Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kamar anyi mata duka, ta na son tuna me ya faru amma ta kasa sai wani ciwon kai ta ke ji. Ta kalli Anty take ta tuna sun fita tare sunje gidan wata gyatuma, sun tafi wani kauye nan take komai ya dawo mata sabo. A firgice tace wa Anty me Baffa ya yi min? A tsorace Anty tace ba Baffa bane wani Dan uwan sune yanzu zamuje gidan Baffan. Asiya tace Anty kaina ciwo yake min muje gida kawai, tace ai gidan Baffan hanyar gida ne.

Asiya bata sake magana ba, amma fa tana tunanin abinda ya wanzu ita da tsohon nan ya kamata ta san waye shi kuma ya samu nasarar yin amfani da ita.? A tsorace ta shiga gidan Baffa nutsuwa da kamalarsa ya sa ta dan rage firgici ya yi mata nasiha suka tafi. A zuciyarta kuwa tana ganin ta fada fushin Allah in har wannan tsohon ya samu damar cin zarafinta.


Halifa ya fita kasuwa tun fitar su. ya yi ta kokarin kiranta amma ya kasa samu. Ji yake wata dangantaka ta shiga tsakanin su da Asiya mai karfi. Wata kimarta yake gani a yanayin da ya same ta.

Kira da sakon Bilkisu sun fara sosa masa zuciya har ma ya yanke shawarar saka ta a cikin wadan da ya toshe layin su.

Ya shigo gidan dauke da leda wadda ya siyo kayan marmari dangin kankana. Ganin ya murda kofar ta budu sai ya Tabbatar cewa sun dawo. Kwance ya sameta kan doguwa kujera tamkar wadda aka zarewa lakka. Ta jiyo fuskarta cike da tsoro ta Kalle shi ga hawaye na zuba, ganin shine sai taji wani kwari ta tashi da sauri ta rungume shi kam, tana kuka. ya matseta a jikin shi yana shafa bayan ta, yana tambayarta menene?
ga abin a ranta amma ta kasa fada masa ta kuma rasa dalilin hakan bata san ya zai amshi abin ba. Abinda ta iya fadi kawai shine bazan sake zuwa Unguwa ba. Ya zauna tana jikin shi, ya gyara mata zama a cinyar shi tamkar dai yadda zaka yi wa kara min yaro, cike da sanyi murya gami da lallashi yace "Me ya faru a unguwar." ta girgiza kai, nifa ina jin tsoro. "Na me" Ya kuma tambaya. cikin sauri. Ta girgiza kai alamun babu. Abin mamaki ta hanashi motsi ko ina, hatta salla magriba da isha i duk agida ya yi suka yi tare abinci kuwa kasa ci ta yi dan haka shima bai iya cin na kirki ba. Ya rasa dalilin faruwar duk wadannan abubuwan. Ya tofa addu'o'i a ruwa ya bata ta sha ya shafe mata jiki suka kwanta ta kudundune masa ajiki kamar yaro irin mai kiwar nan anzo cikin mutane.

A haka suka kwana da safe, yace su je su gaida Anty Ya kula kamar ta dan tsorata amma baice komai ba. Anty ta na falo zaune Halifa yace Anty lafiya kuwa yau da sassafe a falo jiya na dawo na samu wannan agigice kamar wani Abu ya sameta. Anty wadda ta yi kamar mara lafiya ta kalli Halifa ta kuma kalli Asiya, cikin tsana " Matar ka tana da matsalar aljanu ta tayar min cikin a daidaita kamar matacciya muka dawo. " Sannan ina son zan maka wata tambaya ta dan bamu guri. Asiya ta mike da sauri ta fita daga falon domin zuwa yanzu tana zargin Anty kuma tana son sani waye wanda suka je gurin shi. Kamar ta tafi sai ta dawo bakin kofa ta makale. Anty tace" Halifa yarinyar nan da nace ka kyale ta sai ta warware ashe abinda nake tunani ba haka bane, yarinyar nan ta gama lalacewa tun a waje, abin ya dame ni kwarai.

" Halifa yace kamar yaya ban fahimta ba? Tace jiya muna cikin a daidaitasahu sai muka tsaya a danja, wani yaro yana cikin dan sahunsa ya kwala mata kira Asiya gaba daya sai naga tana Kallon shi ta gigice, ta tsorata amma sai ta ki ta kula shi, sai yace ke Asiya ni zaki yarfa dan kinga kinyi aure to kije dakin Bangis ki dauki breziyar ki da fant. Tun daga jin haka shike nan na dauki salati yarinyar nan ta rikice ta gigice ta fita hayyacinta ta tada min aljanu har muka zo gida.

Halifa ya yi shiru yana mamaki tabbas ya sameta a rikice to kuma dai duk da bai san ya 'ya mace ta ke ba sai a kanta, irin wahalar da suka sha ita da shi har rauni yaji mata, shima yaji dan rauni irin kuka da neman dauki da ta yi gaskiya wadda ta taba sanin namiji hakan baza ta faru gareta ba.

Ya kalleta Anty kinsan mutane da sharri ba mamaki kazafi ne kawai, tace "To ai zaka gane hakan dan kuwa zaka sameta fanko ragowar maza. " Yace Dan Allah Anty a bar wannan maganar duk shirme ce, ya mike ni bari in tafi. Asiya ta wuce da gudu cike da mamakin wannan sharrin da Anty ta ƙaga mata bayan ta kai ta gurin wani tsoho zai yi lalata da ita, ko ma ya yi shine abinda bata sani ba har zuwa yanzu kuma shine abinda ke firgita ta, duk da ta duba jikinta babu wata alama da ke nuna an kusance ta, amma fa tana zargin kanta.


*** *** ***

Ya zuba mata ido, Anty ta jefa mishi shakku, domin nashi ganin babu wani dalilin da zai sa Anty ta yi mishi karya ko ta shirya labarin da ta bashi, tsorata da firgita da Anty ta yi magana gashi ya gani. Yace Asiya fada min jiya da su wa kuka hadu a dan sahu suka miki magana? Ta girgiza kai, ni bamu hadu da kowa ba babu wanda ya yi min magana mai kama da wannan.

Ni da muka tashi kai tsaye gidan wata dattijuwa mukaje har ta bani kudi gasu can a kan gado, sai muka je wani kauye tafiya mai nisa gidan wani tsoho yace in zauna akan buzu in rufe ido ya soma zagayani Ina ta adduo'in. Ta fashe da kuka cikin zakuwa Halifa yace ci gaba ina jinki. Ta bashi labarin abinda ta sani duka.
Halifa ya girgiza kuma ya kasa yarda da abinda Asya ta fada, kamar yadda ya kasa yarda da abinda Anty ta fada, sai dai Anty ta fi Asiya hujja tunda ga yadda ya sameta, to da labarin wa zai yarda a cikin su. Iya sanin shi da Anty mutuniyar kirkice ya zata kai amaryar sa ayi lalata da ita, ko dan ta tona mata asiri shine zata kirkiri labarin karya ta ce anyi?.

Ya zauna ya tausasa murya Asiya ki fahimta bana zargin ki domin ni a budurwa na same ki, ko kin taba zuwa dakin wani ya yaudare ki amma bai samu nasara ba shine ya ke son ya fallasaki a gaban Anty, shine ke kuma yanzu ki ka kirkiri labarin da kika bani dan ki kare kan ki.?
Asiya Ta yi shiru tana kallon shi. Yace haka ne ko? Tace " Hasashe ka yi ko tabbaci ka samu? Dan Allah inyi maka wata tambaya? Yace ina jin ki. Menene alakar labarin da ta bayar da kuma wanda na ba yar ta ina suka yi kama?" Ya danyi shiru sanan yace duka labaran suna magana ne akan ki da kuma yin amfani da ke. Ta ce "Ka wai ka dauki labarin da kake ganin shine na gaskiya a cikin guda biyun ka yarda wanda ka ke ganin shine ba na gaskiya ba.

Allah shine mafi sanin gamshashshen labari,ina ganin zaifi kyau mubar zancen a haka. Ya yi shiru cike da damuwa. Dole ya goge shakku ta hanyar bincike...


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[6/14, 21:18] Ummi Tandama😇: Gaba daya Asiya ta gama gane cewa Anty har yanzu bata sonta kuma ta shirya mata gadar zare ne domin ta hau ta fada. Sai dai shi Halifa ba zai fahimci haka ba, da alama ma bai san wacece ainihin Antyn ta shi ba. Sannan ba zai gane ta da wuri ba, domin kuwa ya yarda da ita sosai. Dole ta dage da adduo'i akan Allah ya kare ta daga sharri da kuma makircin ta.

Bros Adamu ya ɗakko maman Nihal daga Asibiti sunje awo,danja dai dai kofar famfo ta tsaida su kamar ance waiga Hafsi ta hangi motar Bros da wata mace a ciki tana shan mangwaro, kamar Maman Nihal take gani amma bata san ta da kayan jikin ta ba, suna hira suna dariya. Tana tunanin ta fita daga Dan sahun taje dan ta tabbatar da abinda idonta yake zargi sai aka basu hanya.

Da ita kadai ce ba wasu fasinjan sai ta bisu. Har tsuma take yi ta isa gida ta bawa Anty labari.

Wani abu taji tun daga yatsanta har tsakiyar kanta. Adamu tare da Matar sa wannan wane irin sabon bala'i ne!! Ta mike jiri ya debeta ta koma da sauri yaraf ta fada kan kujera. Hafsi tace "Anty kiyi a hankali fa,ba zai kashe mana ke ba." Anty ta sadda kai tana tunanin ta ina zata fara, da wancan aikin na gurin matar Halifa ya yiwu da ko shakka babu zata samu iko mai karfi wallahi da sai ta lalata rayuwar matar nan,.

Ta Mike. Ko shakka banayi Maman Nihal ta shiga malamai ne ta dawo da Yayanku cikin rayuwar ta. Bazan taba kyale wannan ba. Ta soma danna waya ta kira Numbar shi daidai lokacin sun tsaya a gurin wani mai takalman yara tana zabar wa su Nihal da Nur.

Ya daga tare da fadin Anty barka da yamma. Adamu!!! Anty ta furta cikin ihu da kara ji. Cike da firgici yace na'am Anty me ya faru? Domin a duk lokacin da yaji ta ambaci sunan sa, ya tabbatar cewa wani babban bala'ine zai faru. Ubanka ne ya faru. Ta furta a fusace, me ya hada ka da Maman su Nihal? Gaban shi ya yanke ya fadi, wanene ya fada mata kenan. "Ina tambayar ka ne fa."!! Ta sake katse shi. Yace Anty mamaki nake yi kuma waye da wannan maganar ni dai ina Kaduna tun sassafe? Tace "Kana nufin ban ma san ka ba kenan, to nice da kaina na ganka ko ni da na haife ka ma bazan gane ka ba?"

Zufa ta shiga keto masa ya yin da Maman Nihal ta shiga tashin hankali. Ya daure yace Bazan taba karyata ki ba Anty amma zaki iya bincikawa ki tabbatar idan ina gari, kila wani kika gani da irin mota ta na yi miki gizo, to amma a wajen inane haka? Hafsa dake gefe tana jin su ta ce a kofar famfo a danja.
Anty ta ce. "Adanja ta kofar Famfo tunda so kake sai ka titsiye ni.. " Ya jiyo wata muryar tana fada mata Dan haka ya tabbatar ba ita bace ta ganshi ba, yanzu haka munafukar yarinyar nan ce Hafsi. Dan haka ya samu kwarin gwiwar faɗin to ni kuma me zai hada ni da kofar Famfo ko ina garin ma Anty kinsan ba hanyata bace, amma dai ki bincika din dan ki tabbatar ba na ma garin ni.
Ya jefa mata shakku dan haka sai ta dan sassauta murya tace ai dai ina son ka sani ko a mafarki na ganka kai da wannan mai kashin tsiyar mai farar kafa tauraruwa mai wutsiya sai na yi maka baki bare kuma ace a fili kaji na fada maka. " Yace To!


Da sauri ya kalli Maman Nihal ina wayar ki? Tace tana mota yace su tafi su bar batun takalma ɗin nan, a mota ya yi amfani da wayarta ya kira Halifa yace Dan Allah ko da Anty zata kira ka, ina Kaduna. Halifa yace" Yanzun kuwa ta kirani kana ina na ce mata wallahi ba sani ba, sai dai ina zaton baka gari domin hakan nake tsammani da gaske, amma me ya faru? " Bros ya bashi labarin komai. Halifa yace" Kasan Allah Ramin karya kurarrene kawai ka fito a mutum a yi wacce za ayi. " Bros yace Halifa bawai bazan iya bane muna da banbancin, kai kani ne, ni kuwa ɗa ne dole inyi taka tsantsan in ta jefeni da kalaman la ana sai in lalace. Halifa yace Allah ya kyauta sai ka yi ta addua.


Ya kira yaran shagon sa ya fada musu duk wanda ya kira ya tambaye shi ace yana Kaduna. Kiran Hafsi ya shigo wayarsa Maman Nihal ta Mika masa yana daga wa ta katse. Ya yi dariya yace kinsan me yasa na kira da wayar ki, zasu yi ta kira na wai ko zasuji tana busy sai su ce ina fadawa mutane ace bana gari. Har ta kira Uncle Halifa. Maman Nihal ta sauke ajiyar zuciya har lokacin a tsorace ta ke, tace "Baban Nihal kullum zullumina Anty ta san muna tare, shiyasa nace maka da mun hakura.

Ya kai hannu ya shafi cikinta. to da ta yaya zakiyi da wannan? Ta lumshe ido tare
da fadin"Allah gamu gare ka."

*** *** ***

Nihal ta kwankwasa kofa Asiya ta bude ta ga yarinya tsaye tace shigo ta zaunar da ita a kusa da ita tana tambayarta sunan ta. Ta ce Nihal kanwata kuma Nur.Asiya Tace ina ne gidan ku? Cike da wayo yarinyar tace nan gidan muke Bros ne fa Dadynmu."Asiya ta danyi shiru tana jin sunan Bros amma batasan shidin waye ba. Dan haka tace ya yi kyau,mamanku ma tana cikin gidan? Nihal Uwar zuba tace a a, Momin mu ai Anty ta koreta shine ta kwace mu ta kawo mu nan gidan."

Gaban Asiya ya yi mummunan faduwa Tofa! Yarinyar ta ce, Anty kullum sai muce ta kaimu gurin mamanmu amma ta ki sam sam". Cikin tausayi Asiya ta shafa mata kai, karki damu zaki ga Maman ki kinji. Nihal ta daga kai, alamun eh.

Tun bayan zuwan su gidan malamin Anty tace a daina kaiwa Asiya abincin rana da na safe, shima na daren ta ce a kai ne domin ko wani dalili zai samu na zuba mata wani maganin.

Halifa ya samu Anty da maganar rashin kai abincin, tace ita gaskiya tunda suka fita aka fadi maganar nan akan Asiya yarinyar ta fice mata a rai, dan haka su yi girkin su na dare kawai za a ba su, kuma shima ya shirya ya koma kasuwa, ranar kwanan Asiya uku a gidan. Shine da ya dawo daki ya samu Nihal a dakin. Har yanzu ya kasa natsuwa da Asiya akan abinda Anty ta fada hakan ya sa yanke ɗan dake mata, sai kawai ta dake ita ma, domin bazata yarda da irin wannan sharrin ba.

Nihal ta Kalle shi Tace Uncle Halifa kana da Number Momin mu ka kira min ita? Yace kullum sai kin tambaya bakya gajiya Nihal Number Dady ku gare ni ki bari in ya zo sai ya kira miki ita. " Tace ai shima haka yake cewa bashi da Number Momyn mu." Halifa yace to tashi kije Anty Hafsa ta shirya ki lokacin islamiya ya yi.


Bayan fitar su Asiya ta mike ta nufi cikin daki dan tana jiyo kiran sallar la asar. Halifa ya bi bayan ta da kallo wani abu ya tsirga mishi, ya so ya dake amma sai tsigar jikin shi ta kama tashi. Ya mike yana mika ya nufi cikin dakin ta aje dankwalinta a kan gado, dogon gashin ta ya zubo, ta daga ido ta kalle shi ya iso daf da ita ya tsaya. Ya kai hannu ya shafa gashin sai kuma ya janyo ta zuwa jikin shi, ta tuna wuyar da tasha ranar tace dan Allah Yaya Halifa karka sake da zafi bazan iya ba. , cike da shagwaba ta yi maganar. Yace a hankali zan miki ai na yau bazakiji zafi ba,. Tace " To ba kana jin haushi na ba." . Yace Inji wa na isa inji Haushin ki kawai duk shedan ne ya ke so ya shiga tsakaninmu. Zata sake magana ya datse mata baki da nashi sai labarin kuma ya canza.

Abinda Anty ta manta su mata da miji sai Allah, alaka ta saduwa a gurin ma aurata tana kara kusanci da shakuwa dan haka ko an shiga dole aji kunya bare sabbin ma aurata. Shi Halifa da alamu yana da karfin shi awa dan haka ko a daren ranar bai barta ba haka kuma da safe, duk ta jure musamman da ta lura da yadda tsakanin jiyan zuwa yau wani tattalin ta ya ke yi, sai ta sha alwashin in zai zo so goma a rana zata amshe shi ba tare da nuna gajiyawarta ba.
Halifa ya koma kasuwa zuciyar sa tas ga hasken angwanci duk tunanin shi yana gida, kadan kadan yake kira yaji halin da Asiya take ciki, domin ya baro mata wayar shi, da zai koma gida ya duba a shagon sa ya daukar mata waya IPhone komai ya gani na kwadayi sai ya sai mata.

*** *** ***

Wajen ƙarfe shida Asiya fesa wanka bayan ta gama girka taliyarta jolop ta ji kifi. Tana bude masa kofa ya shigo ya aje ledojin sai ya rungume ta. Tace muje ka watsa ruwa ka warware Yayana ko mai yana nan fiye da jiya. Haka tayi ta janshi har aka yi Isha I bayan ya ci taliya yana mamakin ashe ta iya girki.

Kicin ta koma ta fashe kwai guda biyu ta rumtse ido ta shanye ta zo ta dibi madararr da ya kawo musu mai sanyi ta shiga dakin tana sha. Ya na waya da wani kwastoma ya nuna mata jikinsa ta lafe a cinyar sa zuwa kirjinsa sai maganar sa ta soma canzawa yace zai kira shi da safe yanzu akwai matsalar network. Asiya ta sa masa kofin madarar a baki tana fadin nice Network din ko? Yace ""Ai ke kin fi network karfi Babyna. " Sunan ya mata dadi, ashe itama za a kirata baby kamar dai yadda take karantawa a littattafai. Gaskiya ne labarin littafin yana faruwa akan mutum......


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[6/18, 20:04] Ummi Tandama😇: A tsawon sati biyu ma"auratan sunyi kaffa kaffa da juna, sun shaku da yawa ta yadda Halifa yake ganin ba shakka ya dace da abokiyar rayuwa matsalar guda daya ce akwai wasu girke girke wadanda bata iya ba daga taliya sai wake da shinkafa sai tuwon masara bata boye ba ta sanar da shi, ta bukaci ya sai mata littafin girki yace ai yanzu ko a Soshiyal midiya zaki koyi yadda ake girke girke na zamani ya sa mata data ya bude mata kafofin sadarwa na zamani ya ce duk ta koya.


Wata safiyar Juma a taje gaida Anty da safe suna tare da Hafsi, ta gaida Anty wadda ta ke amsawa da kyar kullum cikin lissafin yadda zata bullowa wannan shegiyar yarinyar take, ta dubi Hafsi tace ina kwana? Hafsi tace "Ni bangan shi ba, kwana nan. " Asiya ta kama hanyar fita Hafsi ta ce "Dubi yarinyar nan tafa murmure Anty wai ace ubanka ya mutu amma ka manta ka zo ka yi ta shagalin ka da namiji.

Anty ta saki dariya Asiya ta fice da sauri dan bata son jin abinda Anty zata fada. Ta samu Halifa ya fito wanka ta hada masa shayi da wainar kwai da dankali. Yana karyawa suna hira, ya gama ya mike yana mika tare da fadin zan tafi kasuwa gashi bayana na ciwo zo kimin tausa. Suka shiga daki kasuwa dai ranar sai da ya yi azahar ya ci abincin rana.


Lamarin da ya sa Anty shige da fice, da dogon nazari, yadda ta san Halifa ina ka fito kasuwa ina zaka kasuwa ko ciwo Halifa ya ke yi sai ya fita kasuwa amma wai ace shine saboda wannan mokadaddiyar yarinyar wai Halifa har azahar yana gida me gareta ne da zata bashi har ya zauce irirn haka. dole taje ta yi masa magana tun goma na safe ta ke aike ana duba mata motar sa har aka yi salla bai fita ba.

Ta iso kofar dakin daidai lokacin da Asiya ta rako shi zai tafi tana fadin Dan Allah Yaya idanun ka amana ne karsu kalli kowa sai kwastoma.

Yace "Kar ki damu kanwata ai nima yanzu idanun na sun rikide sun zama irin naki, ba sa ganin Kowace mace a matsayin mace face ke,sauran mata yanzu duk Kallon maza nake musu." Yakai karshen maganar tare da kamo hancin ta cike da wasa.

Turus suka yi ganin Anty. Ta kalli Halifa cikin fuskar tausayi tare da fadin Jikin ne Halifa?" Yace jiki kuma Anty kamar yaya? Ta kalli gurin motarsa, gani nayi nafita motarka tana nan baka dauka ba har na dawo baka fita ba wanda hakan ba al adarka bace baka wasa da nema." Ya dan sosa kai, Wallahi Anty ga wadda ta cikani da hira nan. Ya nuna Asiya cike da wasa.

Asiya tace au Yaya haka ma zakace, cike da shagwaba ta kalli Anty tana fadin Wallahi Anty ba ruwa na nikam shine nan yaki tafiya.... Ke dalla yi ma mutane shiru inda zama yake a gidan ya samu abinda zai kawo ki gidan? Halifa ya kalli Asiya da sauri saboda hantarar da Anty ta yi mata. Ji ya yi har cikin zuciyar sa baiji dadi ba.

Asiya ta sunkuyar da kai ta ki dagowa Halifa ya tausasa murya yace Baby ki koma ciki kinji za mu yi waya. Ta dago kai ta dube shi cike da fuskar tausayi ta daga masa hannu tana masa bye bye ta Juya ciki da dan gudu. Ya bita da kallo ta kullo kofar.
Ya kalli Anty yace Wannan fa bai dace ba Anty, dan Allah ki kama girman ki banji dadin abinda ki ka mata ba. Anty tace "Ba shakka lallai Halifa ni kake jawa gargadi akan matar ka, har zamu fara da haka? To ina mai baka shawara ka kama kanka kaima.

Ya wuce rai bace baice komai ba. Tunda ya fita a motar ya kira Asiya ta daga tare da fadin" Baby ki yi hakuri kinji ni?" Asiya cike da shagwaba tace haba

Please Login or Register in order to submit comment