Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fara rokon Allah ya sa tare suka zo da Halifa.
Na fito daga daki ina fadin sannu da zuwa yaya Sulaiman. Ko amsawa bai yi ba ya shiga tambayar Asiya wai kuwa me kika aikata na ganki a Tiktok? Gaban Asiya ya yanke ya yi wata muguwar faduwa, Wani sabon Sharrin ya sauka kenan, ta furta tana Kallon idon Sulaiman. Ya ce kalli kiga ni yadda abin ya yadu mutane sai sharhi suke yi suna kara yada abin. Asiya ta gama kallo gaba daya zuciyar ta tana bugawa da sauri, ta mika mishi Wayar ta koma ta zauna Sulaiman ya ci gaba da fadin wallahi nasan sharri ne sai dai na yi mamaki yadda Halifa ya yarda. Asiya tace dole ya yarda ta fada masa duk yadda abin ya faru da kuma yadda ta sani.

Sulaiman ya yi ta mamaki tare da yi mata addu"a Allah ya fidda ita, sannan yace yanzu ya za ayi da mutanen Soshiyal midiya din nan? Yan jarida ma nasan in suka ji labari sai sun zo gidan nan yadda abin nan ya yadu kyau ki bar garin nan zuwa nan da kura ta lafa. Inna ta fito cikin mamaki tace "Abin har ya kai Haka? Gaskiya dai ina ganin ba sai taje wani guri ba, kawai dai baza ta fita ko ina ba." Sulaiman yace to shike nan Amma ina mai tabbatar miki cewar yanda kowa ya zama dan jarida yanzu ba sai ta fita ba, har gida zaki ga ana zuwa domin gani da kuma jin ta bakinta. Asiya tace inaga zan zauna a daki kawai. Sulaiman ya ce Allah ya kyauta ya fita.


Maganar Sulaiman. ce ta ke neman tabbata, yayan makota suka. soma shigowa daga nan sai iyayen sai kuma ga wani gida radio wai sun zo jin ta bakin Asiya. Ta kulle kanta adaki. Dole Asiya tabi duhun magriba ta tafi gidan wata yar Uwar su a Kurna ta kwana washe gari ta yi asubanci hanyar Malumfashi dangin Innar su.....



*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

[7/29, 21:25] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w

Ga zaton ta barawo aka kama, ta dubi Halifa ta ce a ina ya yi sata? Kafin Halifa ya bata amsa sai taji barawo na cewa Dan Allah ku yi hakuri wallahi sai da nace wa Asi baby kawai ta zo inda muka saba haduwa gidan abokina wanda ya rabu da matarsa can take zuwa idan Halifa ya tafi kasuwa, to da yake ina zuwa wasu lokutan a nan idan ya fita yauma wallahi na musa amma tace yanayin jikinta ya sa ta kasa...... Halifa ya sa kafa ya tokari cikin sa, sai da ya yi kara sannan jini ta hanci ta baki aka rike Halifa yana fizgewa akan cewa a sake shi sai ya kashe shi. Sai lokacin Asiya ta fahimci sharrin da aka yi mata ta daga ido ta kalli Anty sai ta saki wani murmushi irin na takaici. Tace tanan aka sake bullo min? Ta je gaban mutumin ta kalle shi. Ina son ka fadi tsakanin ka da Allah ka taba ganina? Ya fashe da kuka tare da fadin Asiya kalli ki gani kefa ki ka ce inzo gidan ki ke kika ce mijin ya tafi kasuwa amma shine kike alaye kamar baki san komai ba. Zufa ta karyo wa Asiya lallai sun tsara abin su. Ta kalli Halifa Dan Allah Yaya kar ka yarda da shi wallahi ban san shiba.

Anty tace amma wannan yazo gidan nan ba so daya ba akwai ranar da na ta tambaye shi ya ce min yayanku ne, to amma ganin yadda in ya fito yake sanda shiyasa na kasa yarda da shi. Halifa wanda takaici ya hana shi magana ya fidda hannu ya wanka wa Asiya mari yace kinsan tin yaushe nake a gidan nan tun ina fita kasuwa Anty ta kira ni tace ga wani ya zo tana ganin shi yana yawan zuwa, har nace kila Dan Uwa ku ne sai kuma na kasa nutsuwa kasancewar yadda mata suka koma a wanna zamanin. Nayi awa daya ina jiran fitowar shi sannan ya fito daga dakin mu dakin auren mu Asiya yana gyara wando ya dakko takalmanshi a inda ya boye ya saka ina Kallon shi ba zan iya barin shi ya fita ba, ni ne nayi masa wannan dukan. Sai Halifa ya fashe da kuka. Asiya cikin firgici da tashin hankali, ta kama hannun shi tace "Yaya kar ka yarda wallahi wannan shiryayyen al amari ne ka yi tunani sosai wallahi ni bacci nake ina kwance a dakina wannan hayaniyar ce ta farkar da ni. Halifa ya hankade ta da karfi ta fadi, yace ki daina taba ni hakikar ke abar kyamace,kin bani mamaki. Zafin maganganun Halifa sun fi mata zafin faduwar kuma ta tabbatar Allah ne kawai zai wanke ta. Sai lokacin ta soma kuka tana furta Allahumma ajirni fimusibati. Ta mike domin bata da sauran wani abu da zata fadawa mijin nata giyar kishi da bakin cikin abinda ya gani ke dibar sa, ta yi masa uzri a yanzu tasan lokacin yi nadamar hakan zai zo a gaba. Bazata yanke hukunci cikin fushi ba, amma tasan auren ta ya gama lalacewa.

Ta mike da nufin ta tafi dakin ta ta saurari hukuncin Ubangiji sai taji ana ku rike shi ta bishi da kallo ya kama bishiya ya haye katanga ya dira ta baya wanda kafin a zagaya ta tabbata ya gudu.
Ta zauna akan kujera ta fashe da sabon kuka. Tana fadin Allah yau kuma da wannan na wayi gari ya Allah! Allah ka kubutar dani kamar yadda ka kubutar da Annabi Yusuf daga khaidin mata. Allah ka wanke ni kamar yadda ka wanke Uwar muminai Nana Aisha daga sharrin masu sharri. Alwala ta yi da ta samu sanyi a zuciyar ta. Ina ma ace mafarki ne.

A tsakar gida kuwa kwarto ya gudu Halifa yaji takaicin haka domin ya so yasa a daure masa shi. Ya shiga dakin a fusace Asiya wadda ta gama sarewa ta dube shi. Yace "Wai Asiya in tambaye ki, dame na rage ki har ki ke kula wannan kazamin daga gani ko sana'a bashi da ita. Ko bana iya gamsar da ke a shimfida ne? Asiya sai Kallon shi take ba shakka ya gama yarda cewa ta aikata laifin.
Ta mike ta shiga daki ta gama amincewa auren su ya kare ta sauke akwati tana duba kayan da zata dauka a kayanta na gida dai kala daya ne wata doguwar rigar atamfa Dan haka ta ciro ta da wani hijabbinta na idin da akayi kafin auren su. Ya shigo dakin lokacin ta gama sakawa ta duba jakar ta ta dauki dan kudin ta wanda yakan bata. Ya ce ina zaki ko binshi za kiyi? Ta dube shi cikin wani yanayi wanda bazata iya fassara shi ba. Duk abinda aka yi ba sukai wannan kalmar da ya fada mata yin daci a zuciyar ta ba. Hawaye suka kwaranyo daga Idanuwanta. Cikin rawar murya tace "Ka yi duk zargin da zaka yi bazan hana ka ba. Gaskiyar ita ce, ban aikata komai ba, banda masaniya akan komai, sannan yanzu kuma gidan mu zanje. Zaki je ki tona wannan maganar ta yi ta yawo cikin mutane? Abinda ya sa ban samu ba koda wancan yaron ya gudu bana son in kai shi gaba maganar ta zama abin tattaunawa a satin nan, can kuma abin ya koma Soshiyal midiya. Asiya tace ni ba zan damu ba ko waye ma zaiji ya ji kuma ba zan hana shi yarda ba tunda kaima ka yarda. Kuskuren da nayi na dauka cewa zaka bani kariya a matsayin ka na mijina ashe nayi kuskure. Ta fito fallo ya biyota ban fa baki izinin fita ba. " Halifa bana bukatar izini domin aure da zargi basa haduwa." To kin fi son kije ki tada hankalin Inna gata da hawan jini? Asiya tace bari kaji Inna tafi kowa sani na, ko a mafarki bazata taba yarda da wannan wasan kwaikwayon ba.

Ta kama kofa ta bude yace Cikina kar kije min dashi ko ina. Anty dake bakin kofa ta a she. Ta ce ta ina ya zama cikin ka, kana jin me cikin ya fada? Ka barta taje gida tunda tana gaddama cewar bata aikata ba sai ka bincika ka samu Tabbaci. Halifa bai ce kala ba har Asiya ta fice.

Shima ya rufe dakin ya fice. A baya yake bin Napep din da ta hau har Unguwar su.
Asiya ta shiga gida Inna tana kwance Abba yana girki Maman Annur taje gidan aiki. Inna ta tashi zaune tana fadin Asiya ce yau da wuri haka? Asiya tace inna ai ba zuwan dadi bane. Nan ta kwashe komai ta sanar da ita. Inna ta shiga salati da sallallami tace yau kuma da haka na wayi gari. Allah ka fidda wannan yarinyar sai kuma ta shiga lallashin Asiya tare da bata magana. Inna dai ta boye wa Asiya damuwar ta ne kawai amma fa ta shiga tashin hankali domin duk yadda Asiya take Kallon abin ya fi haka, ga shi su ba karfi ba ta yi imani Asiya bazata taba aikata abinda aka danganta ta dashi ba.

Da dare Halifa yana ta kai kawo daga falo zuwa daki yana auna abin da ya faru wata zuciyar tace kai. me yasa baka zo ka shigo dakin ba a lokacin? Ya tuna yadda Anty ta rike shi tana karkaje kar ayi mugun abu, zaka yi mugun gani. To amma gashi yana kokwanto kodai sharri ne aka yi mata masu bata guba din nan. Ya kamata ya fahimci cewa lallai akwai wani abu. Ya fita zuwa sasan Anty tana waya da ƙawarta Wai ta kira tana cewa ta ga abinda ya faru a gidan an dora a tiktok. Anty tana cewa wallahi kuwa nima dazu Hafsa ke nuna min ko suwaye suka dauka suka dora ga shinan shi kwarton an masa duka ita kuma Asiya tana ta kuka, aiko ta sha zagi. Halifa yace Anty me aka dora a Tiktok? Matar tawa aka dora? Waye yake da tabbci ko shedar cewa zina ake aikatawa adakin? Waye ya yi musu kamu irin Na shari 'a?
Anty ta juyo da sauri cike da mamaki ta kalli Halifa tana murna ta zare masa yarinyar daga zuciya yanzu Sai batun zubda ciki amma shine zai mata tsalle? Ta mike a fusace " Halifa idan har na isa da kai wallahi sai ka bar yarinyar nan. Wane irin asiri ta yi maka haka wallahi ko waye ya tsaya maka sai ka barta ba dai a zuri a taba. Halifa yace Anty gaskiyar magana ina son mata ta kuma zuciyata ta ki amincewa da cewar Asiya ta aikata wannan abin in halinta ne da ta yi kafin ta zo gidana amma yarinyar nan a budurwa na same ta, ni ne mutum na farko da na fara kusantar ta. Bazan manta hakan ba. Dan haka saina bincika sosai kuma duk wanda na gano da hannun shi a dauka ta a Video ya yada sai na yi shara a da shi.

Ya Juya a fusace. Baki Anty ta saki ta bishi da kallo lallai wannan sai ta yi da gaske.
Yana shiga daki ya dauki waya Sam bai damu da hawa Internet ba, amma sai ya kunna data da nufin duba Tiktok. Kiran Bros ne ya katse shi ya daga cikin sauri domin yana bukatar jin ta bakin wani. Cike da tashin hankali yace Uncle me yake faruwa ne dazu maman Nihal take nuna min Matar ka a Tiktok. " Ina zan same ka yanzu? Halifa ya tambaye shi cike da damuwa. Bros yace ina gida kuma kaga muna da tazara Amma mu hadu a zoo road yanzu." To Halifa ya furta ba tare da ya tsaya tunani ba.

Jikin motar Halifa suka jingina inda Halifa ya zayyano wa Bros komai. Ya kara da cewa kasan menene Bros sam zuciyata ta ki aminta cewa yarinyar nan zata aikata abinda ya faru. Tana ta kawo min hujjoji masu karfi, Bros yace "To ina yarinyar yanzu? Tana gidan su. Halifa ya amsa tare da girgiza kai, ya furzar da huci, ya ci gaba da fadin ban so ta tafi ba, abinda ya bashi haushi ke nan na kyaleta ya kamata ta min uzri a lokacin domin abinda na gani ya isa hujja ko a gaban Alkali cewa ta yi laifin. Bros yace Uncle Baka da wata hujja da ka ke fadin ko a gaban Alkali ka yi mata kamun shara a ne. Ina son ka nutsu ka saurari zuciyar ka wadda ta ki amincewa da zargin da ake yi wa matar ka, kuma dorashi da akayi a Soshiyal midiya ya kamata kasan cewa akwai masu yakar ka da nufi aka yi Allah kuma shine ya san masu yin da kuma dalilin su na yi din.

Halifa ya sauke ajiyar zuciya yace yanzu ka bani shawara menene abinda zanyi? Bros yace ka fara kare matar ka daga sharrin yan Soshiyal midiya dinnan Sannan ka sameta ka bata hakuri kuma ka tashi daga gidan nan ka koma gidan ka. Halifa yace tafiyar da ta yi bayan na hanata ya bata min rai sosai har yanzu ina jin haushin abin. Bros yace ka bari nan da sati daya kowa ya huce kai da ita sai kaje ka same ta ku sasanta.

Da safe ya gama shirin fita ya dauki kayan sawar Asiya da wayarta ya je har kofar gidan ya ba wani yaro yace ya kai yace gashi a bawa Asiya. Tana kwance ta kasa karin kummalo ta rasa yadda zata yi tare damuwar ta. Bata San tana mugun son Halifa ba sai yanzu da auren su ke gargarar mutuwa. Ta tabbatar in har auren nan ya mutu ita ma mutuwa zata yi.
Sai ga yaro da kaya niki niki wai inji Halifa. Ta kalli Inna hawaye suka zubo mata tace ya tabbata Haliifa ya gama yarda cewa na ci amanar sa. Inna cike da tausayawa yar ta cikin lallashi tace. "Bana zaton hakan yana nufin ya yarda muci gaba da addu’ar neman mafita ga Allah.

Sallamar Sulaiman ce ta dakatar dani take na fara rokon Allah ya sa tare suka zo da Halifa.
Na fito daga daki ina fadin sannu da zuwa yaya Sulaiman. Ko amsawa bai yi ba ya shiga tambayar Asiya wai kuwa me kika aikata na ganki a Tiktok? Gaban Asiya ya yanke ya yi wata muguwar faduwa, Wani sabon Sharrin ya sauka kenan, ta furta tana Kallon idon Sulaiman. Ya ce kalli kiga ni yadda abin ya yadu mutane sai sharhi suke yi suna kara yada abin. Asiya ta gama kallo gaba daya zuciyar ta tana bugawa da sauri, ta mika mishi Wayar ta koma ta zauna Sulaiman ya ci gaba da fadin wallahi nasan sharri ne sai dai na yi mamaki yadda Halifa ya yarda. Asiya tace dole ya yarda ta fada masa duk yadda abin ya faru da kuma yadda ta sani.

Sulaiman ya yi ta mamaki tare da yi mata addu"a Allah ya fidda ita, sannan yace yanzu ya za ayi da mutanen Soshiyal midiya din nan? Yan jarida ma nasan in suka ji labari sai sun zo gidan nan yadda abin nan ya yadu kyau ki bar garin nan zuwa nan da kura ta lafa. Inna ta fito cikin mamaki tace "Abin har ya kai Haka? Gaskiya dai ina ganin ba sai taje wani guri ba, kawai dai baza ta fita ko ina ba." Sulaiman yace to shike nan Amma ina mai tabbatar miki cewar yanda kowa ya zama dan jarida yanzu ba sai ta fita ba, har gida zaki ga ana zuwa domin gani da kuma jin ta bakinta. Asiya tace inaga zan zauna a daki kawai. Sulaiman ya ce Allah ya kyauta ya fita.


Maganar Sulaiman. ce ta ke neman tabbata, yayan makota suka. soma shigowa daga nan sai iyayen sai kuma ga wani gida radio wai sun zo jin ta bakin Asiya. Ta kulle kanta adaki. Dole Asiya tabi duhun magriba ta tafi gidan wata yar Uwar su a Kurna ta kwana washe gari ta yi asubanci hanyar Malumfashi dangin Innar su.....



*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[8/6, 20:53] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w

Kwatsam Baba Tabawa ta ga Asiya Baba Tabawa Kanwar mahaifiyar Innar su Asiya ce, itace autar su. Itace ta rike Inna har ta yi aure. Ta jima a Kano lokacin rasuwa da bikin Asiya. Taji mamakin ganin Asiya afujajan ta tabbatar ba lafiya ba. Asiya kam bata fada mata komai ba, sai kuka data ishe ta da shi har zuwa washegari da Inna ta iso ita ta sanar da Baba tabawa komai, ta zowa da Asiya kayanta da wayar ta. Tana hawa Tiktok ta ga har yanzu video dinsu ke tashe dan har wasu sun kafe hoton ta sun hada wata murya tana kuka tana fadin ta yi nadamar yin soyayya da wani bayan ga mijina Asiya ta saka kuka wannan wane irin sharri ne me ta yi wa wani har haka. Ta kashe wayar ta maida ita can kasan kayanta.

Washegari sai Inna ta hada yan komaatsanta ta koma Kano.
Halifa bai san illar yada wannan Video ba sai da yaga yan jarida sun same shi har shagon sa a kasuwa wai suna son su samu labari game da abinda ya faru ga abokai da yan kasuwar su zancen yana ta yawo. Har ya soma tunanin kowa ma shi yake kallo ana ta nuna shi, Hakan ya tilasta masa zaman gida. Bros ya same shi kwance a sabon gidan shi kamar yadda suka yi zai same shi.

Yace Bros Ina ganin zan Dan motsa ko zan samu nutsuwa. Bros ya dube shi zaka motsa zuwa ina? " Ya tambayi Halifa cike da mamaki domin ya san shi mutum ne mai nacin gida. Zan tafi China gurin harkokin kasuwanci na, daga can in wuce Saudiyya inyi Umra, zan dawo lokacin abubuwa sun lafa, ina son ka zama shaida bana zargin Asiya kuma aurena yana nan dana ne a cikin ta., ya zama dole ne in bata rata komai ya lafa ita ma ta huce tukunna.
Bros yace to amma ko zaka bata rata kar ka wofintar da ita, ka kira ta ka sanar mata cewa za ka yi tafiya dan kar ta dauka cewa kaima kana zarginta.

Halifa ya numfasa, Na kira wayarta tun jiya amma a kashe kuma ta tafi gida bayan na hana ta fita kawai sai naga kamar ta soma raina ni, dole ina bukatar uzri ya yin da naga kato ya fito daga dakina. I zuwa yanzu wallahi na gane akwai mai bina da sharri kuma zan kai karansa gurin Allah in naje Umra din nan.
..

Ya sani ina ta zargin kowa. Bros yace To nidai addu a zan taya ka Allah ya bayyana maka gaskiya ka ganta da idon ka, amma ko waye zai zama na kusa da Kai ne wanda baza ka taba kawo shi ba. Halifa ya numfasa sannan yace Allah ya fishi.

Sai ranar da zai tafi Abuja dan ta can zai tashi sannan ya sanar da Anty ta yi mamaki sosai wai yau Halifa ne ya ke boye mata abubuwa, sannan ta kasa fahimtar me yake nufi da matar sa da bai sake ta ba. Tace "Wai Halifa naga duk ka canza min tun da wannan masifun suke faruwa kai ni wannan auran ma gara dai ya kare kaima ka huta." Yace Anty Asiya fa har yanzu matata ce, Na yi tambaya cikin ta nawa ne ko da ta aikata abinda ake zarginta da shi shari'a ta bani ɗan balle zuciya ta taki sam ta amince cewa ta aikata laifin, kuma dorawa da akayi a shoshiyal midiya shine ya sa na gane cewa tabbas wanda ya so ya hanani haihuwa ta hanyar saka mata abin tsarin iyali shine dai ya bata guba dan ta mutu kar in haihu kuma dai shine ya shigar min daki dan ya yi mata sharri zanje na roko Allah ya nuna min wannan babban makiyin nawa ko da a mafarki ne.

Anty ta girgiza da jin kalaman bakin Halifa kamar ya ganeta kuma kamar bai gane ba. Sai ta wayance da fadin "Gaskiya Allah dai ya sa mu gano ko waye in har ta tabbata abinda ka ke zargi haka to kuwa sai na yi shari' a da ko waye. Halifa yace Anty kar ki daga hankali Allah baya zalinci za ayi walkiya abinda ke boye zai bayyana. Anty ta sake zare ido kamar fa ya gane. Halifa dai ya koma ya ci gaba da shirin sa.

Yaje har gidan su Asiya ya samu Inna bata nan haka ma Asiya. Maman Annur ta je aikin gidan aikin ta, sai Abba ya fada masa Inna tana kauye.

Ya bashi sako cewa Asiya ta kunna wayar ta, kuma ya fada mata ya yi tafiya.
Bilkisu ta yi farin ciki da ganin Videon su Halifa kuma tana cikin wadanda suka kara yada abin da yin sharhi sannan tana ganin wannan. wata dama ce da zata samu shiga dan tasan kowane namiji dole ya saki wannan matar. Ita kuma lokacin ta zai fara. Saidai duk kira da sakon jaje da ta ke yi Halifa bai daga ba kuma bai nuna mata cewar ya ga sakonta ba. Dan haka ta soma fadada tunanin ta dan samu dama ta biyu.


A kauye Asiya ta kasa ci bare sha ga laulayi ga damuwa haka Baba Tabawa ta yi ta kokari gurin tausarta da kuma sama mata yan jike jike na gargajiya. Ta san zata iya jin saukin jikinta amma bazata iya jin saukin mugun raunin dake zuciyarta na soyayyar Halifa ba.. Sai a yanzu ta sake tabbatar da tana yi masa wani mugun so kuma makaho domin ta daina hango laifin sa a duk wadannan matsalolin ta fara dora alhakin a kanta, me yasa bata rufe dakinta taba har sai an kwankwasa kafin a shiga? Me yasa da Halifa yace karta tafi ta ki sauraron shi.

Gaskiya ita kam in har taji sauki zata koma gurin mijin ta wanda take bacci a kafadarsa wanda yake fada mata dadadan kalamai a kowane lokaci wanda ya maida ita macen da zata

Please Login or Register in order to submit comment