Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba kawai ya kira ni yana ko'karin gaya mini magana ni na d'orawa yarinyar ciwo wane irin bala'i ne wannan ne."
Tsabar takaici da damuwa ban iya zuwa dubiyar Dada ba a ranar saboda jikina ya riga ya gama mutuwa da rashin lafiyar yarinyar da kuma abinda ya gaya mini a kan hakan.
Can wajen sha d'aya ya sake kira na na daga ban ce masa komai ba na ji yana fad'in.'" Za ku gaisa ko?'' Da yaran yake na ji muryar Usaina tana kiran Mama na ce." Naam Usai ina Hassana." Ta ce gata nan." Minal fa?"
Ta ce." Ta yi bacci ta fad'a muryarta tana rawa.
Na ce." Ya jikin nata."
"Da sau'ki ta fad'a kamar za ta fashe da kuka. Na ce." To ba ni Hassana itama mu gaisa ko Ina Khalil?''
Ta ce." Yana 'kasa da Hassana." Na ji maganarta. "Mama ina yini."
Na amsa "Lafiya lau Hassana ina dariyar da babu nisha'di na ce." Ya kuke ina Mairo." Ta ce." Tana can k'asa Minal ba ta da lafiya."
Na ce." Allah Ya ba ta lafiya na kusa dawowa."
Da sauri ta ce." Yaushe?"
Domin na kwantar musu da hankali na ce." Gobe." Ina ji suka fara tsalle da dariya. Ya kar'bi wayar daga hannunta yana fad'in." Me yasa za ki gaya musu haka Amina kwananki nawa da tafiya."

littafin nan na kudi ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba

A tak'aice na ce." Biyu." Ki ka ce za ki yi sati daya ko kin fasa."
"Ban fasa ba." Na fad'a kai tsaye ina ji yana magana da yaran kan cewa su sauka k'asa wajan Mairo. Na daina jin motsinsu. Ya cigaba da cewa kin ga kuwa idan ba ki dawo gobe ba za su d'auke ki makaryaciya domin kuwa yaro baya mance magana kina dai jin tsalle da murnar da suke yi."
"Umm! kawai na ce na yi shiru.
Ya d'an yi gyaran murya kafin na ji shi yana fad'in." Yanzu kin tsane ni Amina ban yi miki komai ba wai menene lefina anan tare dake duka aka dinga wannan d'auki ba dad'in akan kwantar da ni da Maryam ta yi Malamin nan ya tsaya tsayin daka a kaina har sai da ya tabbatar da tabbatuwar lafiyata na cigaba da rayuwa da iyalina. Yanzu don Allah bai cancanci komai ba ban yi tsammanin zan samu wannan turjiyar daga wurinki ba tunda ai da farko ba haka ki ka nuna mini ba."
Na ce." Har yanzu kuma ba ni da damuwa akan hakan ba. Ai kai ka ga zaka ka iya amma dai Ina gaya maka ba zan zauna a gidan da zaka haye kan k'aramar yarinya kamar Hajara ba babu ni a cikin wannan rashin sanin ciwon kai ba kuma zan kara had'a inuwa da Hauwa ba. Ka canza mini mazauni idan ya zama lallai sai ka zauna da ni."
"Shikkenan za ki zauna gidanki na kano tunda hakan ki ke so amma ki sani za ki dinga d'aukar dogon lokaci kafin ki gan ni."
Na ce." Babu damuwa ai." Ba tare da ya sake wata magana ba ya kashe wayarsa.
Da safe da wurwuri na je na duba jikin Dada alhamdulillahi ta warware sai dai jikin girma idan abin ya motsa mata amma yini muka yi muna hira tana gaya mini abin alherin da ya yi musu a lokacin da ya zo dubata wattanin baya.
Bayan sunan Fadila da kwana biyu na fara shirin tafiya tunda mun gama magana dashi kan yanke zamana a kano abinda dai ban yarda da shi ba shine barin yarana a gidansa na abuja da Hauwa dole za mu zauna akan hakan sai ya ba ni yarana wallahi ta ri'ke na ta.
Ya kira ni yana gaya mini na tafi gobe domin shi ma a goben yake so ya shiga garin kanon saboda juma'ar da za ta zo za'a yi d'aurin auran a Bunkure kamar dai yadda ya gaya mini da farko.
To kawai na ce masa. Ban kuma tafi a ranar da ya ce ba sai a washe garin ranar tukkuna Babansu Fadila da kansa Ya d'auke ni a mota zuwa kano.
Gidan Hajja na yada zango anan shi ma ya kwana da sassafe yana karin kummalo ya d'auki hanya.
Hajja ta dinga rarrashina tana tausata ban san me ya gaya mata ba amma yanayin yadda take rarrashina ya nuna mini cewa kamar ya gaya mata wata magana a kaina wadda take nuni da cewar ni ce yanzu ba ni son zaman lafiya tunda Hauwa ai ta mato a kan sonsa kuma dama kulawarsa da tarasa ne a baya ya sanya take yin hauka da tsananin kishi yanzu kam tunda tana samun abinda take so a wajensa yana juyata son ransa ba zai fad'i aibunta ba. Kuma a lokacin da ta fahimci akwai rikici a tsakaninmu ta bud'e wuta da kissa da ko'karin kafa kanta a wajensa.
Ban katse ta ba na yi shiru Ina ta sauraranta tana cewa itama ta fi so na zauna anan din Hauwa da amarya kuma su yi zamansu a can abuja
Sai yamma direbanta magaji ya d'auke ni a mota lokacin shi bai dawo daga bunkure ba duk da ba ranar ne daurin auran ba na lura da yadda yake ta rawar jiki da kai kawo har an yi masa invitation irin na wata da kuma na kati ya d'ora a status dinsa.
A daran na kira Sahura na ce ta zo gobe da wuri dole sai ta taimaka mini mun gyara gidan.
Can misalin sha daya saura na dare ya shigo gidan.
Na gama shirin kwanciya ya shigo dakin ya same ni. Ya zauna gefena da alamar gajiya a tare da shi da kuma yanayi na damuwa da ta riga ta zame masa jiki
yadda bai yi mini magana ba haka ni ma ban yi masa magana ba d'akin ya d'auki shiru na tsayin wani lokaci
Na ji yana fad'in." Amina ya kamata mu yi gwajin nan na jini ( gyonotp) da yarinyar nan ko?"
Shiru na yi ba tare da na ce masa komai ba. Ya dube ni yana fad'in." Yadda Malam D'aha ya d'aukaki wannan lamarin ba na tsammanin idan an ci karo da wata matsalar wadda ka iya rusa auran ya janye ku'dirinsa sanin halinsa na magana d'aya da kuma 'kin yarda da zamani da hasashen yahudu da nasara........✍️
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124...BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*146*
Gida a kawo Fadila tunda haihuwar fari ce kuma dai gidan nata ba shi da wani spece inda Allah ya ta'kaita nasa ne ba ya haya ba ce wai hausawa suna fad'in guntun gatarinka ya fi sari ka ba ni. Duk da haka ya yi kokari tunda d'aki uku ne da kicin da bandaki sai dai dak'unan duka ba ma su yalwa ba ne.
Haihuwa da lafiya akwai anya farinciki yarinyar tana zauna da babyna a hannu tana bashi nono na cika da mamaki kwarai da gaske wai yau Fadila ce ri'ke da jinjiri har tana shayar da shi gani ni uwarta gotai-gotai da ni ban gama haihuwa wato idan da Kamaluna ma macace haka za mu jera haihuwa da shi duk da Fadila ta girme shi sosai amma dai da mace ne a yanzu da ake yi wa yara auran wuri wata'kila da tuni na aurar ni ma
Yusuran Sahura ma tana can da nata tsohon cikin haihuwa ko yau ko gobe wai a haka ma ta yi 'bari na wata hud'u.
A washe da safe Sukairaju ya d'auki hanyar komawa gida bayan ya karya kummalo. Yawan shige da ficen da ake yi a gidan dangin mijin yarinyar da danginmu suna zuwa ganin jarari Hakan bai ba mu damar 'kebewa sai a daran ranar dana kwana biyu a gidan tukkuna muka zauna muna tattauna al'amura masu yawa. Nan na gaya mata irin abubuwan da suke faruwa tsakanina da Hauwa da shawarar da na yanke sannan da auran da yake shirin yi a tsukin kwanakin nan tunda ya ce satin na sama suka yanke za a daura aure.
Ta dinga mamaki tana fad'a kamar ta ari ba ki wai shi bashi da bakin da ba zai ce ya yi wa yarinyar girma ba ai ana barin halas don kunya wannan babbar asara ce da jin kunya idan har ya amince aka daura masa aure da yarinyar da ko shakka ba ta yi ta ji jinkanya da shi.
Abin ya dinga ba ni dariya ganin yadda ta hakikance da gaske tana ta fad'a tana cewa girmansa ya zube a idonta tunda ya shigo da son zuciya dama can yana so idan ba haka ba daidai gwargwado ya yi wa malamin alheri mutumin ya rushe masa gida ya zamanantar dashi tare da sabunta tsangayu irin na zamani aikuwa ya yi abin a yaba masa kuma idan biya zai yi akan hidimar da ya yi masa ya biya shi mai zai sanya kawai a d'auki yarinya a bashi ya kuma sanya hannu ya kar'ba har yana cewa don babu yadda zai yi ne wannan karya ce tsantsa da yaudara.
Da muka wayi gari ma ta tashi da mita shiga fita dari sai ta yi maganar tana cewa kin yi daidai ya kawo yarinyar su zauna da Hauwa a gidan ke ya canza miki wani idan ma ba zai yarda ki zauna a gidanki na kano ba ai yana da iko anan abujan sai ya samar miki da wani. Irin wad'annan masifun ne ya sanya wasu mazan ko basu da wadata suke rabawa matayensu gida to balle shi da yake da suttura da wadata tunda har abinda Hauwa take yi ya'ki ya'ki cinyewa kawai ya rabawa kowa mazauni sai a samu zaman lafiya.
Na ji dad'i sosai ganin yadda wannan karon anti Yagana ta goyu da bayana na saki raina sosai ina jin sasaauci Kuma ban kunna wayata ba yau kwana biyu kenan wanda nasan yana can yana ta lalubena a wayar bai samu ba.
Sai da na yi wanka na karya kullumalo tukkuna na fito falon na sami yarinyar tare da kawayenta na makaranta sun zo ganin jaririya suna ta tsokanarta sai suka ba ni sha'awa muka gaisa ina yi musu dariya cikin raina ina cewa duk yadda za ta kai ga baku labarin nakuda ba za ku fahimta ba sai ta riske ku tukkuna.
Anti Yagana tana ta gyara kaji a kicin nace." In ban da abinki anti Yagana ai sai ki kira ni na taimaka miki."
Ta ce." Ke ma ba lafiyar ce dake ba Amina na gode Allah ni da ya hore mini lafiyar wannan hidimar ta same ni Dada ciwo ya dabaibayeta nasan da ita za ta zo ta zauna mini"
Na ce." K'warai hakane shirin da na yi yanzu zan tafi can babban gidan ne na duba jikinta zan dan zaga dangi mu gaisa."
Ta furta. Hakan yana da kyau."
Kujera na ja na zauna na kama mata aikin Muna gyara kajin a tare na ce." Na lura yaron nan da yake auran Fadila yana da zuciya wallahi gashi nan komai ya yi na al'ada."
Ta gyad'a kanta tana cewa." K'warai Kam tunda ta haihu yake hidima domin da ta fara nakudar ma bai iya kaita asibitin gwamnati ba kudi ya fitar ya kai ta wanda za a bata kulawa wallahi sai da ta haihu ya kira ya gaya mana."
Na furta." Irin wad'annan matasan ya kamata ace an d'auki aure an ba su masu zuciya da dogaro da kansu da kuma ko'karin ri'ke iyali daidai gwargwado."
Daya daga cikin yan matan kawayen nata ta fito tana fad'in.''Mama ana kiran ki wayar ki." Ta mika mata wayar na riga ta kar'ba domin hannunta gaja-gaja yake fa jinin kajin da take gyarawa.
Ina duba fuskar wayar naga sunan Alhaji Tajuden da haka ta yi serving lambarsa
Na daga tare da sanya mata a kunne ina ji yana gaisheta da mutuntawa kamar yadda ya saba itama ta amsa cikin nutsuwa har tana tambayarsa yara ya ce duka suna lafiya sannan ya yi mata barka da arziki kafin ya fara tambayarta ina nake ya yi ta kirana a waya baya samuna.
Ta dube ni kafin ta ce masa gani nan a zaune. Sai na ji yana cewa da ita ta gaya mini na kunna wayata akwai muhimmiyar maganar da za mu yi.
Ta ce masa to in sha Allahu suka yi sallama.
Ta d'an dube ni a sanyaye tana fad'in." Na ji shi a sanyaye yana magana babu nutsuwa Amina kada dai ki ce da biyu ki ka zo nan garin kar ki ce da ni yaji ki ka yi akan wannan matsalar domin idan bacin haka ai ban ga dalilin da zai sanya ki kashe wayarki ba."
Na ce." E, to ba yaji na yi ba amma dai Ina tsammanin ba ni komawa Abuja kai tsaye daga na bar nan kano zan sauka gidana na sharad'a tunda ya'ki fahimtar abinda nake nufi."
Ta gyad'a kanta tana cewa." Ba ni son hakan ya haifar miki da wata matsalar Amina amma ni kaina a son raina nafiso a raba muku muhalli sai hankalina ya fi kwanciya.
Na furta." Duk mai hankali da tsinkaye abinda zai duba kenan matsawar muna zaune a inuwa guda da Hauwa ba za a taba samun zaman lafiya ba Shima ba zai huta ba tunda ni dai na zame mata ciwon ido anti Yagana wallahi har mamakin yadda Hauwa take zafafawa kanta a kaina ni kuma ba ta raina kwata kwata ban kuma dauketa a matsayin kishiya da zata daga mini hankali ba. Kawai yanzu nutsuwa da kwanciyar hankali nake buk'ata shiyasa na ce ba ni buk'atar zama da ita a gida daya."
Ta furta." Hakane akwai hujja mai karfi a tare dake ni ma ina bayanki amma yanzu tunda ya ce ki kunna wayarki za ku yi magana ki kunna din mu ji mai zai ce."
Na ce." To shikkenan zan kuna."
Sai da muka gama aikin gyara kajin tukkuna ta d'ora a wuta na wanke hannuna da omo sannan na koma d'akin na d'auki wayata na kunna minti goma sha biyar a tsakani ya kira na daga a nutse na yi sallama ya amsa na gaishe shi nan ma ya amsa babu annasuwa. Kafin ya d'ora da fad'in." Yarinyar Minal tun bayan da suka dawo daga makaranta ta samu ba kya gidan kwanta zazza'bi ya rufe ta ya hau ya sauka har takai da sai da aka yi mata karin ruwa Amina ida ta rasu wallahi ba zan yafe miki ba."
Gabana na d'an fad'uwa na ce." Ban gane abinda kake nufi ba."
Ya ce." Kin ji abinda na fad'a Amina ai kin san ba ki da gaskiya shiyasa ki ka kashe wayarki tsayin kwana biyu."
Na ce." Mayya ce ni ma shiyasa na kama kurwar Minal na taho da ita nan maiduguri to don Allah idan ta rasu ka d'aure ni har igiya ta yi rara."
Ya ce." Abinda za ki ce kenan?"
Na ce." To me zan ce maka ka ce yarinya bata da lafiya saboda na taho da kurwata idan ta mutu ba za ka kyale ni ba to ka d'aure ni don Allah shine abinda za ka yi."
Ya kashe wayarsa jin yadda na bud'e masa wuta idan ba rashin mutunci ba kawai ya kira ni yana ko'karin gaya mini magana ni na d'orawa yarinyar ciwo wane irin bala'i ne wannan ne."
Tsabar takaici da damuwa ban iya zuwa dubiyar Dada ba a ranar saboda jikina ya riga ya gama mutuwa da rashin lafiyar yarinyar da kuma abinda ya gaya mini a kan hakan.
Can wajen sha d'aya ya sake kira na na daga ban ce masa komai ba na ji yana fad'in.'" Za ku gaisa ko?'' Da yaran yake na ji muryar Usaina tana kiran Mama na ce." Naam Usai ina Hassana." Ta ce gata nan." Minal fa?"
Ta ce." Ta yi bacci ta fad'a muryarta tana rawa.
Na ce." Ya jikin nata."
"Da sau'ki ta fad'a kamar za ta fashe da kuka. Na ce." To ba ni Hassana itama mu gaisa ko Ina Khalil?''
Ta ce." Yana 'kasa da Hassana." Na ji maganarta. "Mama ina yini."
Na amsa "Lafiya lau Hassana ina dariyar da babu nisha'di na ce." Ya kuke ina Mairo." Ta ce." Tana can k'asa Minal ba ta da lafiya."
Na ce." Allah Ya ba ta lafiya na kusa dawowa."
Da sauri ta ce." Yaushe?"
Domin na kwantar musu da hankali na ce." Gobe." Ina ji suka fara tsalle da dariya. Ya kar'bi wayar daga hannunta yana fad'in." Me yasa za ki gaya musu haka Amina kwananki nawa da tafiya."

littafin nan na kudi ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba

A tak'aice na ce." Biyu." Ki ka ce za ki yi sati daya ko kin fasa."
"Ban fasa ba." Na fad'a kai tsaye ina ji yana magana da yaran kan cewa su sauka k'asa wajan Mairo. Na daina jin motsinsu. Ya cigaba da cewa kin ga kuwa idan ba ki dawo gobe ba za su d'auke ki makaryaciya domin kuwa yaro baya mance magana kina dai jin tsalle da murnar da suke yi."
"Umm! kawai na ce na yi shiru.
Ya d'an yi gyaran murya kafin na ji shi yana fad'in." Yanzu kin tsane ni Amina ban yi miki komai ba wai menene lefina anan tare dake duka aka dinga wannan d'auki ba dad'in akan kwantar da ni da Maryam ta yi Malamin nan ya tsaya tsayin daka a kaina har sai da ya tabbatar da tabbatuwar lafiyata na cigaba da rayuwa da iyalina. Yanzu don Allah bai cancanci komai ba ban yi tsammanin zan samu wannan turjiyar daga wurinki ba tunda ai da farko ba haka ki ka nuna mini ba."
Na ce." Har yanzu kuma ba ni da damuwa akan hakan ba. Ai kai ka ga zaka ka iya amma dai Ina gaya maka ba zan zauna a gidan da zaka haye kan k'aramar yarinya kamar Hajara ba babu ni a cikin wannan rashin sanin ciwon kai ba kuma zan kara had'a inuwa da Hauwa ba. Ka canza mini mazauni idan ya zama lallai sai ka zauna da ni."
"Shikkenan za ki zauna gidanki na kano tunda hakan ki ke so amma ki sani za ki dinga d'aukar dogon lokaci kafin ki gan ni."
Na ce." Babu damuwa ai." Ba tare da ya sake wata magana ba ya kashe wayarsa.
Da safe da wurwuri na je na duba jikin Dada alhamdulillahi ta warware sai dai jikin girma idan abin ya motsa mata amma yini muka yi muna hira tana gaya mini abin alherin da ya yi musu a lokacin da ya zo dubata wattanin baya.
Bayan sunan Fadila da kwana biyu na fara shirin tafiya tunda mun gama magana dashi kan yanke zamana a kano abinda dai ban yarda da shi ba shine barin yarana a gidansa na abuja da Hauwa dole za mu zauna akan hakan sai ya ba ni yarana wallahi ta ri'ke na ta.
Ya kira ni yana gaya mini na tafi gobe domin shi ma a goben yake so ya shiga garin kanon saboda juma'ar da za ta zo za'a yi d'aurin auran a Bunkure kamar dai yadda ya gaya mini da farko.
To kawai na ce masa. Ban kuma tafi a ranar da ya ce ba sai a washe garin ranar tukkuna Babansu Fadila da kansa Ya d'auke ni a mota zuwa kano.
Gidan Hajja na yada zango anan shi ma ya kwana da sassafe yana karin kummalo ya d'auki hanya.
Hajja ta dinga rarrashina tana tausata ban san me ya gaya mata ba amma yanayin yadda take rarrashina ya nuna mini cewa kamar ya gaya mata wata magana a kaina wadda take nuni da cewar ni ce yanzu ba ni son zaman lafiya tunda Hauwa ai ta mato a kan sonsa kuma dama kulawarsa da tarasa ne a baya ya sanya take yin hauka da tsananin kishi yanzu kam tunda tana samun abinda take so a wajensa yana juyata son ransa ba zai fad'i aibunta ba. Kuma a lokacin da ta fahimci akwai rikici a tsakaninmu ta bud'e wuta da kissa da ko'karin kafa kanta a wajensa.
Ban katse ta ba na yi shiru Ina ta sauraranta tana cewa itama ta fi so na zauna anan din Hauwa da amarya kuma su yi zamansu a can abuja
Sai yamma direbanta magaji ya d'auke ni a mota lokacin shi bai dawo daga bunkure ba duk da ba ranar ne daurin auran ba na lura da yadda yake ta rawar jiki da kai kawo har an yi masa invitation irin na wata da kuma na kati ya d'ora a status dinsa.
A daran na kira Sahura na ce ta zo gobe da wuri dole sai ta taimaka mini mun gyara gidan.
Can misalin sha daya saura na dare ya shigo gidan.
Na gama shirin kwanciya ya shigo dakin ya same ni. Ya zauna gefena da alamar gajiya a tare da shi da kuma yanayi na damuwa da ta riga ta zame masa jiki
yadda bai yi mini magana ba haka ni ma ban yi masa magana ba d'akin ya d'auki shiru na tsayin wani lokaci
Na ji yana fad'in." Amina ya kamata mu yi gwajin nan na jini ( gyonotp) da yarinyar nan ko?"
Shiru na yi ba tare da na ce masa komai ba. Ya dube ni yana fad'in." Yadda Malam D'aha ya d'aukaki wannan lamarin ba na tsammanin idan an ci karo da wata matsalar wadda ka iya rusa auran ya janye ku'dirinsa sanin halinsa na magana d'aya da kuma 'kin yarda da zamani da hasashen yahudu da nasara........✍️
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *PAID BOOK VIP 1K ON TALGRAM WHAT'S APP GRUOP KUMA #700 VIA 0542382124....BINTA UMAR GTBANK*
*V-VIP AREWAPEN*
*07084653262*
*147*
Na d'an jima ina kallonsa tare da yin nazari a kan maganarsa na kasa tantance shin shawarata yake nema ko kuma umarni. Sai kawai na yi shiru ba wai don ba ni da amsar da zan bashi ba maganar ce kawai ta sake jefa ni cikin mamaki tunda har yana maganar gwajin jini (gyonotype) ya shirya kwanciya da yarinyar duk da k'arancin shekarunta kuwa.
Na yi shiru tare da juyar da kaina saboda tsabar takaici. Ya sake maimaita mini maganar . Sai na dube shi a sakarce na ce." Kai duk shige da ficen da kake yi ba ka yi gwajin jinin ba."
Ya d'an b'ata ransa yana fad'in.'' Amina ba kya yi mini lafazi cikin dad'in rai ko kina magana da sa'anki ne abubuwan fa da ki ke yi sun take shari'a kuma suna yi yawa."
Na d'an daidaita yanayina ina ce wa." To shikkenan na ji yanzu me kake so na ce?''
Ya sauke ajiyar zuciya tare da matso ni sosai ya kama hannuna ya rike sai kuma ya had'e yatsunmu ya matse gam. A dan tausashe ya furta." Ke ce abokiyar shawarata shiyasa da na fara wannan tunanin na tuntubeki dacewar yin gwajin jini ko ya ki ka ce."
Wani abu ya sake tokare mini wuya."
A tak'aice na ce." Hakan yana da kyau."
Sai ya cigaba da cewa." Ba ni fatan sake auran macce wadda za mu yi ta haifar yara masu lalura Amina wannan cikin da kike d'auke shi yana raina koyaushe da tunanin abinda za ki haifa mini nake mai lafiya ne ko mara lafiya saboda wannan ciwon gaskiya ne akwai shi. Ba ni so a 'daura auran nan jinina dana yarinyar bai jitu ba ta zama k'aramar bazawara domin ba zan iya kar'bar kaddara a karo na biyu ba wannan shine."
Na dai yi shiru ban ce komai ba ba wai don ba ni da abin fad'a ba.
Ya sake matsowa jikina yana magana can kasa." Ya ki ke ganin ya za mu yi,?"
Na dube shi babu yabo babu fallasa na ce."Fisabillahi me kake so na ce akan hakan?"
"Ki ba ni shawarar yadda zan yi." Ya fad'a yana d'ora bakinsa a dokin wuyana.
Na ce.''To shawarata ku je ku yi gwajin jinin ina ga kamar zai fi alheri."
Na ji hucin numfashinsa yana cewa." Idan an samu matsala na yi yaya da malam 'Daha."
"Sai ka yi masa cikakken bayani zai gane!" Na fad'a ina d'an janye jikina jin wani abu ya fara yi mini yawo.
Ya ce." Ba zai yarda ba Amina."
Na ce." To gaskiya kaima kana da lefi me yasa tun farkon fara maganar ba ku yi gwajin ba idan an tabbatar da daidaituwar jini sai a yi godiya ga Allah idan kuma jinin bai inganta daidai yadda ake so ba sai ka datse maganar da wuri ka kawo masa hujjoji da

Please Login or Register in order to submit comment