Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sam bata taba zato ba. domin Malamin ta ya bata tabbacin cewa Halifa zai dawo fiye da baya kuma za su yi aure.

Sulaiman ya kira sauran abokan su ya sanar da su abinda ya faru,bajimawa suka nufo gidan su Asiya. Daf da magariba Sulaiman ya kira Halifa Dan jin ya ake ciki game da kai Amarya? Yace to shi bai yi wani shiri game da haka ba, amma yana ganin zai fi kyau a bar shi sai anyi uku. Duk da haka Sulaiman yace yana ina za su same shi, yace yana gida.
Can gidan suka same shi ya fito suka gaisa saura suka yi masa gaisuwa da murna ya amsa. Sulaiman yace na so a ce da ka yarda an kai ta yau an wuce gurin. Halifa Yace " Abarta sai anyi ukun kawai zai fi.kafin nan na gama abinda ya dan saura a gidan. Suka amince da haka.
Halifa kwance a kangadon shi, ya rasa wane tunani zai yi tsawon dare har ƙarfe uku, ya mike ya dauro alwala ya fuskaci Ubangiji. Bai tashi ba har aka soma kiran salla ya fita zuwa masallaci, ko da aka idar da salla bai fito ba sai da ya zauna ya yi karatun safe wanda suka saba yi ya gama ya dawo gida kanshi har sarawa yake, idanun sa sun yi masa nauyi, ya kwanta bacci ya tafi dashi, sha daya bugun kofa ya farkar da shi. Sai ya ji zuciyar sa ta yi masa fes ya bude Hafsi ce ta sanar da shi Anty na kira. Tare suka tafi.
Anty tace Halifa lafiya tun jiya nake neman ka. Yace "Ina gida jiya da yamma bakya nan, saboda rasuwar nan da kuma daurin auran nan shiyasa banje kasuwa baa." Ga mamakin sa sai yaji tace "To Allah ya jikan sa, ita kuma Allah ya sa matar gida ce, ga abinci can na sa a dafa anjima zamuje gaisuwa. Ya ce Anty ni gaba daya kuma abin ya dame ni, naji haushin kaina da banyi wa Bilkisu uzri ba. Tace" Halifa ka gane matar mutum kabarin sa, nima shiyasa na zubar da komai Allah ya baku zama lafiya. Yau she za a dauki amaryar ne? "Yace sai ranar uku ni yanzu zan shirya ne in tafi kasuwa. Tace" To bari in shirya mu tafi ka kaimu da abincin kuma ka kara gaisuwa ya kamata ace yau ka hakura da kasuwar kaje gidan ka yini. Yace jiya ban leka kasuwa ba shine dalilin amma ku shirya na kai ku din sai mu kara gaisawa.


Duk an watse sai wasu daga cikin dangi kadan sai makota da suka dan kara shigowa. Asiya tana zaune tana kara tun ƙur ani iya abinda ta ke iya yi kenan ta ji sanyi, sai ta jiyo ana fadin sannun ku da zuwa ku shigo. Ta baza kunne sai taji ana ayi musu shinfida a dakin Baba inda a nan take a zaune. Kanwar innarmu ta shigo tana cewa ku shigo nan, har barin jiki take yi dan ta yi musu shinfida. Hajiya Talatu ce a kan gaban shigowa dakin sannan sai Anty A gigice Asiya ta Mike tsaye.


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[5/29, 13:51] Ummi Tandama😇: Suka kalli juna da Anty, ta yi wani murmushi mai wuyar fassara ga Asiya Allahumma ajirni fi musibati Asiya ta fada a kasan zuciyar ta. Anty tace Allah Sarki baiwar Allah sannu kinji Allah ya baku hakuri ina Uwar ta ku? Asiya ta fita da sauri tana fadin Inna kije ku gaisa.
Inna ta zauna daga bakin kofa, suka gaisa. Anty tace "Allah Sarki sannu da kayan lada gaskiya wannan mutuwa ta dake ni ta fashe da kuka. Hajiya Talatu ta saki baki tana kallon al ajabi Anty tana kuka tana fatar hanci ana ta bata hakuri. Lallai akwai wani makirci Babba da ta hada.

Inna tana sharar kwalla tana fadin Kiyi hakuri muma dai hakuri muka yi. Ta ce Ina Amarya mijinta yana waje ta leka su gaisa. Nan take kanwar Innar su Harira ta ce ki saka hijabi ki fita. A soro ta tsaya ta leka, yana zaune a dakalin gidan su Sulaiman yana waya.
ta daure ta fita tana isa ya katse wayar ya kalle ta ta risina ta gaishe shi. ya amsa tare da fadin "Ya hakuri?" tace Alhamdulilah. Yace Alllah ya jikan Baba tace ameen ya rabbi. Ta ce sai anjima ta juyo ya bita da kallo cike da tausayinta. Duk ta kara ramewa dama ya lafiyar giwa. Ta koma cikin gida. Bayan tafiyar su aka yi ta maganar yadda Anty ta ci kuka Ana bata hakuri, nan aka shiga nuna wa Asiya cewa ta rike Anty ƙauna ce ya sa ta nuna kulawar ta gare su. ta yi mata biyyaya kuma ta rike ta tunda ita ce ta tamkar uwarshi kamar dai yadda ta basu labari. Asiya dai tana sauraron kowa amma zuciyarta ta kasa nutsuwa da abinda Anty ta yi, ta tuno zagi da kuma gargaɗin da ta yi mata cewar karta sake ko da wasa ta auri kaninta, ta nuna kyama da kyankyami gare su amma yanzu wai tana kukan mutuwar wanda ta ciwa zarafi. To duk da haka ta kudurce zata yi mata biyayya fiye da yadda aka fada mata..
Halifa yana kwance yana tunanin gobe za a kai Amarya duk da gida ya kammala amma ya san su Asiya ba su da abinda za su zuba a gidan dan haka dole ya yi daya cikin biyu ko dai ya sayi kaya ya zuba a gidan ko kokuma ya bata bangaren bakin gidan tunda bashi da girma abinda Allah ya hore masu sai su zuba mata a gurin. Wata zuciya tace ka zuba kaya kawai. To shi komai lissafine a gurin dan kasuwa. Ya tura oder bata karaso ba, sannan ga wasu kudade da yake jira shiru ba su shigo ba. A haka bacci ya kwasheshi.


Da safe ya shiga ya samu Anty a falo ana yi mata kitso ta can baya ya jiyo hayaniya yace lafiya? Anty tace ango da kanshi ka ke tambaya yaune taron mu na nan tunda yau za a kawo Amarya dukda dai mutuwa a ka yi ai ma Ɗan taru ko? Halifa ya yi murmushi, mata sarakan bidi a. Tacewa me kitson dan tsaya zamuyi magana ta nufi tsakargida tare da fadin Halifa ya zo su yi magana.
Ta dube shi, tace "Ka kai musu makullin gidan ne? Ya yi dan tsaki yace Ni na rasa ma ina za a kaita gidan can ya mata girma sai dai na bata gefen baki sai yanzu nake ganin gaggawa ta da tuni har za a tashi wani cikin kananan gidajan nan na Kundila ya isa a Sakata a ciki . Anty tace zo muje, suka nufi gefen shi, tace dubi dakinka sai anso a kara fenti zata yi zaman ta a ciki in ta kara wayo ta warware sai ku kama can. Ya danyi shiru baya ra ayin zama da matarsa a inda ya yi samartaka. Sai dai dole ayi hakan na wani lokaci. Ya dube ta, to Bari zan kira me fenti in zai yiwu yau din ayi a maida kayan. Anty Tace " Ba zata zo da kaya ba kenan ko yaya?" Ta tambaya cike da kwanciyar hankali. Yace To naga Babansu ya rasu kuma dama yana cikin halin jinya. Anty tace hakane to ka daure ko baka canza komi ba ka canza gado, kayan aikin kicin dai na san ko da sadakin ta zai yi mata.

*** *** ***

Kamar yadda Baban su Sulaiman ya sanar a masallacin sallar asubahi cewa dan Allah kowa ne makoci ana son ya bada gudunmawar abinda Allah ya hore masa za ayi wa yar gidan marigayin kayan daki, abin Allah sai gashi nan da nan an hada kudi masu kauri a ranar bayan gama addu a ya nufi Gwauron dutse shi da daya maƙocin na su inda ya saya mata kayan gado da kujeru katifa kadai ya saya da kudinsa. Innar su Asiya ta saka kuka dan murna ga sadakin ta ya kawo ya danka mata.

Kamar yadda Anty ta tsara hakan ne ya faru, domin da Sulaiman ya kira Halifa yace za a kawo kaya suna son makullin gida, sai yace ai gidan su za a kawo amaryar can gidan ba a gama gyara ba. Lokacin da kayan suka Iso tara da yan jere Kanwar Innar su Asiya itace Amara gashi ta kaunaci Anty tunda Antyn ta nuna kauna da tausayawa dan haka masu jere na yi tace bari taje ta gaida Hajiya mutuniyar kirki.
Gidan cike da mutane Harira kanwar Innar su Asiya ta taje gaban Anty tana mika gaisuwa Anty ta amsa tana kare mata kallo, tace inaga kuwa na san ki ok kawar mai aikin gidan su kawata ko? Harira tace "A a kanwar mahaifiyar, su amaryar. Anty ta kalli Hajiya Talatu, oyoyo sannun ku da zuwa, kai ku bata gurin zama cike da izgili take maganar, ita kuwa Harira dadi ya rufe ta abinka da mutan kauye, sai take jira a bata gurin zama. Hajiya Talatu ta kasa kunshe dariyarta sai da ta sheke da wata dariya tare da wasu ƙawayan su..Anty Umaima kanwar Anty ce itama yayar Halifa ce, sun zo ne kawai dan Halifa amma ko ziyara ta haka kawai ba su cika zuwa gidan Anty ba, yadda ta ke musu gadara akan komai. Ta kalli Harira tace " Baiwar Allah ki koma can gurin jeren naku kar yara su yi muku barna. " Harira tace za ko su iya ta juya da sauri tana cewa Anty Hajiya muna godiya. Anty ta bi bayanta da daƙuwar zagi tare da fadin to ga yan rakiya nan.


Asiya ta fito wanka aka bata sabon Kaya cikin dunkunan da Sulaiman ya yo, ta saka tana hawaye tunda akace ga motoci nan hankali ta ya tashi ta shiga kuka wiwi, Da kyar aka banbareta a jikin Inna tana cewa dan Allah ku barni sai anyi bakwai Inna tace kije gidan ki Allah ya baki sa a. Ta kalli Dakin Baban su zantukan sa suke mata yawo a kai. Inda yake cewa"Asiya bazaki yi da kinsanin yin aure da Halifa ba. Allah ne ya kawo miki shi." A haka aka sa ta a mota sai gidan miji.

Gidan babbane da bishiyoyi a yankin masu hannu da shuni, su Anty ne ke zaune a ainihin gidan ya yin da su Halifa da bros suka yi rayuwar su a gefen daukar baki duk da cewa gidan mallakinsa ne bai taba damuwa da hakan ba. Nan aka kai Asiya Falo ne da daki biyu kichin a falo sai bandaki a dakin da aka sa mata gado. Shi kuma gadon da ya siyo aka sa a ɗaya dakin.

Kamar yadda yake a al ada bayan sallar Isha abokan Halifa har da wasu daga cikin yan kasuwa suka rako shi. Asiya tana zaune ita daya a falo sanye da hijabi ta sunkuyar da kai a haka suka gaisa. Anyi nasihohi suka aje ledojin hannun su suka yi mata sallama ya tafi rakasu. Gaban Asiya ya yawaita faduwa ba wai tana tunanin ko Halifa zai nemi hakinsa ba a a, yaya ma zai karbeta.
Ya shigo da sallama ta amsa tare da bin fuskarshi da kallo ko zata fahimci wani abu. Shima ya kalleta yanayin da ya nuna bai wuce ace kamar yanda yaya zai mu amalanci kanwar sa ba, yace kina jin yunwa, ta girgiza kai alamun a a. Yace ki yi magana da baki mana. Tace "A 'a. Yace me kika ci? Tace" Ba komai bana jin yunwa ne., " Ya ce To, kije ki kwanta,ta kalleshi a wani littafin Hausa da ta karanta ance ango da Amarya suna yin wata salla dan neman samun zama lafiya. Tace" Sallar fa" Wace salla kuma ko bakiyi Isha bane? Tace "Nayi mana naji ne ance ne ana yin salla domin neman zama lafiya." Ya yi dan murmurshi. To kuma gashi ni ban iya ba, ban taba ji ba ma, amma zan tambaya. Tace ka tambaya mana yanzu ance fa a rana irin ta yau ake yi ranar da miji ya fara shiga dakin matar sa, in ya wuce ranar kamar fa baza a karba ba. Dariya ta kufcewa Halifa ya je ya kulle ƙofa. Ke dai ki kira ki tambaya a inda kika ji.
Asiya ta zuba mishi ido cikin mamaki iya gaskiyarta take magana, amma sai taga kamar baima fahimce ta ba, ko kuma auren ta bashi da wani mahimmanci ne a gunsa. Ta sa kai ta nufi dakinta ta cire hijabi jikina ta bude akwati tana duba kayan bacci. Maman Annur ce ta ce mata su zata saka duk in zata kwanta. Lokacin da suke kallon kayan lefen.

Ta saka ta je ban ɗaki ta dauro alwala, ta saba da kwanciya da alwala ta yarda sosai cewa babban tsari ne. Ta mike a kan lallausan gadon, Allah sarki ƴar tabarmarta ta yi kewar ta. Tayi juyi a fili tace Allah ka bamu ni'imar kabari. Ta tuno da mahaifinta wanda yanzu yana can kwance, Allah ya sa yana cikin dausayin Aljanna. Hawaye suka soma kwaranyo mata suna bin gefen fuskarta, kuka take a hankali har bacci ya yi gaba da ita.

Halifa ya shigo dakin, bacci take yi sosai ga iskar fanka ga ta laushin katifa ba sauro. Ya kalli hawayen da ya bushe a gefen fuskarta, sai tausayin ta ya kama shi. Karan wayar sa ya jiyo daga falo, ya tafi ya duba Anty da wannan daren ya furta a fili. Tace Ta katse shi da fadin, "Kana jina ko Halifa nace Dan Allah kar kaji wani iri akan maganar da zanyi maka. Dama zance ne karka takurawa yarinyar nan Dan Allah, ka kyaleta ta gyagije, ga mutuwa anyi mata tasamu kamar sati biyu, ni nasan abincin da za a ke bata yadda zata murje." Maganar ta zo wa Halifa a wani banbarakwai. Yace to sai da safe. Anty tace ina jin dai ka gane me nake nufi?" Yace A haba kar ki damu. Ya kashe cike da mamakin yadda Anty ta iya yi mishi wannan maganar.

Anty ta aje wayar cike da jin daɗin haƙan ta zai cimma ruwa. Saboda malamin ta ya Tabbatar mata da cewa aure ba makawa zai auri yarinyar sannan matsawar zata matsa kar ayi to zata mutu, tauraron ta yana da girma da kuma haske da yafi na shi Halifa, da tazara tsakanin su kamar kimanin Sarki ya ka sa bafaden sa, yace in son samu ne kada ta bari a samu daidai to a tsakanin su, saboda duk ranar da ya sadu da ita sai fa abinda suka gani. Cikin tashin hankali tace Malam yanzu Sai ina saka ido Kenan? Yace ko kusa, aiki za ayi amma yana da sharadi tunda har ankai ga daura aure to ki kwantar da kai ki hana a tare har zuwa daren Alhamis zan hada miki aikin da washegari juma'a zai tafka mata saki.
Kinsan masu irin wannan tauraron da su masu kudi ke hada tsafi ta hanyar dauke musu shi. Shine zaki ga anba yarinya wani abun duniya an karbe mata tauraro ta hanyar saduwa da ita akwai abinda muke sawa su kawo mana muna hada musu asiri da shi. Nima dai ladan aikina shine ku kawo min yarinyar nan zan yi amfani da taurarinta dan samun shuhura. Anty ta yi masa Alkawarin hakan. Da wannan take son hana Halifa aiwatar da komai. da iyalinsa. Ta lissafa auren da Juma a ne, sai aka daura Alhamis ta tare lahadi, zata tsaya tsayin daka dan ganin komai ya kammala.

Halifa kuwa zantukan, Anty sun tsokano mishi abinda ya sha na maganin basir da sanyi, ga hadin maza da wani abokinsa shima ya sa yake ta banka lokacin maganar su da Bilkisu da abubuwa suka cabe shine ya manta da komai, yanzu kuwa kamar ta masa allura, sai dai bisa adalci ya kamata ya kyaleta ko Don zafin mutuwa, dama ba dan ita ya sha ba. Da sassafe Anty ta kira Halifa wai sun kuwa tashi tana son ta zo su gaisa. Yace "Haba Anty zata zo. ta gaishe ki, ai ko gidan giya akwai Babba.
Tace ai bakonka Annabin ka, ni din ma sai inzo..... .


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta,alfarmar following zata ƙare a 10-june-2025, daga ranar duk wacce batayi following ba,sai dai tabi hanya ta biyu, hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank,*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[6/2, 18:43] Ummi Tandama😇: Asiya ta idar da sallah ta zauna tana adduo'in fatan Allah ya jikan Babanta, ta yi godiya da ni imar Allah a gare ta, ɗakin nan irin dai wanda take gani a fim. Insha Allah zata jure komai domin ta samu kan mijinta.


Ya shigo sanye da jallabiya ta tashi da sauri sai ya tsaya Kallon ta ya zata wani abu ta gani. Tace Ina kwana? Yace "Lafiya lau ina zaki naga kin tashi da hanzari?" Tace Aljanna. Ya dan yi dim bai fahimta ba. Tace to ance min gurinka zan samu kuma gaskiya ni dai ina son shiga. Ya yi murmushi" Allah ya baki iko.," Tace Ameen kai kuma ka bani dama ba." Na ma baki tunda na aure ki. Yanzu kiyi wanka ki canza kaya waɗanda suka miki daidai zaki sa ki fito ina jira ki a falo. Tace to mabudin Aljanna ta yanzu zan yi yadda kace. Ya fita yana mamakin Asiya to ko dai ba yarinya bace.

Ta saka riga da siket na atamfa ta yafo mayafi ta fesa turare ya kalleta shi mutum ne ma'abocin kamshi. Ya bita da kallo tace a kwai wani abu da bai yi daidai ba ? Ta tambaya cike da salo. Yace babu tashi muje ku gaisa da Anty. Gabanta ya yanke ya fadi. Tace Anty kuma, bata tafi bane? Yace ina zata? ai nan gidan take. Ta hadiye yawu ai ban sani ba. Ta fada in'ina Yace "Menene naga duk kin canza?" Ta girgiza kai, babu komai kawai dai na zata jiyan sunzo ne.


Suna kan gado ita da Hajiya Talatu suna ta zantukan su da suka saba, Hajiya Talatu tana son taji abinda Anty ke boye mata na game da canzawar ta game da Asiya. Anty ta diro da sauri, a a Halifa kune shigo kinji Asiya ta kama mata kafada Asiya ta zube da sauri tana fadin Ina kwana Anty. Lafiya lau zo nan ki zauna bakin gado mana. Asiya ta zame ta zauna kan kafet tare da fadin nan ma ya isa. Hajiya Talatu tace"jiya da aka kawo ki ba'yi irin yadda ake yi in an kawo Amarya a zo a bada amanarki ba,da kinga dangi sosai. " Asiya ta kalleta ta rasa ita kuma wannan din wacece ta kula da wani kallo da take mata irin na ke kuma ke da wa. Anty ta amshe ai ba komai, zata san kowa tunda an zama daya ki saki jikinki kinji Asiya. Ta daga kai alamun to. Anty ta ce yanzu za a kawo miki abin kari, ki zage ki ci kinji ko? Nasan har yanzu akwai damuwar rabuwa da mahaifinki, Kiyi ta masa adduo'in kin ji? Asiya tace to na gode. Halifa yace ni Bari inje inyi wanka. Asiya ta yi zarab ta mike Hajiya Talatu tace ki dan tsaya mana ana miki nasiha shi yaje ya shirya. Anty tace e dan jira kadan.

Daya fita sai Anty ta ce Asiya ina baki hakuri akan zuwa na gidanku dana ci zarafinku lokacin karya aka zo aka yi min a kanku ance ke mahaukaciya ce kina da aljanu. Ni kam ina tsoron cin amana Halifa maraya ne shiyasa. Amma kii yafe min Allah ya huci zuciyar ki, shiyasa nayi ta kuka ranar da na zo gidanku ba yadda zan nemi afuwar Babanku ya mutu shiyasa, ta sake sassauta murya cikin yanayin tausayi, dan Allah kin yafe min?

Zuciyar Asiya ta karye, tana da saurin yarda ga tausayi ba shakka Anty duk abinda ta fada gaskiya ne dan haka sai ta ji ta yarda da Anty, tace Anty ai ba wani abu ya wuce ba komai. Anty tace "Allah ya miki albarka ki rike mijinki Halifa bashi da matsala.

Hajiya Talatu ta fara kokwanto ko dai Anty har zuciyarta tana son yarinyar nan. Asiya ta kalli Anty wannan ma Antyn Halifa ce? Anty tace e amma kawata ce ba wani abu suka hada ba. Hajiya Talatu ta yatsina baki tana Kallon su. Sam bataji dadin wannan yarfin ba, Asiya ta mike tace to bari inje ko ya gama. Anty ma ta mike zaraf ta biyo ta. "Kina jina ko Asiya. Ta tsaya ta kalleta Anty ta ci gaba da magana kasa kasa, nasan kina cike da jimami na rasuwar mahaifin ki, ina so ki kwantar da hankali ki, shi kuma Halifa na san zai miki uzri ki warware. Duk da Asiya bata fahimce ta ba, sai ta gyada kai alamun eh tace yawwa to jeki maza.


Tasamu ya gama wanka yana sanye da shadda ruwan kasa ya yi kyau. Ta yi murmushi haka ka ke da kyau dama, kamar wani Ango. Ya ce "To da wanene in ba Angon ba?" Tace Gaskiya dai kai ba Ango bane. "Dalili?" Ya tambaye ta cike da wani shuki da yake ji. Tace baka ƙiyin sallar ma'aurata ba. Ya rike baki, wai ke me kike nufi ne? " Ta dube shi bana nufin komai wallahi, kawai dai ban so ka ki yarda muyi sallar ba, to kai me yasa baka zo munyi ba baka son zama lafiya din ne kokuwa dai ni ce matsayi na bai kai a yi sallar da ni ba? Ta kai karshen maganar tana dariya. Halifa ya sauke ajiyar zuciya, in an idar da sallar fa me ake yi. Ta girgiza kai bansani ba gaskiya sallar dai ka dai nasan ana yi. Ya yi murmushi ni kuma na san saura abubuwan da ake yi in kin yarda zamu yi to. " Tace Shima din ibada ne? Yace sosai kuwa har yafi salla din ma. Ta saka dariya, to azumi ne? Yace " A'a tace to ni ko wace ibada ce wannan da ba zan santa ba? Ko kuwa zikiri da salati ne? Yace ki dai yarda kawai zaki gani. " Tace to shike nan na yarda amma na so a daren farko mukayi Sallar nan.

Hafsi ta yi sallama suka amsa ta aje tiren a teburin gaban kujera. Sannan ta ce Uncle ina kwana suka gaida. Asiya ta kalleta, tace sannun ki yama ni kuwa sunan matar? Ta tambaya

Please Login or Register in order to submit comment