Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da muka yi waya yake faɗa mini kamfanin Chevron da ya nemi aiki da su daman can kwanaki ya faɗa mini sun yi online interview. To sun ba shi aiki nan da wattani biyu zai fara aiki da su in sha Allahu."

Amma ta washe baki kafin ta ce" Ma sha Allah. To shi wannan kamfanin anan ne ko? Ba sai ya yi ta yawo a cikin jirgin ruwan ba ko?
Hamma Kabiru ya yi dariya kafin ya ce" Ammah duka kamfanonin na gida Nigeria ne, sai dai shi wanda Lamiɗo ke aiki da su yanzu kamfanin Nigerian Port Authority su jirgin da yake tuƙawa suna jigilan mutane ne da kayan masarufi suna zuwa ƙassashe da yawa kuma suna ɗaukan lokaci shi ya sa yake daɗewa bai zo ya ga mutane ba. Ammah ko a can Lagos ko Balkisu ba ta cika ganinsa ba sai su zo Tashar jirgin ruwa dake Apapa Lagos sau nawa bai je gida ba saboda aikin yana da ɗan tsauri shi ya sa na bashi shawaran gwara ya sauya kamfani wanda zai dinga zuwa gida bayan sati biyu ko uku in ya daɗe ne wata ɗaya."

Ammah ta gyaɗa kai tana faɗin" Haka ne, ya fara tara iyalai bai kamata yana yin nisa da gida lokaci mai tsawo ba gaskiya ka ba shi shawara mai kyau Kabiru."
Hamma Kabiru ya karɓa da cewa" Shi ne fa har sun ɗauke shi aiki yanzu ya rubuta takardan ajiye aiki da kamfanin da yake yi ma aiki yanzu sun ƙi saka hannu. Kin san Lamiɗon naki gifted ne suna son shi duk cikin matuƙan jiragensu ba kamar shi, yana musu aiki tukuru sannan yana da jajircewa akan aikin shi aiki yake yi musu tukuru bai damu da jikinshi ko gajiya ba shi ya sa ba sa son rabuwa da shi."

"To ai sai dai su yi haƙuri mu ma muna son ganin shi sannan muna son ya riƙa hutawa"
Ammah ta faɗa tana dariya.
Tun bayan faruwan al'amarin Ummu sai yau Amma ta saki ranta hiran Lamiɗon da suka yi da Hamma Kabiru.


"Ai zai samu hutu da lokaci ishasshe sosai Ammah. A yadda na yi binciken sabon kamfanin da zai fara aiki da su, suna sauyin matukan jiragen in wannan yaje ya yi kamar wata ɗaya to za a bashi kamar break na sati ɗaya yaje gida ya gana da iyalai da yan'uwa sannan ya dawo kuma kin ga su babu daɗewa sosai kamar na wannan aikin."
"Gaskiya wannan ɗin yafi Kabiru to shima duk tuƙin jirgin ne?
Hamma Kabiru ya sake gyara zama yana faɗin" E mana shi ma kamfani ne kamar wanda yake aiki da shi a yanzu amma suna da ɗan bambamci.
Shi wannan kamfanin na Chevron Nigerian Limited.
Kamfanin dake da alhakin fitar da Mai kasashen waje domin a cire su kalanzir, fetur, dessel, LLG. Suna da jirage da matuƙa jiragen dake da alhakin fita da man zuwa waje da dawowa dashi bayan an tantance shi. Su kawai aikin su fita da man zuwa ƙasar waje domin a tantance a cire abubuwan da na lissafa miki, kamfanin na haƙo Mai ne kuma suna da jirage da matuƙan da ke jigilan Mai zuwa in da za a tace shi a fidda abubuwa masu amfani a jikinsa yadda za a dawo mana da shi mu samu damar amfani da shi kin gane Ammah.?

"Na fahimta Kabiru. Ubangiji ya tsare mana ku. Shi kuma Lamiɗo Allah ya sa ya fara a sa'a Allah ya taimake shi ya tsare shi."
Ammah take faɗa Hamma Kabiru na amsawa da Amin Amin.
" Ya ce ƙarshen watan nan ko ba su saka masa hannu ba zai dawo gida ya yi hutu sosai kafin ya fara aiki da sabon Kamfanin."
"Allah ya amince. Allah ya ba shi nasara."

Sun ɗan jima suna ta hira rabin hiran ta su duk akan Lamiɗo ne sai wajen biyar saura Hamma Kabiru ya yi sallama da Ammah da Baffa ya kama hanyar Jalingo tunda motarsa ce tafiyar awa uku ce zuwa da rabi.

Ummu kuma sai da ta yi kwana huɗu a asibiti sannan aka sallame ta tare da dokokin likita, ta riƙa samun hutu da barci sannan sun ba ta bedrest ga maganguna har da na barci tunda an faɗa musu ba ta samun barci cikin ta kuma ya na gabda shiga wattani huɗu likita ya ce tana buƙatar kulawa da an ga wata matsala a dawo da ita asibiti sannan ta riƙa cin abinci mai gina jiki saboda inganta lafiyan abin da ke cikin ta.

Bayan sun dawo gida Hamma Abdulrrahman ya sake zaunar da ita daga shi sai ita a ɗaki ya sake yi mata faɗa daga karshe ya koma lallashi ya faɗa mata ga dokokin likita sai ta kiyaye ma kanta da shiga damuwa in tana son ta tsira da abin da ke cikin ta, bai barta ba sai da ta yi masa alƙawarin za ta daina damuwa sannan za ta kula da kanta ko domin abin dake cikinta da take jin wani son shi na ƙaruwa a tsakiyar kirjinta ba kukan sakin da Habib ya yi mata take yi ba har yanzu  kukan bakin ciki da faɗa da zuciyarta da har lokacin ba ta daina son Habib da tunaninsa ba. Tana yi iya yin ta domin ta manta da shi amma ta kasa da ta keɓe shikenan za ta yi ta tunanin shi da irin good momories ɗin su tare da juna ba ta ma sanin lokacin da ta ke fara kuka.

Ba za ta taɓa mantawa da Baɗɗo ba sai da ta kwana goma da ita tana kula da ita sannan ta koma gida tunda sun koma makaranta. Sannan Ummin ikki ma kullum sai ta leƙo kowa dai burinsa ta samu ta sake ta fara walwala. Ga Baffa da duk ya sakar ma Hamma Abdullahi harkokinsa yana zaune a gida saboda ita. Shi dai nasihan shi ta daina damuwa ta yadda da kaddaranta. Ammah ma tana nuna nata kulawan amma in ta yi lallashin ta gaji za ta fara masifa ne da faɗa, ga Hamma Saddam ma yana iya bakin ƙoƙarin shi wajen zama da ita yana yin duk wani abu da zai sanya ta farinciki, haka ma Hamma Abdulllahi, da matan su in ba su zo ba yau ba za su zo gobe su Hamma Jibo duk da ba sa kusa duk ranar duniya sai ta yi magana da su ta wayar Amma tunda ita wayarta tana cikin kaya ta kashe kanta ma ba chaji, ganin yadda kowa ya damu da ita ya sa ta rage damuwa amma Allah kaɗai ya san halin da zuciyarta ke ciki tare da Ammah suke kwana Baffa ne ya ce ta riƙa kwana da ita amma in ba magungunanta ta sha ba tana daɗewa tana juye-juye ba ta samu barci ba gani take yi kamar a mafarki wai yau ita ce a gida a matsayin bazawara. Ba ta sare ba tunani take da yaƙinin cewa Habib zai dawo ya neme ta, tana ma mantawa da cewa har abada yanzu ta haramta ga Habibu ita soyayyar shi ta gama rufe mata ido da duk abin da ya yi mata ta kasa jin tsanar shi ta kasa daina son shi, duk da tana son ta tsane shi ɗin amma ta kasa tunda ba ita ke da alhakin sarrafa zuciyar ta ba.

Hamma Abdulrah. yana can kasar turai ya ji labarin abin da ke faruwa shi auren ma baya nan aka yi sai ga shi yana can komai ya ƙare. Ya shiga damuwa sosai barin ma da Saddam ke ba shi labarin yanayin da Ummun ke ciki Vedeo call ya kira aka bata ya yi magana da ita kuka kawai take yi tana ma kasa mgana shima daga ƙarshe kashewa ya yi ya fashe da kuka, yana da saurin kuka da tausayi shi ya sa bai sake kira ba sai dai duk lokacin da ya yi magana da wani na gida zai ce a gaishe masa da Ummu, ba ya son su sake magana ta saka shi kuka ga shi yana shekaran ƙarshe ne karatu yake yi kamar injin ya yi ya gama shima ya dawo gida cikin ahalinsa.

Mami ma suna Paris Hamma Saddam ya faɗa mata halin da ake ciki ai a daran ta matsa ma Abban islam cikin kwana biyu suka dawo gida Nigeria. Washe gari kuma suka sake biyo jirgi zuwa Jimeta. Tun da Mami ta zo ta ke kuka kowa ya san kukan da take yi kuka ne na fami daga tsohon gyambon dake zuciyanta. In ta kalli Ummu sai ta ji kukanta ya kasa tsayawa ta yi kuka kamar ranta zai fita sai da Baffa ya zauna yana ta ba ta baki Abban islam na gefe domin ko ya ba ta baki ba ta yin shuru sai ta ce wai ba zai gane yanayin ba ne.

Ummu Salma kukanta ya dawo sabo da zuwan Mami da kukan da take yi, tausayin Ummu Salma take ji duk da ta ɗan fi ta shekaru ita lokacin ko ashirin ba ta cika ba ta faɗa wannan kaddaran amma duk yadda za a fassara lamarin ba wanda zai gane yanayin sai wanda abin ya faru da shi.

"Baffa yaron nan ya cutar da Ummu Salma. Muma ya cutar damu kuma wallahi sai Allah ya saka mata."

Mami take faɗa tana kuka kamar ranta zai fita.

"Ummu ki yi kuka ki yi ta kuka ko za ki sami salama. Amma kar ki yi dogon damuwa cuta za ta kama ki, in kuma hakan ta faru za ki samu cikin damuwa."

Haka take ta faɗa ma Ummu lokacin da ta rungumeta a jikin ta dole Alhaji Isa Ɗanmarke ya nemi hotel ya kwana washegari ya juya Kaduna tunda yara na gida tare da su Baraka, ya bar Mami a Jimeta ita ta ce ya tafi kawai za ta zo daga baya.

Zuwan Mami ya tado ma Ummu taɓon ta amma kuma ta samu sauƙi saboda Mami ta zaunar da ita, ta ba ta labarin rayuwarta da yadda ta yi gwagwarmaya da kaddaranta daga ƙarshe ta yi nasara da yadda Ammah da Baffa suka yi ta ƙoƙari a kanta.

"Ummu Salma akwai zafi na sani amma sai kin daure. Yanzu ki sani ke uwa ce a gobe. Ki kula da kanki saboda abin da ke cikin ki, ki yi haƙuri ki yi haƙuri ki cire damuwa a ran ki, in kin ji kuka ki yi kuka domin shi kaɗai ne zai samar miki da salama."

Haka take ta faɗa mata cikin ƙarfafa mata gwiwa.

"Za ki ci wannan jarabawar Ummu. Za ki yi nasara kamar yadda na yi. Muna nan dake Allah zai kawo miki wanda zai share miki hawaye. Shi kuma Habib sai ya yi Fargar jaji da ikon Allah."

Ummu Salma tana kuka ta nuna ma Mami jikinta tana kuka take faɗin" Mamina wa zai aure ni a haka? Me na ke da shi? Ba ni da budurci ba ni da jiki mai kyau, nonuwana sun kwanta, ciki gare ni Mami nan da wata biyar zan haihu na buɗe na zama uwa na shayar da jariri, Mami ki faɗa mini wa zai kwashe ni a haka? Me ya sa shi da ya fara bai ƙarisa ba Mami na?
Haka Ummu ke faɗa tana ta gunjin kuka.

"Allah zai kawo shi, wanda ba jikin shi yake so ba ke yake so Ummu in kina tunanin ba zai yuyu ba ki riƙa duba rayuwata. In kika kalle ni za ki samun ƙwarin gwiwan cewa ke ma komai zai wuce zai zama sai labari, sai dai ki tuna ki yi mirmishi ko kin yi kuka sai dai ki yi kukan farinciki da tuna rayuwar baya."

Ita dai Ummu Salma jin Mami kawai take yi ba ta san irin yadda zuciyanta ta so Habib ba ne. Ba ta san yadda jikinta da rayuwarta ya saba da shi ba ne, shi da ya fara me ya sa bai ƙarisa ba? Me ya sa ya rabu da ita? Ta amince za ta zauna da shi ya yi ta moran jikinta har illa masha Allah, amma yanzu da ya sake ta ina za ta je? Ji take yi kamar ta rasa komai na rayuwanta ne in ta ce komai tana nufin komai, mafarkin ta burukanta da dukkan wani tanadinta na rayuwa Habib ya yi sanadiyar da yau ita Ummu Salma ta dawo ba komai ba, ya kuma ma yar da rayuwarta kwanko babu wani abin mamora a rayuwarta a yanzu.

Kwanan Mami biyu da zuwa Jimeta sai ga Hamma Mustapha da iyalan shi a rana ɗaya suka zo da Hamma Jibo amma shi kaɗai ya zo bai zo da su Nauwara ba, jirgi ya biyo ma. Suma dai duk haƙuri da nasihan suka yi ta Ummu Salma ganin yadda duk ta faɗe ta rame ba ta mgana. Daman a wannan lokacin kowa haƙuri yake ba ta, domin babu wani abu da za a yi mata.

Zuwan su Hamma Jibo aka yi maganar kwaso kaya. Mami da Ummin ikki ne suka je gidan tun da key ɗin gidan da man su Baɗɗo sun taho da shi kaf aka haɗa kayan ta waje ɗaya babban mota mai budaɗɗen baya ta zo ta kwashe zuwa gida a ɗakin kusa da na Ammah mai ciki da falo aka saka kayan aka rufe, kayan abincin da Hamma Jibo ya siya mata jibgi haka aka kwaso su sai dai aka kai su store ɗin Baffa.

key ɗin kuma suka ba ma maigadi sallahu in megidan ya zo ya bashi ko masu duba gidan tun da suna zuwa duk sati kayan Habibu ko ɗaya ba su samu a gidan ba tun washegarin ranar da ya yi sakin kafin ya tafi sai da ya kwashe duk abu da yasan na shi ne daman iya kayan sawa ne da takalma sai takardunsa duk ya kwashe su.

Ranar da aka kwaso kayan kwana Ummu ta yi tana kuka. Ba kuma wanda ya hana ta Mami ta ce a ƙyaleta ta yi kukanta ko za ta samu suƙuni kar baƙincikin ya ƙume mata a zuciya ta samu matsala. Tunani take yi shike nan komai ya ƙare tunda gashi an kwaso kayan ta, shike nan ta rasa komai ba ta da wani abu kuma da ya yi mata saura. Cikin dake jikinta ne kawai ya rage mata shi kaɗai ne abin da ya rage ta ƙarisa a halin yanzu.
Habib ya cuce ta, Habib ya gama da rayuwanta.
Habib ya yi ma duniyarta kaca-kaca, Habib ya yi sanadiyar da labarinta ya shiga bakin mutane ya mayar da ita bazawara ya sanya kanta a cikin mata masu taɓo a zukatan su, ya jijjiga duniyanta sannan ya bar ta da abin tunawa har na tsawon rayuwarta na har abada.




*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"


https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t

*14*

Sai da Mami ta shafe sati ɗaya a garin Jimeta kafin ta koma Kaduna. Kuma zaman ta ya yi amfani tunda Ummu na jin maganarta sannan tana sauraranta, zamanta a gidan kafin ta tafi ya taimaka ƙwarai wajen sake dangana a zuciyar Ummu Salma, tana cin abinci tana kuma samun hutu sannan koke-koken da take yi ya ɗan ragu sai dai abin da ba'a rasa ba.

Mami ta so Baffa ya amince ta tafi da Ummu Salma Kaduna wajenta ta zauna na wani lokaci saboda yanzu garin Adamawa gabaɗaya ya yi mata ƙunci in ta yi nesa za ta fi samun sukuni da jin daɗi lokacin Hamma Jibo na nan shi bai koma ba ya yi na'am da shawaran Mami har Ammah ma ta ce gwara ta ɗauketa su tafi na ɗan lokaci har zuwa komai ya lafa, shi kan shi Baffa ya fahimce su amma sai ya yi tunani a matsayin shi na Babba, bai ba ta Ummu ta tafi da ita da farko ba amma ba wai ya hana ta ba ne.

"Fatima Auta fa ƴ'arki ce, ni ko Amman ku ba mu isa mu hana ki tafiya da ita ba. Sai dai ya kamata mu yi abin hankali, ke fa matar aure ce kina da miji da kike zaune a ƙarkashin ikon sa, bai kamata ba tare  da sanin shi ko izinin shi ba kawai ya ga kin zo da yarinya ba. Ya kamata ki yi shawara da shi in ya amince ki zo ga Auta nan halak malak Fatima ba wanda ya isa ya yi miki iko da ita."

Abin da Baffa ya faɗa mata kenan ana gobe za ta koma da ta same shi da maganar son tafiya da Ummu Salma gidanta dake Kaduna.

"Baffa ka fa san Abban Islam ba shi da wata damuwa. Mun yi ma magana da shi a waya shi ya ma kawo wannan shawaran na cewa ko zan taho da ita ne ta ɗan samu natsuwa? Shi fa ko har abada za ta zauna damu ba shi da wata damuwa."
Mami ta amsa ma Baffa cikin magiyan ya amince ta tafi da Ummu amma ya hana ta, ba da niyyar ba ta da hurumi ba sai da niyyar ta bi komai a hankali da cewa ta koma su tattauna da mijinta in ya amince daga baya sai ta zo ta tafi da Ummu sun ba ta ita har abada.

Dole Mami ta amince amma ba haka taso ba, ita ma ta ce ba domin wajen aiki ba, da sai ta yi wata a garin Jimeta amma saboda aiki ya sa ta yi shirin komawa. Kafin tafiyarta haka ta zaunar da Ummu  ta sanar da ita za ta koma Kaduna amma ba daɗewa za ta dawo ta tafi da ita can ta zauna tare da ita.

"Mami me ya sa ba yanzu ba?

Ummu ta faɗa cikin raunin murya har ta fara hawaye. Za ta fi son Mami ta tafi da ita, domin garin nan da mutanen cikin ta sun gama fita da zuciyarta, wani ƙunci take ji da duhu daga cikin zuciyarta watakila da za ta yi nesa da gida da garin gabaɗaya za ta fara mantawa da kaddaranta har ta manta da Habib daga zuciyarta gabaɗaya.

"Ni ma haka na so, to amma kin san halin Baffa ya matsa sai na koma gida na yi magana da Abban Islam."

Ummu tana ta kuka har da shessheƙa, Mami ta yi ta lallashinta da ban baki, ba ta so Mami ta tafi tana son zama da ita domin ita ce kawai ta fahimci halin data ke ciki, ita ce kaɗai ta san irin raɗaɗi da zafin da kaddaran take da shi, ita ce kuma ta san irin yanayin da ake shiga in ka rasa dukkan wata dama ko mafitar daka ke tunanin ka kama ko ka dafe tuntuni amma sai daga baya ba ka shirya ba, ba zato ba tsammani komai ya kubce daga hannun ka.

"Ki yi haƙuri Daughter in sha Allahu zan dawo na tafi dake. I promise you in sha Allahu."
Da haka ta samu ta lallasheta ta daina kuka. Sannan ta bi ta da kalamai masu sanyaya zuciya da alkawarin ko bayan ta tafi ba za ta cigaba da damuwa ko kuka ba, sannan ta riƙa cin abinci saboda lafiyanta da inganta abin da ke cikinta kuma ta yi mata alƙawarin duk za ta ji maganarta. Sannan ta umarce ta da duk abin da take so kar ta yi ma Baffa ko Ammah magana ta kirata ta sanar da ita, ita kuma ta yi mata alƙawarin komai take so in dai bai fi karfinta ba za ta yi mata.

Ranar Jumma'a da misalin ƙarfe goma na safe jirgin da Mami ta shiga ya ɗaga zuwa Kaduna. Abdullahi ne ma ya tuƙa ta zuwa filin jirgin, bayan tafiyarta Ummu ta yi ta kuka ba wanda ya hana ta kowa ya san akwai shaƙuwa mai tsanani tsakaninta da Mami, balle itama Mamin lokacin da za su yi sallama har tana sharan ƙwalla kamar kar ta tafi haka take ji.

Bayan tafiyar Mami kamar Ummu ta saduda sai kuma ta koma gidan jiya, ita kenan sai kwanciya tana kuka ba ta cin abinci sai Ammah ta shigo ta yi magana ta tsakura kaɗan, ko Baffa in ya tsaya mata ko kuma ta ji zuwan Hamma Abdulrrahman, ga ta da juna biyu amma ba ta taɓa cewa yau ga abin da take sha'awa ba ko Ammah ta tambayeta ba ta magana sai ta ce komai aka ba ta za ta ci, ita a ganinta ba ta da wani sauran zaɓi kuma a rayuwarta tunda Habib ya sake ta kamar tara sa dukkan wata damarta ne.

Koda Baɗɗo ta koma gida saboda makaranta tana yawan leƙewa duba Ummu Salma, wata rana ma in ta yi dare nan take kwana da safe ta wuce makarantan daga nan haka ma Ummin ikki koda yaushe tana kan hanyar zuwa domin duba Ummu, kuma in dai ta zo sai ta zaunar da ita tana yi mata nasihan haƙuri da ɗaukan kaddara zuwa lokacin tuni Ummu Salma ta yarda da kaddaran Habib ya sake ta amma ta kasa gasgasta kaddaran cewa ya rabu da ita har abada, gani take yi zai zo gare ta ko da take gida zai dawo gare ta, ta kasa ba ma zuciyarta hakuri da fahimtar cewa Habib ya yi mata nisa har lokacin ba ta sare ba, saboda tana son shi duk abubuwan nan da suka faru ba ta jin haushin shi sai ma soyayarsa dake sake kassara tunaninta kuma ko yanzu ya dawo gare ta, za ta iya yin komai domin itama ta koma gare shi. Habib kaɗai ta sani shi ne fa Duniyarta ya za a yi ta fara yin wata sabuwar rayuwar da ba shi a cikin ta. Gaskiyan da Ummu Salma ta kasa karɓa kenan gani take yi ba ta da wani sauran jin daɗi kuma tunda dai ba tare da Habib, ta lamkaya jin daɗin ta da samun komai na duniya a lokacin da take Matar Habib ba a yanzu da ta ƙare ba ta da komai ba.

Tafiyar Mami da kwana goma sai ga Shamsiya afufujan tana kuka wiwi tana faɗin ita ba ta san abin da ke faruwa ba kenan ta yi tafiya zuwa Taraba gidan Sister ɗin ta, tun a can take faman kiran wayar Ummu a kashe kuma ba ta ganin ta a chart hankalinta ya tashi shi ne fa ta kira Baɗɗo ita ke faɗa mata wannan mugun labarin mara daɗi.

"Bestie Habib ya sake ni."

Ummu ta faɗa hawaye suna kece mata.
"Ya sake ni Bestie."
Ta sake faɗa tana mai kwantar da kanta saman cinyar Shamsiya dake zaune a saman gadon ɗakin da Ummu Salma take.

"Na yi komai domin na tsira da aurena amma na kasa Bestie. Na kasa na faɗi.."

Take faɗa tana wani irin gunjin kuka Shamsiya na ɗan bubbuga bayanta alamun lallashi take faɗin" Sai da na ce ki bi umarninsa Bestie amma kika yi taurin kai, da a ce kin zubar da cikin da yanzu kina gidan mijin ki, da yanzu ba ki zauna kina kukan nadama da dana sani ba."
Take faɗa tana sharan kwalla itama, amma ba ta fasa faɗa ma Ummu ita ce ke da laifi ba, ita ba ta ganin laifin Habib a wannan maganar.

"Bestie su fa iyayenmu tunanin su da namu ba ɗaya ba ne. Ban so ki kawo maganar gida ba, da kawai kin bi umarninsa kin zubar da cikin da yau duk ba a yi haka ba. Da kina can gidan mijin ki ba wanda ya san abin da ya faru."

"Besite ko na zubar da cikin nan ko ban zubar ba Habib ya gama samun duk abin da yake so a wajena. Ba zai ɗaga mini kafa ba sai ya sake ni, da man kawai cikin ya zo a gabar da ya fake da dalilin shi ne, amma ba ya so na ya ma faɗa mini da bakin shi."
Ummu ta faɗa tana cigaba da kukanta.

"Ni fa ban yarda Habib ba ya son ki ba Bestie kawai kin ɓata masa rai ne da kuma shigowar su Baffa cikin maganar, amma ke kanki kin san cewa Habib na son ki Bestie."
Shuru kawai Ummu ta yi mata, ba za ta gane ba ne, amma tunda har ita ta furta mata cewa Habib ba ya sonta to ai ya kamata ta yarda da ita. Itama da fari ba ta gasgasta ba amma daga baya da abubuwa suka yi ta faruwa dole ta aminta ta kuma gasgasta cewa Habib ba ya sonta , sannan saboda jikinta ya aureta kuma tun da ya gama biyan bukatar shi ai

Please Login or Register in order to submit comment