Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuka na fitar hankali. Babar yarinyar nan Hajara ta zo ta ri'ke ni ta baya ina cire hannunta tana sake ri'ke ni fadi take yi "Yi hakuri ki yi masa addu'a kin ji, Allah ya ba shi lafiya."
Na dube ta ina cewa." Ya mutu ko?"
Sai ta girgiza kanta cikin ko'karin kwantar mini da hankali ta ce." Bai mutu ba ke waye ya gaya miki."
Hawaye ya sake tsinke mini na ce." Kansa na ga ya karye ko'ina na jikinsa ya shika. Kin ga ai lafiya lau ya fito har muka yi muku sallama ko?''
Ta daga kanta cikin alhini ta ce." E, kwarai kuwa amma hakan ba shi yake nuna cewar bashi da rai ba zai tashi in sha Allahu."
Na ri'ke hannunta tamau ina fad'in.'' Ta cutar da ni, ta cutar da yaranmu ta zalince shi, ya yi mata alheri ta saka masa da sharri. Ta gigita mini rayuwata."
Kawai sai itama ta fara kuka ta rungume ni a jikinta tana cewa." Ki yi hakuri ki samu nutsuwa mu je can wajenmu ki zauna ki nutsu kin ji ko, ki yi wa mijinki addu'a."
Hajja ta fad'o mini a rai. Na sake fashewa da kuka mai gunji!
Ta kama ni sosai muka nufi d'an wajenmu a hankali take ta fad'in." Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un. Na kama ni ma idan ta ajiye na d'auka.
Ta zaunar da ni saman tabarma tana cewa Hajara ta d'auko mata mafici.
Ta kar'ba ta fara fifita mini har yanzu ba ta cika ni ba domin ni kaina nasan ba a hayyacina nake ba gabana duf-duf kawai yake yi mini daga zarar na yun'kura zan tashi sai ta riko ni.
Gabad'aya yaransu da manya sun yi cirko cirko a gaba.
Da wani irin sauti na ce." Wayyo Allah anti Yagana kina ina?" Na silale saman tabarmar na kwanta hawaye suka dinga biyo gefan idona. Na riga fa nasan mutumin nan ya mutu kawai a fito a gaya mini ne ba za a yi ba.
Na riko hannunta ina sake tambayarta a karo na biyu ta girkiza kanta tana cewa." Na gaya miki fa bai mutu ba Hajiya yana da rai in sha Allahu."
Na zuba mata Idona kafin na ce." Wuyansa ya karye ana gane alamun rashin rai a jikin dan adam tana nan fa kada ku yaudare ni."
Ta ri'ke ni da kyau a hannunta sai ta dubi yaran tana fad'in." Ku tafi ku yi alwala kowa ya d'auko al'kur'aninsa a yi karatu.
Jin haka ya sanya ni k'ara gazgata abinda zuciyata take gaya mini me yasa ba su yi karatun tun d'azu ba sai yanzu k'wa:kwalwata ta dinga gaya mini cewa a gidan mutuwa ne kad'ai ake yin karatun al'kurani.
Jakata na d'auka da take ajiye a gefena na d'auko wayata a karo na shida number Hajja na kira ta yi ringing sau biyu a na ukun ta d'aga. Tana magana na yi shiru hannuna yana ta rawa kiran sunana take yi Amina, Amina, bakina ya yi nauyin gaske hawaye ya ziraro daga idona cikin 'karamin sauti na ce." Ya mutu Hajja ta kashe mana Babanmu Hajiya Maryam ta cuce ni......✍️
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: *Gudun aure paid book complete 1k akan telegram via 0542382124.... Binta Umar Opey bank*
*127*
Da tsananin damuwa nake jin ta tana kiran sunana na ajiye wayar ba tare da na kashe ba jikina na rawa sosai na 'kunshe bakina da hannu jin yadda wani mahaukacin kuka ke ko'karin kufce mini.
Mahaifiyar Hajara da na ji suna kiranta da Inno ta d'auki wayar tana fad'in. Hajiya halima ce. Daga daya bangaran ita hajjan tana ta fad'in." Ko Baba Sulen ya rasu Amina domin shekaran jiya Kamalu ya ce mini ya je ya duba shi a can asibitin Murtala an kwantar da shi. Amina, Amina kina ji na."
Ta ce." Ni ce Inno uwargidan Malam D'aha nan Bunkure."
Hajja ta ce." Inno me yake faruwa ne, wanene ya rasu ina Amina take?"
Duka ta jero mata wad'an nan tambayoyin.
Cikin sigar kwantar da hankali ta ce." Babu wanda ya rasu Hajiya Halima gigitace dai kawai ta sanya har ta gaya miki haka."
Ta ce." Inno ki gaya mini gaskiya kin san dai ni ba yarinya ba ce?"
Sai ta dabarbarce ta kasa gaya mata komai. Zuciyata ta sake karyewa tabbas bata da abinda za ta fad'a kuma da bakinta take cewa bai mutu ba gashi yanzu an tambayeta ta yi shiru.
Ina jin Hajjan tana ta magana Inno ki gaya mini menene, ki bawa Amina wayar mu yi magana na ji ta a kusa dake tana kuka."
Ta miko mini wayar jikinta a sanyaye. Na kar'ba nasa a kunnena na ji tana fad'in." Yi shiru ki kwantar da hankalinki Amina ki gaya mini abinda yake faruwa kin ji ko, ki gaya mini ko menene ina sauraranki."
Da kyar na daidaita kaina na ce." Muna nan Bunkure ni da Baba amma ban san halin da yake ciki ba yanzu Hajja ki zo don Allah."
Ta ce." Yi shiru zamu zo in sha Allahu, yanzu dare ya yi amma da asuba zamu d'auko hanya dukkan tsanani yana tare da sauki."
Ban iya cewa komai ba sai jan hanci na ji ta kashe wayar sai ni ma na ajiye tawa na matsa jikin bango na takure can 'kasan zuciyata ina ta ambaton Allah akan ya kawo mana d'auki.
Dare ya tsala sosai muna zaune a tsakargidan ni da Inno mu biyu kacal ta yi ta yi da ni na shiga na kwanta na ce mata ta barni ko na kwanta din ba bacci zan yi ba gabad'aya hankalina na sashen malamin shiru ya hana kowa shiga Sukairaju da yan uwansu su Dahuru tunda suka shiga dashi ban sake ganin gilmawarsu a hanyar ba Rabi'u ne ya shiga sau d'aya kafin ya fito ya nufi bangaransa dake cikin gidan bai sake fitowa ba. Muna zaune har aka kira sallar asubahi. Kowa ya fito ya yi alwala yara da manya na yi na shiga d'akin da suka sauke ni a tun farkon zuwanmu gidan na yi sallah ina kuka sosai ina yi wa rayuwarmu addu'a.
Karatun al'kurani tun daga almajiransa na waje da cikin gidan iyaye da yaransu. Na kar'bi al'kur'ani wurin Hajara na bude nima ina karantawa a hankali a hankali na ji zuciyata tana sanyi. Gari ya fara haske Hajja suka shigo gidan ita da Hajiya Saratu da kanin mahaifinsa alh Sa'idu.
jin maganarsu ya sanya na rufe al'kur'anin da sauri na fito tsakargidan.
Inno ta sauke su tare da shimfida musu tabarma suka zauna yanayinsu ya nuna tsantsar tashin hankali a haka suka dinga gaisawa da jama'a.
Ba su wani jima da zama ba. Rabi'u ya fito daga wurinsa suka gaisa a gurguje ya nufi sashen malamin minti biyar a tsakani ya fito tare da fad'in." Hajja Malam yana magana."
Kusan a tare muka tashi gabad'aya ya shige mana gaba kowanne mu zuciyarsa na dokawa.
Yana zaune saman buzu da al'kur'ani warshu mai falle-falle a hannunsa d'akin tsaf Y
yana ta k'amshin turaran wuta. Can muka hange shi kan wata katifa madaidaiciya da shimfidar bargo a samanta. Yana kwance sambal sun cire masa rigar jikinsa daga shi sai singileti da dogon wandon rigar da suka cire hannayensa nade a k'irji ido a rufe.
Kafafuna suka fara kyarma Hajja kuwa kuka ta sanya tana fad'in." Me ya faru Malam ma'kiyane suka jefe shi ko, Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un!
Ta nufe shi tana kuka sosai ta tsaya a kansa tana fad'in." Ni kuwa me ka yi wa jama'a ne Tajo daidai gwargwado kana alheri da kyauta da yawa wasu na ta ganin wautarka akan dukiyar da Allah Ya baka. Ka yi kyautar hajji ka yi ta umara, ka yi kyautar kud'i ka yi ta gida da mota da jari, duk hakan bai yi musu ba sai sun kwantar mini da kai."
Shiru d'akin ya yi tana kuka da sambatu Hajiya Saratu na kusa da ni tana goge hawaye ta ma kasa zuwa inda yake kwance. Gabad'aya ta gigice sai kuka take yi na kasan zucciya.
Ni kam idona bushewa ya yi k'amas ban yi mamakin hakan ba wata'kila hawayen idona ne ya 'kare sai dai wani kutittiran abu da nake jin sa ya tokare mini a wuya. Da na d'aga kaina na dubi wurin da yake kwance sai gabana ya yanke ya fadi.
Alhaji Sa'idu ya tashi a hankali ya je ya kamo hannun Hajja ya zaunar da ita a gaban malamin wanda tunda take koke-koken bai ce komai ba.
A nutse ya had'a al'kur'anin da yake hannunsa ya mayar da shi ma'adanarsa ya kalli Hajja da har yanzu ta kasa nutsuwa ya ce." Hajiya Halima kukan ya isa haka, mu godewa Allah da ya takaita lamarin kuma aka samu hanyar warware shi cikin sau'ki.

Littafin nan na kudi ne yar uwa kada ki karanta ba tare da kin biya ni hakkina ba


Kamar yadda ki ka sani dai ni malamin zaure ne mai almajiran mai kuma hidima da al'kur'ani. Na ji dad'i sosai da Allah ya tsawaita mini nisan kwana wannan al'amarin ya kasance ya kuma ba ni iko da damar warware shi. Ba ni cutarwa ta hanyar sanin da Ubangiji ya ba ni kamar yadda wasu malaman suka d'auki wannan hanyar ta zalinci domin neman abinci da cutar da hallitar Allah.
Hakika a wani zuwa da Alhaji Tajo ya yi gare ni wattanin baya na karanci akwai rikici da makaru a tattare da shi. Wannan dalilin ne ya sanya ni gaya masa cewar ya dage da addu'a akan shi da kuma yaransa idan ban manta ba na tambaye shi iyali da adadin yaransa ya sanar da ni. Na bashi adduoi sosai na kuma yi masa da kaina domin samun mafita da warware wa.
jiya suka zo nan da matarsa ya yi mini bayanin dukkanin abinda ya faru bayan rasuwar matarsa Maryam wadda itace musabbabin kwantar da shi tunda aikin da ta sanya aka yi akansa ni kaina ya tsorata ni ba don komai ba sai don ganin irin d'aurin da aka yi masa bayan lokacin da Ubangiji ya d'iba masa bai cika ba.
Na jima ina aikin warware asiri iri iri wannan ya ba ni mamaki ya kuma tsoratar da ni k'warai da gaske, kuma an cire tsoron Allah wajen aikata shi.
Ya yi shiru yana duban inda yake kwance tare da girgiza kansa tabbacin da gaske abin ya bashi tsoro da mamaki kamar yadda ya fad'a..
Hajja ta ce.'' Ni ai a zatona abokan kasuwanci ne ko wasu da ba sa kaunarsa suka jefe shi tunda kasan yadda duniyar take."
Ya girgiza kansa yana cewa iyalinsa ce Hajiya halima kin san ku mata wani lokacin da son kai kuke da kuma mugunta. Ba dai a tara sani da Allah wata'kila ta ji a jikinta za ta riga shi mutuwa ne sai ta yanke shawarar yi masa d'aurin rai da ajali idan ta rasu a cikin biyu ko ya bi bayanta ko kuma ya kwanta kamar dai yadda yake a haka yana numfashi amma bai san a duniya yake ko a lahira ba."
Shiru ya ratsa kafin ya cigaba da cewa jiya na kwanta bacci bayan na yi sallar istahara akan lamarin domin kara tabbatarwa Ubangiji Allah Ya nuna mini ita ko ba ita ce 'yar fara mai karamin jiki ba da doguwar fuska?"
Hajiya Saratu da sauri ta ce." K'warai itace malam suffarta kenan."
Ya gyad'a kansa cikin jajantawa yana fad'in." Rahama sai ta Allah a wajen da take domin irin shirkar da take yi Allah Ya la'ancesu. Ba za mu yanke hukunci kai tsaye a kanta ba amma tunda har son zuciya da mugunta ya sanya ta kafurta kanta ta iya yadda da juya zancen Allah wurin neman biyan buk'atarta tabbas alkawarin Allah baya ta shi."
Ya nisa kafin ya cigaba da cewa." Na warware duk d'aurin da ta yi a kansa da yaransa zai tashi da izinin mai buwaya. A yadda ta so shine ko ya tashin ya zama mutumin-mutumin kamar gunki tunda da ayar nan ta (Summunbukkum!) aka yi aiki akansa bayan ita suka had'a (Makisinafiyiabada) ayoyi ne masu zafi wurin dakusar da duk wani karsashin dan adam idan aka juya su ta gefan zalinci.
Ita kuma wannan kwalbar ya fad'a yana nuna musu ita ya cigaba da cewa." Kowacce laya akwai sunan mutum guda a ciki. Amina Hauwa Kamalu Yusuf Khalil Hassana Usaina da kuma Minal. Mallaka ce aka yi akan wad'annan sunayen da na zayyano da kuma jefa soyayya a zuk'atansu.
Hajja na kuka tace fad'in." To me ya yi mata ni Halimatu na ga da iyalinsa ta same shi. Tsananin abotar da take tsakaninsa da Alhaji Amadu ya sanya da ya rasu ya aureta ni ma na bashi goyon bayan yin hakan tunda ya gaya mini a rubuce aminin nasa ya bar masa wasiyyar yin hakan. Me ya yi mata da zafi irin haka da za ta yi masa wannan mugun asirin."
Ya ce." Son shi take ainun kuma macace mai zafin kishi abinda na fahimta kenan."
Hajiya Saratu ta ce." Mun gode sosai Malam Ubangiji Allah saka da alheri, yanzu ya yanayin jikin nasa." Ta fad'a tana kallon wajen da yake.
Ya ce." A nan za ku bar mini shi daga nan zuwa sati guda zai warware in sha Allahu rabbi zai tashi ya cigaba da gudanar da al'amuransa."
Alhaji Sa'idu ya ce." Malam abin nan ya jefe ni a rud'ani ba kad'an ba. Ashe akwai irin wad'annan matan marasa Imani da tsoron Allah wallahi idan ana fad'a ba ni gazgatawa."
Ya ce." Akwai su da yawa muna ta fama da su. Ita wannan nata akwai razani k'warai domin tana iya bada jinin adam akan biyan buk'atarta tana aiki da ba'kar iska kuma suna iya neman jinin kowacce irin hallita. Kuma suna nan da yawa. Abinda dai na fahimta ga sha'aninta shine macace mai zafin kishi da mugunta. Kamar yadda na gaya muku da farko ni ba na bugun 'kasa akan neman sanin abinda Allah rufe bai bayyana ba. Istahara irin wadda Annabi ya koyar ita nake a duk dare kan wata mas'ala da aka kawo ta gabana idan na kwanta bacci Allah Ya akan nuna mini abinda yake faruwa. Iya fahimtata soyayyar da take masa ne ya sanya ta aikata masa haka saboda kishin ko bayan ranta kada wata mace ta more shi wannan shine
abinda ya halakar da ita har ta k'etare iyakar Ubangiji."
Hajja na girgiza kai tana fad'in." Kin yi kyawun dan maciji Maryam kin ci amanar mijinki, kin ci amanarmu da muka so ki muka kaunace ki, kuma duk inda muka zauna muke fad'in alherinki. Kin zalinci Tajo da iyalinsa kin mutu ba ki nemi gafara ba zahiri ba mu yafe miki ba maryam "
Tasa gefan mayafi ta goge hawayenta cikin damuwa.
Ya ce." Matarsa ta zauna nan har tashon kwanakin dana d'auka in sha Allahu komai zai wuce kamar ba a yi ba."
Hajiya Saratu ta ce." To shikkenan Malam yadda ka ce haka za a yi Allah Ya saka da alheri amma za mu dinga zagayowa muna duba shi ko?"
Ya ce." Hakan yana da kyau in sha Allahu."
Muka fito daga d'akin a tare da d'an sasaauci ba kamar lokacin da muka shiga ba cikin tsananin tashin hankali.
Hajja ta fara rigima wai itama sai ta zauna. Da kyar da jibin goshi Alh Sa'idu suka rarrasheta kan cewa ta yi hakuri su tafi idan ya so duk bayan kwanaki biyu sai su dinga zuwa.
Sai da suka yi sallar Azhar suka ci abincin suka yi shirin tafiya lokacin malamin ya yi b'aki ba su samu damar yin sallama da shi ba.
Tunda ba kasafai ake shiga wurinsa ba sai ya yi izini.
Da magriba yarinyar nan Hajara ta sake kawo mini dambu cikin langa tana fad'in.Matar yayansu ce ta ce a kawo mini tunda na jiya ya yi mini dadi.
Godiya na yi mata sosai na daure na ci ba don yana yi mini dadi irin na jiya ba sai don korar yunwa. Ba ni son na kwanta ban sake ganinsa ba.
Na fito tsakargidan suna zaune iyayen da yaran. Ban san ina su Sukairaju suke ba nasan dai tunda gidan karamci ne za a kula da su. Ina so ya je ya d'an yi mini sayayyar cikin kasuwa ko dogwayen riguna ne na yi na yi na kira Sahura a waya ta'ki shiga ina so na ce mata ta je can gidana ina da kaya ta debo mini sai ta kawo mini ba a samu network mai karfi a gidan sai an fita waje a tsakargidan kuma idan ya hau sai ya sauka haka yake yi.
Ina tsaye da waya a hannu Malam Rabi'u ya zo yana gaishe ni na amsa cikin dan jin nauyi domin yanayin yadda yake risina mini na sanya ni jin kuny. Ya tambaye ni ko ina da buk'atar eani na ce masa ina son na yi magana da Sukairaju.
Tare muka nufi wajan da aka sauke su. Ya fito ganina a tsaye ya risina na ce." Garin nan babu network mai karfi kasan gidan Sahura ko?''
Ya ce." E, na sani."
Na d'an yi shiru ina kallonsa gabad'aya shima baya nutsuwarsa botiran rigarsa duk sun zube idonsa ya yi ja da alamun bai samu bacci ba..
Na ce." Gidana na can kuntau can ta koma da zama."
Ya gyad'a kansa yana kallona na ce." Ku je tare da ita can gidana na sharad'a za ta debo mini kaya sai ka kawo mini akwai mukkuli a hannunta."
Ya ce." In sha Allahu zan yi wanka yanzu na tafi amma ya jikin oga, mun tambayi Malam Rabi'u ya ce mana da sau'ki ."
Na ce." Da sauki alhamdulillahi amma ku taya shi da addu'a domin ita ya fi buk'ata a yanzu."
Ya ce." In sha Allahu Hajiya amma a wane hali yake ciki yanzu ya tashi ne muna ta so mu shiga mu duba shi ba a ba mu dama ba ."
Na ce." Yana dai kwance har yanzu yadda kuka d'auke shi Sukairaju."
Sai ya yi shiru yana kallona cikin damuwa. Na juya ina fad'in.'' idan ka je ka dawo sai ka sanar da ni."
Na samu Rabi'u a soro a tsaye na ce." Ko za a yi mini iso wurin Malam zan shiga."
Da sauri ya ce. Eh amma yana d'an wani aiki yanzu zuwa an jima idan ya kammala zan sanar da shi sai ki shiga ko"
Na ce." To shikkenan na gode sosai. Ciki na shige gabad'aya jikina a sab'ule har in dai Hajiya Maryam ta samu nasarar nakasta mutumin nan ya tashi da wata tawaya ta cuci mutane da yawa wad'anda suka dogara da Allah suka kuma dogara da shi, halin da Sukairaju ya shiga yanzu abin jajantawa ne da tausayawa, to balle kuma yaransa da wad'anda suke makusantansa....✍️
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/4, 9:19 AM] Ummu Safwan: https://chat.whatsapp.com/E8JgnaAUG13CRwJbYeXImE?mode=gi_t
🌲🌳🌿☘️

*TALLAH!*
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*


*Gudun aure paid book complete 2k akan telegram normal What'sapp group kuma 1k via 0542382124.... Binta Umar gtbank*
*07084653262*
*128*
Haka na yi ta zaman jiran ganin Malam Rabi'u ya yi mini izinin shiga d'akin malamin shiru har dare ya yi nisa ban ji daga gare shi ba hakan nan na ha'kura na kwanta a wannan daran ma bacci sai dai b'arawo domin da ya d'auke ni na 'yan mintina zan bud'e ido har dai asubahi ta yi motsin iyalin gidan ya sanya ni tashi na fito da buta cike da ruwa wadda Hajara jiya ta ajiye mini kafin ta je ta kwanta.
Na jima saman abin sallah ina jan carbi bacci ya fara shammatata tunda dama shi ba a cin bashinsa. Na ji maganarsa yarinyar tana fad'in." Ina kwana."
Na bude idona da sauri tare da shi zaune ashe har na kai ga kwanciya kan daddumar ta ajiye mini dogon kofi na kunu da silbar k'osai a gabana ta juya ta fita minti biyar a tsakani ta dawo da wata langa ta ajiye mini da ruwan pure water guda biyu.
Na bude langar dumamen towo ne na masara miyar kuka tana ta k'amshin daddawa da zafinsà nan da nan yawuna ya tsinke na mike na fita.
Yaran gidan da alama sun shiga makaranta domin shiru babu hayaniya kamar koyaushe. Inno na bakin tukunya da kwanuka a gabanta ta juyo tana kallona sai ta saki fuskarta tana fad'in." Hajiya kin fito.
Na daure sosai ganin yadda matar ke ko'karin ganin lallai sai ta faranta mini da kwantar mini da hankali na ce." Eh ina kwana ya hidima na gode sosai Allah Ya saka da alheri.".
Ta amsa cikin dadi tana fadin." Ai na ce Hajara ta kawo miki dumame nasan zai yi miki dadi."
Na ce." Sosai ma kuwa wallahi Allah Ya saka da alheri."
Ta amsa da Amin ya rabbi." Bakina na wanke na koma d'akin zuciyata cike da zullumi haka na ci towon nasha ruwa d'aya na fito tsakargidan shiru matan gidan na d'akunansu.
Can bakin 'kofar fita na nufa na lura wajen akwai network sosai na kira Sahura muka gaisa na ce." Sukairaju ya zo jiya ne?" Ta ce." A a sai yanzu dai ya zo kin ga ina shiryawa wai me yake faruwa ne ya ce mini Yallabai ne bashi da lafiya kuna kauyen Bunkure."
Na ce." Sahura abubuwa da yawa sun faru masu muni ba zan iya ba ki labari a waya ba amma ina cikin tashin hankali mai tsanani"
Ta ce." Idan babu damuwa zan iya biyo Sukairaju ko Amina wallahi hankalina ya tashi ban san a wane hali ki ke ciki ba." Cikin rauni take maganar. Na ji zuciyata ta yi nauyi lallai Sahura masoyiyace ta hakika duk lokacin da na shiga matsanancin hali takan rasa sukuni tun muna 'yan mata haka muke idan daya ya shiga wani yanayi duk sai mu rasa sukuni."
Na daure na ce." Me zai hana ki biyo shi amma bai zama lallai ki samu ganin Yallaban ba tunda ni ma sau daya na ganshi malamin baya bari."
A sanyaye ta furta." Zan dai biyo shi Amina domin ganin halin da ki ke ciki idan kuma ina da sa'a sai Allah yasa a bar ni na shiga na duba shi din."
Na ce." Shikkenan duk abinda ki ka san zan buk'ata ki kawo mini Sahura zama ya kama ni dole."
Ta ce." In sha Allahu."
Na kira layin Anti Yagana cikin sa'a ta shiga na sauke ajiyar zuciya ina jiran ta daga na ji maganarta tana kiran sunana na amsa a

Please Login or Register in order to submit comment