nake ji, amma dai na daure na ce, “Yaya Hayat dan ALLAH idan babu damuwa kuma oganka bazaiyi faɗa ba mizai hana a sayo kayan amfani na kitchen ɗin sashensa naga wanda suke ciki basu da wani yawa. Tare da kayan abinci sai na dinga mana girki acan. Naga sam bai damu da abinci ba sai kayan chocolate. Sannan ita kanta Ummie ya kamata ace nike mata abinci hidimar nama Mama Balki yawa. Ga kuma Fahad ma ya ƙaru”.
Sosai fuskarsa ta ƙawatu da murmushi. Ya ce, “Wannan shawara ce mai ƙyai Auntynmu. Kuma naji daɗi kamar yanda nasan Boss zaiji daɗi fiye ma da yanda naji ɗin. In sha ALLAHU ki bamu nan zuwa anjima duk abinda kike buƙata za'a kawoshi. Yanzu hakama zanyi waya da companyn da zasu zo su gyara kitchen ɗin su saka komai daya dace, kafin su gama mu kuma mun haɗo cefanen”.
“Nagode sosai Yaya Hayat”.
“Muke da godiya Auntynmu. Koba komai kwanan nan Yayanmu zaiyi kaurin wuya da tunbi”.
Dariya sosai zancensa ya bani, amma sai na murmusa kawai. Shima fita yay yana murmushin dan su Fahad tuni sun fice abinsu...

Kamar ko yanda ya faɗa ɗin haka ce ta faru. Dan na fita zuwa yin sallar la'asar daga nan na dubasu na samu drivern sa (TJ) da Guard ɗinsa da nake yawan ganinsu tare shima (Shu'aibu) tare da baƙi. Gaisheni sukai TJ ɗin ya bani waya. Jin Muryar Hayatu ya sani sauke ajiyar zuciya, shine yamun bayanin na basu damar shiga tare da masu company da zasuyi aiki. Duk da nayi mamaki ganin yammafa tayi yaushe har za'a kammala? Sai ban musa ba na basu dama ni kuma na shige ciki domin duba shi.

Da sallama na shiga ɗakin kamar mai jin tsoro, ganinsa tsaye gaban mirror yana fesa turare ya sani jin farin ciki. Ɗan kallonsa nayi na ɗauke kaina. Dan fesa turarensa yake kamar ma bai san da shigowata ba. Wannan halin nasa na shariya da ɗaukar kai na ban mamaki. Jinai kamar na watsar da shi nima na wuce abina. Amma sai na daure tunda koba komai na barsa babu lafiya. Muryata can ƙasa batare dana sake kallonsa ba na ce, “Ashe ka tashi, yaya jikin?”. Nai ƙoƙarin wucewa abina. Har na gittashi naji ba'a amsa min ba, sai na tsaya cak, dan magana ta ALLAH ban san wulaƙanci sam. Cikin ɗan yanayin jin haushi na ɗago manyan idanuna na kallesa. A mamakina sai na samu shima ni ya zubama ido. Dan ya daina fesa turaren ma ya jingina da mirror kawai yana kallona. Baki na tura masa tare da juyawa zan cigaba da tafiyata caraf aka cafke hannuna. Ƙin juyawa nai na kallesa. Sai dai ban ƙwace hannuna ba daga riƙon da yay min. Munfi sakan goma a haka shi bai sakeni ba shi baice komai ba. Jinai wani takaici ya sake kume mun zuciya, sai nai ƙoƙarin jan hannun nawa. Sake riƙeni yay da ƙyau, tare da matsoni jikinsa ya juyoni gaba ɗaya na muna fuskantar juna. Ban yarda na kallesa ba, ban kuma ce da shi komai ba. Sai kawai ya ƙarasa jawoni jikin nasa ya rungume. A kusan tare ni da shi muka saki ajiyar zukata, kafin ya dagoni fuskata a cikin tafukan hannunsa duka biyu.
“Yau ba magana ne?”.
Ya faɗa da soft murya kuma can ƙasa da ni kaina dan yana a kusa dani ne na jisa. Ban kallensan ba, ban kuma ce komai ba sai kafaɗa dana maƙe masa.
“Oh! Why?”.
Sai da na ɗan murguɗa baki sannan nace, “Ai kaima baka yi ba”.
“Uhhmyim. Dan banyi ba sai kema ba zakiyi ba?”.
Kaina na jinjina masa alamar eh.
“Humm Aku na ta zama kurma kenan yau?”.
“Ni dai ba Aku bane”.
“To miye? Banan kike cika mana kunni da surutu ba ke a dole ƴar jarida”.
Farr nai da idanuna, tare da ɗan jujjuyasu, sannan na ɗan murguɗa baki na ce, “Kaima ai shaida ne tunda na karya maka record. Ko nayi ƙarya”. Na ƙare maganar ina waro masa idanuna sosai.
Maimakon ya tanka sai kawai ya saki murmushi, tare da kissing idanun nawa. Kunya ce ta kamani kuma. Dan haka nayi yunƙurin kwace fuskata amma yaƙi barina. Dole na haƙura amma na rufe idanuna naƙi yarda na sake kallonsa. Sai dai kuma shi ina cigaba da jin tasirin idanunsa a kaina sosai. Ganin bashi da niyyar barina a shagwaɓe na ce, “Gashi can za'a shiga salla fa”.
Tamkar wanda na dawo a hayyacinsa ya furzar da wani irin nannauyan numfashi. Sai kuma ya saki mun fuska a hankali. Jin kamar ba hanyar fita yayi ba na buɗe idanuna. Sai na hangosa zai shige bathroom. Mamaki hakan ya bani, sai dai bance komai ba na tsaya a wajen, babu jimawa kuwa sai gashi ya fito da alama alwala ya ɗauro. Har ya gittani zai wuce sai kuma ya ɗan dawo baya. Dawowar tasa ya sani ɗagowa na kallesa. Dai-dai da ya kawo fuskarsa gab da tawa, dan haka a bazata naji saukar sumba a saman goshina. Kafin ma nayi wani yunƙuri ya fice a binsa. Bamma san sanda na saki murmushi ba da kai hannu na shafi lips ɗina da goshina a hankali. Kasan raina kuma ina dariyar al'awar da ya sake, wato mutumin nan ja... Humm bari dai nayi shiru kada danginsa su min ca..

(Kin taimaki kanki kuwa, dan ba barinki zamuyi ba😎😌.)

Fitowarsa ya saka su TJ masu jagorantar companyn nan dake shigo da kwalayen kayan aikinsu rissinawa suna gaishesa. Kallonsu kawai yake batare daya amsa musu ba. Dan haka Shu'aibu ya fara masa bayanin cewa Hayatu ne ya turo companyn ya kuma kira su akan su sami Aunty ta basu izinin shiga da kayan. Shine yanzu da zata shiga suka sanar mata ta basu izini.. maimakon ya amsa musu bayanin da sukai masan sai ya ɗauke kai tamkar ma bai ji bayanin ba. Takunsa ya cigaba dayi cike da bajinta da mazantaka. Sai da yaje gaf da fita a daƙilen nan nasa ya furta, “Ina fatan dai kunyi salla? Su kuma aikinsu ya koma ta back door”.
Daga haka ya ficewarsa. Sanin basuyin ba ya sasu ajiye aiki suka bar wanda ba musulmai ba. Amma kamar yanda yay umarnin komawarsu ta back door sai suka kulle ƙofar tanan nan falo suka koma ta can ƙofar baya ta kitchen ɗin.....

❤️‍🔥❤️‍🔥💦❤️‍🔥❤️‍🔥

Jigatuwa iya jigatuwa Baby tayi, dan bata tashi farkawa ba sai a hannu Doctors. Su kansu likitocin ma firgitata sukayi. Dan daga ganinsu kaga irin manyan gawurtattun ƴan iskan turawan nan da akafi gani a cikin films matsayin criminals. Illahirin jikinsu ne tattoo baƙi da jaa. Ga wasu irin yan iskan abubuwa kamar stones sun manna a fuska harda haƙora babu ƙyan gani. Sun kuma irin zama ɓarka-ɓarka ɗin nan saboda workout. Idanunsu kam harda kwalli ga ƴan kunne. Kai tako ina dai basu da ƙyan gani. Tana ji tana gani sukai treatment ɗinta. Ba wannan ya tada mata hankali kawai ba. Sai da nishi ya isheta ta waiga ta gefenta kasancewar ko iya zama batayi sai kwance rigingine sai kawai tayi tozali da mijin nata na aikata irin abinda ya aikata da ita da ɗaya daga cikin yan iskan dake a kanta matsayin likitoci. Wani irin uhun tashin hankali ta saki. Sai dai a mamakinta ko'a jikinsu kamarma basu jita ba harkokin gabansu suke, sai wasunsu ne ma da suka kwashe da dariya. Haka ta dinga musu ihun kuka tana zaginsu da Hausa da turanci, tare da tsine musu ta uwa ta uba tana kiransu ƴan wuta.
Oho ita tama san mi take faɗa, dan hatta turancin nata babu alamar suna ganewa. (A Nigeria kuma sune wayayyu ma'iya turanci😝🤣). Haka sukai kunnen uwar shegu da ita har suka gama hidimarsu sannan suka fice suka barta a ɗakin ita kaɗai sai mijin nata daya shiga wanka shi da ƙaton da suka gama aikata alfasha. Tana nan tana cigaba da cin kukanta suka fito riƙe da juna kamar wasu mata da miji. Sai kawai taji numfashinta ma na neman ɗaukewa. Dan duk iskancinta da ƙarancin rashin ilimi tasan wannan aiki ya ƙazanta........✍️



_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._


_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_

_BANK NAME:KEYSTONE_

_BANK ACC NO:6019473875_

_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_

_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_

__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_

*09033181070*

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*


*_Typing📲_*








*_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_*
_(Itama nama ce)_




_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_



_𝑩𝒐𝒐𝒌 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_
_𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚_


.......Wato jama'a kuɗi! Kuɗi! Kuɗi!! Humm dole ma musha wahala akan kuɗi wlhy. Yo duk in kana son abu a rayuwarnan a yi maka shi tamkar ƙyaftawar idanu tofa lallai sai da kuɗi. Shiyyasa gasu nan sun zame mana masifar rayuwa. Talaka da baida su yafi kowa shan wahalar rayuwar. Karna dai cikaku da surutu. Ba komai ya sani muku sambatun nan ba sai da na fito ganin kitchen ɗin da aka shirya cikin abinda bai gaza awa uku ba. Tsaff an gama shirya duk wani abinda za'a buƙata a cikinsa kalar kitchen cabinet ɗin. Tuni ya canja kamar bashi ba a ɗazun tsurarsa sai cabinet. Ban sake tsinkewa ba sai da na shiga cikin store naga yanda aka ajiye wasu extra kayan aikin iri daban-daban. “Tab ɗin, ALLAH dai ya gafarta mana to. Ya bama kowa halalinsa ya kuma bamu tsahon ran mora da neman lahirarmu a cikin duniyarmu”.
Na fito inata ƙara jinjina al'amarin na sameshi a falon da alama shigowarsa kenan. Dan tun fita massalaci sallar la'asar bai dawo ba sai yanzu da ake shirin gab da magriba. Cike da ɗauki na ƙarasa inda yake na zauna ta kujerar gefen. Duk da kunyar yanda ya wani zuba min idanunsa nake yi haka na fuske abina.
“Hummm Yaa Awwab kaga kuwa yanda suka maida kitchen ɗin nan? Tab ɗin jan aljannar duniya. ALLAH yanda kasan mutum ya koma can ya saka gado kawai ace canne ɗakinsa. Gaskiya mutanen nan sun iya aiki tabb”.
“Shi kuma wannan bakin ya iya surutu”.
Ya faɗa yana wani lumshe idanu da buɗewa tamkar wanda ya sha yay marisa. Ɓata fuska nayi tare da tunzura bakin na ce, “Namayi fushi, dama ka samu nake baka labari ko”. Na tashi fuuu zan gudu. Ji nai kawai an fisgoni, sai gani daɓar a saman cinyarsa. Ƙoƙarin ƙwace kaina na shiga yi ina kukan taɓara da faɗin, “Ni ka barni babu ruwana da kai. Kowa yay sabgarsa, ni wajen Ummiena ma zan koma”.
Tsam ya matseni a jikinsa yana mai cusa fuskarsa a gefen wuyana. Yayinda numfashinsa ke shiga cikin kunnena da sautin dan murmushinsa. Ban fasa yunƙurin sauka a jikin nasa ba har sai da ya ɗan cizar min kunne, gaba ɗayana na naɗe masa jiki tare da sakin ƴar ƙara, a shagwaɓe na ce, “Wayyo Ummie King zai cire min kunni. ALLAH ni bazan yarda ba sai na rama cizona”. Na faɗa ina mai hayewa jikin nasa gaba ɗaya nima na shiga kokawar laluben kunnensa ni a dole saina ciza..
“Oh my god, yarinyar nan baki son zaman lafiya sam”. Ya faɗa kamar zai saki kuka yana kare kunnensa duka biyu da hannayensa. Oho bamma nuna na jisa ba, na shiga cigaba da ƙoƙarin zame hannunsa da hannu ɗaya, ɗayan na kaisa gefen cikinsa ina mintsina. Hannunsa ɗaya dake a saman kunnen ya cire yana ƙoƙarin buge nawa dake mintsininsa. Ai ko sai na samu caraf na cafke kunnen. Kaɗan na ciza amma mutumin nan ya wani saki ƴar ƙara da faɗin, “Ouchhh! Ummie kunnina, tiger ta ciresa”.
Sosai na ƙyalkyale da dariya. Na yunƙura zan gudu ina faɗin, “Sai tsoro ga jan faɗa”. Caraf ya riƙoni yana ɓata fuska. Marairaice tawa fuskar nayi kamar zanyi kuka na ce, “Ayya Yaa Awwab ayya!. Nifa ƴar ƙararrama ce kar kace zaka rama”. Harara ya zuba min yana sake ɓata fuska da murza kunnensa da hannu alamar har yanzu yana masa zafi ko kuma shagwaɓa ce ta motsa abinka da Ajebota. Ganin yanda ya zuba min idanunsan nan na maguna kamar zai cinyeni da su, ga fuskarsa babu alamar fara'a ya sani sake narairaicewa. “Na tub...”
“Shii!!!” ya katseni yana sake ƙanƙance idanun da shanyesu kamar mai jin barci. Sai kuma ya ɗan yamutse fuskar da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Sai fa na rama”.
“Mi ɗin?”.
Na faɗa cikin waro idanuna. Hararata ya ɗan yi, da sake matso da fuskata gab da tashi, sosai na sake waro idanun da marairaice fuska zanyi magana a hankali ya wani irin sauke small pinkish lips ɗinsa a kan nawa. A salon daya cafka lips ɗin nawa yasa bamma san na ƙanƙamesa ba.....
“Yau na shiga uku! Mizan gani haka ni Nafisatu Adams”.
A bazata muka ji saukar muryar Hajiya Mammah a saman kammu. Kici-kicin ƙwace kaina na shiga yi duk da shi bashi da niyyar yin hakan kuma sarai yaji abinda naji. Amma bawan ALLAHn nan sai ya wani sake matseni da komawa wani irin salo na taƙadarin namiji da sam babu ɓarɓashin kunya tattare da idanunsa. Ina jin ta sake saka salati har muryarta na rawa...

Ba muryar Hajiya Mammah ba hatta jikinta rawa yake yi. Ba

Please Login or Register in order to submit comment