Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani abokina Mansur kayi nayi.Tela yace Kayi nayi dai wanda na sani dan gidan Dala?Sulaiman yace shi mana wani baki haka. Tela yace shine kuwa ai yana gidan yari ka san kwanaki an kama shi da wata matar aure,shine ina ga dalilin zuwanshi,ance yana gauron dutse.Sulaiman yace Allah ya kyauta Shi kuwa Mansur me ya kai shi irin wannan danye aikin. "Son zuciya mana,da Sana arka da komai kasan pop yake yi ya iya aiki kuma yana samu. Sulaiman yace azal din kenan. Tela ya kawo wa Sulaiman ruwa suka yi sallama bayan ya sha.



*✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[11/6, 08:25] Ummi Tandama😇: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ?mode=wwt

Halifa ya yi murna da Sulaiman ya sanar mishi amma duk da haka sai yace ina son ka samo min cikakken sunan da zan same shi idan naje gidan yari. Sulaiman ya sake kiran Tela ya tura masa gwajin dinki da kuma kudin da suka daidaita,sannan yace masa ko yasan cikaken sunan Mansur dan zai kai masa ziyara can gidan yari din. Tela Yace Ai gaskiya kayi nayi kamar sunan mahaifinsa Garba Dala,kasan tsohon dan canji ne.

Sulaiman yace To hakan ma ya yi Insha Allahu zaije.Ya sanar da Halifa, komai.


Fati ta kalli Kakarta suna cikin Keke napep tace, Ni kuwa Hajjo kin kula yarinyar nan da muke yi wa aiki kamar wata wawuya ko? Hajjo tace kamar Yaya me ki ka ga ta yi? Fati ta ce, kawai dai haka nake ganin Hajjo tace ina kula da yadda ki ke kallon mai gidan nan wallahi ba ruwana kar ki ja abinda za a kore mu. Fati ta ce ai ni da zan samu lambar sa..... bari dai zan dauki wayar ta in dauki lambarsa.Hajjo ki yi tunani ace jikar ki ce a cikin wannan gidan da sai dai in ware miki wannan falon da su ke cewa na baki in samo miki masu aiki,ki saka goma ki tsoma biyar.

Hajjo ta saki dariya ki ce sabuwar Duniya,da dai cewa yai yana sonki shine sai in murtsike ido na in goya miki baya, amma yanzu ki ce zaki sa kanki in yaki fa? Fati tace ai nayi mafarki munyi aure da shi.

Hajjo tace "Tabdi to wallahi ki bi a hankali na fada miki.

Asiya ta sha wanka tana sanye cikin dogowar rigar atamfa ta yi kyau sosai tana dauke da ɗanta a kafaɗa. Ta fito Halifa yana zaune yana kallon TV Ta zauna tana fadin har Fati ta zo kenan naji kamshi ya cika gidan. Yau ba tare suke da Hajjo ba ga maigidanta yana jiran wanka Halifa Yace "Ke kam yanzu ai kin iya wankan ko?Tace tun yaushe na sati daya tayi min. Ya kai hannu ya sagalo wuyanta, kyakykyawata wallahi na takura fa, wai dole sai kinyi wata arba'in ne? Dama ance mai mace daya aminin gwawro,tace Kamar yaya? Yayi dariya Yace To nima dai yanzu ai daidai muke da wanda ba shi da ita. Fin sati biyu saidai a bani shayi da lemon tsami. In ta lashe yawu,kin ga da ku biyu ne shike nan.... Asiya ta yi saurin saka hannu ta dafe bakin Halifa cike da shagaba ta ce, Ka ce Allah katuba, dan gaskiya bana son zancan nan ko da wasa, kana son in mutune? To na ji matsalarka zanji da ita insha Allahu. Amma ka yi min alkawarin cewa ka daina tunanin cuso wata tsakaninmu. Ina fa da kishi Yaya akan ka ba zan iya yin kisa ba,amma ni za ka ga na yi fut na mutu.

Kafin ya yi magana sallamar Fati ce dauke da tiren kayan karin kumallo,ta gaishe su sannan ta nufi Dinning ta shirya ta kuma zuwa ta kwaso sauran. Sannan ta dan matso gurin su kamshin humrar da ta shafa ta bude su,tace Anty an gama shirya karin kumallo. Asiya tace Fati wannan turaren na ki yana da kamshi kina sai da humra ne? Tace "A a daga gida na zo da shi." Amma kin iya hadawa ko?" Fati tace " Ban iya ba wallahi." Asiya tace Kina Maidugurin? Fati a ranta tace ai bazan hada miki bane, a fili tace "Kinsan ba kowa ya iya ba. " Asiya tace OK Baba Hajjo fa bata iso ba ne? Fati ta kalli Halifa wanda ke danna waya kamar baya jin su,ta ce "Zata dauraye kayanta ne,shi yasa, amma yanzu zata karaso. Bari in gyara dakin ku kafin ku gama." Asiya tace to. Tana wuce wa Halifa yace gaskiya turaren da kamshi ki tambayi Hajjo din ko za a samu masu saidawa. Asiya ta kafa mai ido tana kallon shi ta kasa magana. Har sai da yace, Aƙwai kuskure a magana ta? Cike da gatse ta ce babu. Tashi muje ka karya. Fati ta na gyaran daki tana ayyana yadda nan da lokaci kalilan zata mallaki wannan kyakykyawan daki da kuma mai dakin. Ta dauki jallabiyar Halifa da ke kan gado ta rungume tana fadin I love you so much. Idan taga abin Asiya sai ta yi tsaki kafin ta gyara. Tana ganin ta fi Asiya wayewa kuma ta girme mata bata zaton zata sha wata wahala gurin karbe mata miji,gashi ita ba ta da kowa bare wata ta bata shawara,ta fada kan gadon tana manne da rigar Halifa a kirji tana ta sumbatar ta.

Kunun gyada ta yi musu da kosai kamar yadda Asiya ta fada mata tun jiya,sai dai ta kara da farfesun kayan ciki wanda Halifa ya samu ya yi ta sha da alamu ya yi masa dadi. Domin magana ta gaskiya ya yi dadin kuma Fati ta iya girki. Haka ranar da ta yi miyar kubewa Halifa bai boye santin shi ba. Sannan ko shayi mara madara sai yace kisa yarinyar nan ta dafo min shayi. Asiya ta fara jin haushin Fati to amma sai ta lallashi zuciyar ta domin kuwa fushin fari ba nata bane. Za dai ta dauki mataki ne. Fati ta fito bayan ta gama gyara dakin har lokacin suna kan Dining yana fada mata zai je gidan yarine ziyarar wani dan kasuwar su. Asiya ta daga murya ta kira Fati. Fati ta zo gurin tana satar kallon Halifa wanda ya ki dago kai,yana danna waya. Asiya tace Fati da Allah in zaki zo gidan nan daga yau kar ki kara saka wannan turaren. Cike da mamaki Fati ta kalleta "Saboda me Anty?" Asiya ta kalli Halifa, saboda Yaya yace baya son kamshin yana tada masa zuciya. Fati tace To insha Allah ba zan sake sakawa ba,ta kalli Halifa wanda kunya da mamaki suka hana shi ya dago kai. Tace "Alhaji a gafarce ni bazan sake ba. Halifa ya dago ya dube ta, kar ki damu. Abinda ya iya furtawa ke nan ta juya ya bita da kallo,reshen zuciyar sa yana kawata masa surarta, sai ya sunkuyar da kai. Tana fita Hajjo na sallama. Suka mike a tare Asiya ta saba Danta a kafada suka nufi falon Hajjo ta amshe shi suna gaisawa. Halifa ya nufi daki bayan sun gaisa Asiya ma ta nufi dakin dan dakko wa Jariri kayan da za a sa masa in anyi wanka. Halifa yana bakin gado yace "Ke zonan ki fada min yaushe kika soma karya da kulla sharri? Asiya tace bari in bawa Hajjo kaya inzo in fada maka.

Ta maida kofa ta kulle sannan ta zo ta same shi, ta zauna a cinyarsa. Da me kake tambaya? Ya kama kunnenta ya matsa har ta yi dan kara,yaushe ki ka soma karya? Tace yau na fara, kuma akan ka bazan daina ba. Ta haye kirjin shi bayan ta tura shi ya kwanta ta rike masa kunne tana fadin kar ka sake ka kara cewa turaren wata da dadi, nawa kadai zaka yaba kaji ko? Yace "Ai ban fada mata ba fa ke na fadawa." Tace shine saukin ai. Ta soma yi masa wasu wasanni da ya fara neman rasa nutsuwar shi, yace Kar ki haukata ni Baby ke gashi kina cikin wani yanayi da sai hakuri. Tace Ai tunda ka fara kwadayin aure ka daina fita ba nutsuwa. Zan gwada maka banbancin mai mace daya da gwauron da ka ke fada. Haka kuwa da wasanni saida ta sa shi ya nutsu, yace lallai yarinya ashe kinsan yadda zaki yi dani in kina fashin salla amma kike kyale ni ? Tana ta dariya, sannan ya yi wanka ya fita zuwa Gidan Yari.

Anty ta kira Hajiya Talatu yafi a kirga bata same ta ba, layinta ma baya shiga,tun ranar da tijararren nan ya kwashe mata kaya. Amma yau sai ga kiran Hajiya Talatu, cike da mamaki Anty ta daga, ta soma zazzaga masifa Lallai Talatu kin nuna min ke cinnaka ce baki san na gida ba. Ni zaki cuta shiyasa ina ta kiran ki amma ki ka ki daga min waya. "Ba haka bane wallahi." Hajiya Talatu ta katse Anty, Ma u bata fada miki bane, Ina gidan yari a Kaduna, yau din nan na fito ke na fara kira Sahiba yanzu haka kin gani a gida ko ruwan gidan ban kai ga shaba.

Ina tun ranar da na baro gidan ki,to tun ranar ina dira Zariya ko minti talatin ban yi ba a gida, wasu mutane suka kamani suka danna a mota na zata ko yan kidinafin ne, kai tsaye muka tsaya bakin wata kotu a Kaduna aka amshi wata takarda aka kaini aka jefa ni gidan yari ba tare da nasan abinda na yi ba.kuma har zuwa yau da aka je aka kira sunana akace in fito za akaini kotu sai aka tsaya a hanya aka ba wani mai mashin ni aka ce ya kaini tasha ya sa ni a motar Zariya kin ganni nan dirata kenan.

Anty ta cika da mamaki,tace "Ke to da waye ba kya ga maciji ne har haka? Hajiya Talatu tace Wallahi Sahiba ba na ce ba, nasan dai akwai masu jin haushina da yawa, wanda ba su da yadda za su yi dani,dan haka dole sai na nutsu zan gane waye, duk ba yadda ban yi ba amma ko damar yin magana da wani ban samu ba.
Anty tace "Tabdi, to Allah ya kyauta ki ce dai kina cikin matsala ni dai nan damuwar da sauki Asiya ta haukace ta ma bace ba a kara ganin ta ba. Kuma anyi bikin Wannan dan naki, sai dai kuma kamar fa na debo ruwan dafa kaina ne, amma zanji da ita. Kije ku huta ki kuma samo bakin zaren matsalar ki sai ki zo mu san ta kwatanci. Haka dai suka yi sallama.


Da Sulaiman sukaje da kuma lauyan shi, Dan haka kai tsaye suka shiga suka bada suna,an dan samu jinkiri kafin aka gano Kayi nayi. Yana ganin Halifa ya gane shi,nan take hantar cikin shi ta kada. Bayan sun zauna kayi nayi ya soma fadin mai gida dan Allah ka taimaka min wallahi ni ba kwarto bane wallahi san kudi ne zan kai kudin aure gidan su budurwata gashi son zuciya na kare a nan. Kuma yarinyar nan nasan na rasa ta
"ka shirya fadin gaskiya kenan ko? " Zan fada megida, domin na gane cewa Allah daya ne kuma bashi da abokin tarayya. Lauya yace ka bamu labarin yadda aka yi kaje dakin matarsa,daga nan sai mugani me ya kamata ayi?

Mansur kayi nayi. Yace To ni dai wani malami ne zan kira shi ko boka,naje gurinsa da neman taimako akan sana'ata abubuwan basa tafiya yadda ake so, sai yace ga aikin kudi in zanyi,nace zanyi indai ba sata bane.
Yace min zan shiga dakin wata mata ne a wani gida in yi kamar minti talatin, sai in fito za a bani dubu dari kawai dai in yi kamar naje kwartanci. Gaskiya farko na tsorata nace kar mijinta ya dake ni, sai yace Za a bani kudin magani daban. Na ce sai nayi tunani,bayan kwana biyu sai suka sake cewa sun kara min dubu hamsin to daga nan fa sai na yarda tunda sun min alkawarin baza su bari a kamani ba.
Ranar da na yarda matar ta zo har gidanmu ita da kawarta tace bazata bari a tabani ba,dan a gidanta zan yi aikin. Halifa ya katse shi, Kace ta ce a gidan ta? Yace kwarai kuwa. Lauya ya Dakatar da Halifa yace "Ka bari ya gama sai ka tambaye shi abinda ka ke son sani. Mansur ya ci gaba da fadin, nace amma kar a yi min Video tace sun yarda. Naje gidan na yi komai kamar yadda suka ce, amma sai gashi an dake ni, da kyar na gudu ta gurin da ta nuna min,kuma bayan kwana kadan aka kamani aka kai ni gidan yari ba tare da an kaini kotu ba, yanzu haka bansan zaman da nake yi ba, domin so daya mukaje kotu ko gaban alkali ba a kaini ba aka amso wata takarda aka kawo nan.

Halifa ya numfasa yace "Me kasani game da takardar saki da aka rubutawa mata ta? " Kayi nayi yace Megida wallahi bansan wannan ba, iya bayanin nan wallahi su na sani. Kuma wallahi ni ko ganin matarka ban yi ba har sai da ta fito ,ina shiga kicin na shige na boye har sai da suka kira wayata suka ce in fito, kuma duk maganganun da na fada mata na cewa tana zuwa guna wallahi sharri ne ku yafe min. Halifa ya yi murmushin takaici, yace Kasan cewa sanadiyar abinda ka yi yanzu matar ta bace ana zaton ma ta haukace ko?" Kayi nayi ya dauki salati yana fadin ya shiga uku. Halifa yace "Abinda ke bata min rai yadda gaba daya abin ke nuna cewa Anty ce ta hada shi." Kayi nayi yace Yawwa ita ce duk Anty ce ta hada komai wallahi. Da wata kawarta. Halifa suka fita suna tattauna wa akan abinda ya kamata ayi, Sulaiman yace zuwa za ayi a samu Anty a nuna mata ansan komai ina mai tabbatar maka sakin ma ita ce ta hada shi ba wani ba. Lauya yace "Ita ce mana, ai babu dogon bincike kai yanzu Halifa ya ka ke ganin za ayi, musa yansanda su kamota ne ayi case ko me kake gani? Halifa wanda idanun sa suka yi ja,zuciyar sa ta yi zafi a fusace yake ya daki gilashin motarsa na gefen da yake tsaye take ya fashe, suka rike shi suna fadin Haba haba wannan ai ba dabi'a bace. Halifa yace Me kuke son inyi ku fada min. Ya yi maganar murya a sama, har mutane suka fara tahowa,nan suka tura shi mota suna kwantar masa da hankali, Yace "Kamar kaine Barrister mahaifiyar ka ta yi maka haka, Yaya zaka mata ka fadamin?"
Duk suka cika da mamaki,yace wai mahaifiyar ka ce? Halifa yace haihuwata ne kawai bata yi ba,amma tun ina tsumma itace ta raine ni.Uwarmu daya.Barrister yace To zamu tattauna yadda za a bullo wa abin. Bayan su sauke Sulaiman sai Barrister yace Kasan ni na aje wannan yaron a gidan nan tun lokacin da ka turo min Video na abinda ya faru,kawar Anty ku din ma ni na saka aka aje min ita a Kaduna sai jiya na sa aka sake ta, da ka sanar dani halin da ake ciki, amma dole zamu sake dakko ta zuwa nan Kano din, sannan zamu kawo ta nan ayi case din in kuma baza ka yi case da suba,to dole mu hada su guri daya mu warware matsala,sannan shi yaron mu sa ya yi video ya wanke matar ka.



*✍🏻✍🏻HALIMA ABDULLAHI K MASHI*
[11/15, 17:31] Ummi Tandama😇: https://chat.whatsapp.com/K4eDi8FhbXk5887RdW2GrQ?mode=wwt


Koda Halifa ya shigo gida Asiya bata gane kansa ba,yana cikin bacin rai sosai, suna falo da Hajjo ya wuce daki, ta aje dan ta bishi da sauri ya jingina da sif ya dafe fuskar shi da tafin hannun sa. Taje ta shige jikin sa ta rungume tana fadin Allahumma ajirni fiimusibati. Yaya me ya faru,dan Allah kar ka daga hankalin ka, zo mu zauna ka fada min ko da banyi maka maganin abin ba za muyi shawara kaji Yayana. Kamar rakumi ya bita domin ta yi maganar cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Suka zauna bakin gado, Ya kalleta Asiya duk abinan da ke faruwa ya tabbata Anty ce ke hada shi, me na yi mata haka da take shirya min makirci kala kala, in kece matsalar ta ta fito fili tace min bata sonki, shike nan ni ina son ki sai kawai in muku tsakani ta yadda ko ganin ki bazata yi ba,ba sai ta yi ta wannan wasan kwaikwayon ba,harda yunkurin kashe ki, wai ma me kika yi mata?Hawaye suka soma zubo masa. Asiya ta saka hannu tana share masa hawaye, Haba Yayana bana son kana hawaye zuciyata zafi take yi, karka damu jarrabawa ce komai zai warware kamar ba a yi ba.

Zata gane kuskuren ta kuma ni na yafe mata saboda kai. Yace "Ni bazan yafe ba, zan bi miki dukan wani hakki na ki har sai ta yarda ta cutar da ke. Asiya ta tashi ta je ta bude karamin firjin da ke dakin ta ta dakko ruwa ta tsiyaya a kofi ta bashi ka sha. Ya karba ya shanye sannan ya bata labarin dukkan abinda ya faru. Asiya ta cika da mamaki amma sai ta boye mamakinta da damuwar dan kada ya kara shiga damuwa. Ta samu ta kwantar masa da hankali.
Ya fada mata abinda lauya yace.

Tace kar kayi shara'a da ita,ta ci albarkacin zumunci
da kuma 'ya'yanta, ka samu Bros ka fada masa dan kaji ta bakin sa, sannan ka tara duk wata hujjar ka sanan ka tara manyanku dan su san me yafaru, sannan saboda mu warware matsalar mu da Inna ita ma ta zo gurin.
Halifa yace kema kin kawo shawara amma zan duba. Asiya tace saboda ni damuwata yanzu bai wuce Inna ta gano gaskiya ba, sai nafi sakata in walwala.
Halifa yace kar ki damu fa, in yi miki ta wani mawaki da yace ko mutuwa baza ta rabamu ba,in tazo tare zata dauke mu. Asiya ta saka dariya.
Dama kana jin waka? Yace fisha ba.

Sulaiman ya samu Inna da hantsi ta idar da sallar walaha tana zaune tana Jan carbi, bayan sun gaisa yace, Inna dan Allah ki daure ki sanar dani wani abu daya, kila ta haka zamu samu bakin zaren warware matsalar Asiya. Inna Tace "An samu labarin Asiya din ne? A a ba a samu ba, bincike ne dai duk akan abinda ya shafi sakin ta,muna sa ran gano bakin zaren.

Inna tace wannan yaron dan gidan Fatsuma mai dashi ne ya kawo takardar yace wai Inji Halifa.Kuma da na bi bayan shi na na leka na hange shi, yana tafiya, Sulaiman yace Dan gidan Malam Danyaro kenan? Shi kuwa inji Inna Sulaiman yace to ba komai zan samu yaron inji wanda ya bashi sakon takardar saboda gaskiya Inna ba Halifa ba ne. Inna ta ce ni dai Allah ya bayyana min yata,yan zu nasan cikinta ya isa haihuwa, matsawar tana raye, ko akan bola ko wasu su taimaka mata,Allah yasa ta fada hannu na gari, kullum addu'a ta kenan. Hawaye suka zubo mata.

Sulaiman ya bata baki tare da kwantar mata da hankali. Kafin ya fita a gidan.

Anty ta fito zata fita sai ta ga a nata fenti a gefe da Halifa ya tashi, ta tsaya ta cika da mamaki ashe har anzo lokacin da za a dinga yin
abu ba shawarar ta kuma babu sanin ta,to Halifa ne ko kuwa Dady ne wanda aka ba wa gidan?

Ta isa gurin masu aiki,tace kai waye ya saka ku wannan aiki? Babban su yace "Sannu da fitowa Hajiya, Alhaji ne me gidan." Tace Tofa! Lallai kuwa mai gidan. Ta wuce tana danna waya. Ta kira shi ya daga, ko sallama babu tace Wai me kake nufi ne?Dan Halifa ya baka gidan shike nan sai ka dinga yin wasu abubuwa gaba gadi ban isa ka fada min ba ko?

Ya yi yar dariya "Habiba kikan so saka kanki a matsala meye abin daga hankali gyara ne na saka a yi mutane ne za su dawo ciki da zama." Mutane kuma! Ta katse shi wadanne mutane ina fatan dai ba dangin ka zaka rakito min ba? Dan wallahi sai in karbe gidan inga ta fadi. Dady yace kinga ba zancan waya bane inna dawo ma yi.

Anty tana mamakin yadda Dady ke yi mata musu dole sai ta sake bazama akan shi gaba daya asiran da ta yi sun karye a lokaci guda haka.

Dady ya shigo gida cike da kwarin gwaiwar sa, ya samu kuwa shi Anty ke jira har daki ta bishi babu ko sallama bare gaisuwa ta saka shi gaba sai ya fada mata su waye zai saka a gurin. Yace Bintu ce zata dawo gidan nan, tace wace ce Bintu din nan da kake ta magana? Yace Matar Abokina da ya mutu ya bar amanar su a hannu na, kin tsane su saboda su ba masu shi bane ba zaki iya hulda da su ba baki taba zuwa gurin su ba tun mijinta yana raye, da ya mutu da kyar ki ka je gaisuwa, ai bazaki san su ba.

Anty tace OK to menene matsala ta da su? Bayan haka kuma me yasa za su dawo nan bata da dangi ne?" Dady yace tsawon shekarun nan bakwai ni ke biyan haya yanzu kuwa tunda Allah ya sa ina da gida su zo su ci arziki kamar yadda nima arziki ya sa aka bani. Dan haka bai zama dole sai na fada miki ko inyi shawara da ke ba, gargadin da zan yi miki ba ruwanki da Bintu kar ki sake ki ce zaki takura mata domin komai zai iya faruwa.

Anty ta sake fusata, kana nufin zaka kore ni ka zauna da ita,kokuma zaka sake ni ka aureta? Ya ja tsaki ya shige bandaki ya barta tana fadin.

Da kuwa ka ji haushi wallahi , wannan kucakar matar wallahi ko a yar wanke wanke ni bata min ba bare kuma kishiya,ai kana aurarta ni kuma zan san ta kwatanci domin ba hauka ake yi ba. Wani takaici ya kara turnike Anty da ta danganta ta da kishiya, tace kai wallahi ma baka isa ta tare a gidan nan ba, tunda ba gidan ubanta bane. Daga bandaki Dady cikin takaici yace ke ai gidan naki Uban ne.

Anty ta shiga salati tana ihu tana fadin yau ni ka zaga saboda wata shegiya har zaka zagi ubana, kai kan ka yau sai ka bar gidan nan ba ma wai ka shigo min da wata ba. Ke naki uban hoto ne ko kalanda ce da baza a zage shi ba, Ina zaton uba baifi uba ba. Ta fito a dakin ta tsaya tsakiyar falo ta na fadin Hafsa zo ku ji min Babanku wai yau ni yake zagi. Hafsy Ta fito da sauran yara, suka yi cirko cirko.

Zagi kuma Anty kamar Yaya? Anty ta fashe da kuka tana fadin zagi dai da ki ka sani wai Ubana, akan wata banzar mata da ya ke ikirarin zai taimaka mata ta dawo gidan nan da zama. Kuma dai na yi rantsuwa saidai ya zaba ko dai ni ko ita.

Hafsi tace Anty dan Allah ki daina cewa ko ke ko ita, akwai wadda ta isa ta shigo gidan nan ba ke kika kawo ta ba, kije kawai ki kwanta shima Dady ya fada ne kawai dan ya daga miki hankali a banz...... Saukar wani wawa mari Hafsi ta ji a kuncinta. Kafin ta fahimci ko waye ya sake sauke mata a daya gefen. Dady yace "Yanzun rashin kunyar ki har ta kai ki kutso kai cikin magana ta da mahaifiyar ki kuma har kina nema ki zage ni?"
Dukan su suka cika da mamaki suka juya suna kallon Dady kamar wani TV. Hafsi ta fashe

Please Login or Register in order to submit comment