Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai in zo?
Ya kula da yadda duk suke kallon shi, har ya dubi jikin shi ko wani abu ne, yaga ba komai a jikin shi. Daidai lokacin Asiya ta katse su da fadin ina kwanan ku? Babu wanda ya iya amsa mata, sai Baffa da ya dubi Halifa yace "Ina wayarka?" Halifa yace tana mota.Ya juya da sauri ya dakko yana fadin ashe ma a kashe take. Dady yace me yasa ka kashe kuma baka sanar da Antynka ina kaje ba? Sai lokacin Halifa ya tuna da ya kashe wayar sa tun da suka shiga gidan domin su samu sakewa.

Yace Tab aini na shafa'a cewa na kashe wayar, Anty ma shafa a nayi munje ganin gidana ne domin ina son mu koma cikin satin nan, to munyi yan gyare gyare muka gaji sai kawai muka kwanta. Bros ya ja tsaki, amma ka dauki alhakinmu ka taso kowa tsaye. Halifa yace Ya Salam! Bros ya ci gaba da fadin "Antynka ta ce yan kidnafin sun sace ka. Asiya ta zaro ido. Baffa yace mikawa Dady hannu yana fadin to ni zan koma tunda Allah ya takaita. Ya dubi Halifa Kai kuma Malam Umar ka daina kashe waya sannan ko baka sanar da kowa cewar ga inda kake ba, lallai Antynka ta sani.
Zan kiyaye Baffa ina neman afwa na fito da kai tunda safe. Babu komai yarinya kije ciki ko? " Baffa ya fada yana Kallon Asiya. Ta rusuna a gaida gida. Ta wuce sasanta tana jimanta abin yayin da Halifa da Dady da Bros suka nufi cikin gida.
Anty ta mike da sauri lokacin da Halifa ya shigo falon ta na fadin Allah na gode maka ta fashe da sabon kuka ta zo ta rungume shi tana fadin Halifa ba su taba ka ba ko? Da.ma Malam yace zaka dawo da safe. Halifa ya dago ta daga jikinta cike da kauna yace, Anty babu wanda ya kama ni, kuskure na yi na kashe wayata Mun bita gida na ne, dan inason mu koma ciki sai na biya Inga me gidan ke bukata kawai daga kallo muka yi bacci. abin daya daure min kai wa ya fada muku barayi sun kama mu? Anty ta cika da mamaki har anzo lokacin da Halifa zai yanke wata shawara ba tare da ya fada mata ba?! Tadanne abinda take ji na takaici muryar ta a disashe tace shikenan Dan uwana tunda Allah yasa ka dawo lafiya kana cikin koshin lafiya Na gode wa Allah. Sauran yan uwa suka yi ta jajantawa Halifa.

Yayi musu alheri kowa ta koma gidanta.
Asiya kam ta hada masa abin kari harta canza kaya. Ya kalleta ke ce kika yi kidinafin dina fa, tun jiya kika tada hankalin kowa a dangi na . Asiya ta lumshe ido tana tuno yanayin da suka samu kansu a jiya.
Ta bude idanu ta zuba su akan nashi, tace "Jiyan nan ji nake mu kadai ne a Duniya daga ni sai kai, akwai wasu kalamai da ka furta ka yi ta maimaita su, tun jiya ni kam da na tuno su sai inji babu macen da ta kaini sa'a a Duniya. Ta mika mishi tafin hannun ta sai ya dora nashi, tace kamin wani Alkawari guda daya. Ya matso "Fadi inji" Duk yadda rayuwa zata juya mana baza ka sake ni ba? Sosai ya jawo ta jikin shi ya rungume kam. "Babyna kar ki kawo maganar rabuwa ni dake ina fata mutuwa ce zata rabamu, nima kuma ina rokon ki kiyaye. duk abinda zai iya haifar da hakan." Ta dago fuskarta ta dube shi, ta kai hannu ta kama dan gemun sa na gayu tace, Wane irin laifi ne zan maka har ka iya rabuwa dani? Yace Ki ci gaba da girmama magabata na iyayena sun mutu amma suna da madadi kamar Anty da Dady. Kalli yadda suka rude iya jiya da basu jini ba. Dan Allah ki girmama su. "Asiya ta fita daga jikin shi ta koma ta zauna. Idanun ta cikin nashi tace. Zan zame maka rabin Duniya mace ta gari zaka yi alfari da ni insha Allah. Ban san menene so ba, amma ina matukar son ka, ina kaunar ka. Ta kai karshen maganar tare da kai hannu ta shafi kumatun shi.
Kalaman suka yi masa dadi. Ya janyo ta jikin shi tare da fadin " Ki gode wa Anty da ta kawo shawarar cewa sai mun gwada gidan su Bilkisu. Har ga Allah lokacin da na ganki banji komai ba, amma yanzu da gaske ina son ki. Dadi ya kama Asiya. Ta shiga hango irin rayuwar da za su shimfida ita da Halifa a sabon gida.

Anty tana kwance cikin bargo zazzabi ne ya rufe ta tun da Halifa ya fada mata cewa zai tare kuma har ya iya tafiya ya kwana ba tare da ya kira ta ba, abin ya kona mata zuciya. Wannan ya hadda sa mata zazzabi.

Halifa ya shigo yana fadin Subhanallah Anty aje Asibiti mana a duba jikin naki? Tace "Zazzabi ne zai sauka, zuwa anjima. Halifa dama kiranka na yi wannan abu da ka yi ka saka ni a damuwa, ace zaka tashi amma ban isa ka sanar dani ba harma ka dauki matar ka kukaje gyaran gida?" Ba gyaran gida mukaje ba kawai dai mun biya ne, amma to ki yi hakuri Anty bazan sake ba. Idan kin samu sauki kuma sai mu tsaida ranar da zamu tare din. Sannan Anty zan baiwa Asiya kayan lefen nan a gurinki saboda ta yi sabbin dunkuna amma za mu cire wadanda suka yi mata yawa kamar jallabiyun ciki sai a canzo mata daidai ita ko Anty.?

Wani sabon takaici ya cikata duk ta saida rabin kayan kuma ta zaci ba zai sake magana ba.
Ta cije tace to ba damuwa. Yace to Bari na tafi Na shirya Na fita tun jiya oder ta ta zo,ban samu nutsuwa ba bare a bude kayan. "Anty tace Allah ya taimaka. Halifa yana fita Anty ta tashi zaune ta dakko waya tana tunanin wane malamin zata kira.
Wanda ya yi wannan aikin yana da zafin hannu shine ya dace ta kira, domin ai dama ita ce tace yan kidnafin sun kama Halifa, shi cewa ya yi yana mugun hannu kuma wannan yarinyar itama ai mugun hannun ce. Yace mata zai dawo gida da sassafe kuma dai abinda ya faru kenan.

Ta danna kiran shi suka gaisa tana sake yi masa godiya tace Dan Allah wani aikin zata bashi tana son ya kulle mata bakin Halifa domin ya bata ajiyar kaya ta siyar da kusan rabi ta kashe kudin. Sannan zai tare a wani gidan sa, tana son ayi abinda gidan zai gagare su zama su dawo kusa da ita.

Yace "To yanzu dai yana son ta fada mishi abinda suka fi tsoron maciji ko mage ko dai wani abu a kwari, sannan maganar rufe baki angama amma kudin aikin sa dubu dari biyar. Tace Haba Malam kai matsalar ka cika kudi Dan Allah ka min sauki dubu dari biyu zan bada.

Yace "Haka ne kudin, ba wai suna na saka ba, ina son aikin nan harda aljanu zan hada kinsan me za su bukata ni a gurina? Ko zaki iya basu jinin mutum? Anty ta yi shiru tana tunanin kudin inda zata samu. Tace Malam zan bada dubu dari kafin alkalami. Ya ce duk lokacin da kika shirya ki sanar dani, ina nufin in kin tanadi kudin. " Ya kashe wayar sa. Tace Shege mayen kudi duk da nasan cewa aikin shi kamar yanka wuka, dole in San ya zanyi in yaga dari uku cash zai yi aikin,domin dai da kunya Halifa ya zo kan kayan nan ace ba su. Yanzu aciki zan dibi sarkokin nan in yi kasuwa da su.



*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[7/14, 07:16] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w

Kamar da wasa Anty ta hade kan sarkoki ta cefanar, ta shirya ta kaiwa Malami kudi ya amshe dari uku da saba'in ya mata laminin sauran ya bata magungunan da zata yi, yace mata duk ranar da ta gama amfani da maganin ta tunkari Abba ta fada masa cewa bata son ya bar gidan sannan ta sanar da shi cewa ta yi amfani da kayan shi. Yace babu abinda zai iya.

Asiya ta ga har ankai sati amma Hailfa bai kara batun tariya ba, ita kuma tana son yi masa maganar amma tana tunani. Ta daure tace Yaya wai kuwa ya batun tarewar mu tunda naga jikin Anty da sauki. Yace Anty ta sameni taroke ni akan wai in taimaka in hakura da tashi zuwa gaba kadan. Sannan ta bani hakuri akan kayan ki na lefe wai ta taba. Duk da banji dadin abin ba, amma dai bani da yadda zan yi tunda matsayin Uwa ta ke. a guri na. Dole in yi hakuri da wasu abubuwan dan haka kar ki damu mu bata lokaci insha Allah komai zai zama daidai. Duk da Asiya bata ji dadin abinda ya faru ba amma bata nuna komai ba, cike da fara a, take fadawa Halifa Allah Sarki Anty tana kaunar ka shiyasa ta haka. Dan ma kaine ka damu mu koma can amma ni gwara nan din da motsin mutane. Halifa cike da jin dadi yace Allah ya yi miki albarka wallahi har ina tsoron ta ina zan fara magana.

Asiya tace 'Haba Yayana nifa abin ikon ka ce, umarni kawai zaka bani a kan komai. Ya kama hannuwanta shi yasa nake kara son ki. Anty ta yarda aikin Malam ne ya ci. Dan haka ta kuma wankar jiki ta kuma zuwa gunsa da wasu bukatun tace Tana son a yi wani a bu tsakanin Halifa da matarsa wanda zai hana su zaman lafiya domin bata son ace matar Halifa ta haihu ya samu mai gadon abinda ya mallaka,Malam yaron yana da dukiya da shi kanshi saidai ya yi kiyasi kuma gashi da nasibi, dan abinda aka tsakura mishi a kudin sa yanzu ya ninka yafi sau dari. Ni dana sha wahalar shi har yanzu banda komai in matar shi ta haihu. Malma yace Kash da kin zo nan kafin bikin nashi kika zo da ko auren ma ba zai taba yi ba. Kinga yana mutuwa kin tabbata ke ce mai gadon sa." Anty taja tsaki tace ai lokacin ban San nan ba. Amma yanzu ma in dai da yadda za'ayi a toshe mahaifar ta kar ma ta dauki ciki bare ta haife shi. Ina da burika game da Halifa sosai.

Malam ya mata Alkawarin matsa war da kudi magana ta kare.

Asiya ta kara so falon da gudu tana ihu,. Anty ta taso a gigice tana cewa waye meye! Gadangare ne ya biyo ni Anty ta ja tsaki tana fadin meye abin gudu a kadangare? Asiya harda shidewa Dan tsoro. Tace "Wallahi Anty sam ni bana son kadangare ina tsoron sa sosai.
Bayan fitar Asiya take Anty ta kira Wayar Malamin tana sanar dashi cewa Allah ya saukaka mata yarinyar nan kadangare ke firgita ta. Malam yace sa kudin aiki yau gidan ba za a kwana lafiya ba.

Cikin bacci Asiya ta shiga firgita tana tsorata domin farkawa tayi taji ta a jikin Halifa ya rumgume ta gam yana tofa mata addu'o'i ta kalleshi ta hada zufa sharkaf sai ta sake kankame shi. Yace kinyi bacci babu addu'a ko? A wahalce tace na yi adduo'in dana saba kawai dai jiya ne wani kadangare ya biyo ni dama ina tsoron sa, sosai. shi ne nayi mafarkin sa yana ta bina. Halifa yace "Shiya sa cikin baccin naji kina nishi kina karanta addua, to kar ki damu ki canza yanayin kwanciyar ki sai ki sake yin adduo'in,ta yi yadda yace shima ya tofa mata, saidai kuma da bacci ya soma fizgarta zata ga kadangaru bakake sun cika mata kan gado sai ta farka a gigice. Haka suka kwana. Da safe yake fadawa Anty Halin da ake ciki ta yi murna sosai amma sai ta boye ta jajanta tace "To Halifa me zan muku baya ga addu'a ance tana da jinnu kunce ba haka ba, Na kawo mai magani ta masa sharri ka hau kai ka zauna, yanzu kam ai sai dai ku nemi magani da kanku ko ka sanar da iyayen ta. Halifa dai ya mike ya koma ya samu Asiya zazzabi ya rufe ta sai rawar sanyi take yi. Ya rasa ina zai saka kan sa yace tashi ki sa hijabi mu tafi Asibiti.
Halifa ya yi wa likitan baya ni game da yadda suka kwana da kuma yadda take fama da zazzabi. Likitan ya tambayi Asiya ta sanar da shi yadda abin ya faru. Yace "Ta tsorata ne sosai, saboda tana jin tsoron kadangare duk da ni ba likitan kwakwalwa bane amma ina da wata yar masaniya kasan, kasan Ita kwakwalwa kamar kwamfiyuta take in ta Karbi abu ba a cikin shiri da tsaro ba sai ta birkice ta yi ta abubuwa ba daidai ba. To itama abin ya zo mata ba zato ta tsorata da yawa ne ba komai da ta samu bacci komai zai zama daidai. Sai dai shi zazzabin ta yuwu rashin bacci ne ko maleriya bari a yi mata gwaji mugani. Kusan gwaji kala uku likitan ya sa aka yi mata. Bayan kawo sakamakon ya tabbata akwai malaria likitan yace to ko wannan maleriya ta isa ta saka ta yin abinda yafi haka. Sannan ya duba daya sakamakon yace saukin ta kuma ba taifot. Ya kalli dayar yace ko wannan ma zai iya saka komai dama tana dauke da ciki ne?
Halifa ya mike tsaye da sauri, tare da fadin me kace likita. Yace tana dauke da ciki karami Dan sati biyu. Sai kawai suka ga Halifa ya zube a tsakiyar ofishin ya yi sujjada yana fadin Allahu Akbar. Ya Mike ya rungume likitan yana fadin likita na gode da wannan albushirin naka. Ka dai tabbatar ko? Gani nake yi kamar a cikin mafarki.
Likitan yana dariya yana Dan buga ka fadar Halifa yace ko shakka babu mutumina matar ka tana dauke da ciki kamar yadda yake a rububuce. Halifa yace ina mamaki Wai ni ne na yi ciki ya Allah ya juya gurin Asiya wadda kunyar kalaman da Halifa ke furtawa suka sa ta sunjuyar da Kai. Ya rungume ta yana fadin ina kaunar ki maman yarinyata. Ya kalli likitan mace ce ko. Cike da dariya likitan yace "Sai dai in kunje hoto za a fada muku,suma sai ya dan kara kwari. Halifa ya saka hannu a aljihunsa ya ciro kudin dake ciki bai kirga ba ya mikawa likitan Ba yawa goron albishir ne, ina son ka rubuta abinda ya kama ta ci Sannan ka fada mata dokoki kaga yarinya ce karama kar ta yi ganganci. " Likita ya sa dariya yace ba komai zata iya Allah da ya bata shine zai bata kariya da danta. Halifa yace ka gama magana Allah ya baka lada. Tamkar ya yi wa Asiya tafiya haka ya ruko ta, yana fadin ko in dauke ki? Asiya kuwa ji ta yi karfi ya zo mata tama daina jin komai tunda likitan ya ambaci ciki. Tace "Yaya kana sani jin kunya sosai ka sake ni zan iya tafiya." Duk da haka ya rike mata Hannu duk kunya ta ishe ta cikin mutane, Haka suka ratso har mota. Ya bude mata ta Shiga ta zauna ya rufe ya zagayo cike da farin ciki ya bude gefen shi ya shiga. Ya kallo Asiya wadda take jin ranar yau ta musamman ce a gurinta. Yace " Ina son ki sosai Asiya ya kai hannu ya daga hijabin ta ya zura hannu ya shinfida a cikin ta yace Yanzu dai dana yana kwance a nan ko? To ya naji be yi girma ba? Asiya tace to duka baka ji ance sati biyu ba?
Halifa ya dauki waya ya fara danna number dole in fara yi wa Anty albishir sai dai wayar Anty Busy. ya kira Mijin Anty ya fada mishi, ban sha mamaki ba sai da naga ya kira Baffa. Nace Yaya yanzu kuma sai ka fada mishi? Sosai ma zan fada mishi kuwa ai abokin kuka shi ake fadawa mutuwa. Haka dai ya yi ta kiran abokai da yan uwansa. Yace bari dai zan kira Sulaiman ya kaiwa su Inna waya sai ki fada musu. Asiya tace kunya zanji sosai ka bari a hankali sai in fada musu ko sugani. "Anty har yanzu tana waya, ya fada cike da haushi bayan ya sake kiran ta. Ya kira layin Hafsi ta daga yace kina gida ko"? Tace ina gida. Ya ce ki kaima Anty wayar akwai abinda ya kamata ace ita ce farkon ji yanzu za ta zama itace karshe. Hafsi tace menene ya faru Uncle? Yace Anty zata fada miki.
Ta shiga gurin Anty daidai lokacin da take fadawa Malaminta cewa ga shi nan ta turo masa kudin aikin daure mahaifar Asiya. Hafcy ta mika wa Anty wayar tare da fadin Uncle zai miki albishir. Anty ta amsa tare da fadin ya wuce kaya sunyi riba oder ta yi kyau. Daidai lokacin ya sake kira. Ta daga yace "Anty albishir mai dadi." Tace miliyan nawa aka samu? Ciike da jin dadi yace Anty girman lamarin nan yafi batun kudi. Zan zama Baba kyautar Dan mutum Allah ya bani sati uku kenan.....



*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[7/22, 21:10] Ummi Tandama😇: https://whatsapp.com/channel/0029Vb6H4trFsn0pEII5by1w

*🔉 NASIHOHIN MALAMAI🔉*


*ADDU'O'I MASU MAHIMMANCI. Vol 2👇🏼*


1️⃣ *Addu'ar da ake yi domin ganewa da fahimta da hadda, haka nan gurin warkar da in ina. Wannan ce addu'ar da Annabi Musa,Aminci Allah ya tabbata a gareshi ya yi lokacin da aka umarce shi da ya tafi wajen Fir'auna*. Alƙur'ani sura ta 20 aya ta 25-28

رَبِّ اشْرَحْ لِي صَدْرِي، وَيَسِّرْ لِي أَمْرِي، وَاحْلُلْ عُقْدَةً مِّن لِّسَانِي، يَفْقَهُوا قَوْلِي

Rabbi ishrah li sadri, wa yassir li amri, wahlul 'uqdatan min lisani, yafqahu qawli.
_Al-Qur’ani, Surah Taha._


Wani abu ne ya taso tun daga yatsa har tsakiyar kan Anty, take ta Mike tsaye cike da tashin hankali." Halifa ciki matar ka ke gare ta? " Yace Wallahi Anty ashe ma shine yake sata duk Wannan firgicin gamu nan zuwa gidan nace dai bari in fara sanar da ke ne kuma sai kina ta waya. Ta sauke numfashi. "Lallai wannan babban albishir ne Halifa Allah ya kawo ku gida cikin aminci ka yi tuki a hankali. Jifa ta yi da wayar a kan gado tana fadin ya Allah ka kawo min dauki ciki kuma Halifa zai yi ɗa to me zan samu kenan? In yi wahala da shi wata banza ta zo ta haifi Magaji. Ta sake zabura ba zai yiwu ba, gashi Na tura kudin aikin.

Ta dauki wayar ta kira Malamin yana dagawa tace Aiki fa ya jika, yarinyar nan dai ta samu ciki. " Malam yace to menene abin daga hankali? Sai a zub da shi kuma a daure mahaifar ni fa in kina so sai in kwantar da cikin." Anty ta zabura kamar tana gabanshi, tace "A a Malam karka kwantar da shi zai iya tashi, inda za'a iya cire ma haifar cak,sai a aika aljanu su cire su yi taushen su su cinye." Malam ya saki dariya Sannan yace, Kai kina da mugunta sosai wallahi. To ba matsala yanzu dai za a cire cikii a kulle mahaifar kowa ya huta.

Halifa ya tsai da mota bayan ya shigo gidan Asiya zata fito sai Halifa ya ce tsaya, ya kai hannu ya bude motar yace fito. Asiya ta fito suka nufi daki. Kan doguwar kujera ta kwanta ya yace Bari na fadawa Anty mun dawo. Da murna Anty ta tari Halifa tana addu'a sai kuma ta fashe da kuka. Inama Hajiyarmu tana raye. Halifa wanda bai san mahaifiyar ta su ba saidai kaunar ta da yake ji a ransa yace "Allah ya yi mata Rahma amma Anty ni ai kece Uwata, ina jin ki a zuciyata fiye da ita tunda ban shaku da ita ba. Anty cike da jin dadi tace Allah ya yi maka albarka Halifa yadda kake min biyayya Allah ya sa wannan dan da za a haifa maka Shima ya yi maka biyayya. Ameen Halifa ya amsa da sauri domin ji yake kamar daga makogwaron mahaifiyar shi addu'ar ta fito. Anty cike da makirci tace muje in ga jikin nata.

Ido cikin ido suka kalli juna da Asiya a hankali ta furta Allahumma kafini him bina shi"ita. Addu"a ce da malamin su ya basu yace in sun ji tsoron cutarwa daga wani mutum to su karanta masa. Anty ta Iso tana fadin sannu da jiki Asiya Allah Sarki baiwar Allah matar firauna. " Halifa yace Anty ni ne Fir'aunan? Cikin dariya tace" A a kawai dai na tuna da mai sunan nata ne. Asiya ta yi guntun murmushi, tuni ta gane cewa rashin abin fada ya sa Anty fadin haka.


Aka shiga rainon ciki,
Haka dai Asiya ta shiga laulayi komai taci sai ya dawo dole aka kwantar da ita a Asibitin ana ta karin ruwa Halifa kuwa ko kasuwa daina zuwa ya yi duk ya fita hayyacinsa kamar shine mai cikin. Asiya har tausayin sa ta ke ji. Sadiya ce a gurinta Innar su ma tana kai kawo a gurin. Anty kam kullum tana hanya da girki, sai dai Asiya ta kasa yarda cewa Anty tana murna da cikin dan haka ta Kaurace wa duk wani abu da Anty zata kawo da sunan ta ci ko ta sha.

Wannan matakin ya kona ran Anty domin ta lura Asiya ta fake da amai ne dan kar ta ci abubuwan da take kawo mata wanda da ta ci da tuni cikin sai labarin sa. Shi kan shi Malamin ya ji haushi Dan haka yace ta barshi da ita ai dama Wai yaga karamin aiki ne amma zai mata abin da zata yi mafarki kuma da ta farka cikin zai fita. Duk wanda ya yi imani cewa Allah ishashshene babu shakka sai ya isar masa. Abinda Asiya ta dogara da shi kenan.

Kwanci tashi a sarar mai rai inji yan magana ciki har ya shiga wata hudu, duk da irin abubuwan da Anty ke yi Amma ko gezau kuma ta kasa ganewa bare ta daina narka kudinta a bokaye.

Karshe dai Malamin da yaga Anty ta saka masa kuka wiwi tana fadin har yanzu bai biya mata

Please Login or Register in order to submit comment