Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai "Dakta dama haka Na fada maka daga allurar riga kafi kuma sai ka saka mata tsarin iyali? Yace Hajiya dan Allah kiyi hakuri, ranar gida biyu zani da nan gurin ku da wani gidan wancan gidan suma ni ke duba su. Mijinta ya kira ni ya fada min inje in saka mata wannan tsinke to kuma nima ina fama da matsalar mura a ranar sai na saka mata sai da naje wancan gidan sannan na gane abinda na yi.

Halifa ya fisge wayar tare da fadin To amma kai jahilin ina ne da zaka sawa matar wani abin tsarin iyali, ina son ka sani daga yau ka daina domin sai na shigar da korafin ka a hukumar lafiya ya kamata su bincika lasisinka. Sai an dakatar da kai. Anfy ta karba tace dole kuwa mu kai kararsa. Bani wayar in kira masa yan Sanda.

Halifa yace "Anty ai wannan ba karamar matsala bace ni zai tsarawa yayan da zan haifa, ni da ubana yake da yaya sama da talatin kuma sai na gaje shi. Bazan taba kyale shi ba ko waye ma ya turo shi sai ya fada, domin yadda nake ji zan iya kashe mutum ko waye shi. Ya nufi dakin sa a fusace.

Asiya Ta kalli Anty sai tsuma take tana zufa tana fadin ina bayan ka wallahi karka yarda zan kaika har gidansa. Asiya ta girgiza kai tare da fadin Allah ya kyauta.

A ban daki ta samu Halifa ya sakarwa jikin shi shawa ko single da gajeran wando bai cire ba. Ta aje hijabin taje ta shige jikinsa ita ma da kayan jikinta. Kam ya rungume ta ruwan yana ratsa su, tsawon minti hudu sannan ta ce muje ka kwanta. Baya shige umarnin ta suka kwanta tana shafa masa baya har bacci ya dauke shi. Asiya ta zame a hankali taje kicin tana girki. Anty ta aiko wai taje.

Ta samu Anty a falo. Tace "Kije ki shirya mu tafi gurin magani ba biye tashi za ayi ba, lafiyar ki ce. da kin lalace wata zai auri" Asiya tace Anty kiyi hakuri kawai in ya huce sai ki tambaye shi, yana cike da tashin hankali. Anty ta mike tana magana cikin lallashi, ki daure muje banda shirmen ki harna mallaka ba sai ki samo ba namiji fa ba dan goyo bane dan yana nawa bazan ƙi ki ba. Asiya ta juya tare da fadin Na tuna na saka mai a wuta Anty, zan dawo.

Hankalin Anty ya gama tashi, ko da wasa ta san Halifa bazai taba yarda ya bar Asiya Zuwa gurin Malam ba. Ta kira Malam din ta sanar da shi halin da ake ciki. Yace Wannan kuma ke ta shafa ba ni ba. Anty sai kai da kawo take a falo. akwai bukatar ta samu mafita cikin gaggawa.
Halifa ya dawo sallar azahar ya ci abinci sannan ya ce zai tafi kasuwa. Asiya tace Anty tace min ko zamu je gidan magani ɗin, ni kuma dai nace insha Allah ai ciwon ya warke ko? Yace babu inda zaki je zan ma fada mata dan ta sani. Asiya ta rakashi ya tafi.

Anty ta na ganin fitarsa ta kira Malam tace "Dan Allah Malam ka zo ka yi mata wankan a gidan nan mijin ya fita baya nan sai dare zai dawo. Malam wanda ke cike da tashin hankali tun bayan da ya ji cewa a hakan ma yarinyar bazata samu ba. Sai da ya bi matakai ya bi sharudda ya yi hadaya sannan aljanun suka kawo wannan hanyar. Ko me zai faru kam dole ne yaje gidan.
Yace kin tabbatar ba wata matsala? Anty tace ba matsa ka taho kawai.

Ta kira Hafsi ta ce tattara kan ƙanannan naki da su Nihal da Nur ki kai su shoprite su hau lilo kar ku dawo sai gaf da magariba. Hafsi ta soma murna amma dai Anty da abinda ki ke kullawa, ko wata kyauta kika samu? Ta yi murmushi kawai yau naga ya dace su shakata. Nima zanyi baki ne za su yi wani aiki a gidan.

Suna tafiya ta sake kiran Malam a waya taji ko ya kusa. Yace "A kwatancen da kika bani direban yace muna gab.

Ta fito ta nufi sasansu Asiya. Tana zaune tana Kallon TV Anty ta kwankwasa kofa tare da fadin Asiya. Gaban Asiya ya yi wata mummunan faduwa bata san daliliba sai ta kama fadin La ilaha'illallahul Azimul Halim! La'ilaha'illallahu rabbul arshil Azim!! La'ilahaillallahu Rabbussamawati wa Rabbul Ardi Wa Rabbul Arshil Azim!!

Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

[7/3, 08:23] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w/9223372036854675807


Asiya ta bude Aunty ta danna kai cikin falon. Tace "Asiya Dan uwan Babanmu zai zo yanzu zan rako shi ku gaisa,ya jima bai zoba a Saudiya ya ke da zama. Asiya tace to amma da yaya ya sani ai da ya jira shi, ko kiransa za ayi?

" Ba sai an kira shi ba... Anty ta katse ta," Ki barshi kawai, ya tafi kasuwarsa shi Halifa ai suna waya. Asiya tace to Allah ya kawo shi lafiya.
Sam bata kawo komai a zuciyarta ba.

Anty Na tafiya ta ji karan mota dan haka ta daga labulen windo dan taga ko waye. Bros ne ya shigo a motarsa Abban su Nur ta koma ta ci gaba da sabgoginta. Ba jimawa sai taji kwankwasa kofa tana budewa sai taga Sadiya su maman Annur harda su Annur din ta zo. Ihun murna tayi ta dane ta. Sadiya cikin dariya tace kai Asiya Allah ya shirye ki. Suna zama ta zubo musu abinci ta hado musu shayi mai kauri, tace su sha inma basu koshi ba zata sake dafa musu wani abin. Ta kira Halifa cike da murna ta sanar dashi. Yace ta gaishe su kafin ya zo.
Sadiya tace kafin ya dawo mun gudu, ina jin nauyinsa. Asiya tace "La shi ai Yaya bashi da damuwa sam dan Allah ku jira shi.

Anty ta gimtse fuska lokacin da suka hada ido da Bros," Uban me ya zo yi yanzu. " Ta furta a zuciyar ta.
Ya zauna yana gaishe ta. Ta amsa babu walwala ya soma bata uzrinshi ga zaton sa dan bai zo kiran da tace tana yi masa ba a jiya.

"Anty Dan Allah ki min afuwa jiya baƙin mu ne na nijar nan suka kwana har goma na dare muna tare yanzu ma ba mu dade da rabuwa da su ba na yo nan.

Cike da kagara Anty tace kaje yau Nima inada uzuri gobe ma yi maganar. Ga zaton shi haushi ta ji dan haka sai ya shiga ba ta hakuri. Ta kalle shi baka gane yaren Hausa ne ko? To baƙi zanyi yanzun.... Ta katse maganar daidai lokacin da kiran ya shigo wayarta. Ta daga tana sake yi wa su Malam kwatance. Ta dube shi "Ka iya tafiya domin zanyi baki.
Ya mike yana fadin ina su Nur ne? Tace Sun tafi can gurin lilo na wasan yara. Mamaki ya cika Adamu yau Anty ce zata ce a kai su Nihal shakatawa. Ya dake tare da fadin To Allah ya dawo da su lafiya. Ni to bari in tafi. Cikin sauri tace "Kaje gobe ka dawo.

Yana fita harabar gidan motar su Malam tana tsayawa. Ya tsaya yana Kallon su Malam ya fito rike da wani abu kamar carbi amma ba irin diyan carbi bane, ya sha wata alkyabba kamar basarake. Bros ya cika da mamakin ina Anty ta samo wadannan kuma. Bros ya mika masa hannu Malam ya dafa hannun sa a kirjin sa yana fadin "Lafiya lau. Hajiyar tana ciki? " Kafin Bros ya yi magana tuni Hajiya ta bayyana tana yi wa Malam sannu da zuwa. Dan haka Bros ya yi gefen matar Uncle dan su gaisa. Anty tace bata nan dama tafiyar ka kayi.
Adamu ya zargi wani Abu tunda ya ga yadda Hajiya take gaida wannan mutum kamar wani abin bauta sai sunkuyawa take yi yaji yana zargin cewa kodai bokane dan ya yi kama da su.

Ya juya zai fi ce sai ga Sadiya da Asiya da kuma yaran za su gaida Anty. Bros ya tsaya suka gaisa sannan ya tafi. Ran Anty ya baci da ganin Sadiya dole ta kai Malam falon ta ya jira ta san yadda za ta yi ta kori bakin. Asiya bata ga fuskar Malam ba amma dai tabbas shine wannan mutumin da Anty ta kaita gurin shi, dan haka ta gigice.

A Ciki ta amsa gaisuwar Sadiya sannan tace wa Asiya ba nace bako zai zo dan ke ya gan ki matar Halifa ya yi murna shine kuma zaki gayyato wa mutane tarkace. "Asiya tace Anty yayata ce fa, Uwar mu daya Uban mu daya ai kuwa ta wuce ace tarkace. Tace to ki min rashin Kuya ina son ki sallame su yanzun nan. Asiya ta bata fuska tace Anty Yaya Halifa yace su jira shi sai dare in ya dawo. Anty tace ok kice kwadayi da maula suka zo. Sadiya ta kalli Anty cike da mamaki tace Allah ya baki hakuri bari mu tafi yanzu. Dama haka Antyn ke so shiyasa ta yi haka a gaban Sadiyar dan ta yi zuciya ta tafi. Tace dadai ya fi miki ta wuce.
Asiya tana ta kuka tana dan Allah kada ki tafi wannan mutumin boka ne zasu cutar da ni.Ta kwashe labarin baya ta fadawa Sadiya tace amma dan girman Allah kar ta fadawa Inna zata shiga tashin hankali. Sadiya tace kira Halifa ki fada masa cewa Anty tace mu tafi saboda zuwan wani bako da zai gana da ke. Asiya tace bana son yin abinda zai kawo sabani tsakanin su ina dai rokon Allah ya sa Halifa ya fahimci wacece Anty. Halifa ya yarda da yar uwarshi, zai shiga tashin hankali sosai in har ya kasance ya fahimci tana cutar da shi. Kawai ki tsaya a nan din in har kina nan wallahi baza su min komai ba.

Sadiya tace danno kiran shi kawai ki bani cikin hikima zan fada masa abinda zai taho gidan.
Sai dai cikin rashin sa a kira biyar Halifa bai daga ba. Dan haka Sadiya tace dole kam in tsaya Allah ne ma ya turo ni, domin ban tashi da niyyar zuwa gidan ki ba, kawai dazu ina dawowa daga gidan aiki sai na yanke shawarar zuwa gidan nan.
Asiya tace Allah ne ya kawo min ke..... "Asiya.! Kiran Anty ya katse mata zance. Gaban Asiya ya fadi, Ta mike tare da fadin gani Anty. Ta shigo dakin ganin Sadiya sai ta yi turus ta daure fuska. Baku tafi ba?
Sadiya tace sai mun yi magariba Halifa yace mu jira shi. Nan take Anty ta rikice ta shiga fadin "Akan me zaki ce wai sai magariba ina ce kanwar ki ce ba yarki ba? Ke wannan ba abin kunya bane? Sadiya tana da wata dabi'a sai ta yi banza da mutum dan yana magana ba lallai bane ta tanka. Dan haka ta inda Anty take shiga ba ta nan take fita ba amma Sadiya sai ta zuba wa TV ido kamar ba da ita ake ba.
Anty ta koma ta kasa shiga gurin Malam tana ta kai da kawowa a harabar gidan, ta dauki lokaci kafin ta dawo ta kira Asiya tace ta zo su gaisa da bako. Sadiya ta kalla cike da tsoro. Sadiya ta daga mata kai.

Yadda Anty ta sata a gaba ne yafi bata tsoro amma ta san Sadiya zata yi wani abu.
Wata kwarya ce a gaban shi cike da wani abu kamar tsimi yace "Zonan yata kinji ko insha Allah yau zaki rabu da duk wasu matsalolin ki. Asiya cike da tsoro tace ai bani da wata matsala anyi min magani a Asibiti. Anty ta daka mata tsawa tare da fadin" Kijini da kyau ki matsa kusa ya yi miki magani ana taimakon ki ke kina ganin kamar cutar ki ake yi. Malam yace yi mata a hankali ai bata san tana da matsalar ba.

Halifa ya kira wayar Asiya bayan ya gama da kwastomomi ya ga kira da yawa. Sadiya ce ta daga tace taje gurin Anty wai anyi wani bako za su gaisa, amma kuma duk fa naga ta tsorata. Yace "" Kamar yaya ta tsorata ki kai mata wayar please. A kulle kofar Anty Na buga ba a bude ba.. Halifa ya kasa nutsuwa. Kira uku ya yi wa wayar Anty bata daga ba.

Asiya wadda suke ta lallashinta akan ta tsaya za ayi mata magani sai kuka take ta na fadin Lahaula wa la kuwwata illa billah!!. La ila hailla anta subahanaka inni kuntu minazzalumin!!!
Malam ya mike da nufin zuba mata ruwan da kayan jikinta tunda taki yarda ta cire kayan gashi tana ta kiran Allah. Yana daukar kwaryar sai kamar an ta kade shi can gefe. Ruwan maganin ya zube kwaryar ta tarwatse.
Ya zaro ido ya kalli gurin sannan ya kalli Hajiya, wannan yarinyar tana da gaddama gashi ta korar mana Aljanin da zai yi mata wankan. Anty tace tace Na shiga uku da matsiya ciyar nan, yanzu ba wani abu da za ayi Kenan? Bai tanka ba ya nufi hanyar fita a falon Anty ta bi bayan shi tana fadin Allah ya huci zuciyar ka. Ta bude masa kofa daidai lokacin da Sadiya take sake bugawa. Anty ta dube ta tana tambayar lafiya? Sadiya tana kokarin danna kai cikin falon tana cewa ina Asiya ga wayar ta Halifa yana ta kira.
Anty ta amshi wayar ta ce kije zata zo. Ta ci gaba da bin Malam tana magana kasa kasa. Bai tanka ta ba sai da ya shiga mota ya zauna sannan ya dube ta, baki shirya ba kika kirani, tun a wancan lokacin na sanar dake ki jata a jiki amma kin ƙi, kin gama tsorata ta yaushe zata yarda. Yanzu kam bansan abin yi ba. Ya rufe gilashin motar suka fice. Sadiya ta koma da sauri ta shiga falon Anty ta samu Asiya tana ta shirbar kuka. Ta kamota cike da fargaba tana tambayar "Me suka miki?" Asiya ta mike suka fito Anty ta kalle su ta ja tsaki tace "Ke menene na rungume ta,? wani abun ne ya faru sarakan zuzuta magana. Magani za a bata kuma ta barar, shine harda wani kiran Halifa a waya to me zaku fada masa?
Ta mika musu wayar, ga wayar sai ku sanar dashi abinda kuke son ya sani. Ta wuce kamar ba wata matsala.

Sadiya ta amsa suna isa daki Halifa yana kira. Asiya. Ta daga yace Baby Wai me yake faruwa ne? Ta sai saita muryar ta ce ba Anty ta fada maka ba? Ta fadi hakan ne domin bata san me Anty tace masa ba. Yace "Ta fada min amma me yasa zakiyi haka? Ko ba kya son maganin tunda ta nuna kulawa ta karbo miki ai sai ki amsa ko da bazaki sha ba akalla dai zataji dadi. Asiya ta sauke ajiyar zuciya tace zan kiyaye gaba ka bata hakuri ban yi dan taji haushi ba, data bar gurin ne mai maganin yaga bata nan sai yace wai in cire kayan jikina ya yi min wankan magani zai cire min dattin jikina. Ita kuma Anty ta ki tsayawa in mata bayani..... What!! Ya katse ta kamar yaya ki cire ya miki wanka? Anty kuma ta kawo shi gidan? Ni tace min ruwa tofi ne ta sa aka amso miki saboda kariya shine kika zubar a gaban ta kuma kina ta kuka wai zata yi tsafi dake. Haka ne? Asiya ta danyi dim Anty bata jin tsoron Allah bare ranar mutuwarta. Amma nasan ya zan mata. Yace ki bani amsa mana. " Tace haka ne amma ni nayi kuka ne kuma na zubar da maganin ne da nazo fita. Dan yace in cire kayana ya min wanka. Anty ina son in fada mata bata saurari magana ta ba, shine yace mata wai nace za suyi tsafi da ni.

Sannan kuma dan Allah ka fada wa Anty lafiya ta kalau masu maganin nan yan iskane, inhar ba za a barni da maganar magani ba ni zan bi Maman Annur mu koma gida ni Ina jin tsoro. Ta fashe da kuka. Halifa ya yi shiru ya rasa wane tunani ma zai yi.
Amma shi kanshi yasan gaskiyar magana bai kamata Anty ta matsawa yarinyar nan tace wai lallai tana da aljanu sai ta nema mata magani ba, Sannan baya son ya yi abinda Asiya zata raina Anty yana ganin mafi dacewa kawai ya tare a gidan shi abin ya isa haka.
Cikin sarkewar murya yace Baby ki yi hakuri idan Na dawo zan yi abinda ya dace.

. Da gaske Asiya har ya dawo a tsorace take, dan haka yace ta shirya sukai maman Annur gida. Sai da yayi musu tsaraba sa anan ya kai su. Inna tana ta godiya da addu"a maman Annur tace da Asiya ta kula da kanta sosai. Asiya tace to Amma dan Allah karta fadawa Inna.
Sai da suka biya ta wani gurin shakatawa Halifa ya yi musu oder kayan kwalam suka ci suna hira. A ranar ne ya furta cewa Asiya da zu da kika ce zaki koma gida ko wallahi sai naji kamar kin ce Duniya zata tashi, kamar yadda Na sha alwashi zan yi maganin matsalolin ita Anty bata san halin wasu masu magani ba, sam babu Allah a ransu. Hukuncin da na yanke shine kawai zamu koma gidana shike nan komai ya zo karshe. Asiya tace duk yadda ka ce amma ni dai bana son harkar masu maganin nan ne. Yace zamu biya kiga gidan an gama komai gefe na har na saka kaya. Asiya cike da nurna tace suje ta gani.

Gidan ya matukar birge Asiya ya zaga da ita ko ina_ta gani, tace Yaya ni ce a wannan gidan zan zauna kamar gidan Shugaban Kasa? Ya sa dariya suka shiga sasan shi ya kunna wuta haske ya game ko ina. Halifa ya daga ta sama yana juyi a kan kafet din dake tsakiyar falon. Ina son ki Asiya sosai in kika barni wallahi rayuwata zata tsaya cak. Ya zauna tana kan cinyarsa. Tace nima ba zan iya barin ka ba Yayana kai ne Duniyata Aljanna ta. Ni dama tun a ranar farko Na fara son ka.

Zo muje ki ga dakin baccin mu a nan zamu samu babynmu yau din nan ba sai gobe ba. Tace a nan zamu kwana? Yace sosai gidan mu ne gobe zamu je can mu kwaso iya kayan sawa, kafin sati daya zan saka komai na gida. Shike nan mun tare.
Wata irin rayuwa suka yi a daren wadda baza ta kankaru a zuciyar su ba. Sun kwana cike da nishadi da so da kauna. Da safe suka yi wanka sannan suka maida kayan jikin su suka nufi gida.
Anty ta kwana cike da zullumin inda Halifa ya tafi kuma shida matarsa, abu mafi tsoro ya kashe wayoyinsa duk inda tasan zata iya samun labarin sa ta buga amma shiru. Daga karshe ta kira wani malamin ta domin ya yi mata bincike. Jim kaɗan ya kira ya sanar da ita cewa yana raye amma fa yana mugun hannu dan haka ta aiko da dubu dari domin ayi mata wani aiki da zai bayyana da gaggawa asubahin fari. Duk da zuciyar ta tayi farin ciki dajin haka, sai dai dolenta ta danne domin da sauran lokacin, yanzu da Halifa ya mutu ba tare da ya mallaka mata kaf dukiyar shi ba ai aikin banza Kenan. Dan haka ta tura kudin kuma tashiga kiran yan uwa tana sanar da su harma wadanda suke Uba daya. Kafin waye war gari hankula sun tashi domin fa babu wanda ya samu Halifa a waya. Ana idar da sallar asubahi dangin suka soma tururuwa dan zuwa jin ko a samu wani karin bayani game da batan Halifa da matar shi.



Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[7/7, 22:15] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w


Baffa ya yi sallama da Dady, ya fito, bayan sun gaisa Baffa cike da damuwa, yace wai sai na samu labari wadannan mutanan sun sace Halifa to ta yaya abin ya faru? Dady cike da jimami yace "To ni dai na dawo Antyn ta su take sanar da ni cewa an kama Halifa abinda har yanzu na kasa fahimta shine kiran ta suka yi ko waye sanar da ita oho. Sai kuka ta kwana yi. Baffa yace har wayar matar tasa ba a samu ba kenan? Dady yace " Ita ai ba wanda ya san lambarta ma bare a kira. Baffa ya nisa sannan yace " To Iyayenta sun samu labari kuwa? " Dady yace Gaskiya da kyar ne, domin ba wanda ya tuna da su ma, amma bansani ba. Baffa yace" To ni abin ne na rasa gane kansa, ance ba su kira waya ba, ta yaya aka san cewa an sace shi? Jikina yana bani yaron nan ba haka bane. " Dady yace Allah ya sa, domin ina cike da dimuwa.

A cikin gida kuwa Yayun Halifa wadanda suka kasance kannan Anty Uwa daya Uba daya duk sun hallara a gidan suna ta koke koke a batan Kaninsu da matar sa. Maman Ummita kuwa tana zargin ko dai Anty ce ta salwantar da shi, domin ita ta jima da fita daga halin Anty ta fada wa sauran sunce ba haka ba, sunsan dai Anty ta kanainaye Halifa ko su zai wa alheri dole sai ta sani in ta ga dama ta hana shi, ko kuma ta amsa ta rage ko ta rike ma in taga dama amma basa zaton zata iya salwantar da Halifa akan dukiyarsa, dan haka ita a gurinta Duk inda Halifa yake dole Anty ta sani.

Bros ya Iso gidan cikin wani mugun gudu ya yi fakin sam bai kula da su Dady ba zai yi ciki. Dady ya ce "Kai Adamu.! Bros ya dawo da sauri ya ce Dady ban kula da Kuba, ya gaishe su. sannan yace da safen nan naga sakon Hafsi wai suna ta kirana ban daga ba, wai ƴan kidinafin sun sace Halifa da matarsa.! Dady yace" To, abinda dai muke ta zato kenan Mamanku da zata bamu tabbaci sai kuka take Taki fadin yadda a kayi ta samu labari.... Ya katse maganar sakamakon motar Halifa da ta shigo cikin gidan. Cike da al ajabin ganin Baffansa a gidan da sassafe haka ya fito a motar yana fadin Baffa lafiya da sassafe haka da ka kira ai da

Please Login or Register in order to submit comment