Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yayana ai ni ba haushi naji ba, Anty ai Anty mu ce, tana da dama ta yi mana fada in munyi ba daidai ba taya zanji haushi kai ne kace wai in koma ban raka ka mota ba, kuma baka min wannan sumbatar da kake min ba kuma bakace in kula da kaina ba kamar yadda ka ke yi.

Ya yi yar dariya "Shike nan ayi hakuri zan biya bashi gobe Allah ya yi miki albarka."Ameen na gode mijina Allah ya tsare gaban ka da bayan ka, ya kai ka lafiya ya kawo rabo mai amfani." Ameen masoyiyata ina kaunarki. Tace me zan dafa maka anjima? Komai me dadi, in babu wani abu na girki da ki ke bukata kimin waya zan aiko. Asiya ta ce to. Bayan sun yi sallama Asiya ta yi shiru tana tunani ba shakka zata sha wahala da Anty amma ta san yadda zata bi da lamarin insha Allah.


Anty ta kara tunzura sosai karfa yarinyar nan tace zata shigar mata hanci da kudundune. Ta koma tana fadawa Hafsi abinda ya faru. Hafsi tace " Anty gara ki dauki matakin ɗan hakin daka raina shine yake tsole maka ido. Anty ta yi kwafa, tace ina takaicin sakacin da nayi ne har ta samu dama ta shigo cikin gidan nan. Hafsi Tace" Anty ai baki makara ba,,ki ka kori mai 'ya' ya ma bare wannan tsuntsuwar karamar alhaki. " Anty tace To Hafsi in kin haifu cikina ko ke din nan zaki fidda ta gidan nan. Hafsi ta sa dariya tana fadin " Sai dai in baki bani Umarni ba ta jima ta yi sati daya in na dinga tashin balli a gidan nan... "

Anty ta sa dariya ke abinda ba kamar yadda ki ke tsammani bane. Halifa zai iya raga min amma ke ubanki zai ci ba ruwa na. Hafsi ta saka dariya tace "Anty in har dai kin bani dama to ki zuba min ido ki bani sati daya, kowa dai da irin baiwar sa da kuma tasa Basirar ke tsohon lissafi ki ke yi, ni kuwa yar zamani ce.

Anty cike da mamaki tace ba shakka dama ance magaji mafiyi. To na baki dama sai dai ina son ki rinƙa sanar dani duk abinda zaki yi. "Ba matsala." Hafsi ta fada cike da yakini.

Asiya ta gama aiki tana zaune tana tunanin yadda zata bullowa Halifa ya yarda ya kai ta gida, tun jiya take latsa shi amma yaki zancan. Ko abinci take ci sai ta tuna Umman su da Sadiya da yaranta da kuma Abba, ta yanke shawara in har yaki kaita zata sa ya kira mata Yaya Sulaiman ya je ya kai ma su Inna waya mu gaisa.
Sallamar Hafsi ta katse mata tunani ta amsa kamar abin kirki ta shiga ta zauna Asiya tace za a kawo miki abinci? Hafsi ta ce tab "Gaskiya ni ba kowane kwado nake ci ba, da ƙazanta shi kanshi Uncle na yi mamaki yadda yake da kyankyami amma har kike yin jagwalgwalo yake iya sawa a cikinsa mai daraja!.

Asiya ta yi murmushi tare da fadin Kina da gaskiya sai dai kuma shi Uncle din naki kullum cikin yabon wannan jagwalgwalo da ƙazantar ya ke, ga shi yana santi, ta kai hannu ta dakko wayar tare da fadin kiga, kalli tukwaicin da ya bani. Hafsi ta kalli IPhone 13, ta zaro ido wayar da take ta naci Anty ta sa Halifa ya bata shine ya ba wannan wadda bata san darajar wayar ba. Asiya ta ce ya kikaji a ranki? Kin taya ni murna? Hafsi ta mike tsaye ta nuna Asiya da yatsa, tana fadin "Yana da kyau ki shiga hankalin ki, domin ni ba sa ar ki bace, kuma duk bala'inki wallahi sai ki fita a gidan nan banza yar matsiyata"

. Asiya ta yi yar dariya tace to zamu gani, gaskiya domin mutuwa ce kadai zata iya rabani da mijina, ina miki addu a Allah ya baki mijin irin nawa. Ta kaici ya kama Hafsi ta rasa me zata ce ta zuba ma Asiya ido tana huci . Asiya tace to ya kika ji a ranki, ba dadi ko? To ki kiyaye da cin zarafin mutane. Hafsi tace zaki yi da kinsani ta fice tana huci.


Halifa ya yarda zasuje gidan su Asiya tare sannan da dare murna gurin Asiya zata ga Inna.

Sun fito suka shiga dan yiwa Anty Sallama ya ga Hafsi tana ta cika tana batsewa, cike da raha ya ce Dota lafiya kuwa? Ta turo baki tace lafiya lau Uncle dama so nake ka dawo in kawo maka karar matar ka. Anty Asiya. Anty tace Kash Amma dai tun da kuka yi abinnan dazu nace kiyi hakuri ko? Shi aure ai lokaci ne da shi. " Cike da mamaki Halifa yace me ya faru? Anty tace waya sanar musu ni ko sauraron ta banyi ba, banda abinta ma da me zai sa tace wai zata je ta koya mata girki? Hafsi tace Uncle Dan Allah laifi ne idan naje sasanka na taya matar ka aiki? Ya girgiza kai alamun a a. Taci gaba shine ina zuwa wai ta ce wai in tafi bata so kuma in je inyi aure nima wai na tsaya yawo banza banda ko saurayi Wai me bakin jini.

Halifa ya kalli Asiya wadda mamaki ya hana ta yin magana sai Kallon Hafsi ta ke ta yi cikin daga murya yace menene gaskiyar lamarin??


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[6/24, 08:20] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w/9223372036854675807


*🔉 NASIHOHIN MALAMAN SUNNAH🔉*


Manzon Allah (saw) yace duk wanda wani bala'i ko damuwa na daga al'amuran duniya ke damunsa, idan ya yi ɗaya daga cikin waɗannan addu'o'in Allah zai yaye masa damuwarsa:-

1️⃣ LA'ILA HA ILLA ANTA SUBHANAKA INNI KUNTU MINAZZA'LIMIN.

2️⃣LA'ILAH ILLALAHU AZEEMUL HALIM,LA'ILAHA ILLAHU RABUL ARSHIL AZEEM, LA'ILAHA ILLAHU RABBUS SAMAWATI WARABUL ARDI WARABUL ARSHIL KAREEM.


Asiya tace a ranta wai haka abin ya zama kenan, dan haka sai ta yanke shawarar zuwa musu ta yadda basa zato. "Ina sauraron ki, Asiya cike da kwanciyar hankali tace duk yau yaya banga Hafsi ba sai yanzu. Gaskiya ba dani bane. Halifa ya kalli Hafsi" Kinji me take fada? Hafsi tace ki fadi tsakanin ki da Allah."

Da karfin gwiwa Asiya tace ke zance ki fadi tsakanin ki da ALLAH. Hafsi tace " "Humm kamar nasan zata musa na yi recording a wayata ta. Ta dakko wayar wadda ta zauna ta gama editing ta cire maganganun ta. Gaban Asiya ya fadi da ta ji yadda aka jera maganganun tiryan tiryan, ita kanta banda ta san yadda suka yi ita da kanta da sai tace tabbas haka ne. Halifa ya cika da mamaki ya kalli Asiya a fuskar shi ta ga Bacin rai karara. "Me kuma zaki fada yanzu? Asiya ta ce bani dashi domin ko na fada bazaka yarda ba tun da na riga nayi karya tun a farko nace ba ayi ba.

Gaskiya dai tazo kuma duk maganganun na da ta dauka amsar magaganunta ne, da ta fada min inda za a sake kunnawa tsaf zan fidda yadda zantukan suka faru a tsakanin mu. Anty ta amshe, da fadin ni dai abar maganar kawai ke Asiya ki daina gorin aure ga budurwa komai lokaci ne. Ke kuma kiyi hakuri. Ta kallo Halifa wanda har lokacin bai ce komai ba ka rinƙa yi mata faɗa duk da cewa harda kuruciya. Halifa ya Ja tsaki yace wace kuruciya a nan. Ya juya.

Asiya ta kalli Hafsi sannan ta kalli Anty tace Hasbunallahu wa ni'imal wakil. Ta wuce tabarsu suna dariya, basu san wannan addu ar da ta yi ta ce Allah ya isar mata komai babbar magana ba ce.

Kamar yadda ta zata Halifa ya bude daki ya shiga, ranta ya sosu, kenan sun fasa fitar, ta daure ta cije domin dai fushin fari ba nata bane. Ya yi matukar bata rai yana zaune akan kujera. Ta kwantar da hankalin ta kafin ta ce Yaya munfasa zuwa duba su Innar tamu ne? Tun kafin ta rufe baki ya ce, na fasa. Asiya. tace saboda me? Ya dube ta cikin daga murya "Kina ganin cewa abinda ki ka yi ba laifi bane ke nan? Asiya kin bani mamaki kin iya karya har haka? Ina son ki sani duk duniya na tsani karya, duk lokacin da mutum ya zama makaryaci a idona darajar shi zubewa ta ke yi, yanzu fa ba wata magana da zaki fada min inji cewa gaskiya ne ko da kuwa gaskiya ce sai na tsaya kokwanto. Sai yanzu Asiya ta gano illar da suka yi mata. Ta kwantar da muryar ka yi hakuri, na yarda cewa na yi karya, kuma karyar cewa duk yau banga Hafsi ba iya itace laifina na zabi in faɗi haka saboda kawo karshen rigimar da tazo har daki ta takale ni da ita.

Yace Malama yi min shiru, me ya hana ki fada tun a lokacin gaban kowa, ina son ki sani a duk yadda Duniya ta rikice miki ko rayuwa ta riske ki kar ki taba daukar karya wai ta zame miki mafita. Kirike wannan domin bazan sake maimaita shi ba. Asiya ta lumshe ido hawaye suka kwaranyo cike da nutsuwa tace na rike kuma insha Allaahu bazan sake yi maka karya ba, ta silalo kasa ta zube gwaiwa biyu a gaban sa cikin sanyi murya tace natuba.

Halifa ya sauke ajiyar zuciya sannan ya yi mata alama da hannu wai ta tashi. Ta mike ta nufi cikin dakinta tana kuka yanzu kam ta tabbatar yaki dan zamba ne kuma dole ta kara sanin da suwa take zaune.

Anty ta saka dariya bayan Nur tace Anty naji Uncle yana ta yi wa Amarya fada tana kuka shine ban shiga ba na dawo dama kince in naji yana fada in dawo. Anty tace jeki kuyi kallon ku kin gama aikin ki. Dama ta tura tane wai ta amso mata chajar waya amma in taji Uncle Halifa yana fada to ta dawo. Sako ya fado wayarta ta dauka ta duba Hajiya Talatu ce. A fili tace lalatacciya har na manta da rayuwar ki, sakon uban me kika turo min in bashi ki ke nema dai bani da shi.

"" Ki duba whatsapp din ki. " Abinda aka rubuta Kenan, bata iya magana ba sai dai ta wuce kai tsaye zuwa whatsapp din nata. Odiyo ne Ta kunna wayar su da Malam ne tiryan tiryan kafin Anty ta gama saurara zufa ta rufe ta, sannan ta tsine wa Hajiya Talatu babu Adadi.

Ta danna kiran Hajiya Talatu cike da karfin hali tace, Talatu manya, to wannan Odiyo din da kika turo min me zai amfane ni da shi? Talatu ta yi yar Dariya. "Kawata ta kaina, ke kuwa zai amfana da zarar angoge shi, amma in aka tura musamman ga Halifa ko da bana nan nasan kin aiwatar da abinda kika yi kuduri, daga nan sai asirin ya tonu." Anty ta zaro ido amma sai ta cije tace. Ba shakka na cika kuduri na, amma ki sani shi kanshi Halifa ko yaji wannan babu abinda zai iya, domin na samu damar juya shi a yanzu haka.

Hajiya Talatu ta danyi shiru cikin sanyin jiki, jin haka sai Anty ta san cewa karyarta ta samu shiga dan haka cike da kwarin gwiwa ta ce. Amma zaki iya tura masa din ki gwada ki gani. Talatu kin bani mamaki shiyasa naki kai ki gidan malamin tunda na fahimci da sharri kika zo min gida. Kuma duk abinda kike ciki wannan malamin yana sanar dani hatta wannan kuduri naki, da wannan Wayar da zamu yi duk ya fada min. Kuma ni da na so zan saka ya cutar da ku ke da Ma'u din amma nace masa zan sake baki lokaci ko zaki nemi yafiya ta.

Talatu ta tsorata matuka Tace "Sahiba to duk ba wani abu bane, kawai dai ina son Halifa ya auri Ma'u ne, duk kan haka ne na miki rakodin kuma da zan tura mishi ai da tuni na tura. Anty ta yi dariyar samun nasara, tace Talatu baki gama sanina ba har yanzu, ni yanzu jini nake ba aljanu suna kawo min bayanai yanzu haka sunce min maganar da muke yi dake kin sake kunna rakodin to ina gargaɗin ki, zanyi hadaya dake matsawar baki goge duk wadannan Odiyo din ba, zan basu jinin ki ba ruwana. Hajiya Talatu jiki ya soma rawa domin ta danna din dan samun wasu bayanan. Ta kashe wayar Tana mamakin Anty gaskiya ta zama abin tsoro dole ne ta goge su. "

Anty kuwa ta shiga tintsira dariya tana cewa Kai gaskiya barazana ta yi, da na tsaya rokonta da yanzu tana nan zata hada min jangwal. Da Hafsi ta dawo take bata labarin abinda ya faru suna ta dariya.

Kiran Hajiya Talatu ya shigo. Hafsi tace Anty kar ki daga sai a kira na uku dan tasan abinda gaske ne, kuma in tace ta goge sai kice Aljanun sunce saura daya ne bata goge ba, kinga in ta makale wani zata kara gaskata hakan kuma zata goge, in kuma ta yi ta rantsuwa akan ta goge sai kice mata dayan shine wanda ta turo miki ta goge shi da kanta.

Anty tace kai gaskiya kin haifu Hafsi ina ma ace haka yayanku yake, da yaushe zan sha wahala.

Haka kuwa suka yi wa Hajiya Talatu kuma ba shakka lissafin ya tafi yadda Hafsi ta tsara.

Cikin bacci Asiya taji Halifa yana lalubarta, duk da cewa harta kwanta yana fushi da ita hakan bai hana ta bashi hakkinsa ba, ya kunna wuta ya kalli fuskarta, ya kai hannu ya shafi busassun hawayenta kina yawan kuka sai dai nafi son irin wanda kike yi din nan idan mun kasance tare. Ina jin dadin da farin ciki. Asiya ta rufe fuska ita fa batasan tana wani kuka da yake yawan fada mata ba.

Zuwa da safe kamar babu wani abu da ya faru na fitina tsakanin su. Ya dai kara yi mara nasiha akan karya, yace "Bana son karya sam sam kuma bana zama inuwa daya da me yinta. Asiya tace zan kiyaye nima ba ɗabi ata bace.

Tace to ya kira Yaya Sulaiman ya kai waya gidan su, sai yace ta bari da dare zasuje.

Anty ta cika da mamakin ganin Halifa sun sake zuwa sallama kamar dai jiya. Dole ta wage baki tana yake tare da fadin ki gaida Innar taku, sannan Halifa kar aje hannu rabbana. Yace "ai dama."
Sahat suka fara zuwa kayan abinci ya saiwa su inna sannan suka wuce. Murna Asiya ba a magana Inna ta kara yi mata nasiha da shawarwari, sannan suka tafi.

Kwana biyu tsakani Asiya ta shiga gaida Anty sai tace mata anjima masu allurar riga kafi za su zo, za a yi ta annobar sankarau saboda zuwan zafi. Asiya ta tsorata dan ita bata son allura sam. Tace Ni kam ba sai anyi min ba. Anty tace ai kuwa yi ya zama dole domin bazan bari ki kamu da cuta ki yada mana ba.

Da rana da ya dawo take fadawa Halifa ita bata son allura. Yace Anty ta faɗa min tun jiya wai za ayi riga kafi ki hakura a yi miki don bana son magana yanzu Sai wannan karamin abun ya zama issue.

" Asiya tace shike nan.
Tana bacci aka tashe ta ake faɗa mata ga me allura. Tayi mamakin ganin an tsaga mata hannu an saka wani abu an like. Ta sha kuka sosai domin azaba da kuma rasa ko me aka sa mata. Halifa ya yi mamakin ganin yadda gurin allura ya yi tsagu, da ya yi wa Anty magana wai ita ce Taki tsayawa shine ya sa har aka karce ta.

Bayan kwana biyu sai jini ya balle wa Asiya wanda bata san kanshi ba. Ta zaci lokacin al adarta ne ya canza. Tun abin baya damunta har ta shiga tsoro. Halifa kuma ya shiga takura, saboda jini yafi sati kuma sai ya dawo kwana biyu uku da daukewa sai ya kuma dawowa. Halifa ya samu Anty ya fada mata. Tace Aljanu ke yin haka, an fada maka yarinyar nan Aljanu ne suka aureta amma ka ki yarda.gashi sun nuna kansu gidan magani kawai za a kai ta. Hankalin Halifa ya tashi sosai, kuma ya amince da suje gidan magani. Asiya tace masa bata da komai ita babu gidan maganin da zataje. Hakan ya kawo musu matsala wadda ta sa Halifan Kauracewa gadon su.

A kasuwa yake fadawa wani abokinsa abinda ke faruwa da matarsa, yace gaskiya ana samun haka shima wata kanwar su budurwa haka aljanu suke sakar mata jini. Halifa ya sake yarda dan haka yace lallai Asiya ta shirya Anty ta kai ta gidan magani.

Farin ciki ya cika Anty domin malamin nan ne ya bukaci ta kawo masa Asiya zai yi mata wani wanka wanda zai wanke abinda ya sa aljanun ba su yarda sun karbeta a waccan ranar ba, wato da suka ce ba budurwa bace. Sun bincika sosai ba su samu mai irin tauraro ta ba....


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[6/28, 21:44] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w/9223372036854675807


Tace masa sha biyu za su fita dan haka ya basu kudin kekenapep ya bawa Anty kudi yace su dauki shatar abin hawa kuma duk yadda ake ciki su kira shi. Ƙala Asiya bata ce ba lokacin da zai fita ya kalleta yace "Kiyi hakuri baby gaskiya dole ayi maganin wannan ciwo yana shiga hakkina da yawa yanzu yau kwana nawa rabon mu da ke? Ta kalle shi, me yasa baka yi tunanin mu fara zuwa Asibiti likita ya tabbatar ciwon ba? Na yi mamaki yadda ka ke ahalissuna kuma ka yarda a kaini gurin yan tsibbu masu amfani da aljanu. Yaya Halifa bani da kowa a kaina ban taba ko mummunan mafarki ba, to yawanci masu bada maganin nan wallahi ance suna lalata da yaya da kuma matan mutane yanzu kai ka yarda a kaini wani ba kai ba ya kwanta da ni? Ta kai karshen maganar tana kuka.


Halifa ya ji wani abu ya soki zuciyar shi yace amma ai Anty ba irin gurin zata kai ki ba, Anty bata hulda da masu zuwa irin wannan gurin. Asiya ta yi shiru tana tunanin dole fa ta sa Halifa ya janye zuwanta gurin wannan maganin. Babbar matsalar shine Halifa bai san wacece Anty ba.

Ta sau ke ajiyar zuciya cike da kwanciyar zuciya tace. Zanfi yarda muje tare da kai a yi komai a gaban ka kokuma yanzu muje Asibiti muga likita ya tabbatar mana da matsalar bata su bace,, domin nifa tundaga wannan ranar da aka min allurar riga kafi komai nawa ya canza ina zargin likitan bai yi abinda Anty ta saka shi ba. Halifa yace "Kin tabbatar tun daga ranar ne kika fara samun canji? "

Asiya tace gaskiya haka ne. Halifa yace me ya sa baki fada min ba? Bari in yi magana da Anty. " Asiya tace Yaya kar ka fadawa Anty domin zata ga kamar munki shawarar ta ko taji babu dadi akan ita ta kawo me allurar aka samu matsala. Inda zaka yarda kawai mu tafi in mun dawo sai mu fada mata, in kuma likitan yace ba na Asibiti bane shike nan sai mu yi shiru. To muje ya fada ya na daukar wayar shi akan kujera. Hijab Asiya ta saka suka fice.

Likita ya kalli Asiya "Baki yi makaranta bane?" Asiya tace nayi makaranta amma bangama ba. Ya kalli Halifa wannan gurin ba allurar riga kafi bane, tsinke aka sa mata na tsarin iyali wato tazarar haihuwa,, tana me bata sani ba? Halifa yace likita wallahi ta fada min cewa kamar an saka mata wani abu amma sai aka ce min taki tsayawa ne ayi mata allurar kuma dama tun farko ta nuna cewa tana jin tsoron allurar dan haka sai kawai na yarda da abinda Antyna ta fada.

Likita yace gaskiya babu wani kuskure wannan abin ana sane aka yi shi dan karta haihu. mamaki ya cika Halifa yana kokwanto cewa anya Anty tana sani zata yi haka. Likita ya kira nurse ta cire mata abin Halifa ya kalla yace tabbas wannan babu kuskure daga cewa yi allura sai kawai mutum ya saka wannan. Ya dai yi godiya tare da tambayar jini ko zai daidaita. Likita yace zai daidaita insha Allah.

Asiya ta lura da yanayin da Halifa ya shiga na tashin hankali yana ta maimaita me ke nan Anty ta yi? Ta sanyaya muryar tace, kar ka zargi Anty fa babu mamaki laifin shi mai allurar ne. Halifa ya sauke ajiyar zuciya yace ina fatan ya zama haka, dan zaifi yi min sauki a bisa a ce wai Anty da nake mata kallon mahaifiyata nake mata kauna irin ta ɗa da mahaifiya, ace tana da hannu a yunkurin hana ni samun ɗa.

Ga mamakin Asiya sai taga hawaye sun kwaranyo daga idanunsa. A firgice Asiya tace ka samu guri ka dan tsaya dan Allah. Kamar mai kar ɓar umarnin ta sai ya tsaya cak. Sannan ya yi gefe. Asiya ta matsa ta rungume shi, kamar hakan yake bukata sai shima ya rungume ta tsam sai kuma ya saki kuka. Asiya bata hana Shiba har kusan minti daya sannan ta fara fadin "Ya isa haka Yaya, ka yi hakuri dan Allah insha Allah ba ruwan Anty, ni da zaka yarda ma da sai mu yi shiru mubar maganar kawai kace mata gurin wani maganin mukaje shike nan. muryar Halifa a dashe yace" Kinsan matsalata daya da zarar na zargi abu in har na cika bibiya sai ya zama gaskiya.
Asiya tace ka yi hakuri insha Allah ba haka bane.

Sun iso gida suka samu Anty tana ta faɗa. Halifa ya kalleta cike da zargi lokacin da take cewa "Sakar cin banza kawai banda shashanci sai ku fice bayan kun san zamu fita, ba sai ku bari sai mun dawo ba. Halifa ya yi karfin halin cewa mun samu magani a Asibiti yanzu da muka je.

A firgice Anty ta ce," Asibiti kuma bafa ciwo Asibiti bane". Halifa yace tsinken da kika sa a saka mata ne aka cire. Ta dau salati wane tsinke kuma ni Habi. Halifa yace Na allurar riga kafi mana wanda aka ce min karcewa ta yi. Anty ta dauki salati ta sallame. Ta dakko waya tana fadin sai na sa an daure dakta din nan, tsarin iyali kuma yaya ya yi haka ne. Ta kira ya daga ta saka a free. Tace

Please Login or Register in order to submit comment