Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

irin dogon namiji ne faffaɗa, ga tsaho ga jikin murjewa ta cikakkun maza. Lamiɗo na da tsawo sosai domin ko size ɗin takalminsa 45 ne, kuma wannan tsahon na zuru'ar sarkin Jafaru ne, sarki na 11 a tarihin masarautar Daura, shi ne asalin tsatson su har kawo yanzu. Su ke da wannan tsawon kamar ƙiran samudawan farko, sannan suna da girman jiki matansu da mazan su. To Lamiɗo haka yake har ma yafi mahaifinsa Maimartaba Alhaji Dr Nasiru Muhammad Daura cika ido da ƙwarjini. Ahalinsa na Daura ba su da hasken fata sosai amma shi Lamido fari ne jajir, saboda Mami farar bafullatana ce kyakyawa, a wajenta ya ɗauko dogon hanci amma fuskarsa tana da ɗan faɗi ita kuma ta mahaifinsa ce, amma sumar kansa mai santsi da cika ta Mami ce, da yake shi ma'abocin tara suma ne gashi nan sumar ta yi yawa ta kwanta luf tana shan gyara. Sannan bakin sa yana da ɗan faɗi kaɗan zagaye da sajensa da ya zagayo har gemunsa da ya yi ɗan tsawo. Lamiɗo tun yana saurayinsa yana son tara sumar kai da barin gemu har kuma yanzu bai sauka daga kan wannan daɓi'an nasa ba.
Ko a yanzu ma gashi duk ya cika fuskarsa amma duk da haka kyawunsa da cikar zatinsa sun bayyana. Balle ma da ya fara tafiya ya bar gaban Balkisu cikin tafiyarsa ta gif gif ta cikkakun mazan duniya kallo ɗaya za ka yi masa ka shaida Muhammadu ɗan Nasiru da Fatima Sadauki ne, kuma jarumi ne yanayin sa irin na fusattatun maza ne giant masu mazantaka da ke dukan zuciyan duk wanda ya kalle su, jarumatar su ba ya ɓoyuwa, sannan suna iya rike numfashin wanda ya kalle su gaba da gaba na wani lokaci saboda ƙwarjini da haibar da baiwa ce Allah ya ba su, sannan yanayin su komai karatun mutum akan sanin hallayan ɗan adam baka isa ka fahimci yana yin su ba, ko ka ce ga abin da suke so ko ba sa so ba, irin su Lamiɗo sai zama ya haɗaku na shekaru masu yawa shi ne har za ka iya fahimtar lamuran rayuwarsu, amma ba wai don su furta da bakin su ba.

"Wanka za ka yi ranka ya daɗe?

Balkisu ta faɗa tana mai kallon bayan shi.
"E.."
Ya amsa mata cikin dakakkiyar muryansa amma cikin sanyin amo a karon farko sannan ya tura ƙofar tiolet ɗin ya shige ya rufo.

  Numfashi ta fesar tana mai sake bin bayan shi da kallo bayan ya shige. Sanye yake da bakin wando wanda iyakarsa gwiwan kafafunsa sannan jikinsa wata farar riga ce mai dogon hannu tana da botira a gaba amma bai saka boturan ba, ƙirjinsa mai cike da gargasa ya bayyana a waje kuma tasan ma dalilin da yasa ya yi saurin barin in da take tsaye saboda haka ne.
Tunda take ba ta taɓa ganin namiji mai kunya irin mijinta Lamiɗo ba

Yau shekaran su shidda da auren su tare da albarkan ya'ya biyu amma bai taɓa yarda ta gan shi daga sama har ƙasa naked ba, itama za ta yi rantsuwa bai taɓa kallonta haka ba. Da farko ta ɗauka ko ba ya son ta ne yasa yake yin haka sai da zaman su ya mika ta fahimci haka Allah ya yi shi, yana jin kunyar tsaraici shi ya sa ko kayan barci baya sakawa masu sharara, in zai kwanta sai ya saka dogon wando, da riga mai dogon hannu ya rufe jikinsa ba ya so ya fidda wani tsaraici na jikinsa duk ko da ita ɗin matarsa ce, yana jin nauyi da kunyar ta gan shi a haka, shima bai iya mata dogon kallon matukar ta fidda masa tsiraici, domin akwai wani lokacin tana da cikin Sultan suna gudanar da Sunna ta kudiri niyyar sai ta ga abin da Allah ya hallata mata. Ita da mijinta amma ace ba ta san girman shi ba, sai da ta bari sun natsa cikin harkan sannan ta kunna hasken ɗakin, ranar ta ga abin mamaki da saurin gaske ya faɗa gefenta cikin zafin nama ya jawo bargon dake gefe ya rufe jikinsa, sannan ya juya mata baya cikin wani sauti amon murya ya ce itama ta rufe jikinta. Ta daɗe lamarin yana ba ta mamaki kuma ta ji haushi har sai da ta yi masa magana da cewa ita fa matarsa ce halaliyarsa amma yana jin kunyar ta ga jikinsa, ko shima ya ga jikinta. Har ta gama maganganunta bai ce mata komai ba, bai ma sake tayar da maganar ba sai da ya tafi ne ya tura mata da saƙon cewa ta yi haƙuri daga haka bai ce komai ba kuma bai sauya ba, dole ita ta bi shi a yadda yake tunda haka Allah ya hallice shi, hallayan shi ne a haka kuma ba zai iya canza kan shi ba.

Gadon ta ɗan kakkabe tana ninke farin bargon. Gabaɗaya ɗakin kalan baki da fari ne Lamiɗo na son abu fari kuma yana son baki ko kayan shi rabi farare ne rabin su kuma baƙaƙe ne, bayan ta gyara gadon ta ninke bargon ta ɗan saka shi a gefen gadon ya ɗan ba da styel, itama sai ta koma ta zauna tana ɗan mirmishi.
Tana son mjinta tana son Lamiɗo, lokacin da mahaifinta ya kirata akan Lamiɗo ta ji wani iri, da jin labarin Baban shi ne ya yi gadon Sarauta, mahaifiyar shi ba yar kowa ba ce. Bata taɓa tunanin haka za ta ga Lamiɗo ba, sai da ya zo haɗuwar su ta farko anan ta fahimci ko a cikin maza shi na dabam ne, ko ita da take jinin sarauta gaba da baya tunda kakanta na bangaren uwa ya yi sarautan Kano, to ba za ta nuna ma Lamido iko da sarauta ba, tafiyar shi, maganar shi, yanayin tsarin rayuwarsa kaf kamar wanda aka haifa a gidan sarauta ya kuma girma acan, sai ga shi ta ji labarin shi bai ma zauna a Daura ba sai da ya girma ya zo. Kenan duk wani abu na hallayar shi ko yanayinsa halitar shi ce haka Allah ya yi shi.

Ba auren soyayya suka yi ba kakar sa Fulanin Daura ce ta zo ta nema masa auran ta, saboda kyayawan alaqan da ke tsakanin masarautun ba jayayya aka amince, kuma daman a zamanin da muke ciki ƴa'ƴan sarakuna sai ƴaƴan sarakuna ƴan'uwansu ko kuma ƴaƴan masu riƙe da madakan ikon a kasar gabaɗaya. Shi ya sa sai haɗin ya yi daidai duk da ana ta cewa mahaifiyar Lamiɗo ba ƴar sarauta ba ce wataƙika ba zai yi gadon Sarauta ba amma kwarjinsa da tasirinsa bai gushe ba. Balkisu ma tun a ganin farko da ta yi masa ta ce ya yi mata tana son shi. Duk a tunanin ta wannan shuru shurun na shi, da wannan ji da kan duk zai sauke su bayan aure. Itama jinin sarauta ne tana ji da takama da girman kai amna haɗuwarta da Lamiɗo sai ta sara ta kuma jinjina masa ta san ita ba ta yi komai ba. Bayan auren su babu abin da ya sauya Balkisu ta yi tunanin za su yi soyayya ta kwatance a yanayin yadda take, yar gayu wayayyiya mai ilimi. Amma sai ta ga sabanin haka, shi fa ba ka iya gane yanayin da yake ciki yana son abu ko ba ya so duk ba ka isa ka gane ba. Ta sha wahala sosai kafin ta fahimci Mijin data aura, komai in za ta yi masa ko ya yi masa ko bai yi masa ba, ba zai taɓa magana ba in ya yi masa ba zai nuna alamu ba, in ma bai yi masa ba, ba zai nuna ba.

SSai da ta yi ta karatun nazarin hallayan Lamiɗo sannan ta fahimce shi, shekaran su shidda da aure ba ta taɓa jin ya ce yana son ta ba, sunan ta ma bai wuce sau goma ya taɓa kira ba, in ma magana ta kama sa dole sai dai ya yi maganarsa kawai kai tsaye, da yawan lukata baya gida in ya kirata a waya suna gaisawa ya tambayi yara bai kara cewa komai sai dai in ita ce ta dauko masa hira. In ya dawo za su zauna a gida ɗaya amma bayan gaisuwan safe in dai ba itace ta yi masa magana ba za su iya yini su kwana ba su sake yi ma juna magana ba. Zai iya yini a bangarensa bai fito ba, wani lokacin sai dare in ya fito cin abinci tare da yara. Tunda duk da yanayin shi yana son yara yana wasa da su Sultan, suma ɗin akwai lokacin haka in yana son kaɗaici ma ba zai fito daga bangarensa ba yana son shuru fiye da komai a rayuwansa.

Bangaren abinci kuma sai da Ammah ta taimaka mata ta ɗan ba ta satar amsa, duk da ba ita ke yin abincin ba sai dai ta ba da umarnin a dafa masa. Lamiɗo na cin tuwo amma ba ya shan duk wata miya mai yauƙi, ba ya son yaji ba ya son mai ya yi yawa. Ba ya cin naman jan akuya sai kaza ko kifi, kuma ba ya cin shinkafa tsura ko wani abu sai da miya, miyar ko wata iri amma ban da miyar yauƙi, yana son ganye sosai. Da Balkisu ba ta sani ba ta yi ba shi miyar yauƙi sannan ita tana son cin yaji. Gashi dai ba ya so amma ba zai taɓa magana ba, sai dai ta ga baya ci da yawa sai dai ma wani lokacin ya yi ta cin abun gaya ba miya, in ta yi masa mgana sai dai kawai ya yi mata shuru, Ammah ce ta taimaketa anan ne ta san ba ya shan miyan yauki. Shi fa in dai shi zai fada maka abin da yake so da bakinsa to ba za ka taɓa sani ba. Tuni Balkisu ta sauke jin kai da sarauta ta fara karantan mijinta domin ta san cewa ba irin mijin kowa ba ne, Lamiɗo mijin Balkisu na dabam ne a cikin maza.

Da haka ta samu ta karance shi tsab har suke zaune lafiya cikin mutumtawa. Ko bai furta da bakin shi yana son ta ba, tana ganin haka a aikace. Ba ta damu ba ta amince da na shi salon nuna son ne a haka bai taɓa danne mata hakkinta na aure ba, tana daga cikin sahun gaba a matan da suka yi sa'an aure, ta samu miji na nunawa sa'a ga shi gwarZo kuma jarumin namiji mai iyawa da duka bukatunta, farkon auren su sai ta zauna jiran sai ya zo gareta ta yi ta cutuwa shi kuma ko yana son abu ba ya nema. Ba ma ka gane yana so ko ba ya so. Shi ya sa da ta fahimce shi ta riƙa ba da kai bori ya hau abin mamaki kuma sai ya fi ta ma rawan jiki da son nuna jin daɗinsa, tun daga lokacin ba ruwanta in tana bukatarsa za ta je gare sa shi kuma a kowani hali yake ciki bai taɓa tankwafar da bukatarta ba sai ya tabbatar da ta samu gamsuwa ɗari bisa ɗari.

Ta yi nisa cikin tunaninta ba ta ji karan buɗe kofar toilet ba sai dai kawai ta gan shi ya fito sanye da rigan wanka baka, gaban rigan ta ɗan buɗe, ganin ta a zaune kuma sun haɗa ido.  Da sauri ya juya baya lokaci ɗaya yana jan rigar wankan ya rufe ƙirjinsa.

"Me za ka ci na sa Debora ta dafa maka."
Ta faɗa cikin harshen turanci lokaci ɗaya tana mikewa tsaye.

"Anything is ok. Buh zan fara da Coffea mai zafi."
Shima ya mayar mata da martanin maganarta cikin harshen turancu muryansa mai kama da ta jaruman maza.

"Okay"

Ta faɗa, bai ma jira ta fice ba shi ya fara shigewa cikin clothset ɗin sa, domin ya sauya kaya. Ita kuma sai ta fice tana zuwa main falo su Sultan na shigowa falon James na bin bayansu ɗauke da jakunkunansu da basket ɗin su na makaranta
Suna ganinta Beena yarinya yar shekara uku
Yar ajin Baby class dabar dabar da lukutun jikinta na yara ƴan hutu ta nufe ta da gudu da karamar muryanta tana kiran sunanta

"Momi."

Da sauri ta tarbeta ta ɗaga ta sama tana nishi, tunda Beena akwai jiki kamar kazar turawa.
"My Beena."
Ta faɗa tana jan kumatun ta, ita kuma ta tsinke da magana tana fada mata ta ci egg a makaranta da plantain, da muryansu ta yara da turanci tana jinta tana dariya, Sultan kam a natse shi ya kariso falon yana faɗin.

" Good Afternoon Momi."

"Afternoon My Sultan. How was school?.

Ta faɗaa tana ɗan shafa kan shi. Shi nursery 1, yake shi ne sak Lamiɗo Beena ce ke kama da ita.
Ya amsa mata da lafiya lau da turanci yaro ne ɗan shekara biyar amma yana da tsawo da ɗan kiba shi ya sa sai ka yi zaton shekaransa takwas in ba ka san shekarunsa ba.

Anitha ta fito daga wani korido daga yamma da sauri domin ta na sane da lokacin dawowar yaran tunda alhakin kula da su yana wuyanta ne suna ko ganinta Beena ta ƙwace a hannun uwar ta nufeta ita kuma ta tarbeta tana mata oyoyo.
James cikin ladabi ya gaisar da Balkisu sannan ya  sauke kayan hannunsa ya fice daga falon.
Har Anitha ta ja Beena zuwa cikin ɗakin su Sultan yana bin bayan ta Balkisu ta kira shi yana juyowa ta ce

"Ku sauya kaya ku ci abinci Papa is at home."
Jin ta ce Papa ya sa ya fara tsalle yana murnan Papa ya dawo ya bi bayan Anitha har suka ɓace ma ganin ta, tana tsaye tana kallonsu tana mirmishi,. Ba su san ya dawo ba tunda a jiyan ma cikin dare ya iso gidan kuma ya kwanta yau yana ta barcin gajiya ba su haɗu ba.

Kitchen ta shiga ta iske Debora na ta aikin Dinner tana ganin ta ta rankwafa tana gaisheta ba ta amsa ba ta ce ta haɗa ma Baban su Sultan coffea mai zafi nan da nan ta amsa falo ta fita ta zauna ba daɗewa sai ga shi ta haɗo ta kawo mata a cikin wani karamin fulas fari da karamin mug fari da faranti, Balkisu ta karɓa ta wuce da shi ɗakin Lamiɗo ta iske shi ya sauya kaya zuwa wani wando blue da farar riga mara hannu yana gefen gado yana kunna wayarsa da tafi sati a kashe.
Karamin teburin tangaran ɗin da ke cikin bedroom ɗin ta jawo ta sauke farantin hannunsa.

"Thanks"

Ta ji ya ambata a saman leben shi, halin shi ne duk abin da za ta ba shi ko za ta yi masa zai yi mata godiya wannan daɓi'an shi ne..
Zuba masa ta yi ɗan daidai a mug ɗin sannan ta miƙa masa ya karɓa yana sake yi mata godiya wannan karon da harshen fillanci, duk da ba ta ji amma tana tsinta a bakin shi da bakin yaran tunda yana yi musu magana da fillancin.

Gefen shi ta koma ta zauna shi kuma sai da ya kunna wayar sannan ya kai mug ɗin baki ya kurɓi coffea ɗin. Tun safe bai saka ma cikinsa komai ba rabon sa da wani abu tun jiya da daddaren da ya dawo ya sha tea. Barci ya yini yi na gajiya yanzu haka ma yana jin kamar kasusuwan shi suna naɗe tsabar gajiya.

Sama da wata ɗaya shi ke tuƙi saboda zai bar aiki da kamfanin don kar su bar shi ya tafi haka shi ne sai da suka wahalar da shi, yanzu dai ya samu sun karɓi takardan barin shi aiki sun saka hannu shi ne dalilin dawowar shi gida, nan da wattani biyu zai fara aiki da abon kamfani amma yana da sauran hutu kafin ya kama aiki.
Yana kurban tea din yana ɗan duba saƙonnin dake reto a saman wayarsa.

"In ka samu natsuwa ka kira Maimartaba da Fulani sun kirani suna tambayana kai, da cewa ba su same ka a waya ba"

Balkisu ta faɗa tana kallon shi. Kamar ba zai yi magana sai kuma ya ce a hankali
"Har su Ammah ban yi magana da su ba."
Sai kuma ya yi shuru ya ɗan ka fasali kafin ya cigaba da faɗin." Zan kira su, "
Sai kuma ya kalleta kafin ya ɗan kurɓi tea ɗin hannun shi
"Ina so ma na je,"
Ta san bai gama maganarsa ba shi ya sa ba ta katse shi ba.

"Na samu sauyin kamfani. "
Numfashi ya fesar a hankali sannan ya a jiye mug ɗin hannunsa a saman teburin gabansa.

"Zan yi hutun 2 month."

Jin ya yi shuru ya sa ta san ya gama magana.
"Ranka ya daɗe dogon hutu haka? Har Daura za mu je?
Ta tambaya cikin fara'a.
Kai ya ɗan daga mata kafin ya ce" In sha Allahu."
"Har da ni za a yi tafiyar?
Ta tambaya
"In za ki je.".
Shima ya ba ta amsa a yanayin maganarsa.
"In ba za mu daɗe ba, zan iya ɗaukan excuse a wajen aiki "
Sai ya jinjina mata kai, ta san halin shi zai ce in da takura ta yi zamanta

"Har da su Sultan?

Bai kalleta ba, amma dai ya ɗan motsa kan shi alamun e, sai ta fara yi masa bayanin sun koma makaranta, amma dai ba matsala in dai ba za su dade ba

"Sai ki dawo tare da su."

Ya furta daga haka kuma ya tsuke bakin shi.
Ma'ana shi yana can ita za ta iya dawowa da yara.
Tana da murna da jin daɗi za su samu tafiya ita da shi da yaran su abin da ba sa samu sai a shekara bai wuce sau ɗaya ba.

Duk da ba hira suke yi ba amma tana tare da shi har aka kira mangariba sannan ta kwaso fulas da mug din zuwa kitchen shi kuma ya sauya kaya zuwa jallabiya ya fita masallaci.
Bai dawo ba sai da ya tsaya ya yi isha'i bayan ya shigo ya ɗan bata lokaci a haraba suna gaisawa da su Baban Adila da Jamess, Lamiɗo kowa ya san shi mutum ne mara ƙyamar mutane duk da yanayin shi, da ya shigo falon ma haka su Sabuwa suka yi layi suna gaishe shi kansu a kasa duk ya amsa musu cikin yanayinsa.
Kafin ya dawo Debora ta shirya tebur da abinci sama da kala uku, Balkisu kuma ta sake wanka ta sauya kaya zuwa material doguwar riga.
Tana fitowa ta iske shi a falo tare da su Sultan suna masa hira Beena na hawa jikinsa tana sauka.

Sultan ko faɗi yake yi Papa zan sha icream, papa zan ci shawarma Papa sai hira yake yi masa shi dai sai ya yi ta uhm kawai yana ɗan mirmishi, Beena kam tana ta wasa da gashin kansa kuma bai hana ta ba.
Balkisu ta kalle su cikin alfahari.

Tare suka yi Dinner jalop rice mai kaza sai kuma mandirice, shi Lamido Jalop din ya ci sai ya sha lemun abarba. Su kuma ita da yaran suka tsakura sauran abincin Beena ma madaran Naan na yara ta sha, Sultan kuma pepe chicken ya ci Bilkisu kum ta ci Mendi rice din da lemu.

Bayan sun gama cin abincin  ba daɗewa Anitha ta zo ta tafi da su domin su yi shirin barci gobe makaranta, suma ba daɗewa suka shige ciki. Debora kuma ta zo ta kwashe komai na saman dining ɗin zuwa kitchen, abincin gabaɗaya ake dafawa su ɗiba na su da na su James ba shamaki, sannan Balkisu ba ta son a gama cin abinci a bar shi a wajen shi ya sa da sun gama take yin saurin kwashe komai zuwa kitchen.



*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L6zUax648eTERbvw8Bqyie?mode=gi_t

*16*

*Zone ,3. Jimeta*

BAYAN SATI ƊAYA.

Ummu Salma na zaune a tsakar gida a saman kujera yar tsugunno da misalin ƙarfe goma sha ɗaya na safiyar ranar talata.
Farin wake ne a cikin wani farantin silba tana gyarawa Ammah kuma na daga cikin kitchen tana ɗora sanwa amma jefi-jefi tana yi ma Ummu hira wacce ta yi shuru kamar ruwa ya cinye ta. Ammah ce ke ta maganarta ita kaɗai. Baffa baya nan tun jiya suka tafi ibadan shi da Hamma Abdullahi.
Gidan sai ya rage daga Ammah sai Ummu Salma, Saddam ma ya koma makaranta shekaranjiya.

Gajiya da kwanciya ya sa take ɗan fitowa tsakar gida ko za ta samu abin da za ta iya taimaka ma Ammah da shi amma ba ta barinta ta yi komai sai ta ce ai Likita ya bata hutu, ita kuma ta bata tabbacin ta warke, jiya ne ma Hamma Abdurrahaman  ya zo ya ji suna wannan takaddaman, shi ya yi ma Ammah magana ya ce aikin da za ta yi daga zaune ta riƙa bata saboda ta riƙa ɗan motsa jikinta hakan ma lafiya ce ga abin da ke cikinta shi ya sa yau ɗin Ammah har ta amince ta bata wake ta ce ta gyara mata.

"Saura fa kwana biyu zuwan su Lamiɗo Auta, daga yau sai gobe jibi ne ya ce mini za su taho."
Ummu ta yi shuru hankalinta na kan waken da take gyarawa amma kuma hankalinta da tunanin ba ya wajen ta tafi duniyar tunanin rayuwarta.

Yau wajen kwana uku kenan Ammah ta kasa zaune ta kasa tsaye murnanta ya kasa ɓoyuwa tunda Hamma Lamiɗo ya kira ta ya ce za su zo shi da matarsa da yara ranar al'amis kuma za su ɗan kwana biyu ta kasa sukuni tun jiya ta tura matan su Hamma Abdullahi su Adda Suwaiba da Adda Ummu Sulaim suka je gidan shi dake anguwan Jambutu Haske suka gyara suka yi share-share. Sannan yau da safen nan ta ji Ammah na waya da Hamma Abdullahi tana tunasar da shi Hamma Lamiɗo ya ce ya ɗauki motarsa ya kai ta wanki sannan a ɗan duba ta tunda ta yi wattani a ajiye ba a hauta ba, tana can gidan lullube a cikin tamfol.

Alhalin ba Ammah ya bama saƙo ba da kan shi ya kira Hamma Abdullahin ya faɗa masa, shi ma jiya ne kafin su wuce da Baffa yake mata maganar shi ne yau ta kira shi tana sake tunasar da shi har da cewa in ba za su dawo ba ne ya kira Abdularrahaman shi ya je ya ɗau motar ita dai maganarta kar shalelenta ya iso garin nan ba a yi masa abin da yake so ba.

"Da man Kabiru ya faɗa mini zuwan nan da ya yi kwanaki Lamiɗo ya samu sauyin wajen aiki yanzu zai dinga samun hutun sosai tunda ya sauya wajen aiki."
Ammah ta sake faɗa tana daga cikin kitchen.

Ummu Salma dai na jin ta amma har a lokacin ba ta yi magana ba, tunani take yi in da ace tana da in da za ta je ta ɓoye ma ganin Hamma Lamiɗo da matarsa za ta je, har sai sun tafi sannan ta dawo, tana jin kunya da nauyin su zo su ganta a haka,  su ga yadda rayuwarta ta dawo baya, yanzu kunyar mutane take ji da Ammah tayi baƙi ko tana falo za ta shige ciki tana jin nauyin haɗa idanuwana da Jama'a ko yayyenta kunyar haɗa idanuwana take yi da su, tana ganin kamar ita ba ta da sa'ar rayuwa ta tafi gidan aure amma ga shi ta dawo musu ba ma ita kaɗai ba tare da nauyin cikin jikinta. Duk da Ammah ta ce ba ta faɗa masa ba amma in ya zo ya gan ta ko bai ta tambaya ba Ammah za ta iya faɗa masa dalilin zamanta a gida tunda shi tambaya ba ɗabi'ansa ba ne ko zai shekara yana ganinta ba zai damu da ya tambayi dalilin zamanta ba.

Ta yi nisa cikin tunanin ta ba ta ma san Ammah ta fito tana yi mata magana ba, sai da ta ji ta taɓa ta sannan ta yi firgigit ta dawo hayyacinta.

"Ammah kina magana ne?

Ta faɗa tana kallonta lokaci daya tana koƙarin shanye hawayen da suka cika mata kwarmin idanuwanta.

"Auta"

Ammah ta kira ta, sai ta sunkunyar da kanta tana jin kamar ta kace da kuka.

"Ba an hana ki shiga zurfin tunani ba, sai yaushe ne za ki saduda ki fahimci duk abin da Ubangiji ya yi daidai ne? Sai yaushe za ki dogara da Allah ki san cewa Habibu ya shuɗe daga rayuwarki Ummu Salma.?
Ammah ta gama faɗa tana tsaye tana kallon Ummu wacce har ta fara tsiyayan

Please Login or Register in order to submit comment