Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fada masa ko dai tabuwar hankalin da gaske ne Baffa ya ce za su je Dawanau,ya yi sauri ya amshe ruwa har tana kware wa,cikin tari tace "Yaya zan kara.' Ya bata tare da fadin To kisha a hankali.
Ta shanye ruwan tas,sannan ya zuba mata madara mai sanyi cikin kofi ta shanye sannan yace in kara miki? Ta gyada kai. alamun e,ya kuma zuba mata ta kafa kai karshe dai sai data shanye madarar da ya ke sawo wa su kwana biyu suna sha. Yace tashi kije kiyi wanka. Ta shiga bandaki yaje ya tsaya ya hada mata ruwan zafi a bahon wanka yace ta wanke jikinta sosai dan tana tsami sai ta kuma hada wani ruwan ta kara wanke wa. Ita dai kai kawai take dagawa, domin mugun ciwon kan da ke damunta yasa tana jin kan kamar ba a jikinta ba.

Ya dawo yana dubawa ko zai ga kayan da zata iya sawa,amma babu kayanta a gidan sai wadanda ba a dinka ba duk dinkakkun ya kai mata.karshe ya dakko jallabiyar sa ya tafi bandakin dan yaji shiru.
Turus ya tsaya bacci take a ruwan ta cuda jikin bata dauraye ba.A tsorace ya karasa ya girgiza ta ta bude ido luuu ta kuma lumshe su.Ya koma ya cire ya dawo daga shi sai gajeren wando,ya zage ya wanke ta tas ya dauraye ya nado abar sa a tawul.

Ya kwantar da ita ya ja bargo ya rufe ta.Ya dan rage karfin Ac, ya zauna bakin gadon yana kallonta, fargaba ya cika zuciyar shi,ya rasa wa zai kira ya ce gata nan ta zo. Daga baya kuma sai ya yanke shawarar yin shiru da bakin shi haka zai taimaka ya san wasu abubuwan dake bibiyarta.

Sai dai akwai bukatar likita.Nan take ya kira likitan da suke zuwa gurin sa ya fada masa yana da mara lafiya da yake son likitan ya taimaka ya zo ya duba masa. Likitan yace Har ya kwanta amma yana jin nauyin irin alkhairin da Halifa ya ke masa dan haka yace To ya kwatanta masa gidan zai zo.
Kusan mintuna Talatin sai ga likitan ya zo Halifa ya zura mata jallabiyar sa sannan ya shigo da likitan Gwajin farko na hawan jini ya ga ya haura dari biyu,ya tsorata sosai ya ce wannan zai iya taba mata kwakwalwa tun yaushe take fama da ciwo? Halifa yace wallahi bai sani ba jiya ta zo daga gidan su. Likitan yace To zai mata allurar bacci tare da wasu allurai ya barta ta yi baccinta sosai ko ta kai rana bata farka ba kar ya tashe ta,sai ta tashi dan kashin kanta sai su zo Asibitin. Halifa yace Ranka ya dade ka yi hakuri ko nawa ne zan biya ka dinga zuwa kana dubata a gida. "Ba damuwa in ta farka sai ka sanar dani. Likitan ya fada da sauri.Halifa ya raka shi mota tare da fadin Yallabai katuro min da account. Dr yace Ina godiya Alhaji. Dr Yana jin dadin yadda Halifa yake girmamashi. Duk da ya kula haka dabi ar shi take yana da girmama kowa.

Ya koma Shima ya kwanta ya zuba mata ido yana kallon ta bai yi wani bacciba sosai kadan kadan ya farka..

Ya dawo masallaci yana zaune a falo ya daga waya ya kira Baffa yana tambayar shi ko ya labarin jikin Asiya din yana son sanin inda magana ta kwana dan zai yi tafiya ne zuwa Dubai. Baffa yace bai sake tuntubar su ba,amma ya dan yi hakuri zuwa ta warware. Sannan yace ya daure yaje ya dubo ta. Halifa yace sai in ya dawo domin nan da awa daya jirgin su zai ta shi. Halifa ya yi haka ne dan kar ko cigiya ta biyo ta gurin Baffa ya kawo shi a ransa. Dan shine kadai ba zai iya yi wa karya ba.Ya kira Bros ya fada masa cewar ya tafi Dubai.

Inna ta samu bacci domin yau babu koke koken Asiya da alama itama ta samu bacci.Wani ikon Allah bata kula babu Asiya a gadon ba har sai da ta idar da salla ta soma hada kaya dan da wuri zasu tafi Dawanau din dan ganin likita. Taje tashin Asiya ta yi salla sai ta ga gadon babu kowa,ta daga abin rufar da sauri ta yi bandaki kafin minti goma labarin bacewar Asiya ya baza Asibitin. Aka ce taje gida ta gani ko can taje,sai kuma ga Sadiya da kokon su na kari,tace Asiya bataje ba.

Inna ta soma kuka Sadiya kuka. Likita yace shi dai tsoron shi kar ciwon ya yi karfin da zuciyarta zata dinga bata umarni mara kyau kuma ta na bi.hakan babban hadari ne in ba a kula ba sai taje ta fada wuta ko ruwa wanda zai halaka ta.

Haka suka bazama neman ta ga shi su ba waya ba bare duk inda suke zaton cewa tana can su kira su ji .
Nan fa Unguwar ta dauka Asiya ta bata a Asibiti wasu su ce ance ta haukace ne har mutane suka soma ba Inna shawara wai su bi bololi su duba.

Haka Inna suka gama yawo har sha daya na dare suka fawwala wa Allah suka dawo gida suka zauna. Sai kuma gobe su ga ta inda za su fara.

Asiya bata farka ba sai karfe biyu na rana. Halifa ya tsorata amma likitan ya ce masa babu komai da yake suna waya.

Ta yi mika da salati ta bude ido, ashe dai ba a mafarki bane gidan Halifa ta ke, ta tashi da sauri ta zauna a tsakiyar gadon. Halifa ya fita ya karbo abinci a restaurant yana shigowa ya ganta a zaune.

Da sauri ya kara so ya na fadin kin tashi babyna,baby na ya jikin naki? Asiya ta lumshe ido tana kallon abincin da ke hannun shi. Ya ce zaki ci? Ta daga kai alamun e. Ta kama abinci ta cinye a take away din ko plate bata bari an dakko ba,cikin mamaki yace ko a karo miki? Sai lokacin ta yi magana ",Na koshi. Yace Alhamdulillah tun jiya sai yanzu kika yi magana har na fara tsorata,yanzu me yake miki ciwo? Tace "Kai na ne ya ke yi kadan kadan kuma ya yi min nauyi sosai." Yace zai bari likita yana zuwa.
Kiran likitan ya katse masa magana. Ya daga yace masa ya shigo.

Likitan ya duba hawan jininta ya dan ragu akan jiya,yace Insha Allah zai sauka da sauri tunda bata kumbura ba saboda ciki hakan ba zai shafi abinda ke cikin ba.

Saidai tana bukatar a kwantar mata da hankali,duk abinda zai daga mata hankali ko ya sata tunani a yi kokarin kauce masa. Yace shi kanshi likitan da ke kula da ita bai san aikin shi ba,tana da irin wannan hawan jinin bai sha kan matsalar ba kuma zai tura su wani Asibitin. Ya bada magunguna kuma zai ci gaba da zuwa duba ta har ta warke,sannan ya sake bada shawarar kar a barta cikin hayaniya. Halifa ya kudirci ba wanda zai san inda take.


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

[10/16, 10:31] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w


Inna sun gama sarewa amma dai sun kai rahoto tare da hoton Asiya karkashin jagorancin Sulaiman.


Sulaiman sun yi magana da Halifa ta chat cewa ba a ga Asiya ba. Halifa ya nuna wa Sulaiman damuwar sa musamman saboda cikin da Asiya take dauke da shi, yace yana Dubai amma zai dawo duk da bai gama abinda ya kai shi ba sannan
Yace wa Sulaiman dan Allah ya yi iya kokari shi dan ganin an samu labarin Asiya.
Labari ya riski Anty farin ciki kamar me bata boye ba sai ma tunaninta ya tsaya akan aikin da ta sa malaman ta ne ya ci Asiya.

,. Inna ta rasa wane irin tunani zata yi ta yi kuka ta yi addu'a tace dama Asiya mutuwa ta yi ta ga gawar a gaban ta da sai ya fiye mata wannan bakin cikin.

Wasa gaske yau gashi har kwana uku,Inna ta gama debe tsammanin har wata gawa suka je suka duba da aka ce an tsinta a ruwan jima, su ka ga ba ita bace ta dawo gida ta ci gaba da addu'a amma a kasan zuciyar ta tana zargin wani abu.

Cikin kwana uku Asiya ta dan murmure ta dawo ciki hankalin ta. Halifa ya siyo mata jallabiyoyi da riga da wanduna dan ta ke sakawa. Suka fita da dare suka tafi dan a wanke mata kai. Ta yi kyau matuka sosai, ga turaruka ya saya mata tana ta kamshi, ya kai hannu ya shimfida su akan nata da ta aje a gefen ta, ya dan murza yace Asiya har yanzu ina mamakin yadda ki ka iya share ni tsawon watanni baki tunanin halin da zan shiga ba ki kusa da ni ko bayan ke kinsan mijinki bashi da juriya? Sannan wai har ki ka iya kaini kara kotu Asiya ina mamakin ki fa. Asiya tace Yaya wallahi ba ni bace itama Inna taji haushin takardar sakin da ka aiko min ne.Bai san lokacin da ya taka birki ba, tare da fadin saki? Har ya rage kaɗan wata mota ta daki bayan su.Bai damu da me mutane suke fada ba, a gurin ganin yadda ya kusan hada hatsari. Tambayar Asiya ye ke yana maimaitawa . Saki fa ki ka ce,waye ya kawo takardar? Asiya tace "Kana nufin baka aiko min da saki ba?" Yace Haba Asiya ke yanzu sai ki yarda in aka ce miki na sake ki? Asiya tace dama ni banyarda ba tun da aka kawo sakin, saki uku kuma aka ce in nemi Uban dana kai ba cikinka bane. Takai karshen maganar tana kuka. Ya gungura motar gefen titi lokacin da ya fahimci mutane sun fara ce masa bari su tura masa ita ya tare hanya,a zaton su ta lalace ne.

Asiya taci gaba da fadin "Nafadawa Inna ba kai bane baza ka sake ni ba munyi alkawarin hakan,kuma yadda nayi Imani cewa ban kawo namiji daki na ba,haka na yi Imani cewa kai ma sharri ne. Shi ne su Inna suka ce kaina ya tabu wai na haukace,Ina ji ina gani aka dora min hauka. Dole na karba domin sun fini hujja, wannan damuwar ce ta hanani bacci na kwanaki ta hana ni ci da sha,domin gara in mutu bani da wani amfani ina raye kana raye bama tare. Ban san so ba kai ka koya min,ban san namiji ba kai ka sanar da ni,kai ne ka sa nasan cewa ni din mace ce kuma mai dauke da wata daraja da ni'ima da Allah ya bani ta Yaya zan barka. Halifa ya rungumo Asiya cikin wani irin yanayi ya ce 'Muje gidan su Inna yanzu in tabbatar mata da sharri ne ake binmu da shi ba ni ne na sake ki ba, Asiya hakika lokacin da na aure ki wallahi fushin zuciya ne ba wai son zuciya bane,amma da na zauna da ke sai na gane ashe da sha awa da kyale kyale ke ɗiba na, ke nake yi wa asalin so da kauna yanzu. Dan Allah muje in fadakar da su."

Asiya ta kai hannu ta shafi kumatun Halifa Kar muje yanzu domin Inna tana da matukar sauki amma kafin ta hau dokin naki,yanzu abu daya ne zai sa Inna ta yarda, shine aje mata da hujjar cewa baka sake ni ba,abin nufi sai ka nemo wanda ya shirya sakin iya maganar fatar baki baza ta wadatar ba. Sannan zaka iya yin abu daya,ka je a zuwan ka dawo daga tafiya kuma kaji labarin ɓata na, nasan maganar saki zata ta so sai ka fada mata ba kai bane,daga nan sai ta sanar da kai wanda ya kawo takardar ta haka zaka iya binciko ko wanene.

Halifa yace Allah ya min baiwa da ya bani ke, kina da basira. Yanzu bari muje gida sai mu kara tattauna yadda zamu bullowa lamarin.

Inna ta kalli Sadiya bayan sun dawo daga dan kara zagawa neman Asiya,tace nifa jikina yana bani Asiya ko gurin mijin nan nata ta gudu, ki leka shagon Sulaiman ki ce ina nemansa. Sadlya tace "Anya kuwa Inna, nafa tambayi Yaya Sulaiman din yace min ya yi tafiya amma bari na dubo miki shi.

Bayan sun gaisa Sulaiman ya ce Inna an samu wani labari ne? Inna tace 'Ko kadan,kawai dai wani zargi na ke yi game da mijin Asiya, kamar tana gunsa bayan ya yi mata sakin nan har uku,kasan ance Allah yasa jarabtar su da son macen da suka yi wa saki uku.ko ya jarrabe su shi da ita.'

Sulaiman yace Kai Inna ina shakka,domin a sanin da na yi wa Halifa ba zai yi hakan ba,shifa ba ma ya nan yana Dubai yace min dai zai dawo saboda faruwar wannan matsalar,kuma za a ganta insha Allahu zai kokarta. Inna tace To Allah ya sa a dace,dama wannan ne dalilin kiran. Saidai ya bar kokarin shi bana so,yaje ya samu wadda ta dace dashi zamu nemota da kan mu,indai addu'ar Mahaifiya tana aiki. Sulaiman yace Inna Allah dai ya sa mu dace.

Yawan addu'a ya sa wa Inna dangana da kuma yan uwanta da suka zo jaje suka kwantar mata da hankali. Sai dai kukan zuci. Halifa yana kwance rigin gine Asiya ta tada kai da kirjin shi tana lallashin sa akan ya tashi ya tafi gidan su Inna dan ya gano mata halin da Inna ke ciki. Shi kuma yana cewa shima a yi masa alkawarin yau za a bashi hakkin shi tunda dai sauki ya samu kuma sun tambayi likita yace babu matsala za su iya yin mu amalar su ta aure.
Tace to naji amma so daya.Yace Haba baby ko ba a dade haka ba kin san dai ya yi kadan. Wayar shi da ta hau ruri ce ta hanata magana.

Yace Anty ke kira kinsan na bude wayar domin na nuna musu cewa na dawo.

Ya daga da sallama. Tace "Halifa manyan gari, duk yadda na so in yi fushi da kai bana iyawa, amma kai yanzu ka ma tare a gidan ka ni ban isa ka sanar da ni ba saboda na taɓa maka abin duniya, to ba komai Halifa zan biya ka ka rubuta ko nawane in ma bansamu ba ya zama bashi ko na mutu yarana su dauki nauyi su biya ka....Takai karshen maganar tare da fashe wa da kuka. Hankalin Halifa ya tashi yace "Anty ai kinji ke matsalar ki komai kuka dan Allah ki yi hakuri ni na yafe kayan kin fi karfin su a gurina kawai naji haushin a bin ne amma ya wuce."

Ta ce Ya kuma labarin yarinyar nan ashe ta bace ko? Halifa ya kai hannu ya shafi cikin Asiya sannan yace" Abinda ya dawo da ni kenan daga Dubai Anty ya za ace yarinya ta bata kamar wata kaza."

Anty tace ni da zaka yarda wallahi da ka share su kar ka shiga zancan nan tunda kai ba a gidan ka ta bace ba, ai danake fada maka tana da ciwon hauka ai baka yarda ba,yanzu dai gashi yar fara ta nuna.

.Halifa yace "Ta ya zan kyaleta da cikina a jikinta?"Anty dan Allah kar ki fadi wani abu da zanji babu dadi. Ta dan yi shiru sannan tace "Shike nan Halifa amma ka bi a hankali Allah ya bayyana ta,dama ni dan naga yanda yarinyar ta kawo mana kwar.... "Antyy" Ya katse ta da sauri, ya ci gaba da fadin, karki karasa wannan maganar bana bukatar ta.! Tace Na yi shiru kana sabon gidanka ne? Yace Hotel na sauka,anjima zan shiga gidana,zan shigo nan gidan ma zuwa dare ya katse wayar domin tuni idanunshi sun kada sunyi jajir.

Mai siyan akwatuna ya Isa kofar gidan Anty da babbar mota,ya shiga yana sallama. Nihal ce to sanar da Anty ta yi bako.
Gaban Anty ya fadi lokacin da ta yi ido biyu da shi. Ta daure fuska ta iso gabanshi. Lafiya malam da sasafen nan zaka diro min gida? Yace dole In diro kin ki daga min waya bayan yarjejeniyar mu ta cika shiyasa na shigo cikin biyu a yi daya a bani kudina ko kayan kudi ga mota can waje.
Anty ta ce "In kuma babu fa?" Yace dole ma akwai.

Hayaniyar su ta tada duk yan gidan. Dady ya tsaya kallon mutumin cike da takaici yace kai me ya kawo ka cikin gidan matar aure? Mutumin yace ita ta gayyato ni,ai ni na zata ma bata da miji. Dady yace "Ni ba abinda na tambaye ka kenan ba, abinda kawai nake son in sani me ya kawo ka yanzu?"

Yace kudi na ta ara akan zata saida min akwatuna, miliyan daya, daga baya tace dama na kaninta ne kuma ya kwashe kayansa, amma kudin ta ara,na fada mata sati biyu zata dora min ribar dubu dari biyu da hamsin ta yarda,gashi yanzu an kusa wata bata daga kirana,yanzu dai kudina a gurin ta miliyan daya da rabi da dubu saba'in, dan kullum kwanan Duniya kudi na karuwa suke yi. Dady ya dubi Anty rai bace, yace ki bishi waje kuje ku yi case dinku a can dan Allah. Ku fita waje! Anty Ta dubi Dady cikin wulakanci tace sai dai kai in bazaka iya ji ba ka fita domin dai gidan ba naka bane kuma bana wanin ka ba. Dady yace "Ko sarkin gori,to albishirin ki, yanzu wannan gidan mallakina ne, Halifa ya mallaka min shi ya bani takardun sa haka wanda Adamu ke ciki ya mallaka masa ya bashi takardunsa!!
Anty bata san lokacin da ta kai kasa ta zauna ba,sai da taji su Hafsa na fadin Anty kiyi a hankali.ta dafa ta. Ta kalli Dady Kasan Allah bazata sabu ba, kura da shan bugu gardi da kwashe kudi. "Kiji da ni dan Allah. "Mutumin ya katse ta,cike da bala'i tace kai bani da su bani da dalilin su ,haukatani za ku yi ? Ta fashe da wani irin kuka na tsananin takaici. Dady ya dube shi yace shigo ka duba duk abinda ya kai darajar kudin ka ka dauka amma kaima ka yi Don Allah. Ya koma ciki ya shirya zai fita lokacin suna fita da kujeru Ko kallon su bai yi ba ya wuce.

Anty ta na kwance ta sa Hafsi ta kira mata layin Yayansu ya daga Anty ta karba ta ce kazo yanzun nan ina nemanka duk inda kake ko me kake ka bari kazo.

Bros ya saki baki yana kallon Falon Anty ba komai ba kujeru bare firji ba TV Ya nufi dakin ta,turus ya yi da ya ganta a kan katifa ga shirgin kaya wandan da su ke cikin sif An tule su gefe. Cike da mamaki yace Anty lafiya?

Ta dubeshi "Wato har na yi lalacewar da zaku hada kai da Dadynku da Halifa ya baku gida ya mallaka muku amma ban sani ba, kuma ban isa ayi shawara da ni ba ko?"
Bros ya ce wallahi Halifa ne ya hana mu fada wai zai fada miki in lokacin hakan ya yi,amma ya ba Dady takardun gidan nan da ya amsa a hannun lauyoyin sa,sannan nima ya bani nawa gidan da nake ciki.Anty tace magana dai ta tabbata. Hummm lallai Halifa ya dauka da zafi daga taba kayan akwatin sa shine yake ta min irin wannan ramuwar gayyar!!
Hafsa tace "Kema Anty na fada miki fushin fari ba naki bane ki kira shi a waya kiyi masa godiya karki nuna kinji haushin komai sai kiga ya baki naki rabon ki samu ko gado ki saya." Uban gado Anty ta katse Hafsa suma ba su wahala da shi ba ya basu gidaje bare ni da nai rainon sa? Adamu yace 'Haba Anty infa ya bamu tamkar ya baki ne, ke yanzu me zakiyi da gida? Burinki bai wuce ki barma gado ba,to mun yafe karki damu, kina karkashin Dady ne,shine cinki da komai,dun radda babu Dady mu gamu zamu rike ki.....'.Kai Adamu sa idonka cikin nawa. Anty ta fadi tare da Mikewa zumbur. Kana nufin ni yanzu na tsufa bani da sauran lokacin da zanyi wata rayuwa mai dadi?In yi gayu in hau mota in fita kasashe inga gari.....


✍🏻 *HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[10/27, 09:26] Ummi Tandama😇: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ?mode=wwt


Adamu yace Haha Anty ya kamata ki daina zafafa al amura,kina dagawa kanki hankali ko masu yawo kasashen da kike magana da yawa dalili ke kai su daga kasuwanci sai ciwo masu yawan shakatawar a wannan karnin ba su da yawa. Amma in kin yadda,ki yi zamanki kiyi istigfari in Allah ya kawo hajji ko Umra sai ki je kiyi adda"a kema ki huta da damuwa.

Anty ta girgiza kai tare da fadin "Bashakka,dole ka fadi haka tunda kun rufe min alkhairin da dan uwana ya yi muku, amma ba komai. Yanzu sai ka fada min dalilin da ka daina zuwa gidan su yarinyar can." Ya dan yi jim sannan ya ce Anty In fada miki gaskiya ko kuwa in yi miki karya? Ta dube shi menene ribar karya,kawai ka fada min gaskiya. Yace kiyi hakuri Anty wallahi bana son yarinyar nan ne. "Kayi kadan ta katse shi ,ciki. daga murya ta ci gaba indai ni ce na haife ka wallahi sai ka aureta....Jiri ne ya debeta sai gata wanwar ta fadi kasa ba tare da kowa ya ankara ba.

Agigice suka kama ta suna mata sannu.Adamu yace muje Asibiti Anty ta dafe kai tana fadin kaina ciwo yake min. Aka kwashe ta zuwa Asibiti Bayan gwaji likita ya gano cewa Anty jininta ya hau dan haka ya kamata ta kwanta a Asibiti . Anty ta buga kafa tace ita fa baza ta kwanta ba, gida zata koma dan tana da abubuwa a gabanta. Hafsi tace to Anty gida kuma akan me zaki kwanta ba gado ba kujera. Sai suka ga Anty ta saka kuka.

Abinda ke bawa Adamu haushi duk wannan halin da Anty ke ciki babu wata nadama a tare da ita. Badan ta so ba ta kwanta. Adamu ne ya kira Halifa ya sanar da shi cewa Anty tana Asibiti. Sai dare yaje tare suke da Asiya sai ya barta a mota.
Ya kalli Anty duk ta rame, yace "Anty wallahi ki daina damun kanki game da wa su lamura da basu shafe ki ba. Yanzu me likitan yace? Tace "Ni kawai ka ce masa ya sallame ni zan sha magani a gida ina da sabgogi da yawa a gaba na, wannan kwanciyar zata kawo min cikas.

Wane irin sabgogi kenan kike magana? Halifa ya katse ta. Hafsi tace Uncle ko ta koma gida fa wani mutum ya zo da mota ya kwashe kayan gidan duka. ,"Kamar Yaya? Halifa ya tambaya. Kafin Hafsi ta amsa Anty ta fara wani irin nishi da kuka ,dole suka maida hankali a kanta. Kuma ta yi haka ne dan kar ta fadawa Halifa maganar.
Halifa dai ya fada wa likita lallai kar a sallameta sannan duka abinda take bukata a yi mata.

Da suka bar Asibiti kai tsaye unguwar su Asiya sukaje ya aje motar Inda ya saba ajewa sannan ya tafi gidan su ya bar Asiya amotar yace ta jira shi kar ta fito.

Ya kira Sulaiman suka tafi gurin Inna.

Tana zaune tsakar gida ta zabga tagumi

Please Login or Register in order to submit comment