Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Sulaiman ya shiga ya sanar mata zuwan Halifa. Inna tace To kuma me ya zo ya yi min bayan ya yi min silar diyar tawa. .Sulaiman yace Inna duk ba wannan bane ki saurare shi muji abinda ya kawo shi, domin shima yana cikin tashin hankali yau din nan ya dawo daga Dubai ya kasa hakura gari ya waye ya taho kuma kin san bai fa gama abinda ya kai shi ba ya dawo. Inna tace "Ummm Ai sai ya shigo din muji kuma wace karyar zai yi min.

Asiya ta ce kai a zo har Unguwar nan in tafi banga Inna ba,kai gaskiya dai da sake, ta duba lokar mota ta dakko face marks ta saka ta fita tunda kayan jikinta irin rigar nan ce wadda ke hade da mayafi ta san ba wanda ya san ta da kayan. Unguwar su ce ta san duk wani langu mara haske dan haka ta sakada ta isa kofar gidan su har ta ci karo da Abba suna fada da wani yaro yaki kamar ta raba su sai kuma ta tuna, ya sheko da gudu ya bige ta ya waigo yana fadin yi hakuri,ta ki kallon shi amma shi sai ya tsaya yana kallonta ta dan waigo ta ga ya tsaya kamar yana son ya gane ta sai kawai ta wuce gidan ta yanke wani lungu ta tsaya, ta dan leko sai taga shima ya biyo zai leko lungun sai kawai ta ci gaba da tafiya.Taji ya daga murya yace "Asiya! Asiya!!! Kai gaskiya sun yi kama ashe ba ita bace." Ya fada tare da juyawa. sai da ta tabbatar ya fita a lungun ta fito ta fada gidan su ta makale a soro. Tana jiyo yadda Halifa ke yi wa Inna rantsuwa da abinda zai kashe shi cewa bashi da wata masaniya akan sakin. Inna kuma ta dage akan cewa gaskiya dai Asiya ta saku duk ranar da Allah ya bayyana ta to gaskiya dai ba matar shi bace. Cikin dai in ka yarda na ka ne to ba maganar kotu. Halifa yace Inna "Dana ne kuma mata ta ce, Asiya Allah shine ya tsare ni da ganin ranar da zan furta kalmar saki ga Asiya, me ma zata yimin har haka,wallahi Inna makircine kawai na wadan da ke bibiyar mu.Abinda kawai za ayi shine in har zaki gane Yaron da ki kace ya kawo sakon to abin zai zo da sauki zan gano wanda ya rubuta wannan takardar.
Inna ta ce "Zai wuce Antyn taka ce ta ke aikatawa,domin dai bata kaunar yarinyar nan,har gidan nan ta zo ta fada min, kai ni ai ko bakai ka yi sakin nan ba, dole ka hakura da yarinyar nan,dan bazan jure ba sam." Halifa yace To Inna yanzu dai ki kwantar da hankalin ki zan yi bincike tare da kokarin gano inda Asiya ta ke, daga nan kuma ko mai zai warware dan Allah Inna kiyi hakuri insha Allah zan nemo Asiya.

Tace "Allahu ya bayyana ta. Sai dai fa kamar yadda nace hakuri dai za ayi ko ka ganta yadda yan uwanka basa sonta. Da sauri Asiya ta fita ta koma gurin mota domin kar Halifa ya fito.
Tana cikin motar tana kallon dawowar shi,Halifa namiji ne kamar irin na littafan nan da zaka ji ana fada, kowace mace zata so ace Halifa mijin tane ya kai namiji ko ta ina. Yana ta dorawa yara tare da Abba kayan abincin da ya sai musu ita bata san ma ya siya ba.

Ya rungumo ta bayan ya shiga motar, yace kyakykyawata insha Allah Inna zata hakura amma ba da gaggawa ba, sai dai munbi mun gano kowaye ke aikata wannan sharrin .Asiya tace "To Allah ya tona shi. Ya sake ta suka kama hanya duk sun yi shiru kowa yana tunani.
Halifa ya katse shirun da fadin, "Baby, shin akwai wani wanda ki ke zargi ne ke? Asiya ta dan yi dim sannan tace "Anya kuwa?" Yace Inna ta fada min wasu abubuwa da Anty ta yi miki wanda ni bansan da su ba,kai tsaye Inna tana zargin Anty ce ke shirya duk wadannan abubuwan.

Asiya tace "Gaskiyar magana Yaya ka yi hakuri amma ka binciki Anty sai dai ina rokon ka kabi a hankali kuma ni abinda ya sa kaga ina ta rufe maka komai saboda na ga irin tashin hankalin da ka ke shiga ne game da lamarin Anty. Halifa ya numfasa ya ce Asiya kamar yadda ki ke so da kaunar Inna haka nake son Anty,bansan Uwata ba ita na sani, duk wata Soyayya da da zai yi wa Uwa ita nake yi wa Anty. Amma a wayi gari tana yimin irn wadannan abubuwan kice bazan shiga tashin hankali ba. Ya kai karshen maganar da kai duka jikin sitiyari tare da rishin kuka.

Asiya cike da tashin hankali tace Yaya to ka tsaya muyi magana yi fakin. Bai saurare ta ba ya ci gaba da tafiya cikin wani mugun gudu har gida.

Ko kashe motar bai yiba yafita ya nufi cikin gida. Asiya ta rasa yadda zata yi ta kashe motar cike da tsoro Allah ya sa ta murda makullin sai kuwa motar ta mutu.

Ta nufi ciki sai dai wani abin tsoro ta same shi ya yi fashe fashe ya yi jifa da abubuwa a falo yana dada kai wa bango duka yana cewa yanzu da wa kuma zan yarda in har uwa zata cutar da danta.

Hannuwan shi suna zubar da jini. Da gudu ta je ta kwakume shi ta baya tana fadin haba Yaya sai kace ba musulmi ba, hankade ta ya yi, ta fadi cikin kirsa ta ce wayyo Allah cikina. Da sauri ya nufo ta cike da tsoro yana cewa Baby ya daga ta cak zuwa kan gado ya kwantar kin gani ko shiyasa bana son in raina ya baci a zo kusa dani, me nene tashi babyna kinji ciwo? Ina waya ta bari in kira likita. Baiga wayar ba dan kuwa can ya baro ta mota. Tashi in kai ki Asibiti. Asiya cikin nishi ta kama hannun shi ba zan iya ba ka bari cikin ya dan lafa sai muje.
Ya zauna yana mata sannu ta ja ji ki ta dora kanta a cinyar sa yana shafa mata kai tana nishi har dai ta gaji sai ta yi lamo kamar ta yi bacci, shi kuma yana zaune ya zuba mata ido wai baya son ya motsa kar ta tashi.

Kusan minti goma sai ta dan motsa ta tashi zaune ya kai hannu ya shafa cikin ta Yaya kinji sauki. Ta tura baki,na ji sauki, Yaya ashe zaka iya duka na?" Yace "kiyi hakuri in raina ya baci ne ban iya fushi ba, ki daina zuwa in kinga na fusata.

Asiya Ta ce "To yanzu sai ka tashi kaje a wanke maka hannun ka ko? Yace ai ya daina zuba zan gyarashi yanzu akwai akwatin gaggawa.

Kwanan Anty uku a Asibiti kullum Halifa yana zuwa kuma shine ya biya kudin Asibiti. Bai nuna wa Anty komai ba.

Yanzu abinda Anty ta gane yin amfani da rashin lafiya dan ta tursasa su. Saboda likita yace kar a dinga bata mata rai . Halifa ya sake sai mata gado da kujeru yace Bros ya sai mata TV da sauran su.
Haka kuma ta uzzura batun auran Bros babu dama ya yi gaddama dan tsoron kar ciwo ya ta shi su ke yi ,dan abu kadan sai ta soma jirin karya kamar zata fadi sai an kamata an zaunar.

Cikin Asiya yana ta girma sauran wata daya ta haihu tuni duk wani abu da ake bukata Halifa ya siyo musu shi. A na tsaka da bikin Bros wanda Anty ta matsa sai anyi, ta tilasta ya gyara gidan da Halifa ya bashi nan zasu zauna da amarya. Bros bai halarci komai na bikin ba,yana gida tare da matar shi yana lallashin ta,kukan ta daya ita dai kar ya canja mata. Ya kuma daukar mata alkawarin kar ta tashi hankalinta ita kadai yake so.

Asiya tana kwance jikin Halifa tana mishi mitar ita dai kar yace zai kara aure dan ita wallahi baza ta zauna da kishiya ba.

Halifa yace bazan miki alkawari ba, Mahaifina matan shi hudu,ance har ya rasu hudu ne suka yi masa takaba,kuma ance ko wata ta mutu ko ta fita baya jimawa yake maye gurbin ta. Ya dago fuskarta suna kallon juna yace nima kuma akwai alamar haka Baby in har zaki kula za ki min adalci ga yadda nake damun ki,da akwai wata yadda cikin nan na ki ya girma ai da kyale ki zan yi sai kin haihu.
Asiya ta turo baki tace "Amma ka fadi tsakani da Allah na taba raki ko in hana ka hakkin ka, ko so nawa ka bukata bana nuna gajiyawata." Halifa yace na sani kina kokari,amma ki sani in kika haihu dole mu hakura. Sam Asiya bata san tana da irin wanna kishin ba, ji ta yi wani abu Yama mata tukuki a kirji,ta soma kuka,kamar wasa sai ciwon baya,sai mara. Duk basu san haihuwa bace, dan sun ga wai EDD dinta da saura yana ta lallahi yana fadin wasa ne amma abu sai ta azzara ya ke ga dare Halifa ya kira likita yace ya kaita Asibiti shima yana gurin zai yi wa wata tiyata ne. Asiya ta ji ciwon da bata taba jin irin sa ba, dan haka ta shiga neman yafiyar Halifa da kuma bada sako zuwa ga Inna...........



*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[10/30, 22:19] Ummi Tandama😇: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ?mode=wwt

Ganin yadda ta ke shan wahala likitan ya bada shawarar kawai ayi mata aiki ya kara da cewa dama ta yi karama kwarai da haihuwa kawai dai ya bari ya ga ko zata iya haihuwa ne da kanta.

Take Halifa ya sa hannu aka soma yi mata shirin shiga tiyata. Ana yunkurin saka mata ledar fitsari sai wani nishi yazo mata kafin su yi wani yunkuri haihuwa ta zo. Halifa yana ta kai kawo yana ta addu'a Allah ya sa a yi aikin cikin nasara. Gashi ba bu dama ya kira kowa kar a san inda take. Aka fito masa da jariri nade cikin tawul ya sha kayan sanyi likitan da kanshi ya miko masa ɗan yaro namiji .kyakykyawa yana fadin na taya ka murna. Cike da farin ciki da kuma rawar jiki Halifa ya amshi gudan jininsa hannunsa na rawa dan shi ba ya iya daukar jarirai.
Yace "Yanzu wannan da na ne? To ita kuma Mamansa din fa tana ina ne?
Likitan yace tana cike da koshin lafiya ina yi maka albishir da cewa ta haihu ne da kanta. Yanzu nurse za su gyara ta. Halifa ya ce "Alhamdulillah " To bari mu zauna mu jirata,goron albishirin ka kuma sai mun samu nutsuwa. Likita yace sai a kira wayar a sanar da yan uwa da abokan arziki. Halifa yace zan sanar da su.
Bayan likitan ya koma ciki Halifa ya shiga tunanin yanzu shikuwa ya zai yi gurin kula da ita da kuma jariri ita kanta bata san ma ya zata kula da kanta ba bare Yaron.

Ko ya kira Inna? Kai Inna zata raba su ne.Anty kuma bai gama binciken da yake yi ba,Allah ya rufa asirin su kuma har yanzun ba a san suna tare ba.

Ya tashi da sauri ya nufi office din likitan yana rungume da dan a kirjin sa. Likitan ya taso yana cewa a kwai wani abu ne? Halifa yace a a, Ina son ka ba ni wata nurse da zata kulamin da su a gida kamar yadda zata kula da jikinta da kuma shi yaron nata. Likitan ya dan yi mamaki har ya kasa shiru, yace amma wannan mai sauki ne da ka sanar da dangin ka,ko nata.

Halifa yace "Ka san kowa da irin nasa tsarin ni kuma dai haka nawa ya ke. Likitan yace To wannan ba zai zama matsala ba, za a duba nurse guda daya da kuma dattijuwa ko a cikin masu kula da tsaftar mu ne sai mu baka suna zuwa suna duba su.

Asiya kamar ba ita ce ta haihu ba, tana zaune a mota rungume da danta ta kafa mishi ido tana jin wata kaunar sa, suka nufi gida. Halifa yana tuki a hankali kamar ya dakko kwai.
Asiya ta kalle shi cike da murmushi tace yana kama da ni fa. Halifa yace "Ko dai da ni, ki kalli fuskar shi sosai ki kalli hancin. "Asiya tace da kuwa anyi kyakykyawan yaro Allah dai ya yi masa albarka. Halifa ya sa hannu ya shafi kuma tunta Ameen Babyna.

Kwanciya ta yi dama likita yace ta ci abinci ta sha magani ta kwanta ta huta tunda Halifa ya matsa kan cewa su tafi gida..Halifan ne ya hado mata shayi zafin ruwa baya baya ta sha ta kwanta. Shi kuma dama Halifa ya kwana gadin su sai bayan ya yi sallar asuba sanna ya kwanta.

Kuka Yaron ya tada Asiya bata san ya zata masa ba.gashi tana tausayin Halifa ya samu bacci.

Ta dauki wayar sa ta fita falo ta duba lambar likitan ta kira shi,bayan sun gaisa ta ke sanar da shi yaron ya ta shi yana kuka. Yace ina baban tace yana bacci, Likitan yace yunwa ce kawai ke damun baby zan masa text na madara sai ya siyo yanzu kafin ruwan nono ya zo,ki ci abinci ki sha shayi sosai da kunun kanwa dan ki samu ruwan nono da wuri, kar yaron ki ya rame. Asiya tace to tayi godiya.

Kukan yaron ya farkar da Halifa,ya ce "Ya baki tashe ni ba?" Ta fada masa yadda suka yi da likitan yace To bari in je neman madarar ya dauki makullin mota da sauri ya fita yana kiran wayar likitan yana fada masa abinda zai siyo wanda maijego da jariri ke bukata a yanzu.

Ya dawo ya samu yaron yayi bacci. Ba jimawa Nurse Anty Amina da gyatuma Wadda tace Hajjo ake ce mata, suka iso. Anty Amina tana tsaye Hajjo ta wanke yaro tas sannan ta yi wa Asiya wanka ta gasa mata jiki. Ta ci abinci ta fito fes.

Anty Amina ce ta nuna wa Asiya yadda zata hada mishi madara da kuma yadda zata bashi, sannan ta gargadeta akan cewa da tasamu ruwan nono to fa ta aje madarar nan nonon Uwa shine abu mafi amfani a gurin jariri. Ta dubi Halifa tace Ranka ya dade ai ni ba sai nazo kullum ba jifa jifa zan ke zuwa, amma ita Hajjo sai ta zo kullum sai dai ku samu mai aikin gida kuma kafin matar gidan ta yi kwari. Halifa ya yi godiya tare da bata kyautar kudi.

Hajjo tace akwai wata jikarta ta zo daga maiduguri in suna so sai take zuwa tana ta ya Asiya girki da kuma shara. Halifa ya ce ba damuwa su rinƙa zuwa.

Kwana biyu Halifa ya kwashe bai leka kasuwa ba, ga abin fadi babu dama shi ya yi wa dan sa huduba da sunan mahaifinsa wanda shima shine sunan sa wato Umar.


Halifa ya samu Sulaiman ya ce, Dan Allah zan baka wani aiki ne, na fara shi ni kadai amma naga bazai yiwu ni kadai ba.

Tun lokacin da aka yi posting din video wanda ya shiga dakin mata ta, na ke bi comments na mutane duk posting din da na gani lokacin na dauki lambar wani wanda yace shege Mansur kayi nayi yau Kaine kuma da kwartanci. Na bibiyi wanda ya yi wannan rubutun ta hanyar number sa da ke a kan shafin sa, na ga cewa tela ne shi,dan haka na bukaci zan kai masa Dinkin mata ta. To abinda nake son ka min guda daya ne,zan baka kaya ka kai masa a kofar ruwa yake,sai ka ce masa kai ne kuka yi chatin da shi,ka kira shi da lambar ka,kace masa shine daya layin ka.

Sannan ina son ka tambaye shi Mansur kayi nayi,cikin hikima na san dai ka san me zaka yi,sai muji ta inda zamu same shi.

Sulaiman yace "Ka yi dabara,amma kuma ba abin ya wuce ba?"
Zai dai wuce insha Allahu iya shi in na kama zuciyata zata samu saukin domin zai fito min da duk wanda ke da hannu akan komai.
"Haka ne Sulaiman ya fada cike da kwarin gwiwa. "Zan kokarta in ga na yi maka wannan insha Allahu za mu samu nasara.

Bros bayan amarya ta tare ba yabo ba fallasa tana ta kokarin farantawa ango dan haka ya zubar da komai ya kula ta aka sha amarci, sai dai tun safe yake barin gida sai kuma dare, can yake tafiya gurin maman Nihal ya yi wanka ya yi shirin kasuwa, da ya ke su maza yayan Baban su ne,sai yake nuna mata bai yi komai da amaryar ba,ita kuma tana ta lallashi wai ya kula ta saboda hakkinta da Allah ya dora masa.

Zuwan Anty uku gidan bata samun shi amarya kuma ta tabbatar wa da Anty cewar gida yake kwana sai dai yana fita da wuri dan wani lokacin ma a gidan wanka na kasuwar ya ke yin wanka ya canza kaya. Anty tace "gi
Gidan wanka kuma duk bandakunan da ke gidan nan amma ace sai ya yi wanka a kasuwa? " To rigima kuke yi tace a a lafiya lau muke.To yana cin abinci ko baki soma girkin ba?" Amarya tace Gaskiyar magana bai tabacin abinci na ba. Fitar wuri yake yi, in ya dawo kuma sai ya zo da nama ko kaza. Anty tace "Kuma ke hakan ya miki?Amarya ta fara jin haushin tambayoyin Anty dan haka tace Umm.Anty ta fahimta yarinyar bata son maganar tace Nifa kamar Uwarki ce shiyasa ki ka ga ina tambayar ki domin in ya miki ba daidai ba in taka masa birki,amma tunda ke kin ce ba matsala shike nan .

Ta mike tana fadin ni zan tafi. To ki gaida gida. Har ta kai bakin kofa ta tsaya, ke kuma haka ki ke yi wa bakin duk wanda ya zo ba dan cincin ba lemo ko tayi ruwa zuwana uku fa. Amarya tace "Na ga ai an kai muku na ku ne cincin din da sauran kayan gara,nawa na baki ne,ke kuma Anty ai ba bakuwa bace. To ruwan kuma fa shima bazaki iya bani ba. " Dan ruwa sai in baki mana ruwa dai Allah na tuba dawo ki sha."Amarya ta fada tana yatsina baki. Anty tace Allah ya amfana,na yi miki magana ne kar wani ya zo bare a yi masa haka ni ai ta gida ce. Amarya ta yi yar dariya. Anty dama ai dan ke ce shiyasa nima na yi haka.

Maganar ta doki Anty ta dawo ta tsaya, kina nufin idan Uwarki ta zo gidan nan itama haka zaki yi mata?
Amarya tace "Anty ina tabbatar miki daga nan har in shekara ba lalai uwata ta zo gidan nan ba matsawar lafiya lau,ita kuma haka Allah ya yi ta da kamun kai zan ce ko kawaici,bare har ta doko sammako,to kin san Allah Anty gidan Yayanmu shekara biyu matarsa ta haihu sai lokacin ta taka gidan ta yi musu barka,in anyi maganar bata je ba sai ta ce me zakaje gidan yaro ka yo masa, indai suna lafiya haka ake so,ni bana wannan gayyar sa idon da kwakwafi, da kalan nema raini gurin yara. Anty ta gama gane yarinyar nan ta fake da Guzuma ne take harbin Karsana. "Wato ni ki ke yada wa magana baki san ni ba ko? Kiyi a hankali kar ki dakko irin wannan ta kun tsakanin mu, an bini ma ya aka cika bare kuma Anja da ni. Amarya ta ce kiyi hakuri Anty yadda ki ke zato ba haka nake nifi ba.Anty taa wuce fuuu a fusace. Amarya ta raka ta da harara tana fadin nima din ba sani na ki ka yi ba.


Kafin kwana hudu Asiya ta yi shar da ita, ta gyagije, abinda ke ta damunta ba taron suna. Halifa yace kar ki damu zamu yi sunan mu kuma idan Allah ya yarda muka warware komai sai mu yi wa jama a na su.

Ana gobe suna Halifa ya kawo wa Asiya kaya akwati uku da ya sa aka dinka mata, sarka takalma mayafai harda kayan ciki dangin pant.
Ya kawo raguna guda biyu da asuba aka rada sunan a masallacin unguwar su.
Sai lokacin makota suka san da mace a gidan har ta haihu, da suka koma gida suka sanar da matan su, kuma sun zo suna, Hajjo da jikarta Fati sune suka yi girki, tunda ba mai yawa bane. Gidan dai gaba daya ko mutum goma ba a kai ba. Halifa ya kira mai hoto inda ya dauke su kala kala shida Asiya da Jariri mai sunan Ubanshi da kakan shi. Hajjo ce ta samo wata 'yarta suka yi aikin raguna. Asiya ta basu da yawa ta ɗibi na cin su sauran ta ce
su sa a cikin mai. Hajjo tana zato aiki ya kawo su Asiya Kano dan haka ba su da kowa.

Tun ranar farko da Fati jikar Hajjo ta dora ido akan Halifa sai ta kasa sukuni bata taba ganin namijin da ya kwanta mata kamar Halifa ba,gashi matashi mai aji ga kudi ga kyan siffa,tana ta mamaki yadda akayi ya auri Asiya wata
lange lange da ita kamar kara, duk da daular da ke
gidan amma gata nan ita ba wata kyakykyawa ba. Ta sha alwashin sai wannan gidan ya zama na ta. Haka take sakawa kullum in tana zagaya gidan ko tana aiki a kicin.

Asiy tana zaune a falo a na ta gwagwagwa da shan nono har yanzu baya iya kamawa saboda irin mara kunyan nono nan gare ta wanda ke tsaye car dole sai dai ayi sama da dan ita kuma hannuwanta gajiya suke sai Hajjo ta tallafe sannan in ya samu ya kama yana fara tsotso gaba daya sai zafi ya isheta. Halifa ya fito yana rike da kugu yana murmushi yana kallon ta, birge shi hakan ke yi, ta dube shi cike da shagwaba ta ce Yaya kawai a dakko mishi wannan abin tsotson ko a hada mishi madara, zafi nake ji. Yace Baby kin fiye raki kema haka kika yi wa Inna. Hajjo ta yi yar dariya tare da fadin a haka zata saba Maman nata ne ba masu sakkowa ba shiyasa dole sai a hankali. Halifa ya matso ya sa yatsa ya lakuci kumatun yaron tare da fadin Babana ayi wa Momy a hankali ka ji ko? Suka sa dariya. Fati dake can gefe tana goge goge ta shagala da kallon Halifa a jikin shi ya ji kamar ana kallon shi ta gefe TV ya kalli gurin ta yi saurin dauke kai tana kara kakkabe gurin. Ya lura da irin kallon da yarinyar take mishi ba tun yau ba.
Yace Baby ni zan fita tace Kadan jira mana Yaya mu raka ka? Yace na yafe baki ne da ni yau yan Niger za su dauki kaya. Su sun fi son su ganni. Asiya tace To Yaya sai mun yi waya Allah ya bada sa a da rabo mai amfani.Yace Ameen ya wuce.

Ji ya yi an ce Sannu Alhaji ya waiwaya ya kalli gurin yarinyar nan ce, tace ina kwana "Lafiya" ya amsa yana mai ci gaba da tafiya.Sai da ya shiga mota sannan ya kallo gurin har yanzu yarinyar tana tsaye a gurin tana kallon motar. Ya dan taba baki ya fice.

Sulaiman ya hadu da Tela bayan ya kwatanta masa inda yake ya bashi dinkuna Tela yace "Ina gwajin kayanta?" Kash Inji Sulaiman bari zan turo maka, na shafa a,yace "To ba matsala. Tela yace bari a kawo maka lemo ka sha tafiya gashi duk da bamu da nisa da titi sai gashi ka wahala." Sulaiman yace ruwa zaka bani, Nifa zuwa na daya nan Unguwar lokacin da

Please Login or Register in order to submit comment