Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bukatar ta ba, gashi ya amshe mata kudi. Shine ya ce gobe ta dawo.
Wani Apple ya bata yace matsawar ta ci shi to saidai buzunta. Anty ta rasa yadda zata ba wa Asiya Apple. Sai ka wai ta dakko ta Bawa Nur da Nihal tace ga shi maza ku ruga ku kaiwa Antyn ku, kuce Babanku ne ya kawo.

Har ga Allah Asiya ta dauka Babansu ne ya kawo dan haka tuni yawunta ya tsine, ta gatsa hakori tana fadin gashi da zaki ta sake gatsa tana ci gaba da fadin shi Babanku din ya tafi ko yana ciki? Nur tace ya tafi. Nihal tace "Ke Nur sannu da karya, Dady bai zoba yau dinnan." Da sauri Asiya ta furzar da Apple din tare da kokarin kakaro na bakinta.
Su Nihal suka shiga yi mata sannu. Ta soma karanto addu'o'i domin ta gama gano gadar zare Anty ta ƙulla mata kuma ta fada. Da sauri ta dafa cikin ta ta ce Allah ka tsare min wannan kyautar da ka bani, Allah kar ka bar wani ya cutar da abinda ke cikina.

Ta soma jin yanayi Na tashin zuciya da jiri tana daga zaune ta dauki wayar ta da sauri ta danna kiran Halifa, sai a kira na biyu sannan ya daga lokacin muryarta ta fara sarkewa, tace ka zo maza ka kaini Asibiti na ci wani abu ahhh...maganar ta sarke Wayar ta fadi. Ya firgita ainun ya baro kasuwa afujajan tun a hanya ya kira Anty wadda su Nihal suka zo suna fada mata cewa Antyn Uncle ta fadi. Sai taje dakin ta dauke Apple din ta kutsiri mai kyau daidai yadda Asiya ta gutsira ta aje shi inda ta dauki wancan. Ta fice ta bar gidan dan haka Halifa yana kiran ta yace Anty ki duba Asiya bata da lafiya ki yi mata wani Abu kafin in dawo.

Tace "Subhanallah bana gida naje Ƴankaba amma yanzu zan nufi gidan.

Halifa ya samu Asiya tayi amai ga kumfa kuma ta suma ya sunkuceta zuwa Asibiti da gaggawa. likitoci suka hau kanta. Anyi nasarar shawo kan gubar bata gauraye jikin ta ba, sun gano guba taci mai tsananin haɗari wai dan ma bata ci da yawa ba, kuma tayi amai bayan taci din. Halifa ya girgiza kwarai da jin cewa Asiya ta ci guba to waye kenan ya bata guba, a sukwane ya koma gida ya ga Apple din da aka gatsa da kuma wani karami wanda ta balla ta to far da shi ya koma Asibitin ya kaiwa likitan kamar yadda likitan ya bukaci abinda taci a lokacin dan su gwada su gane wace guba ce a cikin nau in gubar da ake da su Dan su san maganin da za su bata ga ciki.

Anty ta shigo tana ganin Halifa agigice tace ina Asiya. Ta so ace cewa zai yi ta cika, sai taji yace tana ciki. Ya tsare Anty da ido Anty waye ya ba Asiya guba.? Ta zabura "Guba kuma Halifa ina za asamu guba?"

To waye ya bata Apple? Tace "Wai kana nufin Apple din dana raba musu aka kai mata nata shine aka samu mai guba? Ya sunkuyar da kai, yana jin zargin Anty a zuciyar sa. Amma wani sashen na zuciyar yana hanashi da cewa Sam Anty bazata yi haka ba.
Ya dago ya dube ta. Ina aka samo Apple? Ji tayi kamar yana tuhumarta kamar yana zarginta. Ta fashe da kuka "Halifa kar dai zargina ka ke yi? Na siyo ne a Unguwa na zo na raba musu. Yace ba shakka sai ya fito wanda duk ya yi yunkurin kashe min mata da yata. Anty tace ni da kai zan kira masa hukuma zo muje in kai ka gurin da na siya. Likitan ya katse su da cewa zaka iya shiga ta farka.
Anty ta ruga tana fadin Allah ka shiga lamarin wannan yarinya. Halifa ya tsaya gaban gado yana kallo Asiya wadda ta kara ware ido tana Kallon Halifa take ta tuna ashe fa ta ci Apple nan take komai ya dawo mata a kai, ta kalli Anty wadda take fadin Allah mun gode maka sannu Asiya. Sai kawai ta ji murmushi ya sauka akan fuskar ta tare da fadin Allah na gode maka da ka sake bani dama ta rayuwa ina me jaddadq imani na agareka ya Ubangijin Musa da Isa ya Ubangijin Sayyadina Muhammad Sallah akai wasallam. Halifa ya matsa kusa ya kara kunne da baya jin me Asiya take fada, ya dai ga ta kafe Anty da ido, zuciyar shi ta darsa cewa kodai Anty tana da hannu a cikin lamarin. Yace me kike fada Asiya? Ta kalli fuskar Anty wadda ta gama tsorata tana fadin me take cewa ne Halifa.

A zuciyar Asiya tace, Anty karki damu ba wanda zan fadawa abinda ki ke yi, bazan hada ki da Halifa ba, amma zai ci gaba da kai wa Allah kara, shine zai tsaya mana.
Muryar Halifa ta katse ta. "Asiya me kike fada? Naga kina murmushi." Can kasa muryarta tace ina son in karfafawa Anty zuciya ne naga ta tashi hankalin ta. Ka fada mata karta da mu in Allah ya yarda tunda Allah yasa na farka to zan tashi. Yace "Sannu Asiya zan fada mata amma waye wanda ya baki Apple mai guba?. Ka bari in samu kwarin jiki sai a yi magana. Yace shike nan. Anty wadda ke a firgice ta tsaya a gefe gaba daya ta sadakar Asiya tana zayya ne mishi abinda ya faru ne, tunda ta kasa kunne amma ta kasa jin abinda suke tattaunawa kasancewar muryar ta ta yi kasa.

Daya daga cikin likitocin ya shigo yace "Kayi hakuri fa, kar ku sakata magana da yawa domin Allah ne yasa ta tashi mu kammu mun kasa gane ko wace nau in guba aka bata amma zamu tura Asibitin Aminu Kano. Babban likita zai yi maka bayani. Sannan bisa shawara ka sanar da Yan sanda dan su yi bincike akan lamarin nan. Anty dai ta kasa magana tsabar fargaba. Halifa yace gaskiya dole muje gaban Hukuma gaba daya na kasa gane ma al'amarin Ya kalli Anty. Duk yadda aka kayi wanda ya turo aka sa wa yarinyar nan abin hana daukar ciki, shine dai ya sa aka zo aka bata guba. kuma wallahi na jikina ne. Har lokacin Anty ta kasa magana. Sai da yace Anty tace ki kwantar da hankalin ki tunda Allah ya sa ta farka zata mike. Anty tace "lnsha Allah ta matsa kusa da gadon tace. Sannu Asiya." Asiya ta saki murmushi, gaban Anty ya fadi ta rasa murmushi me Asiya ke yi. Ta ɗan ja baya tana fadin Allah dai ya baki lafiya.

Babban likita ya kira Halifa ofishin sa, yadda wannan likita ya shigo yana bayani haka ya fada masa. Ya kara da cewa a jikin guntun muka samu gubar an canza ainihin Apple din dan kar a gane Allah ne ya sa ka dakko guntun dan haka wannan matsalar tana bukatar jami an tsaro ko da na sirri ne dan su bincika su gano ina ne matsalar take.
Halifa ya ce babu damuwa insha Allah da mun bar nan zanje na sanar da su. Halifa yace zaije ya sanar da inna dan ya taho da Sadiya ta zauna da ita. Sai Asiya ta rike masa hannu tace karkaje ka kyale su in Innarmu tana da hawan jini zata damu ko na fito dan Allah kar ka fada musu, ni da zaka yarda daka rufe maganar domin kowa ya ji zai zargi yan gidan. Halifa ya ce To amma kuma sai in zura idanu a kashe min ke da dana, me yin abin nan fa bai fara Dan ya daina ba. " Asiya tace kawai kace wa Anty ko ita ko Hafsa nace wa, ni ya zo ya zauna da ni.
Cikin kwana biyu Asiya ta samu sauki ciki kuma yana nan babu abinda ya shafe shi, Hafsa ce ta zauna da Asiya likita ya jaddada wa Halifa lallai gubar mai tsanani ce badan taimakon Allah ba minti biyar Asiya baza ta kara ba a Duniya Dan haka ya hana ta cin kowane abu daga hannun kowaye, domin gudun kar a sake samun matsala.

Suka dawo gida Halifa yana cike da zarge-zarge a zuciyar sa. Suna kwance ya kama hannun Asiya wadda har ta soma bacci ta bude ido tace Yaya kana son wani abu? Yace Yace magana zamuyi Asiya ina cike da tsoro ne kar in zargi wanda bai kamata ba, Dadyn gidan nan na ji ina zargi kuma na kasa goge zargin. ". A uzubillahi Mina shaidanirrajim gaskiya kar ka dauki alhakin sa, me zai sa ka zarge shi? "Shine ya hanani in sanar da jami an tsaro kamar yana tsoron asiri ya tonu" ya faɗi mata dalilin zargin.

Asiya ta fada masa yadda abin ya faru sai ta kara da cewa ina sunan Dadi zai fito a nan? Yace kenan Bros ne? Asiya tace gaskiya bashi ya kawo Apple ba, Anty ta siyo kuma ina zargin wanda ya kawo Apple dinnan bayan na shiga wanka ya zo ya canza. Dan haka kabar zargin kowa kawai mu kyalle koma waye da Allah yake fada bada mu ba. Halifa ya rungumo Asiya yace yanzu ji nake kamar ke kadai na yarda da ke duk Duniya wallahi Asiya kowama zarginsa nake har Anty. Sai lokacin na yi magana. Ka yi hakuri insha Allah ba wani na jikinka insha Allah.
Haka dai suka ci gaba da rainon ciki Halifa ya hana Asiya cin duk wani abu da ya fito daga hannun kowa, kuma ya kasa ya tsare da adduo'i Baffan ya basu ruwan addu a na neman tsari ya zama shine ruwan shanta. Duk inda zata Halifa ke kaita Asibiti kuwa sai ya jirata. Wani lokacin yace kar ta yi girki ya dauke ta su tafi gidan cin abinci. In gurin su Inna ne sai ya kaita in ya taso kasuwa ya jibgo tsaraba ya kai musu.
Anty ta na cike da tashin hankali amma dole ta lafa tukunna tunda ta samu Halifa ya hakura da kiran Hukuma.

Cikin bacci Asiya taji hayaniya; a tsakar gida amma sai bata fito ba, dan ta saba tunda bata zuwa Kallon fada. Kamar saukar aradu Asiya taji muryar Halifa a fusace, yace, Asiya!!
Ta ta shi da sauri tana fadin lafiya? Yace Dan Allah malama ya kike yi kamar baki san komai ba!! Mamaki ya cika ta, ta sakko a gigice ta bi bayan sa zugwi,har tsakar gida. Wani matashi ta gani yasha duka yana durkushe jini na zuba. Ga su Anty da su Hafsa harda da wasu maza wadanda ta ke tunanin cewa maƙota ne...



*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[7/29, 21:25] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w

Ga zaton ta barawo aka kama, ta dubi Halifa ta ce a ina ya yi sata? Kafin Halifa ya bata amsa sai taji barawo na cewa Dan Allah ku yi hakuri wallahi sai da nace wa Asi baby kawai ta zo inda muka saba haduwa gidan abokina wanda ya rabu da matarsa can take zuwa idan Halifa ya tafi kasuwa, to da yake ina zuwa wasu lokutan a nan idan ya fita yauma wallahi na musa amma tace yanayin jikinta ya sa ta kasa...... Halifa ya sa kafa ya tokari cikin sa, sai da ya yi kara sannan jini ta hanci ta baki aka rike Halifa yana fizgewa akan cewa a sake shi sai ya kashe shi. Sai lokacin Asiya ta fahimci sharrin da aka yi mata ta daga ido ta kalli Anty sai ta saki wani murmushi irin na takaici. Tace tanan aka sake bullo min? Ta je gaban mutumin ta kalle shi. Ina son ka fadi tsakanin ka da Allah ka taba ganina? Ya fashe da kuka tare da fadin Asiya kalli ki gani kefa ki ka ce inzo gidan ki ke kika ce mijin ya tafi kasuwa amma shine kike alaye kamar baki san komai ba. Zufa ta karyo wa Asiya lallai sun tsara abin su. Ta kalli Halifa Dan Allah Yaya kar ka yarda da shi wallahi ban san shiba.

Anty tace amma wannan yazo gidan nan ba so daya ba akwai ranar da na ta tambaye shi ya ce min yayanku ne, to amma ganin yadda in ya fito yake sanda shiyasa na kasa yarda da shi. Halifa wanda takaici ya hana shi magana ya fidda hannu ya wanka wa Asiya mari yace kinsan tin yaushe nake a gidan nan tun ina fita kasuwa Anty ta kira ni tace ga wani ya zo tana ganin shi yana yawan zuwa, har nace kila Dan Uwa ku ne sai kuma na kasa nutsuwa kasancewar yadda mata suka koma a wanna zamanin. Nayi awa daya ina jiran fitowar shi sannan ya fito daga dakin mu dakin auren mu Asiya yana gyara wando ya dakko takalmanshi a inda ya boye ya saka ina Kallon shi ba zan iya barin shi ya fita ba, ni ne nayi masa wannan dukan. Sai Halifa ya fashe da kuka. Asiya cikin firgici da tashin hankali, ta kama hannun shi tace "Yaya kar ka yarda wallahi wannan shiryayyen al amari ne ka yi tunani sosai wallahi ni bacci nake ina kwance a dakina wannan hayaniyar ce ta farkar da ni. Halifa ya hankade ta da karfi ta fadi, yace ki daina taba ni hakikar ke abar kyamace,kin bani mamaki. Zafin maganganun Halifa sun fi mata zafin faduwar kuma ta tabbatar Allah ne kawai zai wanke ta. Sai lokacin ta soma kuka tana furta Allahumma ajirni fimusibati. Ta mike domin bata da sauran wani abu da zata fadawa mijin nata giyar kishi da bakin cikin abinda ya gani ke dibar sa, ta yi masa uzri a yanzu tasan lokacin yi nadamar hakan zai zo a gaba. Bazata yanke hukunci cikin fushi ba, amma tasan auren ta ya gama lalacewa.

Ta mike da nufin ta tafi dakin ta ta saurari hukuncin Ubangiji sai taji ana ku rike shi ta bishi da kallo ya kama bishiya ya haye katanga ya dira ta baya wanda kafin a zagaya ta tabbata ya gudu.
Ta zauna akan kujera ta fashe da sabon kuka. Tana fadin Allah yau kuma da wannan na wayi gari ya Allah! Allah ka kubutar dani kamar yadda ka kubutar da Annabi Yusuf daga khaidin mata. Allah ka wanke ni kamar yadda ka wanke Uwar muminai Nana Aisha daga sharrin masu sharri. Alwala ta yi da ta samu sanyi a zuciyar ta. Ina ma ace mafarki ne.

A tsakar gida kuwa kwarto ya gudu Halifa yaji takaicin haka domin ya so yasa a daure masa shi. Ya shiga dakin a fusace Asiya wadda ta gama sarewa ta dube shi. Yace "Wai Asiya in tambaye ki, dame na rage ki har ki ke kula wannan kazamin daga gani ko sana'a bashi da ita. Ko bana iya gamsar da ke a shimfida ne? Asiya sai Kallon shi take ba shakka ya gama yarda cewa ta aikata laifin.
Ta mike ta shiga daki ta gama amincewa auren su ya kare ta sauke akwati tana duba kayan da zata dauka a kayanta na gida dai kala daya ne wata doguwar rigar atamfa Dan haka ta ciro ta da wani hijabbinta na idin da akayi kafin auren su. Ya shigo dakin lokacin ta gama sakawa ta duba jakar ta ta dauki dan kudin ta wanda yakan bata. Ya ce ina zaki ko binshi za kiyi? Ta dube shi cikin wani yanayi wanda bazata iya fassara shi ba. Duk abinda aka yi ba sukai wannan kalmar da ya fada mata yin daci a zuciyar ta ba. Hawaye suka kwaranyo daga Idanuwanta. Cikin rawar murya tace "Ka yi duk zargin da zaka yi bazan hana ka ba. Gaskiyar ita ce, ban aikata komai ba, banda masaniya akan komai, sannan yanzu kuma gidan mu zanje. Zaki je ki tona wannan maganar ta yi ta yawo cikin mutane? Abinda ya sa ban samu ba koda wancan yaron ya gudu bana son in kai shi gaba maganar ta zama abin tattaunawa a satin nan, can kuma abin ya koma Soshiyal midiya. Asiya tace ni ba zan damu ba ko waye ma zaiji ya ji kuma ba zan hana shi yarda ba tunda kaima ka yarda. Kuskuren da nayi na dauka cewa zaka bani kariya a matsayin ka na mijina ashe nayi kuskure. Ta fito fallo ya biyota ban fa baki izinin fita ba. " Halifa bana bukatar izini domin aure da zargi basa haduwa." To kin fi son kije ki tada hankalin Inna gata da hawan jini? Asiya tace bari kaji Inna tafi kowa sani na, ko a mafarki bazata taba yarda da wannan wasan kwaikwayon ba.

Ta kama kofa ta bude yace Cikina kar kije min dashi ko ina. Anty dake bakin kofa ta a she. Ta ce ta ina ya zama cikin ka, kana jin me cikin ya fada? Ka barta taje gida tunda tana gaddama cewar bata aikata ba sai ka bincika ka samu Tabbaci. Halifa bai ce kala ba har Asiya ta fice.

Shima ya rufe dakin ya fice. A baya yake bin Napep din da ta hau har Unguwar su.
Asiya ta shiga gida Inna tana kwance Abba yana girki Maman Annur taje gidan aiki. Inna ta tashi zaune tana fadin Asiya ce yau da wuri haka? Asiya tace inna ai ba zuwan dadi bane. Nan ta kwashe komai ta sanar da ita. Inna ta shiga salati da sallallami tace yau kuma da haka na wayi gari. Allah ka fidda wannan yarinyar sai kuma ta shiga lallashin Asiya tare da bata magana. Inna dai ta boye wa Asiya damuwar ta ne kawai amma fa ta shiga tashin hankali domin duk yadda Asiya take Kallon abin ya fi haka, ga shi su ba karfi ba ta yi imani Asiya bazata taba aikata abinda aka danganta ta dashi ba.

Da dare Halifa yana ta kai kawo daga falo zuwa daki yana auna abin da ya faru wata zuciyar tace kai. me yasa baka zo ka shigo dakin ba a lokacin? Ya tuna yadda Anty ta rike shi tana karkaje kar ayi mugun abu, zaka yi mugun gani. To amma gashi yana kokwanto kodai sharri ne aka yi mata masu bata guba din nan. Ya kamata ya fahimci cewa lallai akwai wani abu. Ya fita zuwa sasan Anty tana waya da ƙawarta Wai ta kira tana cewa ta ga abinda ya faru a gidan an dora a tiktok. Anty tana cewa wallahi kuwa nima dazu Hafsa ke nuna min ko suwaye suka dauka suka dora ga shinan shi kwarton an masa duka ita kuma Asiya tana ta kuka, aiko ta sha zagi. Halifa yace Anty me aka dora a Tiktok? Matar tawa aka dora? Waye yake da tabbci ko shedar cewa zina ake aikatawa adakin? Waye ya yi musu kamu irin Na shari 'a?
Anty ta juyo da sauri cike da mamaki ta kalli Halifa tana murna ta zare masa yarinyar daga zuciya yanzu Sai batun zubda ciki amma shine zai mata tsalle? Ta mike a fusace " Halifa idan har na isa da kai wallahi sai ka bar yarinyar nan. Wane irin asiri ta yi maka haka wallahi ko waye ya tsaya maka sai ka barta ba dai a zuri a taba. Halifa yace Anty gaskiyar magana ina son mata ta kuma zuciyata ta ki amincewa da cewar Asiya ta aikata wannan abin in halinta ne da ta yi kafin ta zo gidana amma yarinyar nan a budurwa na same ta, ni ne mutum na farko da na fara kusantar ta. Bazan manta hakan ba. Dan haka saina bincika sosai kuma duk wanda na gano da hannun shi a dauka ta a Video ya yada sai na yi shara a da shi.

Ya Juya a fusace. Baki Anty ta saki ta bishi da kallo lallai wannan sai ta yi da gaske.
Yana shiga daki ya dauki waya Sam bai damu da hawa Internet ba, amma sai ya kunna data da nufin duba Tiktok. Kiran Bros ne ya katse shi ya daga cikin sauri domin yana bukatar jin ta bakin wani. Cike da tashin hankali yace Uncle me yake faruwa ne dazu maman Nihal take nuna min Matar ka a Tiktok. " Ina zan same ka yanzu? Halifa ya tambaye shi cike da damuwa. Bros yace ina gida kuma kaga muna da tazara Amma mu hadu a zoo road yanzu." To Halifa ya furta ba tare da ya tsaya tunani ba.

Jikin motar Halifa suka jingina inda Halifa ya zayyano wa Bros komai. Ya kara da cewa kasan menene Bros sam zuciyata ta ki aminta cewa yarinyar nan zata aikata abinda ya faru. Tana ta kawo min hujjoji masu karfi, Bros yace "To ina yarinyar yanzu? Tana gidan su. Halifa ya amsa tare da girgiza kai, ya furzar da huci, ya ci gaba da fadin ban so ta tafi ba, abinda ya bashi haushi ke nan na kyaleta ya kamata ta min uzri a lokacin domin abinda na gani ya isa hujja ko a gaban Alkali cewa ta yi laifin. Bros yace Uncle Baka da wata hujja da ka ke fadin ko a gaban Alkali ka yi mata kamun shara a ne. Ina son ka nutsu ka saurari zuciyar ka wadda ta ki amincewa da zargin da ake yi wa matar ka, kuma dorashi da akayi a Soshiyal midiya ya kamata kasan cewa akwai masu yakar ka da nufi aka yi Allah kuma shine ya san masu yin da kuma dalilin su na yi din.

Halifa ya sauke ajiyar zuciya yace yanzu ka bani shawara menene abinda zanyi? Bros yace ka fara kare matar ka daga sharrin yan Soshiyal midiya dinnan Sannan ka sameta ka bata hakuri kuma ka tashi daga gidan nan ka koma gidan ka. Halifa yace tafiyar da ta yi bayan na hanata ya bata min rai sosai har yanzu ina jin haushin abin. Bros yace ka bari nan da sati daya kowa ya huce kai da ita sai kaje ka same ta ku sasanta.

Da safe ya gama shirin fita ya dauki kayan sawar Asiya da wayarta ya je har kofar gidan ya ba wani yaro yace ya kai yace gashi a bawa Asiya. Tana kwance ta kasa karin kummalo ta rasa yadda zata yi tare damuwar ta. Bata San tana mugun son Halifa ba sai yanzu da auren su ke gargarar mutuwa. Ta tabbatar in har auren nan ya mutu ita ma mutuwa zata yi.
Sai ga yaro da kaya niki niki wai inji Halifa. Ta kalli Inna hawaye suka zubo mata tace ya tabbata Haliifa ya gama yarda cewa na ci amanar sa. Inna cike da tausayawa yar ta cikin lallashi tace. "Bana zaton hakan yana nufin ya yarda muci gaba da addu’ar neman mafita ga Allah.

Sallamar Sulaiman ce ta dakatar dani take na

Please Login or Register in order to submit comment