Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta daure musu kugu, Baffa kuma ba zaman gidan yake yi ba, balle ya tsaya miki "

Haka da Baffa ya dawo ta tare shi da cewa Ammah ta yi gayyar yayanta sun saka Auta kuka.
"Baffa har da wannan ɗan nata kamar basamude, shi ya fara zuwa ya yi mata kerere a gaba yana ta masifa, ashe karyan miskilanci yake yi tunda yana faɗa, Ammah na gefe da sauran yayanta suna cewa ya yi daidai."

"Ba su kyauta ba "

Baffa ya faɗa yana danne dariyansa.

"Ammah ce fa ba ta tsawarta musu ba."

"Ammah ma ba ta kyauta ba."
Ya sake faɗa yana dariya.
Ammah ta shigo ɗakin kawo ma Baffa abinci ta ce" An zo an kawo ƙarana kenan?
"E wai har da basamuden danki kika kira ya zo ya yi ma Auta faɗa."
Ammah ta kwashe da dariya Baffa na ta yata.
"Allah ya shirye ki Fatima."
Ammah ta faɗa tana ficewa daga dakin.
"Gwara ki dauki yarki ku koma Kaduna sai kun shekara ba su ganta ba, ina ce va shike nan ba, sai na ga wanda ya'yan Ammah za su yi ma faɗan"

"Ai Baffa ka bar su da ni, boko ce suke gwada mana, nima yar bokon ce sai dai mu buga ta."
Baffa na dariya sosai ya ce" A gaida Fatima Baba, Fatin Gwaggo. Yau da ma suna raye su ga yadda Ubangiji ya mayar da Fatin su."
Sai kuma suka koma tuna rayuwarsu ta baya tare da yi ma iyayensu addu'a daga karshe ma tare suke cin abincin Ammah ta sake dawowa ganin suna cin abinci ya sa ta rike baki tana fadin" Fatima kin zo kin ƙwace mini Baffa, miye nufin ki?

"Jibi za mu bar muku gidan."

"Umma ta gaida Aisha."
Baffa dariya kawai ya yi yana girgiza kansa.
Ammah itama zama ta yi suna cin abincin su uku daga faranti ɗaya, in ya kalle su sai ya tuna a shekarun baya shikenan raba faɗa a tsakanin Mami da Ammah, amma shaƙuwa ce mai tsanani a tsakaninsu, wacce ma alƙalami ba zai iya rubutawa ba.


*1k on Telegram
09069067488.


*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"


https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC

*21*

Washegari asabar Alhaji isa ya iso Jimeta tare da Islam da Faruk. Mami da kanta tare da Hamma Abdullahi suka je filin jirgi suka ɗauko su zuwa gida.

A shashen mazan gidan daman ya kan sauka in ya zo duk da in kwana ya kama shi hotel yake tafiya yau ɗin ma a bangaren su Hamma Saddam Mami ta sauke shi sai bayan ya ci abinci ya natsa sannan ya shigo cikin gida suka gaisa shi da Amma, Baffa ba ya nan ya je cikin garin Jalingo sai can yamma ya dawo tare suka yi sallar mangariba da Alhaji isa har isha'in ma daman abokan kasuwanci ne tun a baya sannan megida ne da yaronsa. Yanzu kuma har da surukanta da ya haɗa su dalilin auran Mami, duk da hakan zumumcin da ya haɗa su bai yanke ba yau ɗin ma bayan sun dawo daga masallaci a tsakar gida Ammah ta yi musu shimfiɗa ta kuma haɗe musu abinci waje ɗaya suka zauna suna ci suna hira, irin ta su ta masu kasuwancin ƙarafa da siya da siyarwan motoci daga jin yadda suke magana a tsakaninsu za ka fahimci akwai kyakyawam alaqa a tsakanin su.

Mami kuma da Ammah suna falo suna kallo tare da Faruk jefi-jefi suna taɓa hira a tsakanin su, Ummu kuma tana cikin ɗakin ta tare da Islam sarkin surutu tunda suka iso tana makale da ita tana yi mata zence, ta sha labarai kala-kala har sai da ta gaji, tamboyoyi har ta gaji da amsa mata su. Tun a can Kaduna Babansu ya sanar da su Ya Ummu za ta koma gidan su da zama to fa suna sauka ɗakinta ta fara zuwa tambayanta na farko shi ne.

"Ya Ummu wai da gaske gidanmu za ki koma da zama?
Ummu Salma na mirmishi ta ce.
"In sha Allahu Islam."

Nan fa ta fara murna da tsalle, Islam yarinya ce mai shiga rai, tana da son mutane da mgana kamar Mami yar kimanin shekara sha biyu 12, Faruk kuma ɗan shekaru bakwai ne 8, shi bai da surutu sai dai rigima ce da shi sosai kamar yaron goye.
To duk bayan mintina sai ta zagayo ta ce"Ya Ummu da gaske za ki bi mu gidanmu?
In ta amsa mata da E bai hana anjuma ta sake dawowa da irin wannan tambayan har sai da ta gaji da amsa mata. Mami ma cewa ta yi ta kore ta daga ɗakin ta ce a ƙyaleta, ganin ta da surutunta na sanyata nishaɗi, kuma ta tabbata ko can ta je islam da Faruk ba za su barta ta yi kewa ba, domin samun yara a gida yana haskaka gida tare da samar da walwala ga mazauna gidan gabaɗaya.

A can tsakar gida kuwa bayan su Baffa sun gama cin abinci sun wanke hannuwansu a roban wanke hannun da Ammah ta ajiye musu, suka ɗan shiga hiran yadda kasuwancin siyar da tsoffin karafan motoci ya yi kasa yanzu ba kamar a baya ba, Baffa na mganar kasuwancin motocin da sabbin ƙarafan ma sun fi tafiya a yanzu shi kuma Alhaji Isa na sake kora masa jawaban, tun da shi dila ne kamfani guda gare shi na siyar da motoci wani lokacim ma su Baffa kan siya motoci a wajen su in hakan ta kama.

A cikin hiran ne Baffa ya kalli Alhaji isa cikin nisawa kafin ya ce" Alhaji ina son mgana da kai, duk da na san kun gama mgana da Fatima amma amatsayina na wakilin Fatima, uban Ummu Salma ya kamata na yi magana da kai."

"Ina jin ka ina fatan ba kan maganar zaman Ummu a wajen mu ba ne ko Baffa?
Tunda shima Baffa yake kiran shi tun ma kafin aure su da Fatima, abokan kasuwancin Baffa duk da wannan sunan suke kiran shi.

"Akan maganar ne."
Baffa ya amsa masa cikin ɗan sanyin magana.

"Haba Baffa, ai ina ce mun wuce haka a tsakaninmu. Ko ban auri Fatima ba ni mai riƙe Ummu Salma ne, ballantana ina auren Fatima. Ba ka da sauran haufi ko tsoro. Ummu Salma za ta samu sauyin rayuwa tare damu na ba ka tabbacin yadda zan yi ma Islam da Faruku haka zan yi ma Ummu Salma. Sannan haka itama Fatima saboda haka ka kwantar da hankalinka ba abinda zai sake faruwa da yardan Allah."
Yana mgana Baffa na ta gyaɗa kansa cikin gamsuwa.
Yana direwa ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce.

"Na gode sosai, Ubangiji ya yi ma arziƙin ka albarka. Da man tsoro na ke ji, kar Auta ta sake tunanin kashe kanta a karo na biyu"
"Hakan ba zai sake faruwa ba in sha Allahu."
Alhaji Isa ya sake ba shi tabbacin sa.
"Allah ya sa haka. Ubangiji ya sa tafiyarta ya zama mabuɗin alherin rayuwarta."
Suka amsa da Amin a tare, tare da su Ammah daga cikin ɗaki domin sun rage ƙaran talabijin ɗin Faruk ne ma ya matsa sai da aka mayar masa da tashar carttoon, shi ya sa hankulansu ya ɗan karkata kan mganganun Baffa da Alhaji Isa.

Wajen goman na dare Alhaji Isa ya tafi makwanci ya kwanta daman jirginsu karfe sha ɗaya na safe zai ta shi zuwa Kaduna.
Shi ya sa sai wajen goma ya zo gidan abin karyawa ma tun a waya ya ce ma Mami kar ta wahalar da kanta, ya riga da ya yi breakfast a hotel ɗin da ya kwana.

Ko da ya zo gida cike da yan sallama.
Ummin ikki da Baɗɗo, tare da matan su Hamma Abdullahi da yayan su, Hamma Abdullahin ma yana nan tunda shi zai kai su filin jirgi, Hamma Abdulrrahaman ne matarsa ta ce ya yi sammakon fita yana da wata sharia da yake jagoranta.

Ko da garin Allah ya waye daman Ummu Salma ta ji kamar ta buɗe idanuwanta ta ga ta yi nesa da garin Jimeta gabaɗaaya garin ya fita da ga zuciyanta a baya ba ta taɓa tunanin wata kaddara za ta iya raba ta da mahaifarta ba sai ga shi kaddaran Habibu ta sa za ta yi nesa da iyayenta da duka yan'uwanta domin tsira da salamar zuciyarta, ta tsani garin Jimeta da duk wani farincikin da ta samu a cikin ta dalilin Habib..
Sai ga shi suna sallama da Baɗɗo tana hawaye itama tana hawaye.

"Zan yi kewar ki Sisna. In sha Allahu in muka samu hutu zan dinga zuwa ina ganin ki."
Baɗɗo ta faɗa tana sharan ƙwallah.
"Na gode Aisha. Ba zan taɓa mantawa da alherinki ga zumuncin mu ba, nima Allah ya ba ni iko da tsawon rayuwa domin na samu damar saka miki."
Ummu Salma ta faɗa cikin kuka sannan suka sake rumgume juna.

Dakyar suka saki juna, Ummin ikki ma ta rike hannuwanta tana fadin" Ki je can ki sake sabuwar rayuwa. Kar ki dawo mini sai da sabon suruki kin ji ko Ummu?
Ta faɗa cikin mirmishi a zuciyan Ummu Salma faɗi take yi wa zai sake sona a haka Ummin ikki? Amma a fili mirmishi ta yi lokaci ɗaya tana gyaɗa kanta cikin fitan hawaye.
Ammah ce kawai ba ta yi kuka ba, ita da ba a ganin raunin ta.

"Ammah zan tafi, ki yafe mini."
Ummu ta faɗa bayan ta duka a gaban Ammah tana zubar ƙwalla."

"Ba ki yi mini komai ba, ki je na yafe miki duka laifukan ki da wanda na sani da wanda ban sani ba.  Ina so ki tuna da cewa rabuwa da Habibu ba shi ne ƙarewar rayuwarki ba Auta, ki sani Allah na tare dake in kika mika masa lamuran ki, shi zai kawo miki agaji, don Allah ki cire komai a zuciyarki ki yi rayuwarki cikin farimciki."

"Zan yi haka Ammah."
Ta sake faɗa tana ta kuka kamar ranta zai fita.
Baffa ne ya ɗagota yana share mata hawaye.
"Bar kuka Auta, can ma Kaduna ai duk gida ne, kuma duk lokacin da kika ji kina son dawowa ai za ki dawo gida kin ji ko?
Sai ta gyaɗa masa kanta tana mai sake zubar da ƙwallah.
"Baffa ka yafe mini."
"Ban taɓa rike ki ba Auta. Ki tuna da Ubangiji a dukkan sakannin numfashinki, shi kuma ba zai barki ba, in sha Allahu."
Kanta ta gyaɗa tana sake sakin kuka har da jan majina.

"Allah ya tsare ku, ki yi ma Fatima Biyayya, ki riƙe Alhaji a matsayin Uba a gareki, domin yanzu alhakin komai na rayuwarki yana hannunsa ne."
"To Baffa.'
Ta faɗa tana sharan ƙwallah

"Fatima kama hannun ɗiyarki ku je. Allah ya sada mu da alherinsa."
Baffa ya faɗa idanuwansa na kawo ƙwalla sai ya bar ɗakin bayan ya danƙama Mami Hannun Ummun Salma, Ammah kuma ba ta ga tafiyar su ba ɗaki ta shige tana sharan ƙwalla a zuciyanta tana yi ma Ummu Salma fatan samun kwanciyar hankali da salama a in da zama zai sake cilla ta.

Masu rako har ƙofar gida akwatina biyu na kaya Ummu ta tafi da su sai kayan haihuwa sauran Mami ta ce ta bar su in suka isa can za a siya mata wasu.
Har da Baɗɗo aka tafi filin jirgi rako. Karfe sha ɗaya daidai jirginsu ya ɗaga zuwa garin Kaduna.
A first class suka zauna hatta da Faruƙu da Islam da kujerunsu, Mami da Alhaji suna waje ɗaya tare da Faruƙu ita kuma
Ummu Salma a bangaren window, Islam na gefenta yaran nan ko a jikinsu daga gani sun saba shiga jirgi, ita ko da ba ta saba ba sai da cikinta ya karta sau ɗaya ta taɓa shiga jirgi lokacin da suka je Daura naɗin Sarautan Hamma Lamiɗo shi ya turo musu kuɗin jirgi ita da Ammah suka tafi shi ne na farko sai wannan na biyu

Lokacin da ta fara ganin gajimare, jirgin ya daidaita a sama ya fara tafiya. Hawaye suka sake kece mata, tana jin shuuuu alamun jirgi na tafiya sai take jin komai na rayuwarta kamar yana gogewa, tabbas haɗuwarta da Habibu a baya tana kallon shi a wani nasara ne amma a yanzu tana cikin fargan jajin shigowarsaa rayuwanta. Saboda shi ya sa ta tsani duk wani ɗa namiji, tana ganin duk halinsu ɗaya saboda Shamsiya ya sa ta ƙara tsorata da lamuran mutane da ƙawaye, sun yi dalilin da ta gudu ta bar in da aka haifeta sun yi sanadiyar haifar mata da ciwon da har abada ba zai taɓa warkewa daga zuciyanta ba.

Amma ta yi ma kanta alƙawarin manta da duka rayuwanta a garin Jimeta. Za ta koma Kaduna a wata sabuwar Hallita. Za ta manta da Habibu da duk abin da ya dangance shi cikin jikinta kuma za ta haife shi, tana son shi amma baƙin cikinta ɗaya in ta tuna akwai jinin Habibu a jikin abin da ke cikinta. Ba ta fatan wata danganta ta sake shiga tsakaninta da Habibu, ba ta ƙaunar sake ganinsa a rayuwanta shi ya sa ta kudirta a ranta cewa za ta yi nesa da rayuwar Habibu da duniyarsa yadda ba zai taɓa cin mata ba har abada. Cikin daman ya ce ya bar mata to babu sauran wani abu da ya rage a tsakaninsu

Tana hawaye wasu na korar wasu, amma tana ji kamar komai na ta na sauyawa. Tabbas dole ne ta manta komai in dai har tana so ta sake cigaba da rayuwa a matsayin Ummu Salma Hadi Baba
Tana kallon gajimare da gizai-gizai tana kuka tana jin ta bar Jimeta har abada sai da ta zo da ziyara amma garin ya bar mata wani wawaken taɓon da ba zai taɓa cikewa ba har gaban abada.

Wataƙila tafiyar Ummu na ɗan lokaci ne, amma Jimeta za ta sake maraba da ita a lokacin da ta yanke dukkan tsammani da samun rayuwa mai inganci.

***
*ANGUWAN DOUGIREI*
JIMETA.
9:50pm

A kayattacen sabon gidan Habib shi ne zaune a saman kujera mai zaman mutum ɗaya kan jikin shi kuma Shamsiya ce a lafe marabanta da tsirara kaɗan ne saboda yanayin ƙaramar rigar dake jikinta da ba ta iya ɓoye sirrukan jikinta ba. shima ɗin ba shi da riga daga shi sai ƙaramin wando amma falon akwai duhu da yake dare ya ɗan fara shiga. Ba kuma don ba wuta ba ne ya sa falon ya yi duhu ba, masu gidan ne suka rage hasken falon suka bar na talabijin ɗin da suke kallo wanda ke ɗan haskaka falon kaɗan-kaɗan.

Hira suke ƙasa-ƙasa ba tare da sun yi wani motsi ba ballatana aji abin da suke furta ma juna, talabijin ɗin ma shi yake ta ɓaɓatu shi kaɗai akan tashar MBC2, su hankulansu na kan junan su lokaci bayan lokaci kuma suna sumbatar bakunan junansu cike da soyayya tare da muradi mai girma.

"Sweety ina son ka, kai ne rayuwata."
Shamsiya ta faɗa cikin irin amo a muryanta.
Kanta na saman kirjinsa yana shafa suman kanta dake tsefe har zuwa ƙasan wuyanta zuwa ƙirjinta tunda rigan mai budaɗɗen wuya ne.

"Nima ina son ki Sweety,da ban same ki ba da na zama mai asara."
Ya faɗa lokaci ɗaya yana mai ɗago fuskarta ya sumbaci bakinta itama sai ta ba shi dama suka rike kan juna suna masu sumbatar juna kamar za su cinye bakin juna lokaci ɗaya hannayensu na kara kaina a kan jikunna junansu cikin soyayya da muradi mai girma.

Sun daɗe cikin wannan yanayin kafin su saki bakin juna su koma su sake curewa waje ɗaya suna masu sauke ajiyar zuciya a jejjere, Habib ya sake matse Shamsiya dake kan jikinsa kamar ya mayar da ita cikinsa haka yake ji, bai san haka yake son ta ba sai da ya mallaketa bai san bai taɓa son Ummu Salma ba sai da ya auri Shamsiya daga lokacin ya fara ganin tarin bambamcin dake tsakanin su.

Shamsiya sonta yake yi da dukkan zuciyarsa zai iya zama da ita na har abada in dai tana tare da shi ba tare da ya takura mata ba. A farkon auren shi da Ummu Salma shi kan shi ya ɗauka yana daga cikin harijan maza ma su yawan buƙata domin yadda yake hakarta kamar Allah ya aikosa sai da ya auri Shamsiya ya ƙaryata haka, yau kimanin sati uku da auran su amma komai na rayuwarsa ya sauya. In dai zai ganta ga ta gashi ko ba za su yi wani abu ba farinciki ya ishe shi, sonta ne ke masa nauyi a zuciyarsa ba sha'awanta ba shi ya sa ko bayan faman da ya yi kafin ya mayar da ita cikakkiyar mace bai wuce sau uku zuwa huɗu suka marabanci juna ba tsausayinta yake ji ba ya so ya ba ta wahala, ita kaɗai ne ya ke jin daɗin yin wasanni da ita aamm a lokacin Ummu Salma wannan ba ya yi masa shi dai kawai sha'awanta ne ke azalzalansa so kawai ya ke yi ya marabance ta domin kauda wannan kaifin sha'awan a zuciyarsa wani abu kamar asiri in yanzu zai gama to yana sake kallonta zai ji yana son ƙari, har yanzu in ya kwanta barci ko in ya kaɗaice tana yawan faɗowa tunaninsa ko da ya saketa ba wai wannan ƙishiruwan sha'awan nata da yake ji ya gushe daga zuciyarsa da gangan jikinsa ba ne, kawai ya rabu da ita ne saboda lokaci ya yi amma karya yake yi har gobe akwai sauran abin mamora a jikin Ummu Salma.

"Sweety'
Kamar daga sama ya ji Shamsiya na kira sunan shi ya faɗa dogon tunani sannan ne fa ya yi saurin dawowa cikin hayyacinsa.

"Naam Sweety me ya faru?
Ya faɗa yana mai kallon fuskarta ta cikin duhun ɗakin.
Baki ta tura masa kafin ta ce" Gani a tare dakai tunanin me za ka yi kuma?
Sumbatar bakinta ya yi yana yi mata mirmishi kafin ya ce" Ai ke ce tunanina kuma ga ki a tare da ni Sweety na"
Itama sai ta sake sumbatar bakin shi tana yi masa wani irin kallo.

"I love you mai tsada na."
"Love you too madara ta."
Ya mayar mata da martaninta yana mai shafa bayanta zuwa ƙugunta.

"Ko tunanin tsohuwar matarka kake yi ne?
Ta faɗa tana masa dariya.
Fuska ya haɗa kafin ya ce" Kin fara ko?
Ɗan gemunsa ta ja kafin ta ce" Ai kun yi zaman aure ba laifi ba ne in ka tuna good memories ɗin ku tare da juna."
Hannunta ya ture daga fuskarsa.
Sannan ya kalleta yana faɗin" In ina tare dake ina mantawa da kaina ne Sweety,  ki sani ko da tana nan ke ce tunanina bayan ba ta ma ke ce tunanina, ni na ma manta da ita ko tana ma wani hali oho."
Ya faɗa cikin alhini da amon tausayi.
Shamsiya ta kwashe da dariya har tana sarƙewa sai da ya riƙa bubbuga bayanta yana yi mata sannu.

"Kin gani ko? Ki yi a hankali kin ji ko?
Yake faɗa yana ɗan shafa bayanta har da ma kirjinta.
Amma duk da haka ba ta daina dariyan da ta fara ba.

"Me ya saka ki dariya!
Ya tambaya shima yana ɗan taya ta dariyan kaɗan.

"Ummu Salma na tuna, baiwar Allah har gobe tana tsananin son ka."
Sai ta sake kecewa da dariya.
Shima dariyan ya ɗan saki kafin ya ce" To ai yanzu dolenta za ta cire ni a zuciyanta domin ta fahimci ba a hallice ni don ita ba, an hallice ni don ke ce kawai. Ke kaɗai ba ki da abokiyar tarayya."
Ya gama faɗa yana sumbatar saman sumar kanta.

"Abin da ke bani dariya in na tuna, ta zo gidammu ana jibi bikin mu ta ga hotunan auran mu amma wai ta kasa gasgata gaskiya ne, ta yarda da ni ta aminta da soyayyar da take yi maka a wautar ta tana tunanin wata rana za ka dawo gare ta? Ka daɗe kana ce mini yarinyar nan ba ta da tunani ban taɓa yarda ba sai ranar."

Ta gama faɗa tana sake kwashewa da wata dariyan daga gani tana cikin nishaɗi da labarin da take bayarwa.
Nan fa ta cigaba da faɗin maganganu marasa daɗi a kan Ummu Salma labarin zuwanta gidansu da duk abin da ya kwana kullum sai ta tuna ta yi dariya kamar ya zama abun tunawarta ta yi nishaɗi.

"Wawancin iyayenta na gani, suka barta da cikin jikinta alhalin wanda ya yi cikin ya ce ba ya so, to mene ne amfanin haihuwar da za ta yi?
Ta faɗa tana kallon shi, sai ya ɗan juya mata ido alamun bai sani ba.

"Ni dai har abada ba za ka kawo mini jinin da ba nawa a gidana ba, ba mu yi wannan alƙawarin ba."

"Ba ma zan kawo ba? Me zan yi da abin da ta haifa! Ke da za ki yi ta haifa mana yara?
Ya gama faɗa yana ɗan jan hancinta mirmishi ta sakar masa har tana sumbatar gefen kumatunsa.

"Da gaske na ke yi na bar ma Ummu Salma da iyayenta wannan cikin har abada ba ni da alaqa da shi"
Ta jinjina kai cikin farinciki.

"Wayyo ta ba ni tausayi, "
Ta sake faɗa tana sake saka dariya.
"Lokacin har wani ɗaga kafaɗa take yi. Bestie Allah kuma ya ba ku miji wanda ya fi Noori na ma komai da komai."
Ta gama faɗa tana kwaikwayon muryan Ummu Salma daga shi har ita sai da suka sake tsintsirewa da dariya.

"Ko haihu ta yanzu? Domin ganina da ita na karshe na ga cikin ya yi kasa. Ko da yake ina ruwanmu ko Sweety?
Ta tambaya tana kallon shi.

"To ai ke ce ke ɗauko maganarta. Ni tuni na gama da babinta."
"Labarinta na sanya ni nishaɗi ne."
Ta sake faɗa tana dariya.
"Na san zuwa yanzu kowa ya san na aure ka, na san na sha tsinuwa wajen yan'uwanta barin ma uwarta din nan bafullatanar banza, da wannan yayanta na ta lauya masifaffe da shegiyar ƙawar nan nata Baɗdo ba ta da mutumci, ka ga saƙon cin mutumcin da ta turamini ranar biki! Wai duk abin da ya samu Yar uwanta ni da kai Ubangiji ba zai ƙyale mu ba to ina ruwan mu? Daman ai aro na ba ta kai kuma na zo na karɓi kaya na sai aka ga laifina Sweety?

"Bai kamata a ga laifnki ba, ai su ba su nan abin da ya faru ba ne."
Ya faɗa cikin sanyin murya.
"Ko da Ummu Salma ta riga ni haɗuwa da kai. Amma ai ni ka zaɓa sama da ita ko?
Ta sake tambayan shi tana ɗan kallom shi.

"Tabbas."

Ya faɗa abin da ya faru a lokacin yana dawowa masa.
"Wallahi tun a ganin farkon da na fara yi maka kishi da hassada suka kume ni, a raina ina faɗin me ya sa sai Ummu ce za ta fara haɗuwa dakai? Ranar na koma gida da baƙinciki ina ganin kai ne irin namijin da nake burin aure ban taɓa tunanin za ka kawo kanka gare ni ba wallahi tallahi da ka makara ba ka zo ba, ni da kaina zan neme ka na yi maka tallar kaina sannan na sanar dakai na fi Ummu Salma bukatar ka a rayuwata."

Ta gama faɗa cikin wani yanayi kamar ta yi kuka.
"Sweety wallahi ina sonka."
Sake rumgumeta ya yi a jikinsa yana faɗin" Na sani, nima ai kinsan ina son ki! In kika yi duba da tsawon lokacin soyayyarmu da yadda na cika alƙawarin kema za ki san bayan ke ba na son kowa a duniyar nan a matsayin matar auran da zan zauna da ita. Na fuskancin komai saboda na mallake ki "
Ta sake ƙamƙame shi tana faɗin" Na sani Sweety na sani wallahi."
Sumbatar sumar kanta ya yi kafin ya ce" Ki bar tuna duk abin da ya wuce, rayuwarmu ce yanzu kawai a gabanmu Sweety, mu zauna mu gina sabuwar rayuwa wacce za ta yaɗu zuwa nan da wani lokaci kaɗan. Can wait na ga ranar da za ki haifa mini ɗa ko ƴa daga mahaifarki."
Ya faɗa yana kai hannunsa ƙasan maranta ita kuma sai ta noƙe wai tana jin kunya.

"Ke ce na zaɓa ki zama uwa ga ƴa'ƴana. Kuma ba zan sauya miki ba."
Gabaɗaya ya gama kashe mata zuciya da kalamansa. Sai ta sake narke masa cikin shagwaɓa shi kuma yana biye mata sun daɗe a haka domin da ya ce su je ɗaki su kwanta sai taƙi karshenta a saman jikinsa ta yi barci ta bar shi da sake shuga tunani mai zurfi.

Tabbas a ganin farko da ya yi ma Ummu Salma ya ji yana son ta amma lokacin da ya haɗa idanuwansa da na Shamsiya sai ya fahimci ashe ba so ya ke yi ma Ummu ba sha'awanta yake yi, in yana tare da ita burinsa kawai  jikinta ne a gabansa amma in yana tare da Shamsiya burinsa kawai ya dauwama tare da ita ko da ba za ta amfanesa da komai ba, tun bai fahimci karatun ba har dai ya fahimta ba shi da mafita illa ba ma zuciyansa abinda take so sai kuma aka

Please Login or Register in order to submit comment