Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ummu-Salma, kuma ni ban ga laifin Habib ba, haka na faruwa ko wata da muke ɗaki ɗaya a makaranta mijinta ya ce sai sun shekara biyar da aure za ta haihu kuma ta amince. So normal ne kawai fahimta ce tsakanin ma'aurata, ke kan ki Ummu nawa kike? Kina da sauran damarma ki masu tarin yawa ma anan gaba ni ban ga laifin Habib ba, ra'ayin shi ne kuma girmama ra'ayin juna a zamantakewa kamar dole ne."

Ummu ta jinjina kai cikin sanyin jiki kafin ta ce'" Ina son aurena sannan ina son cikina Bestie."
"To sai dai ki zaɓi ɗaya ko auran ki, ko cikin."
Ummu ta kasa zaɓan wanda ya fi sauƙi a ciki, duk tana son ta tsira da su da auran da cikin jikinta.
Shamsiya kuma ta yi ta nuna mata ba matsala in ta zubar yanzu gaba za ta iya samun wani a lokacin da suka shirya suna da dama, tun da lamarinn nan ya fara faruwa ba ta ji ta samu salama ba sai da ta yi mgana da Shamsiya sannan ta samu jin wani abu ya faɗa daga ƙirjinta.

Shamsiya ba ta tafi ba sai da Ummu ta ba ta tabbacin za ta amince da umarnin Habib. Ita fa Shamsiya ƴar boko ce, sannan renon yan boko su a ganin su hakan ba matsala ba ne bayan tafiyar Shamsiya Ummu ta yi ta tufka tana warwara, shawaran Shamsiya ta fi zama mata sosai a cikin zuciyarta duk da tana son cikin ta amma kuma tafi son Habib a kan cikin, kamar yadda Shamsiya ta faɗa ne in tana son Habib to ta bi umarnin sa sai su zauna lafiya. Za ta amince da a zubar da cikin amma sai ya ba ta tabbacin zuwa yaushe yake son ta haihu ? Allah na gani tana son haihuwa har mafarkin tana shayar da jariri take yi. In har ba zai wuce shekara biyu ba to za ta iya haƙuri a zubar da wannan amma in dai ya gota ba za ta iya haƙuri ba.

***

A RANAR.

Habib Ya fito daga wajen aiki kenan misalin 4:40pm, ya tsaya tare da wani abokin sa suna magana. Ya ji saƙo ya faɗo wayarsa amma saboda suna mgana bai duba a lokacin ba sai da suka yi sallama kowa ya nufi in da ya yi parking ɗin motar shi ya shiga.

Shi dai yana shiga cikin motar na shi jakar hannun sa ya sauke a gefen kujeran mai zaman banza. Sannan ya fiddo wayarsa dake cikin aljihun wandon shi saƙo ne daga M.S kamar yadda ya yi zato tun farko.

"Habib lokaci yana ƙure mana fa, ina jin tsoro, tsoron kar maganar nan ta je kunnen iyayenta daga nan waliyanka su ji labari alalan mu ya yi ruwa, tsarin mu ya lalace ba yadda muka shirya ba. Don Allah ka yi wani abu da gaggawa ba mu da lokaci"

Mirmishin sarari ya yi kafin ya tura mata da amsa.

"Kar ki damu ba abin da suka isa su yi. Ba kuma wanda ya isa ya lalata mana shirin mu."

"In cikin bai zube ba fa?

"Ba wanda ya isa ya sa ni na karɓi abin da na ce bana so. Da gaske bana son ta sannan ba na son haɗa zuru'a da ita, in kuma ta cigaba da taurin kai to zan saka rayuwarta da na iyayenta a uku."

Yana turawa ba jimawa sai ga wani saƙon ya sake shigowa.

"Ka yi komai, in dai ka san ba zai hana shirin mu tafiya ba."

"Zan yi."

Da haka ya ma yar da wayar na shi cikin aljihun wondon shi ya kunna motar ya yi riverse ya bar haraban bankin, yana tafe yana wani tunani matukar Ummu ta cigaba da taurin kai to komai zai ƙare a tsakanin su, ta je can ta riƙe cikin sai ta zame masa uwa da uba.  Abin da ya sa ya aureta tuni ya gama samun shi babu kuma sauran wani abu da ya rage a tsakanin su

**

Da wuri Habib ya dawo kamar ya san Ummu ta tsala kwalliya tana jiran dawowan shi, da yake ta ji sauƙi tana samun ƙarfin jiki ya sa har girki ta yi masa ta gyara gidan yana tashin ƙamshi.
Lokacin da ya dawo tana falo tana zaman jiran shi, bai yi mata mgana ba sai ita ce ta ce masa ya tsaya ya saurare ta.

"Na faɗa miki ba wani sauran mgana a tsakanina da ke malama."

Ya faɗa a fusace yana ƙoƙarin shigewa ɗakin da yanzu ya ke rayuwa a ciki.

"Ko da a ce maganar na amincewa da ɓukatar ka ne?

Ta faɗa a sanyaye, ai yana jin haka da sauri ya juyo yana kallon ta.

"Me kika ce?

Ya tambaya yana ɗan rage ɗaure fuskar da ya yi.

"Cewa na yi ko da maganar tawa na cewa na amince zan bi Umarnin ka ne?
 
Kamar walƙiya sai ga shi a gabanta yana mai sakin jakar hannunsa kafin ta yi wani yunƙuri ya rumgume ta ƙamƙam cikin matsanancin farinciki.

"Haba ko ke fa Baby, sai yanzu na ji na samu natsuwa."

Murna yake yi a zucci da sarari nan da nan ya fara sumbatar ta a ko'ina na fuskar ta, yana mai nuna mata farincikin sa bisa amincewa da ta yi da bukatar shi, zuciyar Ummu ya cika da farinciki ganin yadda Habib ya ke yi mata rawan jiki, ta faɗa masa ta amince da buƙatar sa amma zuwa wani lokaci ya shirya ya zama uba ita kuma ta zama uwa.

"Nan da shekara ɗaya Baby. Lokacin duka mun shirya zamo wa iyaye amma by now mu cigaba da cin lokacin mu."

Ya faɗa yana yi mata mirmishi, wannan mirmishin da shi ya yi amfani ya sace zuciyarta.

  Sai ga shi ranar tare suka yi Dinner yana ba ta abinci a baki tana bashi, ganin ta ɗan yi sanyi sanyi ya sa ya ke sake jadadda mata kar ta damu zai kai ta asibiti a bata maganin da cikin zai zuɓe ba tare da an samu wata matsala ba yana faɗa mata cikin ƙarami ne ba za ta fuskanci wata matsala ba.
Duk da Ummu ta amince da buƙatar Habib sai ta ji ta kasa samun natsuwa, a cikin zuciyarta ta kasa samun natsuwa cikin ta kawai take shafawa tana jin wani iri, sai take ganin kamar abin da za ta aikata ba alheri ba ne.

"Ummu-Salma ki sake tunani."

In ta amince aka zubar da cikin tana da garantin cewa Ubangiji zai sake ba ta wata damar! Ko kuma ranar gobe ƙiyama cikin da ta zubar ya tambaye ta a gaban Ubangiji da cewa wani laifi ya aikata mata da ta yi masa haka? Ba ta da amsa a wannan lokacin sai ta ji ta sare son cikin ta ya sake shigan ta, tuni ta ji ta sauya shawara gwara ta ce ma Habib ya yi haƙuri tun da cikin ya shiga ya bari in ta haihu sai su tsayar da haihuwar har zuwa lokacin da ya ke so.

Da wannan tunanin ta tsayar da shawara tana ɗakin ta ne Habib ya je ɗakin sa ya dawo ba jimawa sai ga shi ya shigo da gajeren wando jikinsa ba ko riga tana so ta yi masa mganar amma bai ba ta dama ba haka ya fara naniƙarta da sam ta ji ba ta bukatar hakan amma ta kasa yi masa gaddama. Bai bar ta ba sai da ya samu yar natsuwa sannan ya ɗan dakata a gefenta yana mayar da numfashi.

"Gobe Baby za mu je asibiti, ko kuma kawai na siyo miki mganin ki sha zai fi sauƙi ko?

Ya faɗa yana leƙen fuskarta, sai ta yi shuru ta kasa mgana haka kurum ta ji zuciyarta ta karye.

"Kin yi shuru."

Sai da haɗiye miyau sannan ta ce" Habib na sauya shawara."
Yadda ya miƙe zaune a firgice ne sai da Ummu ta ji tsoro itama ta tashi zaune tana mai rufe jikinta da bargon dake gefen ta.

"Raina mini wayau za ki yi?

Ya faɗa a fusace yana kallon ta.

"Aa wallahi."

"To me hakan ke nufi, mun gama mgana kuma yanzu kina faɗa mini wata maganar banza."

Ya katse ta a fusace yadda ya ta so mata in ta yi wasa zai iya kai mata duka.

"Ina so ne, ka bari sai na haihu."

Ta faɗa hawaye na kece mata kanta na ƙasa domin kauce ma wani mugun kallo da Habib ke jifanta da shi.

"Kin haihu a ina?
A gida na? Ba ki isa ba.'

Ya faɗa a fusace kafin ya diro daga kan gado.

"Sau nawa zan faɗa miki bana son na haihu da ke ne Ummu-Salma, ?

"Ai ka ce zan haihu  nan da shekara ɗaya shi ne na ce tunda ina da cikin yanzu ka bari in na haihu daga baya sai na bari sai lokacin da ka shirya sai in sake haihu."

Kafa ya sa ya daki gefen gado cikin ƙaraji ya ce" Ke wata irin daƙiƙiya ce,? Da wani yare zan faɗa miki ki yarda da mgana ta?

Ya faɗa kamar ya kai mata duka, Ummu ta takure waje ɗaya tana mai kuka ƙasa-ƙasa.

"Na faɗa miki ba na son ki, bana son ki me ya sa ƙin ki gane hakan ne?

Ummu ta ɗago tana kallon shi da idanuwanta masu zubar ƙwallah.

"Ko ƙwaƙwalwarki kike so na buɗe na saka miki mganar ne sannan za ki fahimce ni?

Ya gama faɗa yana dafe kansa.

"To ka san haka me ya sa ka aure ni, ka nuna mini so kuma?

Kamar zai dake ta haka ya taso mata da hargagi yana faɗin.
"Ke wai har yanzu ba ki ba ma kan ki wannan amsar ba?
Sai na faɗa miki dalilin da ya sa na aure ki da bakina sannan za ki yarda?

Ya faɗa yana zare mata ido, Ummu ta runtse ido hawaye suka ke ce mata.

"Sabo da ina so na ji daga bakin ka."
Ta ƙarishe faɗa cikin kuka har da shessheƙa.

"Sabo da ba ke na ke so ba, ban kuma aure ki domin ki zo ki haifa mini yara ba."

Sai da ya kalleta sannan ya yi wata dariya kafin ya ce" Kawai ni jikin ki na ke so, auran sha'awa na yi da ke kuma Alhamdulillah na samu biyan buƙatata a wajen ki, ko a haka kasuwa ta watse na ci riba."

Idanuwanta a runtse amma hawaye na ƙwaranya, kukan zucci ta ke yi, da Baɗɗo ta faɗa ta ji zafin mganar ta kuma kasa gasgasta hasaahen ta, sai da Habib ya faɗa sannan ta fahimci yadda komai yake, maganganunsa sun yi zaman da'ira a cikin zuciyarta cikin lokaci kaɗan suka fara yi mata illa, shi ya sa ashe take ta mamakin me ya sa kullum abu ɗaya? Ashe dalilin da ya sa ya aure ta kenan saboda jikin ta, kuma kamar yadda ya faɗa ne ko a haka kasuwa ta tashi shi ke da riba, tunda duk ya gama more wani albarkatun jikinta ya cuci rayuwarta ya lalata mata mata goben ta, tuni ta ji zuciyarta ta yi baƙin ƙirin ɗin da ta ji gwara da ba ta zubar da cikin jikin ta ba, wataƙila da shi ne kaɗai za ta iya tsira a rayuwarta da Habib ya lalata.

Tana jin shi yana ta mganganu ya sake ba ta tabbacin shi bai taɓa son ta ba auran sha'awa ya yi da ita ba auren soyayya ko ta zo ta haifa masa yara ba. Akwai wacce ya yi ma wannan tanadin amma ba ita ba
Daga ƙarshe ya ce ba zai sake ce mata ta bi umarninsa ba amma ta sani sai ta yi nadama daga nan ya bar mata ɗakin har yana banko mata ƙofa.

Yana fita ta saki kukan ta a fili, kuka take yi kamar ranta zai fita, ji ta ke yi kamar zuciyar ta za ta fito waje saboda yanayin da ta ke ciki, mutumin da ta ɗauka a masoyin ta da bayan iyayenta  ba ta da kamarsa, mijinta sirrin rayuwarta wanda ta aminta da shi ashe ashe shi a zuciyarsa ba haka ya ɗauke ta ba, yana da manufarsa a kanta. Ta daɗe tana kuka kafin ta iya tashi ta faɗa tiolet ta tsarkake jikinta sannan ta fito ta saka wata doguwar riga, ta shimfiɗa darduma tana salla tana kuka, bayan ta idar da sallar isha'i ba ta san awannin da ta shafe a saman darduma tana kuka ba.

Abu ɗaya ta sani ba ta ji ta tsani Habib ba, sai ma ji ta yi yanzu take son shi, amma dai ta yanke shawaran gobe za ta je gida ta samu Baffa ta faɗa masa halin da ake ciki. Sai dai za ta za ta roƙe shi ya kira Habib ya ba shi haƙuri, za ta faɗa masa tana son shi kuma ba ta son wani abu ya samu auran ta.




*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t

*07*

Washegari.

Ummu-Salma ta ƙulla ƙawance da kuka. Ta kwana yi ta yini yi, jiya ma kwana ta yi kuka shi ya sa ta tashi idanuwanta sun kumbura sun yi luhu-luhu, fuskarta ta yi jajir abin ka ga farar fata.
Ba ta fito daga cikin ɗakin ta ba sai da ta ji fitan Habib daga gidan sannan ta fito domin tsoron haɗuwa da shi take yi. Ba ta iya tsinana komai ba, ga ciwon kai ga jikinta duk ba daɗi ruwan zafi ta dafa ta sha ruwan lipton saboda za ta sha magani sai da ta sha mgani ta ɗan ji ya kwanta mata sannan ta shiga ta yi wanka tana cikin shiryawa ne Hamma Sadam ya kira wayarta. Tana ɗauka ta ji yana faɗin.

"Ke wai kin mutu ne? Ko an yi miki magana a WhatsApp ba kya dubawa. Sai yau na sake duba ki na ga kin kwana biyu ba ki hau ba."

Mirmishi Ummu ta yi kafin ta ce"  Zan mutu ba ka sani ba ne Hamma?
Ta ƙarishe faɗa cikin sanyin murya.

"To na sani,"

Ya faɗa cikin ƴar dariya. Dariyan Ummu ta taya shi kafin ta ce" Ba ni da lafiya ne fa Hamma."
"Oh haka ne kwanaki mun yi waya da Amma ta ce ba ki jin daɗi, shi ne har yanzu?
"E."
"Me ke damun ki?

"Zazzaɓi ne Hamma."

Ta faɗa cikin kasalan da ta ji ya sake rufe ta bayan ta yi wanka.

"Sannu. Allah ya ƙara lafiya."

Ta amsa da Amin. Shi kuma ya tambaye ta ko ta je asibiti.

"E mun je"

"Allah ya ƙara afuwa sannu."

Ta amsa masa da yauwa. Habib ya tambaya ta ce ya fita aiki.
"Allah ya ba mu sa'a."
Daga nan ba daɗewa suka yi sallama da juna kowa ya kashe wayarsa.
Ɗan wayar nan da suka yi da Hamma Sadam ya ɗan rage mata damuwa. Shi fa ɗan'uwa daɗi ne da shi.

Ballatana Hamma Sadam irin mutanan ne masu amfani da social media sosai, duk gidan su ba kamar sa, komai na shi kowa ya sani, shi ne instagram shi ne Twitter, shi ne Facebook kullum ba shi da aiki sai posting ɗin hotunan shi komai yake yi sai duniya ta sani. Shi ya sa duk wani labarin da ke faruwa Hamma Sadam na da labarin shi da har hoton Baffa da Amma yana kafewa a Facebook Hamma Abdulrrahaman  ne ya yi masa faɗan akan ya daina posting ɗin hotunan su Baffa in zai saka na shi ya saka amma ban da na Ammah da Baffa shi ya sa ya daina amma na shi kam bai daina ba, a ko wani hali ya ke ciki kafin ya yi mgana posting ɗin shi ya bayyana halin da ya ke ciki. Kuma shi ba ma'abocin kiran waya ba ne amma za ku yini kuna chart bai damu ba. Shi ya sa ai Hamma Sadam kodayaushe yana online ne.

Sai da ta ɗan kwanta domin sai ta ji amai yana ta so mata, sannan kasala duk ya rufe ta sai wajen goma da wani abu ta iya rarrafawa ta fita. Doguwar riga ta saka na wata Atamfa sai ta yi amfani da bakin mayafi, ƙaramar jakarta ta ɗauko in da ATM ɗin ta na Banki yake tun da ba kuɗi a hannunta sai ta cire, sai da ta biya ta wani shago ta cire 5k sannan ta samu mai Kekenapep ta yi drop zuwa gida.

Bai sauke ta ko'ina ba sai ƙofar gidan su dake tsakiyar anguwan Zone 3. Ta sauka ta biya shi kuɗin shi sannan ta fara takawa ta tunkari baƙin get ɗin gidan na su, a baya ba baki ba ne da Hamma Lamiɗo ya sa aka gyara gidan ne a lokacin aka sauya get ɗin gabaɗaya. Ba ta tsaya ma ƙwanƙwasawa ba ta tura ta shiga sanin da ta yi get ɗin a buɗe yake, tuni Ammah ta ce a riƙa barin shi a buɗe saboda ba za ta iya wahalan kai da kawo tsakanin get da cikin gida ba shi ya sa a buɗe yake sai dai za a tura shi amma ba za a rufe ba tun da ba maigadi, tun tuni da man gidan Baffa ba mai gadi ballatana yanzu da rayuwa ta gangara.

In ka shiga gidan haraba za ka fara gani, daga yamma kuma akwai wani flat ɗakunan mazan gidan ne falo ne da ɗakuna huɗu kuma kowanne da banɗaki a ciki. Hamma Sadam ke zaune a ciki yanzu amma in su Hamma Mustapha suka zo su kan sauka a wajen ko baƙi daga Mubi dangin Ammah ko Baffa. Daga nan sai bangaren kudu akwai ɗan korido da za ka bi zuwa cikin gida wanda ke ɗauke da tsakar gida daga gefe kuma kitchen ne Babba sai yamma kuma ɗakin Baffa sai daga gabas kuma Ɗakin Ammah ne mai ɗauke da falo da ɗakuna huɗu a ciki. Sai gefen can kuma falo ne sai ɗaki ɗaya a ciki da banɗaki. Ɗakin da Mami ta yi rayuwarta kafin ta yi aure sannan anan Ammah kan sauki baƙin da za su fi sati kafin su tafi. Ɗakin a gyare ya ke, tsab kamar yadda bangaren Ammah ya ke shima kamar ɗakin wata Budurwa. Kusan duk shekara Hamma Lamiɗo sai ya sauya mata tsarin falo, Amma ta yi ta faɗa tana cewa ya bari ita ya gama biyan ta tunda ya kai ta Hajji sannan ya kai ta Umra amma ba ya ji ba ta ma sani sai dai ta ga Hamma Kabiru ya zo yana zuwa to kamar shi ne ya zo tun da duk wani abu da Hamma Lamiɗo zai yi ma Amma na suprising ɗin ta, to da Hamma Kabiru zai fara tattauna maganar sannan Hamma Abdullahi ya gabatar.

Tsakar gidan duk shimfiɗe yake da interlock. Tsakar gidan tas Amma ta share shi Ummu na ta sallama da ƙaramar muryanta ta ji shuru ta dai ta san Baffa baya nan tunda ba ta ga motar da ya ke hawa a haraba ba, ɗayan ta gani Benz ce tana lulluɓe da tamfol ya jima ma bai yi amfani da ita ba.

  Jikinta ba karfi shi ya sa ta kasa ɗaga murya ƙarisowa ta yi kofar falon Ammah ta ɗaga labulen tana leƙen cikin ɗakin.

"Ammah."

Ta faɗa a hankali tana zagaya idanuwanta a cikin ɗakin amma shuru kamar ba kowa ashe ba ta sani ba Ammah na dakin Baffa.
Amma ta fito daga ɗakin Baffa ita kuma Ummu Salma ta juyo sai suka yi ido huɗu.
Mamaki ya kama Amma cikin mamakin a muryanta ta ce.

" Ke kuma daga ina kamar an jeho ki?

Ta faɗa tana nazarinta. Kafin ta wuce ta zuwa cikin falon ta.
Ummu ta ja kafafunta sannan ta cire takalmin kafanta ta bi bayan Ammah zuwa cikin falon.
Kan kujera mai zaman mutum biyu ta zauna tana mai mikar da kafarta ji ta ke yi kamar ta kwanta saboda wata gajiya da ta ke jin tana sauka a cikin gangar jikinta.

Amma ciki ta shiga ba daɗewa sai ga shi ta fito ganin Ummu zaune a yanayin da ba ta gane mata ba yasa ta nemi kujerun gefen ta lokaci ɗaya tana faɗin" Ke lafiyan ki kuwa?
Ta faɗa tana sake kallon Ummu da ke yamutsa fuska duk da ta san halinta amma yanayin ta ya nuna ba lafiya tun ballanta ganin ta rame ta sake yin fari.

"Ina mgana kin yi mini shuru?

Ammah ta sake tambaya cikin fusata da sauri Ummu ta ce" Ina kwana Ammah "
Ta furta cikin harshen fillanci Amma ta amsa da sauri tana cigaba da faɗin" Ko jikin ne har yanzu?
Sai kawai ta gyaɗa mata kai lokaci ɗaya tana bin shawaran zuciyanta ta kwanta a saman kujeren da ta ke zaune.

"Sannu. Me ke damun ki hala?

"Ammah zazzabi ne?

Ta ba ta amsa, ita kuma sai ta sake kallonta abin da ta gani kamar ciki ne laulayi ne ke wahalar da Ummu, amma tunda ba ta faɗa mata ba sai ba ta nuna mata ta gane ba.

"Kun je to asibiti?

Wannan karon ma kai ta gyaɗa mata ba ta yi mgana ba,sabo da ba ta so Ammah ta fahimci wani abu ta san halin ta yanzu nan za ta rikita lamarin ya zama ba yadda take so ba gwara Baffa shi yana da sauƙin kai da fahimta.

"Allah ya sauwaƙe, ya wajen shi Habibun!? Kuna nan lafiya dai ko?

Amma ta tambaya lokaci ɗaya tana mikewa.

"Lafiya lau."

Ummu ta amsa cikin sanyin murya sai da Ammah ta kalleta na wani lokaci kafin ta girgiza kai, jikin Ummu duk ya yi sanyi kamar ba ita ba amma ba ta kawo aran ta ba sai ta ce wataƙila laulayi ne mai zafi shi ya sa duk ta sauya.

"Baffa fa? Ba ya nan ne?

Ta tambaya lokacin da Ammah ke shirin ficewa daga falon.

"Yanzu nan ba daɗewa ya fita zuwa cikin Yola."

"Yaushe zai dawo? Ba zai daɗe ba ko?

Ummu ta tambaya a marairai ce, Amma ta fasa fita ta juyo tana kallon ta.

"Tare da Abdullahi suka fita watakila ba za su daɗe ba."

Sai ta jinjina kai lokaci ɗaya tana mai lumshe ido.

"Ummu Salma."

Ta ji Ammah ta kira sunanta  da sauri ta buɗe ido tana kallon ta duk da tana kiran ta da haka lokaci bayan lokaci amma na yau cikin wani irin amo ne da ya sa ta natsuwa.

"Me ke faruwa ne?

Haka Ammah ta tambaya lokaci ɗaya tana tsare ta da idanuwanta, da sauri ta dukar da kallon ta ga Amma kafin ta ce" Ba komai Amma."
"Kuma kike tambayan Baffa?
"Kawai fa ina son ganin shi ne"
Ummu ta faɗa cikin yar shagwaɓa har tana ɗan turo bakin ta gaba.

Amma ta yi ƙaramin tsaki ta fice tana faɗin" In kin gan shi sai ki haɗiye shi "
Har sai da ta saka Ummu dariya Ammah shagali, tana nan kwance tana mirmishi lokaci ɗaya da tunanin yadda za ta fara taran Baffa da mgana tana tufka tana warwara ba ta san lokacin da barci ya kwashe ta ba, ita dai ƙamshin wani abu ne ya tashe ta, tana tashi sai ta ga Ammah ce ta dama kunu da ya ji kayan kamshi shi ya sa ƙamshin ya cika falon ta.

"Amma zan sha kunun."

Ummu ta faɗa lokaci ɗaya tana tashi zaune, ɗankwalin ta ya fita kanta kitso ne duk ya tsufa har ya fara zarewa da kansa. Ba ta da wata natsuwa ballanta ta iya tsefewa ta sauya wani.

"Ga shi nan ki diɓa, da ma Abdulrrahaman ne ya ce na dama masa yana nan zuwa "

Sai da ƙirjin Ummu ya amsa a cikin zuciyarta ta ce Allah ya sa lokacin da zai zo ta gama mgana da Baffa domin masifaffe ne in ya ji wannan mganar zai iya ɓata komai a lokaci ɗaya ba tare da ya damu ba. Tana kallo Ammah ta diɓa masa a cikin ƙaramin fulas sannan ta bar mata sauran a ƙaramin botikin da ta dama kunun da cewa in ta tashi za ta sha sai ta samu kofi ta diɓa daga nan Amma ta fice daga falon zuwa Kitchen.

Tana son kunun ya biya mata rai, duk da tana tsoron amai haka nan ta tashi ta fita ta ɗauki kofi saman frizan Amma ta zuba kunun ta koma ta zauna tana sha, har wani lumshe idanuwana take yi saboda da daɗi, da man in dai Ammah ta yi girki ko da dama abu daɗi ne da shi ballatana garin kunun ta na daka ne, yana jin kayan ƙamshi in ta dama ma shi ya yi ta tashin ƙamshi.

Kamar abun arziƙi ta shanye kofin da ta ɗiba daga farko har ta kara wani ma, sai dai tun kafin ta yi rabin shi zuciyarta ya fara tashi kafin ta yi wani yunƙuri amai ya taso mata ai da gudu ta faɗa ɗakin Ammah ta shiga toilet ɗin ta, ta fara kelaya amai gabaɗaya abin da ta ci sai da ta

Please Login or Register in order to submit comment