Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ci gaban ka.

Bros ya ce akan son ranta dai, ni mahaifiyata ce bani da yadda zanyi amma kai yar ka ce zaka iya neman hakkin ka ko nuna mata rashin jin dadin abinda ta yi maka. " Halifa ya sauke ajiyar zuciya yace. Na fada maka ne dan inji sanyi kar kaji haushin magana ta. Bros Yace ba wai bakar magana na fada maka ba Uncle wallahi haka shine gaskiya kaje ka ce mata ta baka kayan ka, bai dace abar mutum ya yi tafiya a cikin kuskure ba. Halifa yace zanga me zanyi.


Asiya tace Inna gaskiya Na hakura da yin awon nan ina yawan mafarki da Asibiti wai kuma ga Anty abin dai na kasa fassara shi. Inna tace" Khairan insha Allah babu abinda zai samu ke da abinda ke cikin ki, Kiyi ta adduo'in neman tsarin nima kuma ina yi, kinsan dai Allah baya wofintar da adduo'in mahaifa akan yaransu. Insha Allah zaki sauka lafiya.

Sadiya da ke gefe tace Ameen insha Allah. Ni Mijin nata ne ma ko da dai ance ya yi tafiya amma ya kamata ko a waya ya nemeki in dai ba wai yana zargin ki a gaske ba. Asiya tace Babu mamaki ya neme ni ai nâ kashe wayata. Inna tace shi dai ya sani nikam gara ma ya baki takardar ki in kin haihu lafiya kya samu wani mijin daidai ke. "Asiya tabi Inna da ido tana Kallon ta domin kalaman Inna sun soki zuciyar ta har ma ta rasa kalmar fadi. Sadiya tace muna daya Inna gara su rabu da a kashe ta a banza, dan matar nan ta shirya wa haka. Suka ci gaba da tattauna zancan a tsakanin Inna da Sadiya. Asiya dai bakinta dai ya yi nauyi zuciyar ta kuwa ta shiga zogi gaskiya bata jin zata iya rayuwa ba tare da Halifa ba, gaskiya tana son shi zata iya jure komai saboda shi, sai yanzu ta yi data sanin dawowarta gida da ta tsaya kamar yadda ya bukata. Inna tana da sauki amma in ta cije bata canzuwa ga ciwon ta ba sa son abinda zai bata mata rai. Ta share zufar da ta keto mata ta kuma sauke ajiyar zuciya lokaci guda.
Inna ta kalleta lafiya ko dan ance bazaki koma gidansa ba? Asiya tace Ba haka bane kawai dai bari ya dawo muji ta bakinsa. Inna tace Ai ko ya dawo bazan iya gayyar rashin mutuncin ba abida kawai zaifi shine a rabu. Yansanda kamar anzo kama yan fashi banda Allah yasa muna zaune da yan Unguwa lafiya ba, ai da tuni sun tafi dani, Kasar nan ba a jin kunya a juya takarda a rubuta abinda ake so a kaiwa alkali ya jefa ka gidan Yari..Sadiya Tace nifa Har shi Halifa haushin sa nake ji, da ka yake zaune ace duk abubuwan da ta miki wai yace bai sani ba kuma bai fahimci komai akai ba?!! Asiya tace kar kice haka maman Annur kar ki ga laifin sa dan bai sani ba, Na farko baya yini a gidan sannan ya yarda da ita bata taba yi masa wata mugunta ba bare ya zarge ta. Kuma yadda naga yana shiga tashin hankali idan zuciyarsa ta hasaso ko ta zarge ta shine yasa ban fada masa komai ba. Kinga kuwa dole a yi masa uzri. Inna tace "Dama fa ba sanin su mukayi ba, dare daya yazo rabon dai wannan ciki. Ni mutum ko dan karuna ne ya zo dan kudi wallahi bazan dauki wulakanci ba. Asiya ta sunkuyar da kai. Lallai abin ya wuce yadda take tunani.


Halifa ya shiga ciki falon Anty Hafsi tana waya yace ina Anty? Tace tana ciki ba ta da lafiya. Yace Allah ya sau wake, ki ce mata nazo zan dauki kaya. Hafsi ta ce To ka shiga mana Uncle ita da Hajiyan Zariya ne. Yace Shiyasa bazan shiga ba domin bana son ganin matar nan a gidan nan duk lokacin da ta zo abubuwa sai sun yi ta faruwa babu dadi.

Hafsi ta taba baki "Ai kwadayi ke kawo ta dan ma Anty tana taka mata burki. Ya ja tsaki Sannan ya bi bayan Hafsi.
Anty tana kwance ta rufa cikin bargo tana ta rawar sanyi Hajiya Talatu tana yi mata sannu. Ya kalli sashin akwatuna suna jere kamar yadda suke hatta rinbom din dake jikin akwatunan suna jiki. Ya dan taba baki shikam ya tabbatar wadannan din dai ya gani dazu. Ya dan matsa kusa da Anty yace Sannu Anty zazzabi ne. Hajiya Talatu ta ce Hawan jinin ta ne ya tashi ta samu kanta a bacin rai gidan su wannan matar taka da muka je neman sasanci Uwar ta ta zage mu tas ta zuba mana ruwan wanki har ta yi ikirarin kisan Antyn ka. "Shine dalilin kira mata ya sanda da kukayi? Halifa ya katse Hajiya Talatu. Tace Eh to ai dole dannan kaji yadda ta tara mutane tana shan alwashin kashe Antyn ka kuwa!!? Cike da tsana Halifa ya sake Kallon ta." Nasan ke zaki zuga ta kuje gidan ku yi mata rashin mutuncin kuma ko me ya faru dai ku kuka sameta har gidan ta. Anty wadda ke kwance tana makyarkyata ta tashi da sauri zaune cike da mamaki tana Kallon Halifa cike da Al ajabi yaron da in bata da lafiya ya fi kowa daga hankali yaron da in wani ya tabota sai inda karfin sa ya kare idan da ne ya samu bata da lafiya ba zai bari ta kara minti goma a gidan ba, zai tabbatar tana gadon Asibiti.

Ta soma magana cikin kuka Halifa ni ka ke fadawa magana akan surukan ka shine har kake wadannan zantuka ko? Halifa Ya ce. "Menene karya ko laifi a magana ta Anty? Nace kuje neman sasanci ne da wa muka yi fada ni da mata ta ba fada muka yi ba, anyi mata sharri ne kuma ta yi fushi in kuma ta huce zata dawo to menene naku da zuwa gidan?Wallahi Anty kin bani mamaki kuma kin nuna min cewa lallai mahaifiyata ta mutu domin da tana raye wallahi baza ta dakkowa surukai na mutane muskunai masu rauni kamar su Inna yansanda ba. Kamar yadda ke ma nasan bazaki dakkowa iyayen matar Bros ba tunda danki ne.

Yanzu kam Anty kukan gaske take rerawa ba kamar dazu ba da take kukan kissa da makirci ba. Hajiya Talatu wadda ta hangame baki ta kasa magana har sai da ya kai aya ta sauke ajiyar zuciya tace Amma dai dannan baka kyauta ba, Antyn ka bata cancanci irin wadannan kalamai daga bakin ka ba domin..... Ke da Allah yimin shiru ina wuya dake wallahi in kika kara magana sai nasa an rufe min ke, kuma ki tashi ki fita ki bar gidan nan yanzun.!! Anty mai rashin lafiya ta diro daga kan gado Tazo gaban Halifa ta sa hannu ta dauke shi da wani wawan mari, Ka fara shaye shaye ne a tafiyar da ka yi ko? Ta daga murya ni zaka ciwa zarafi wannan ne sakamako na ko Halifa!! Ta fashe da sabon kuka mai karfi wanda ya janyo hankali kowa na gidan inda suka nufo dakin. Halifa ya dafe kuncin sa ya cike da bacin rai a kofar fita suka ci karo da Dady zai shiga falon. Ganin yadda Halifa ya wuce ba tare da ya Kalle shi ba bare ya yi masa magana ba ya gane akwai matsala dan haka ya nufi ciki da sauri, kukan Anty da zantuka da take maimaitawa ne suka dira a kunnen shi. Tana fadin ni Halifa zai ciwa zarafi akan surukansa wallahi daga shi har su basu isa ba inna haihu cikin iyayena ko asiri suka yi masa sai na karya shi.

Bai shiga dakin ba ya wuce nashi dakin sai da ya cire kayan jikinsa ya saka jallabiyya sannan ya fito ya nufi dakin Halifa dan jin ba"asi.
Yana fitowa tsakar gida Halifa ya fita a motarsa da gudu daga gidan ya danyi shiru yana tunanin abinda zai yi, yana tsoron masifar Anty ne shiyasa bai ma shiga dakin ta ba. Ya yi ta maza ya tunkari dakin danjin meke faruwa.

Ya kalli yaran da suka tasa su gaba suna kallo yace kai duk ku fice. Ya dubi Anty wadda ke ta kuka tana sharbe sam bataji dadin abinda Halifa ya fada mata ba har zuciyar ta. Hajiya Talatu tana fadin daga gani zugashi suka yi. Dady yace Wai me yake faruwa ne? Sabon kuka Anty ta dora tana rattafo mishi abinda Halifa ya fada mata. Dady yace Gaskiya fa ya fada miki kuma ya kamata ki zauna ki yi wa kanki tunani sosai domin kina shiga hurumin yaran nan, menene naki na kirawo musu yansanda kuma?
"Dan Allah ka rufe min baki!! Anty ta katse shi, ai kai dama kullum nice mai lefi akan komai. To Bari kaji Halifa dai dan Uwa na ne in ka so kayi masa fada ya bini ko kuma ka sa mana ido. Cikin mamaki taji ya daka mata tsawa." Ke Habiba saurara kiji, na gaji da abinda ki ke yi a gidan nan ina kauda kai. Ina yi ne fa dan a zauna lafiya ba wai dan tsoron ki ko wani abu ba, ina son ki sani bazan iya ci gaba da wadannan munanan dabi un naki ba, dan haka ina son ki sani komai zai iya faruwa ya sa kai ya fice daga dakin. Sai lokacin ta samu damar magana ta kalli Talatu Ki dubi wannan mutumin fa, har yana da izzar yi min magana kenan? Ta mike rai bace ta nufi kofar dakin shi tace ka fito ka fada min abinda zai faru karkari dai ka ce ka sake ni ko? Kaga sai ka hada yan kayan ka ka yi gaba banda haka me zai faru!! A doke dai ba zan doku ba haka ma zage bazan zagu ba.. Ya fito da karamar waya a hannunsa yana sauraron labarai ya kalleta ya ja tsaki ya wuce..

Anty fa abin ya zame mata goma da I shirin tana mamakin Inda mijinta ya samo kwarin gwiwa. Hajiya Talatu ta ce, Alamu suna nuna ayyuka duk sun karye wadan da kika yi masa, dan haka gobe akwai sammakon gidan malamai sai kuma kin kwance bakin aljihu. Anty tace Kai Na shiga uku yanzu me yafi mahimmanci a guri na aikin Halifa ko na Asiya ko na Dady......

*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[9/20, 15:40] Ummi Tandama😇: Asiya da Sadiya suna tafe fitina irin ta masu ciki ta sa Asiya ta nemi Sadiya da ta yi mata rakiya zuwa gidan wata tsohuwa da suke siyan magarya lokacin suna zuwa primary suna tafe Sadiya tana mitar nisan gidan tana fadin "Allah da ace ke daya ce ba domin cikin nan ba wallahi bazan kama doguwar tafiyar nan ba kila ma muje bamu samu ba. Asiya tace sai mu wuce bakin Asibiti muje rimi can kam zamu samu har a duwa.

Sadiya tace saidai ki biya mana mu hau dan sahu kuma yanzu .ma dare ne bazamu samu ba.

Cak Asiya ta tsaya tana waige waige.

'Lafiya?" Sadiya ta fada tare da dafa Asiya. Tace "Ina jin kamshin Turaren Yaya Halifa, duk yadda aka yi yana nan gurin. Sadiya ta saki baki tana bin Asiya da kallo. Sannan ta taba baki tare da fadin "Waye kuma Halifa?" Mijina Asiya ta fada tare da nufar shagon Sulaiman ta leka shi kanshi Sulaiman baya ciki,ta juya da sauri ta nufi gidan su ta ma manta da Sadiya. Sai biyo ta ta yi tana kwada mata kira.

Ta duba ko ina a kofar gidan tana kalle kalle, bata ganshi ba ta shiga gidan Inna tana tsaye rike da wata farar takarda da sauri suka karasa Asiya tace Inna la.. Lafiya? Bata san me yasa ta faduwar gaba ba. Inna tace Takardar sakin ki ce Mijinki ya kawo. Maganar ta daki kirjin Asiya har ma da Sadiyar duk da ba ita aka saka ba.

Da sauri Sadiya ta amshi takardar ta soma karantawa a fili.

"Ni Halifa na saki Asiya saki uku kuma cikin jikinta ba nawa bane ta nemi ubansa,in kuma bata yarda ba zan shigar da kara kotu. Tun kafin ta kai karshe Asiya take fadin Amma kuwa Inna waye wanda ya kawo wannan takardar? Ta kai karshen tambayar cikin rawar jiki da rawar murya. Inna cike da bacin rai tace koma waye ya kawo ke dai ba ya sake ki ba,ni gara haka da a sabarta min ke,batun ciki kuwa dole ya amsa koda kuwa hakan zata kaimu har gaban alkali ne. Amma zamu fara ta kan waliyyan shi tukunna da safe zan yi magana da Abban su Sulaiman. Sadiya ta sauke gwauron numfashi sannan tace, "wannan zalunci ne aka yi wa Asiya gaba daya tun daga auren zuwa yanzu."

Asiya tace Inna gaskiya ba zan taba yarda cewa Halifa ne ya kawo min ba, domin kalaman da ke rubuce a jikin takardar ba kalaman da Halifa zai yi amfani da su ba ne koda kuwa saki na zai yi, sannan in har Halifa zai sake ni ba zai min saki uku ba.

Kuka ya kwace mata ta fada daki da gudu ta fada kan yar yaloluwar katifarta tana furta Innalillahi wa Inna ilaihirraji un.

Sadiya ta zo ta zauna kusa da ita ta dafa ta cikin sigar lallahi tana cewa, kiyi hakuri Asiya Allah ubangiji shine mai sakayya zai bi miki hakkin ki.
Asiya cikin kuka wiwi take fadin 'Ba zan iya tsayuwa gaban alkali muna shari'a da Halifa ba,ya fi karfin haka a gurina koda kuwa zai karyata cewa cikin ba nashi bane.
Sadiya tace kaji Haukan ba,to wazai yarda da hakan? Inna daga tsakar gida take fadin cewa "Sam bata san illar da hakan zai ja mata ba, ni kuma matukar Ina raye ba zan bari karya ta hau kan gaskiya kuma ta zauna ba."
Asiya ta sake fashewa da kuka tace, Inna , zuciyata har yanzu bata amince da cewa Halifa ne ya sake ni ba,Halifa wallahi ya yi min alkawura da dama yana sona Inna.

Sadiya ta ja tsaki ta fita a dakin da ta shigo dan lallashin Asiya. Inna ma cike da jin haushi tace "To sai ki hada kayan ki ki koma gidan sa ki zauna tunda kin ce ba,zai iya sakin ki ba. Kuma ki rufe min bakin ki kafin ki tunzurani in hau kanki har ke har cikin dake jikin ki,bana son in sake jin muryar ki a gurin nan har ke har cikin naki.

Asiya ta kwanta tana hadiyar zuciya nan take zazzabi da ciwon kai suka diro mata,bata taba sanin tsawon dare da ake fada ba sai a ranar, tufka take tana warwara zuciyarta tana fada mata cewa ba gaskiya bane akwai alkawura masu dama a tsakanin su.To amma ba shakka ta ji kamshin turaren shi a wannan lokacin . Sai taji wata sabuwar kauna da son Halifa a zuciyarta ita kam zataje ta yi idda a dakinta.
Ta tashi ta kalli sadiya tana ta baccinta da yaranta.Da a ce mutuwa Halifa ya yi zai fiye mata akan ace yana raye ita ma tana raye amma basa tare, ina ma ace ta mutu, ta ayyana hakan

Ta mike ta je gurin akwatin kayanta ta dinga daga su a hankali har ta ciro wayar ta. Bata yi mamakin ganinta babu chaji ba,domin iya tsawon lokacin da aka kawo mata bata sa a chaji ba, kuma bata zaton ta kashe kafin ta fita sabgar ta.

Bazata tuna tsawon lokacin da gidan su ya dauka babu wutar lantarki ba tun farkon ciwon Babansu. Kenan ita da chaji sai dai gobe idan ta kai gurin chaji. A fili ta furta Innalillahi wa Inna ilaihirraji un. Hannu ta ji an dafa ta ta baya. Ko bata juya ba,ta san Sadiya ce. Tace "Haba mana Asiya ke da a ka yiwa shedar hakuri da kawaici ya kamata ko bakiji dadin abinda ya faru ba,ki daure ko dan Inna musamman ma da yake bata da ishashiyar lafiya. Asiya ta juyo ta kalli Sadiya. "Maman Annur dan Allah ke kunyi soyayya da Baban Annur kafin ya rasu?" Sadiya tace kin dai san ba auren dole aka yi min ba ko?" Asiya ta lumshe idanun ta, taci gaba da fadin Baki san soyayya ba domin da kin santa ba zaki yi min wannan maganar ba, in da soyayya kuke yi dashi na tabbata da daya mutu da sai kin bishi." Sadiya tace Kina nufin in kashe kaina duk da lokacin mutuwata bai zo ba?
Asiya ta mike tana tangadi ta koma kan katifar bata taɓa zaton Sadiya zata fahimci abinda take nufi.

Sadiya ta ci gaba da fadin ki sani bawai banji mutuwar mijina ba ne ko kuma bana son shi ko kusa, kawai dai tawakkali gare ni. "Baza ki gane ba.' Asiya ta fada tare da kwanciya rigingine ta ci gaba da fadin, ki kwanta kawai. A zuciyarta ita dai kawai zata koma gidan mijinta ta yi idda ko Allah ya sa ya maida ita.

"Ya kamata ki nutsu sosai saki uku ya yi miki,ki kauda kanki daga gare shi karma ki nuna masa kin damu ko da mu kin nuna mana."
Sadiya ta sake katsewa Asiya tunani, da magana kuma kamar ta san tunanin da take yi.

Kan Asiya ya kuma sarawa ashe fa saki uku ne. A fili tace astagfurullah ba shakka akwai wani laifin da na aikata wa Ubangiji.

Kafin gari ya waye Asiya bata iya gane banbancin 7 da 17 . Hankalin Inna da Sadiya ya tashi suka dauketa zuwa Asibiti, likitan ya yi fada sosai akan yadda suka bari jininta ya hau irin haka, ya bukaci ganin mijinta bayan ya ba su gado Inna ta ce shine sillar ciwon saki uku ya yi mata kuma yake da a war cikin ba nashi bane. Likitan ya fusata yace zai hada su da wani lauya mai rajin kare hakkin dan Adam kuma zai taimaka musu dan su kai shi kotu.
Duk da halin da Asiya take ciki bata iya magana amma ta daga yatsa tana girgigizawa alamun baza ta iya tsayawa da Halifa a gaban kotu ba.

Inna tace "Ai ba ta ita zamu yi ba in zamu bi mata hakkinta,makauniyar soyayya ta rufe mata ido.
Likitan yace a kwai yarinta a kanta dan haka baza ku tsaya jin ta ba. Amma yanzu a bari a samu kanta tukunna.

Anty suna tafe bayan sun sauka daga kan dan sahu, gida suka nufa, tun farar safiya suka fita sunje gidan malami ya kusa goma,duk damuwarta akan batun Halifa ne, tana cike da tsoron abinda ya aikata jiya,ta san shi da zuciya ta masifa kuma ta kashe kudi a shekarun baya gurin malamai da dama kafin ta samu aka karya masa zuciya sannan ta samu sassauci,domin in da ne ta yi masa wannan rainin hankalin da kaya samu zai yi ya cinnawa sauran wuta. Kuma ta sa a rufe mata bakin mutumin nan mai kudin da ta karba dan tijara. Hajiya Talatu tace karki damu gashi rabin kudin ma duk sun tafi a malamai, nasan tun yau zamu soma ganin karfin aiki domin mun saka malamai masu zafin hannu.........


*Zaɓi ɗaya cikin biyu ne ga duk me son karanta littafin HASASHE,Na farko zaka shiga wannan link ɗin 👉🏼https://www.facebook.com/share/p/1Bevu6CRwK/ zai kai ka/ki facebook zaka yi following channel ɗina na FASIHIYA ka/ki turomin screenshot ta wannan number👉🏼0814 000 4302 ko wannan 09068032427 zan sakaki group ɗin da zaki samu littafin ƙyauta, za'a cire alfarmar following ɗin a 10-june 2025 saboda haka duk wacce takai lokacin batayi following ba sai dai tabi hanya ta biyu,sai hanya ta biyu waɗanda basu buƙatar yin following zaku turo ₦1k ta wannan account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank*


*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[9/21, 18:35] Ummi Tandama😇: Ta kalli motar Halifa da ke aje a gurin da yake aje ta, tace yana gida ma wallahi Sahiba har wata faduwar gaba naji kinsan bamu hadu ba tun jiya, bari inje gurin dakin sa inga me yake ciki.

Talatu ta ja tsaki karya ki ke ashe ba tsoron haduwa da shi ki ke ba,in kuma ya fito fa. Cike da kuri Anty tace sai me? Ta tsaya inda ta saba yi masa labe, waya yake yi da alamu da lauyan shi yake yi.
Taji yace Barrister mu bar Zaman zuwa ranar litinin. Halifa ya fada yana tari. Ya dan jima yana tarin kafin daga bisani yace Barrister zai fi kyau haka zan kira jimawa mu karasa. Bai saurari amsa ba ya kashe wayar. Cike da tashin hankali ta isa dakin ta. Ta samu Talatu har ta cire riga zata shiga wanka, Anty ta shigo tana fadin "Wata sabuwa na shiga uku Talatu cike da tashin hankali. Hajiya Talatu cike da fargaba tace 'Me aka yi ne Sahiba Anty tace Naji Halifa ya na waya wai za su zauna da lauyoyin sa ko dai zai amshe duk dukiyar shi ne ya koma yana sarrafa su, in kuwa haka ne yanzun ne daidai lokacin da zan mallake shi. Hajiya Talatu tace baki yi tunani akan ko zai kwace wannan gidan yace ku tashi ba? Ya amshe dukiyar sa ta hannun mijinki danki Adamu ?"Anty ta zabura tana kai komo. Ta gaigiza kai,ko a mafarki Halifa ba zai aikata haka ba. Yanzu kin kara jin maganar akwatunan...... maganar ta katse lokacin da idanunta suka sauka akan gurin da akwatunan suke, shakku ya dar su a zuciyarta. Ina akwatunan ta furta a fili Hajiya Talatu ta kalli gurin da sauri,tace "Lallai kam hankali shi ke gani,Talatu ta furta ta mike ta nufi gurin tana fadin Sam ban kula da ba wani abu a dakin nan ba. A gigice Anty ta fita ta nufi falo tana kira Hafsa. Hafsa ta fito a gigice tana fadin "Lafiya Anty? Tace Halifa yaushe ya kwashi akwatunan shi?Hafsi ta taɓe baki wallah har kin tsorata ni. Da rana ya kira su Anty Umma da su Maman Nana suka raba suka tafi."

Anty ta kara zaro ido bai taba ba kannenta wani abu ba shawarar ta ba,bare abunda yake dakin ta. Anty tace "Lallai sabon abu to ba matsala nima na kwashi rabo na ,gara ma ace su ya ba da ya ba waccan shegiyar matar tashi ko da dai na gama da babinta fatana su fusata su kai shi kotu kafin ya motsa na saka lauyoyin da za su ji min da shari ar, ta dubi Talatu Ina alfahari da lamari da ke.

Hajiya Talatu ta ce 'Ni kuma fargaba ne ya cika ni, barin in hada kayana asubahin fari zan dauki hanya in tafi gidana sauran bayani zamu yi a waya tunda na miki me wuyar.Hafsi ta ce "Gara kam ki tafi domin wani huci na ga yana yi

Please Login or Register in order to submit comment